Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
'kofar key yadawo kusa da ita sosai ya kar6i abincin daniyar bata. Da sauri takalleshi a furgice. Shiko ya 'daure fuska yace ko kici ko ranki ya6aci yanxun nan. Tuni tabu'de mai baki yadinga bata ahankali tanaci MASEEFAR SON shi Yana qara shigarta Ya lura batasan tadinga ha'da ido dashi shikuma yanace saita ha'da idan dashi. Dan haka duk lokacin dayakai mata lokali bakinta sai sun ha'da ido. Al'amarin daya farajin wani yanayi kenan wanda yake Allah Allah yagama bata ya ka'daice yayi tunani akai. Na qoshi tace dashi Cikin shagwa6a Wlhi da Matarsa ce ba'abinda xai hanashi kamata yayi mata make✅ kiss dan yanda tayi maganar Cikin shagwa6a da turo baki abin ya tsuma shi matuqa Yace Bakici yayi yawan daxan barki bah....... Aikan yaqarasa tasaka mai kuka. Rikicewa KAMAL yayi yarungumeta arashin sani 🙊 Am sorry na barki bacine bakya soba ko Ta'daga mai kai Saka hankicif 'dinsa yayi yana goge mata hawayan nata Tunda LABEEBAH taxo duniya bata ta6a tsintar kanta a farin ciki irin na yauba Gata ajikin KAMAL tana shaqar qamshinsa Wani sanyi da da'dine yake shigarta Shiko KAMAL yanda talan gwa6e mai hakan ya jefashi Cikin wani hali mara misal tuwa Cikin dabara yarabata da jikin nasa dan yaga tana quqarin yi mishi bacci yagyara mata kwanciya yana cewa karkimin bacci ajiki kisa namanta kaina kebah XARAH bah. Yafa'da idanshi acikin nata. Murmushi tayi dan ta'danji kunyarsa. Cikin shagwa6a Tace toh ai Kaine Ya waro ido Yace nine nayi me Rufe fuskarta tayi tanah Murmushi Shima Murmushi yayi yakalli kofah dan yaga alamun an mur'da kofar Yace yes come.... Tunawa yayi akulle take dan haka yatashi ya bu'de. Sumayya ce mah Tace taci abincin ya KAMAL Yace eh mana ba dolanta bah Tace tab aiko saina kaima Su mamah labari Duk sukayi dariya LABEEBAH Tace naji sauki Ya KAMAL dan Allah kasa asallamemu. Ya watsa mata harara tare da cewa anqi dan sai kin qara kwana biyu Tace biyu.... Ya katseta. Eh biyu akwai wani abune. Yaqarashe da mata kallan tuhuma girgixa mai kai kawai tayi Yace gud ni natafi gun my teema na Sumayya Tace aiyanxu xataxo Yace xanso na tareta acan bari mah na kirata. Yaqarashe da ficcewa Hamdala LABEEBAH tayi tana godema Allah da baice xai jira xuwanta ba. Su tayar mata da ciwan qirjin daya kwanta mata yanxu Yana fitta doctor ya shigo Yace eh gaskiyar Dr KAMAL ne bansan yanda Xanyi dake bane Murmushi LABEEBAH tayi tana cewa aranta shine ciwan kuma shine maganin. Koda XARAH taxo tayi mamakin ganin LABEEBAH garau Tace 'Yar uwata yadai naganki kamar ince tashi mutafi gida Tace eh naji sauqi Amma Ya KAMAL Yace wai saina qara kwana biyu Tace eh nima haka yacemin kuma abinda yadace dama kenan Sumayya Tace nima na goyi bayan haka.... Ya Suleiman ne da matarsa Zainab suka shigo Ya Suleiman Yace sannu LABEEBAH naga jikinma yayi kyau Tace eh yayah Aunty Zainab sannu Tace Yauwa LABEEBAH ai kece da sannu. XARAH da Sumayya suka gaisheta ta amsa Cikin kulawa Nan suka 6arke da hira kamar ba duba Mara lafiya sukaxo yi bah Toh mara lafiyan ta warke....... Washe gari KAMAL yadawo yakafe LABEEBAH da ido Yace da fatan kinci abinci Ta'daga mai kai alamar eh Ya 'dan harareta Tace Allah naci XARAH Tace ba wani me yawa taci bah Yace Yauwa my teema xubo wani abata Nan XARAH tacika kwano tana murmushin mugunta harda mata gwalo Murmushi LABEEBAH ma tayi tana cewa aranta makomarki ne Shiko KAMAL matsawa yayi da gaske wai bata xaiyi agaban XARAH Ya ibo cokali 'daya Yace bu'de bakinki. Kallansa qasa qasa tayi irin kallannan wanda inba wanda akayi dominsa bah baxai gane bah. Kallan ya shigeshi sosai har yaso fa'dawa tunani. tayi saurin cewa Cikin sanyi. Allah Ya KAMAL naci kuma idan naqara amai Xanyi XARAH ce bataci abinci bah. tun jiya saboda kanta namata ciwo Sam batajin cin abincin. katemaka kamatsa mata taci plx Shuru KAMAL yayi aduniya kaf ba macen da yakejin da'din muryarta idan tana magana kamar karta dena kamar LABEEBAH XARAH ko sororo tayi tana jin qaryar da LABEEBAH ta sharara mata Tace Allah my luv qarya takey......... Yayi saurin katseta dacewa akan me xatamin qarya. plx kici dan Allah Karki jaxamin matsala dan akwai cucuka da dama da suke shigar mutum lokacin da yaqi Cin abinci akan lokaci XARAH taharari LABEEBAH Tace Xan ramane ai LABEEBAH tasamu lpy yayinda Jameel yasata agaba da nacin soyayyarsa binta yake tana gwarashi Tafa'da mishi gaskiya ita ba soyayya bace agaban yanxu yayi hakuri da itah Amma ina yaqi Yan xuma shirin walima suke dan gobene Auran KAMAL da XARAH Mamah takalli LABEEBAH da take 'daura 'dan kwani Tace AISHA A'dan furgice LABEEBAH takalleta dan bata cika kiran sunanta bah Tace na'am mamah Wai meyake damunki ne yau naga duk kinyi sanyi Allah yasa lafiya Mamah tagya xama ganinsu biyu ne Tace bana gaya miki Yau Lami'do ya rasu bah. Dammmm xuciyar LABEEBAH tabada wani sauti Cikin sauri Tace aa baki gayamin ba yanxu kakah Lami'do ya rasu Mamah tagya'da kai Tace dama shi 'daya ne ya ragye ma babanki niko dama kowa nawa ya qare sai qanwata Zaitu. Taqarashe maganar da xubar da hawaye Jikin LABEEBAH asanyaye Tace tunda kika fa'di mutuwarnan gabana yayanke ya fa'da Allah yaji qanshi mamah. Tace AmEEn LABEEBAH tagyara xama Tace yanxu Yola xamu Mamah taqara gya'da kai Tace eh kai ai anayin Auran XARAH da kwana biyu saimu tafi LABEEBAH Tace ya kamata kam kin gayama Innah Tace aitun 'daxo Malam ya gaya musu Tace ai. shiyasa itama naga yau duk jikinta asanyaye haka Tace eh kana daga bisani takafe LABEEBAN da ido Tace har yanxu baki gayamin gaskiyar abinda yake damunki bah Cikin wani yanayi LABEEBAH takama hannun mamah Tace ba'abinda yake damuna mamah kiyarda dani Tace qarya kike yi. Na barki duk randa kikaga damar fa'damin nabaki shawara Tana fa'din haka Tatashi Shuru LABEEBAH tayi tana tunanin kodai mamah tagano son KAMAL da take new y XARAH CE ta katse mata tunanin tawajan shigowa da tayi Tace ga motoci sunxo mu ake jirah Da sauri LABEEBAH taqarasa shirinta suka tafi Wajan ya qawatu matuqa Nan malamai suka dinga wa'axinsu tare da jan kunnan amarya akan tabi mijinta dayi masa ladabi da biyayya da dai sauransu Daga bisani kuma aka rarraba abubuwa na'dan ciye ciye da lashe lashe can aka tashi kowa ya dawo gida jiki asanyaye Wasu suka dawo gidansu XARAH dan ganin kayan Auranta Wanda tun ta riyin unguwar ba'a ta6a yima wata 'diya mace kayan da akayima XARAH bah Akwatinane goma Sha biyu kowanne shaqe da Kaya Washe gari takama asabar. Nan aka 'daura Aunren KAMAL da FATEEMA-XARAH Akan sadaki me daraja Kallo 'daya xakama XARAH da KAMAL kagane Suna Cikin farin ciki Toh AISHA-LABEEBAH fah😳 Tunda yamma take kuka anyi tambayar duniyar nan agareta miye dalilin kukanta. Amsa 'dayace take ba yarwa watoh yanxu XARAH xata tafi tabarta. Tun XARAH natayata kukan har tagaji tadena ita kam Amma LABEEBAH bata dena ba Kowa ya tsausaya musu Itako LABEEBAH kukan soyayyar da takema KAMAL takeyi Tana sanshi Amma ya haramta agareta har abadah XARAH tasha Nasiha ba 'dan ka'dan bah. Agun mamah da innah dasu Malam Kai har dasu Bashir Usman Suleiman Qarfe takwas akakai amarya gidanta Hmmm aljannar duniya kenan gaskiya ne Dr KAMAL ya ha'du. mekaratu kai yaka mata kabada tsarin gidan Nan Cikin layinda Kakar KAMAL take nan akakai XARAH Duk wanda yasan gida toko dole ya sarama gidan XARAH Ahakan ma wai ba'aje gidanta na Abuja bama kenan Nan akakai XARAH gun kakar KAMAL da momynsa dake tunda aka fara hidimar bikin tabaro abuja. Nan aka basu amanarta kuma suka amsa Cikin mutunci Dake XARAH da LABEEBAH ba wani yarda sukayi da tarkacan qawayeba shiyasa daga amarya XARAH sai LABEEBAH da Sumayya sai yaran Bashir dana Suleiman ne suka kwana abinsu Itadai LABEEBAH wannan rana batayi baccin nutsuwarta bah. Dan Ko wane juyi tayi sai taga XARAH da waya akunne Suna hirar soyayya da KAMAL Washe gari tunda LABEEBAH tatashi da asubah bata komaba tadinga shirin tafiya XARAH Tace ban gane ba. Badai tafiya xakiyi da safannan vah Tace Wlhi tafiya Xanyi Nan XARAH ta fusata tahauta da fa'da tana cewa baxata tafiba Ganin yanda ranta ya 6aci yasa LABEEBAH haqura da tafiyan Tace da daddare na tafi Harararta XARAH tayi Tace dayafi dai Haka momy ta aiko musu Su Sagna da Safna da kayan kari kala kala Danginsu farfesun kaxa da sauransu LABEEBAH bata iya cin Komai bah XARAH na lura da ita Amma bata mata magana bah *MASEEFAR SOO*🌵🌹 Abokanayan ango sunxo da Ango suna yi mishi tsiya. Shiko idan shi nakan Amaryasa yayinda hankalinsa ya tashi lokacin daya ga tana kuka Bayan sun fitane daniyar jiransa suyi sallama yazo ya ritsata akan tagayamai dalilin kukanta Cikin qara sautin kukan Tace LABEEBAH CE my luv LABEEBAH CE Yace meyafaru toh Tace wai xasu tafi ita Sumayya kuma munrabu tana kuka sosai. nasani yau baxatayi bacci bah my luv. Na da'de da sanin ita tafi sona akan San danake mata katemaken ka rarrasheta dan Allah ko tayi shuru. Yace toh naji shikenan Tace eh Yafitta yana jinjina qaunar da sukema junansu A harabar gidan ya tadda Abo kanayan nasa Yace nagode da kulawaku Allah ya saka da alkairi Auwal Yace nidai kabimin qanwa ahankali dan irinku tuxurai idan kukayi Aure bakwa sa tausayi aranku KAMAL yayi dariya ka'dan Yace LABEEBAH nake nema Jameel ya camke da saurin cewa tana motar Auwal wai shixai kaita gida bakaga yanda nayi nayi da ita akan ta hau tawaba Amma taqi Murmushi KAMAL Yace yayi Yace kaje kakoyo soyayya kasace xuciyar LABEEBAH inba hakabah xaka rasata gabaki 'daya Duk Wanda yayi gangancin hakan Xan fafata dashi Wlhi. Jameel ya fa'di hakan Cikin nuna kishi Duk sukayi dariya KAMAL yaqa cewa toh Kai Auwal saikayi hakuri Madam 'dita tace in mayar mata da 'Yar uwarta gida. Auwal Yace tunyanxu xata fara baka aiki. Yace toh yaxanyi Wani Anas 'daya daga cikinsu Yace ba yanda kam xakayi Amarya tanemi ai mata abu ai dole ayi Haka suka rabu Cikin wasansu Yayinda KAMAL yaje Yana kwankwasa gilashin motar Auwal Yana cewa MATAR KAMAL MATAR KAMAL Da sauri LABEEBAH ta'dago kanta kana tabu'de kofar motar Amma batace mai Komai bah Yace toh fitoh inkaiki gida Batayi musu bah tafitoh tashiga motar tasa Sumayya Tace nima inxo ne Ya KAMAL Yace inaaa Saurayinki Auwal ya mai dake Cikin jin kunya ta rufe idanta Auwal ko sororo yayi sabuda wani lamari da KAMAL ya qaqaba masa yanxu KAMAL ko Murmushi yasakar masa dan shi yasan dai Auwal baida budurwa Yace namaka budurwa ko baka So ne Batare da Sumayya talura bah Auwal ya gallama KAMAL wata muguwar harara dan shidai soyayyar LABEEBAH CE tamai mugun kamo kuma tsaf yasan KAMAL yasani Yace Nagode Dagaji Kasan godiyar tatakai cice KAMAL ya ta6e yace asha soyayya lafiya. Ko kulashi Auwal baiyi ba yajah motarsa Da Murmushi KAMAL ya shiga motarsa. Idan shi Cikin na LABEEBAH Yace Subhanallah meya sameki afuska haka Shuru LABEEBAH tamai dan tafara jin haushinsa yanda yaketa wani murnah wai shi yayi Aure dawani rawar kai _tofah😳 mekaratu kunji LABEEBAH da qarfin hali_ Shiko KAMAL yasan kukan da XARAH tacemai tayine yasa fuskarta kumbura haka Amma yabasar dan bayaso yaqara qaryar mata da xuciya dan yasan LABEEBAH sarai wajan kwarewa a kuka yanxu saita rikitashi Yata motar tasa sukayi hanyar gidan nasu Amma ahankali yake tafiyar Can dayaga bata da niyar magana Yace meyasa baxaki xauna da XARAH nawani lokaci bah Da sauri takalleshi karab ko suka ha'da ido. dama abinda ya keso kenan yako watsa mata wani kallo dashi kansa baisan ya akayi yayi mata shibah bayan XARAH CE tadace da mallakar kallan sunkuyar da kanta qasa tayi batace Komai bah Kinsan Allah idan ba kiyimin magana bah Xan tsayar da motarnan in falleki da mari dan natsani inama mutum magana yayimin shuru Yace da ita hakan............ To to toh to me xan ce mah. Bayan karabani 'Yar uwata. Yanxu bani da damar in kwana da ita ba damar muyi hira da wasa da dariya da ita ako yaushe. Tafa'di maganar Cikin shagwa6a tare da qarashewa da rushemai da kuka kamar iyayanta ne suka mutu...... Wani birki taccan birni KAMAL yajah Wanda daba dan Allah yaso ba. Daya ka'de wani saurayi. Meyasa yake wayan jin wani filing kan LABEEBAH Meyasa shagwa6arta take tsumashi Meyasa yakesan akoda yaushe yake san ys dinga jin shagwa6artata Meyasa idan yaji kukanta hankalin shi yake tashi A qarshe meyasa duk bayajin hakan agare da XARAH Xuciyarshi ce duk take mishi wannan tambayoyin Kifa kansa yayi akan majuyar motartasa yanajin kukan nata har Cikin xuciyarsa LABEEBAH ko rage volume 'din kukan nata tayi sai takeyin shi ciki ciki Cikin wata murya ya 'dago kansa Yace dan Allah kitemaken kidena wannan kukan in dai XARAH ce namiki alqawarin duk lokacin da kikesan ganinta kikirani awaya Xanxo nakaiki gunta dan Allah kidena kukan nan kiyi shuru plx👏🏻 Cak kukan LABEEBAH ya 'dauke. Taturo baki Tace toh nadena Aiko Cikin sauri ya sauke ajiyar xuciya yatada motar sukaci gabah da tafiya Shuru motar ta'dauka nawani lokaci ahaka har suka iso gida Tana qoqarin bu'de kofar motar dan fitta yayi saurin tsayar da ita wajan cewa. Haba jimana malama haka xaki shigarma mamah gida fuska jage-jage da hawaye kalan kisa hankalinta ya tashi Cikin sanyi Tace xan goge kanna shiga ai Yace kigoge me da Allah juyo ingoge miki Da sauri ta juyo ta kalleshi Yako matsa kusa da ita yakama fuskarta ya goge mata tas Sannan shi kansa tsintar kansa yayi takai bakinsa goshinta ya manna wani shook kiss me bin duk qofofin da jini yakebi ya bada sakwanni Yace kiyi bacci lafiya tare da mafarkin KAMAL 'dinki ha'de da XARAH Ka'dan yarage LABEEBAH bata sumeba Dan kafeshi tayi da ido takasa ko 'kif tawa. Shiko ya hura mata iskar bakinsa Wanda yasata jan numfashi daya tafi da iskar dan qamshin sah Ahankali ta fita xata kullemai kofar Yace gud9t.......... Ta turo baki Tace Ya n9t.... Tashige gita da sauri Yayinda shi kuma yajah motarsa Yana kissima abubuwa da dama Ga mamakinsa bayan yayi farking a gidan nasa sai yaga qarfe goma Sha 'daya da rabi ya waro ido😳 11:30pm yafa'da abayyane Cikin sauri yashiga falan nasa da kullewa Sannan yayi part 'din XARAH Yana cewa my TEEMAH Ta sauri tatashi agadan ta duro tana wurga idanuwa sai kuma ta6ata rai Yace am sorry kinji Tace haba my luv Ni ka'daice fah agidan bakaga yanda nadinga jin tsoro bah Yace am sorry yanxu dai jekiyi Alwala kijirani muyi Sallah Tace toh Ya fitta xuwa 'dakinsa, Wanka yayi tare da saka kayan bacci yana kallansa a Miro Yace am sorry TEEMAH yau xaki kar6i wani baqon lamari Wanda nadade inasan injini acikinsa. Hmmmm Allah kasa karnayi 6arna XARAH ko kulle kofar tayi da key Sannan tashiga toilet 'dinta daya rikitata dan kyau da tsaruwa nan tayi wanka tacan ja kaya xuwa wata doguwar Riga ita ba ta bacci bah Amma xa'a iya bacci da ita Tafeshe jikinta da turare tasaka hijab sannan tabu'de 'kofar Tana xama yashigo Yana xubah Qamshi Yace wow kinyi kyau my TEEMAH Allah ya barni da matata Tace AmEEn Nan sukayi Sallah raka'a biyu yamata addu'a da tambayoyi akan tsarkinta Toh madallah bata ba kanta kunya bah ta bashi amsa dai-dai Ya saka mata kaxa da madara a gabanta Yace yunwa nakeji muci ko Tace aa Yace meyasa Tace haka dai Yace dan Allah kici ki temaken. Tace toh Nan sukaci suka kora da madara Daga nanne fah lamura suka xanja KAMAL yafara wasanni da ita. Can yaxo can dukiyar fulaninta nan yanuna xalamarsa kamar baxai barmata Su aqirjin nata bah Cak ya 'dagata ya kaita 'dakinsa Itadai taji yayi addu'ar kusanta bayan nan bata qara sanin inda kanta yake bah Tagumi KAMAL yaxubah lokacin dayaga aika aikan daya aikatama XARAH Wato kwata kwata bata motsi danta sume Toh abune wanda yada'de yana mararin xuwansa Wanda shikansa yasan duk wacce taxama mata agaresa toko saita 'dannani ku'darta Haka ya Shiga toilet ya gyara kansa Sannan yakaita itama daniyar gyara ta Aiko Tanajin ruwa ajikinta tafarfa'do tana ko ha'da ido dashi taqan qameshi Cikin furgice Tace dan Allah my luv kabarni kabarni haka Yace na barki matata Shiya dinga sakata a ruwa tana gasa jikinta Daga bisani tayi wankan tsarki. Yadawo da ita gadan Bayan yacanja xanin gadan Yanemi yanyota jikinsa aikowa tamatsacan qarshen gado tana wulwulla ido Tace dan Allah dan Annabi karka qara ta6ani Ganin tsoran daya ke tattare da ita yasashi barinta Yana Murmushi tare da rayawa aransa yanxu muka somah my teemah. Washe gari Momy da kakah suka turo musu da Safna da kayan breakfast Wanda kallo 'daya xakama kayan Kasan da biyune Wato anyi wani abunne dan ya dace da amarya. dan ginsu farfesun kaxa dana kifi dana kayan ciki KAMAL Yace ke duk wa xaici wannan Safna Tace kakah CE Tace duk na amaryane Yace oho ban dani kenan Tace har dakai Yayah Yayi Murmushi Da'yar yasa XARAH tayi breakfast 'din. Shima ka'dan taci Tsaf yagano tagama tsorata dashi Tace inasan naga LABEEBAH Yace toh kibari sai anjima. Kannan kinqara war warewa ko Toh kawai tacemai LABEEBAH ko tana shiga gida taxube jikin mamah tarushe da kuka Mamah bata hanata bah dan tasan kukan rabuwa da XARAH ne Ya yinda abin ya kasance ba haka bane LABEEBAH kuka takeyi akan tarasa KAMAL har abada Kuma har duniya tana'de baxata manta da abu biyu agame da shi bah Wato rungumarta da yayi a asibity da kuma tsayayyan kiss 'din da yamata. Dan haka ta'dauko hankicif dinsan nan daya bata kwanaki dan goge hawayanta taqi bashi. Toh saita manna shi a hancinta tanata shaqar qamshinsa Washe gari da Misalin qarfe 'daya ne taketa share sharen gidan nasu dan yayi datti da yawa Mamah Tace kinga gobe sai Yola ta'dauka. LABEEBAH Tace eh harfah nashirya kayana 'daxu........ Innah CE tashigo tana cewa aa Aisha aiki kikeyine haka Mamah Tace gidanne yayi datti da yawa Innah taxauna tana cewa Sumayya mah yanxu tagama Dama nashigone inji ko tafiyarnan nanan. Mamah Tace eh tananan yanxuma muke maganar Innah Tace toh dama wani hukunci nayanke mexai hana kutafi keda Malam da Suleiman da Matarsa Kinga mu jibi saimu tawo da Usman da LABEEBAH tunda sunsan kan garin Mamah tayi Murmushi Tace hakan yayi ba damuwa Allah yakaimu lafiya Innah Tace AmEEn LABEEBAH taturo baki Tace kaji innan nan kinwani hana atafi dani gobe Tace nafisan tafiya dakene dan banasan mutawo dagani sai Usman Mamah tayi dariya Tace yau kuma innan taku kike gudu Tace Innah yi hakuri dake xantafi dannaga mamah tafara sa mana ido Duk sukayi dariya Mamah tace tunda mah kinyi wanka saiki shirya kije ki gayama Zainab 'din yanxu dukda dama Suleiman 'din yasan da tafiyar Amma dai kije kigaya mata gobe qarfe tara taxo nan LABEEBAH Tace toh ya xatayi da yaranta Innah Tace kinsanta dasan 'ya'ya da abinta xata tafi ai......... Sumayya CE tashigo Tace Ya KAMAL ne yaxo. Gaban Su mamah yafa'di atare sukace lafiyadai ko Sumayya ta kwashe da dariya ganin yanda suka

Chapter 5 of 22