ta kalli Mimi tana faɗin" Mimi miye aibun Son da ba ki son shi? gaye na nunawa daga nan har london?
Ta karishe faɗa cikin zolaya Mimi ta kasa mgana kanta dai na kasa Hajiya sai Mirmishi ta ke yi ba ta ce komai ba.
Baaba Uwani ta ce"Ai daga nan har gaba da london ma Hajiya, wane mutum.."
Mirmishi ya yi kafin ya mike ya na fadin"To na rasa me ya sa ba ta so na"
Yadda ya faɗ kamar zai yi kuka, Hajiya ta taɓe baki kafin ta ce"Ba dole ta ce bata son ka ba, kana mgana kamar wata mace. Ni kuma Binta na namiji take son aura ba yaron mama ba." Kamar magana ce Hajiya ta sakarma Jaheed ɗin da uwarsa amma sai ba wanda ya nuna
Dariya kawai aka yi, sai ya nufi Hajiya zai mata shagwaɓa ta mike tana faɗin"Ni matsa tafi wurin uwarka ita zata iya da wannan lagen wuya naka kamar wata mace mai laulayi." Mimi sai da ta saka dariya shi kuma sai ya tura baki.
Hajiya Turai ta ce"Ko dai hajiya na kishi ne."
Ta karishe faɗa cikin zolaya Hajiya ta wuce gaba tana faɗin"Allah ya tsareni ko tsohon mijina Sulainmnu kafin ya bar duniya duk tsufansa ya fi min wannan lange langen ɗan naku. Allah ya kara lafiya Hansa'u Binta mu je ko? Hajiya ta faɗa tana kallon Mimi daman kamar akan ƙaya take ta yi saurin fita daga ɗakin.
Mama da Jaheed suka biyo bayansu suna faɗin" Tun yanzu za su tafi ba za su bari Alhaji ya dawo ba?
Hajiya na cigaba da tafiya ta ce"Wani Alhajin kuma? Hamza ko da safe ya zo mun gaisa."
Jin haka suka yi shuru Anty jin tafiyar su, ya sa ta fito suka yi sallama har bakin mota Jaheed ya rakasu.
Ya za ga ya ta bangaren Mimi cikin yar shagwaɓa ya ce," In zo gobe?
Mimi ta ce"No ina wajen aiki?
Da sauri ya ce" Sai na same ki acan mana."
Mimi ta yi saurin cewa"A a ka bari in na dawo zan kira ka."
Karya wuya ya yi kafin ya ce" Jibi zan koma saboda haka promise"
Ya faɗa har ya na mika mata hannu sai taki kamawa sai kawai ta girgiza kai kafin ta ce"In sha Allahu zan kira ka."
Sai lokacin ya yi mirmishi ya zaga ya wajen da Hajiya ke zaune ya zaro kuɗi Sabbi daga aljihun Jeans ɗin da ke Jikinsa ya ɗorama Hajiya a saman cinyarta, sannan ya sagala Hannu ya mikama Baaba Uwani nata ta karɓa tana masa godiya.
Sai kawai ya ce"Baaba uwani addu'a zaki yi min Allah yasa Mimi ta so ni."
Baaba Uwani ta ce"Da ikon Allah zata so ka ɗan Alhaji kuma kun bala'in dacewa da juna." Ta faɗa tana yar dariya, Jin haka ya sa ya kara dumbuza mata kuɗi ya mika mata ta karɓa tana saka albarka da addu'an Allah ya ba shi Binta.
Mimi ta ji hauahi ya isheta ta yi ma motar ta key, ya ɗaga ma Hajiya hannu yana fadin"Amaryata sai na zo, na ba da kudin cefane ba na son gori."
Hajiya ta ce"Sai ka zo tunda kana yi da ni ai shik enan Allah ya yi albarka."
Yana ɗaga musu hannu har suka bar haraban gidan.
Sai da suka hau titi Baaba uwani na dariya ta ce"Dubu ashirin ne ɗan Alhaji ya bani Hajiya"
Hajiya ta ce"Kin gode kuwa."
Mimi na tuki ba ta ce komai ba, Baaba Uwani na soke kudinta a haɓan zaninta ta ce"Binta ina laifin ɗan Alhaji? ga shi ɗan uwanki don Allah ki saurareshi mu yi tuwo na maina"
Mimi na jin ta ba ta yi mgana ba Hajiya ce ta ce"Ai Babanta ma ya ce tunda ba ta so a bar mganar, kuma Ya faɗa ma Hamza, shi dai yaron ne ya kasa hakura."
Baaba Uwani ta ce"Wayyo wallahi ya na son Bintar ki Hajiya ki saka baki ta saurere shi."
Hajiya ta ce" Ba ruwana ai ba ni zan zauna ma ta da shi ba, in sun daidaita kansu zan fi kowa murna da haka."
Mimi na jin haka ta kaɗa kai kafin ta ce"Baaba uwani ni fa Jaheed baya cikin, irin jerin mazan da nake son aura ni da shi ba bambamci ya yi ta wani abu kamar ba namiji ba, ko maganarsa irin na mata ne fa ba ki ji ba?. Ta faɗaa cikin marairacewa, Baaba Uwani ta ce" kuma fa hakane yana abu shima kamar na mata."
Hajiya na dariya ta ce"Ai na matan ne, ko ba ku ga yadda yake nane da uwarsa ba."
Daga Mimin har Baaba Uwani sai da suka saka ma mganar Hajiya dariya.
Ita kuma ta ce"To ina mamakin yaran zamanin nan, kamar sun fi kowa sanin darajan Ƴaya mu namu ƴaƴan ba ƴaƴa ba ne." Mimi na dariya ta ce" Hajiya ta kenan."
Hajiya ta yi mirmishi ba ta dai yi mgana ba.
Suna tafe suna hira har suka isa gida, ammh sai da suka tsaya a hanya Mimi ta siya kayan marmari saboda na su ya ƙare kuma mai kawo cefanan wannan watan ya yi nuƙusa ni, daga gidan Daddy ne kila gobe ko Jibi za'a kawo kayan abinci da cefane.
Washegari kafin Mimi ta je wajen aiki Rukky ta dameta da kira dole ta shirya ta fita gabaɗaya, ta fara biyawa ta gidan su Rukky sannan da la'asar ta tafi wajen aiki, rigimar Rukky ce da ba ta karewa.
Dole wai sun shiga bikin ƙanwarsu sun yi kane kane, to ya ta iya? In bata saka kanta ba, nacin Rukky kaɗai ya isa ya hanata barci cikin salama.
*****
*7rd March, 2022*
11:40pm
Ɗakin Inna Meri cike yake da baƙi mutanen Kano ne suka zo garin tn jiya Mu'azzam da matarsa Hibba da ɗansu mai sunan Baba Danjuma suna kiran shi Junoir. Anty Amina itama tun safe ta zo ita da nata gayyar ƴaƴan, sai kuma Bintu tare da ƴan biyunta.
Sai Anty Halima itama da nata gayyar Ƴayan. Sai Hibba da Walida sai Mariya a ɗakin Inna Meri ya cika da hayaniya, ita kuma daman abin da take so kenan..ta yi nan ta yi nan duk domin ta ga ta farantama ƴaƴanta da jikokinta da suke tafe bin ta wannan ya ce Inna zan sha tea sai wannan ya ce Inna zan sha ruwa. Uwayensu na zaune ita ke tsaye kan kafafunta a kansu.
Iyaye nasu na zaune suna hira suna dariya.
Magajiya na tsakar gida tana shanyan yan kayanta da ta wanke sai kwafa take yi, bakin ciki ya kusa kasheta in ta jiyo shewan Ƴaƴan Inna Meri daga bangarenta.
Gaje ce ta shigo daga bangaransu da botiki a hannunta duk da an raba ƙofa amma itama jin hayaniya ya sa ta wanke wasu kaya ta shigo shanya domin ta ji gulma.
Tana ganin Magajiya na shanya sai ta wayance da cewa"Au ke ma wanki kika yi, nima tun safe na ke wanki igiyan can ya cika sai na ce bari nazo na shanya anan."
Magajiya ta taɓe baki kafin ta ce"Nawa ba su da yawa, ki shanya daga gefe."
Daga haka ta cigaba da shanyanta tana tsaki ita kaɗai. Gaje ta zo ta fara shanyanta lokaci ɗaaya ta na nazarin Magajiya kafin tace" Hala mariya ba ta gidan ne?
Magajiya kamar ta na jira ta fara faɗin" Ta na nan, ammh ta na ɗakin uwarta Meri tunda taji zuwan su Amina da safe.".
Gaje ta rike haɓa kafin ta ce"ashe su ne su ka zo shi ya sa na yi ta jin hayaniya, ke ko dan'uwansu ya zo mana jiya mun sha tsaraba an gode Allah ya ba da lada."
Magajiya ta sake yin kwafa kafin ta sauke ajiyar rai ta na faɗin"Uhm!
Daga nan ba ta kara mgana ba, sai dai jefi jefi ta na ta sakin tsaki ƙananu.
"Salamu Alaimkum.."
Muryan Jummai ya shigo tsakar gidan lokaci ɗaya da bayyanarta a tsakar gidan fakan fakan ta shigo gidan ga goyo ga Ƴaƴanta guda uku kai da kai suna bin ta a baya Magajiya ta dakata da ƙokarin zuba ruwan da take yi za ta yi wanka.
Gaje ce ta tari Jummai da faɗin"A' a Jummai ce a gidan." Jummai na zama saman tayels ɗin dake Kofar ɗakin Magajiya lokaci ɗaya tana faɗin "E Gaje, Magajiya ina kwana, wai Mu'azzam ya zo garin nan ƴaron nan munzali ya ke faɗa min ya ce da safe ya ganshi"
Ta faɗa tana nuna ɗan babba ciki ƴaƴanta.
Magajiya bata yi mgana ba Gaje ta ce"Eh ya zo jiya, kin makara har mun cinye tsaraba."
Jummai tace"Kan uba har kun ma isa, Magajiya ina tsaraban mu?
Magajiya ta kalleta a fusace kafin ta ce"Sai ki shiga ɗakin uwarsa ki tambayeta domin duk abin da ya zo da shi shashenta aka shiga da shi, sai abin da ta ga dama ta aikomin da shi." Ta faɗa tana nuna bangaren Inna Meri ta na jin wani bakin ciki na yi mata suya acikin ranta.
Jummai ta rufe baki kafin ta ce"Wai kaɗan ta baki magajiya?
Kafin ta yi mgana, Gaje ta yi saurin cewa" To ai daman haka take yi, ta wani tattare komai sai kace agolan ɗan ta ne ya kawo, ai ba ita ta haifi Mu'azzam ɗin ba, balle ta rika tattare komai in adalci zata yi sai ta fito da shi ayi raba dai dai.".
Ta karishe faɗa a na waige waige na munafunci jummai ta sauke numfashi ta kwanto goyon ƴarta ta buɗe rigarta daman tuni ta cire hijabi, nono ta jawo wani yaraf kamar tsumma a yamushe ta tura ma yarinyar nono a baki Lokaci ɗaya tana faɗin"Ta wani fannin da ƴar gaskiyarta fa gaje, kin manta lokacin da Maman Mu'azzanm ta rasu, Baba ya yi ya yi da Magajiya ta rike su ta ce ba zata rike ɗan kowa ba, bayan ya auro Inna Meri ya ba ta su ta kuma karɓe su ta riƙe su da Amana to anan fa banga laifinta in ta kankane komai ba, da Magajiya ta rike su da yanzu komai suka samu yana bangarenta ne."
Magajiya kamar ta kai ma Jummai duka haka ta ji, cikin ƙufuluwa da ɗaga murya ta ce"Eh din,na faɗa na kara faɗa bazan riƙe ɗan kowa ba ni ma kaina Ƴaƴana sun ishe ni." Jummai ta ce"Hmm!
Kafin ta mike yarinyar ko gama shan nono ba ta yi ba, ta warceta ta saba a kafaɗa lokaci ɗaya tana faɗin" Bari naje shashen Inna Meri na samo tsarabata."
Harara magajiya ta bi ta da shi kamar Idanuwanta za su faɗo ƙasa. Gaje ta rakata da faɗin" Za ki samo kam, domim Meri ba daga nan ba wajen kyauta."
Magajiya ta kalleta a wulakance kafin tace"Gaje ba kin gama shanyar ba?
Gaje na rawan baki ta ce"Eh dama..!
"To kama gaban ki gaje, kinsan halina bana son Munafunci yanzu sai aji mu da ke."
Take faɗa lokaci ɗaya tana zuba ruwa a botiki rabi ke shiga ciki rabi na zuɓewa saboda bakincikin an yabi halin kirkin Inna Meri, magajiya mace ce mai bakin kishi da hassada da ƙyashi. Gaje ta ɗauki botikin ta kama hanyar fita tana faɗin"Abun bai kai ha ka ba Magajiya sai an juma."
Daga haka ta fice ta na taɓe baki.
Magajiya ta ja tsaki sai a lokacin ta ga munzali yaron jummai.
Tsawa ta daka masa kafin ta ce"Ta shi ka bi uwarka kafin na mare ka."
Sumu sumi ya mike ya bi bayan uwarsa kamar yadda kakarsa ta faɗa ita kaɗai ta shiga ɗakinta Lokaci ɗaya ta na dage labulen ɗaakin ganin shi kaca kaca.
Kyafci ta yi lokaci ɗaya tana faɗin"Sai na yi ma mariya bugun tsiya, yar iska yarinya kawai." Take faɗa ta na faman kaye kaye ta na tsaki ita kaɗai.
A shashen Inna Meri kuma ya kacame da hira, Jummai daman akwai zence in ta zauna kaf sai ta zazzage asirin gidanta kullun cikin babu, ba ranar da Jummai za ta zauna ta faɗi alheri a kan mijinta sai dai ta ce ba ta da shi Saboda a taimaka mata.
Mu'azzam in yazo gari haka ya ke fama da babun ƴan'uwansa marasa godiyan Allah, Mansoor dai ba ma ganinsa suke yi ba shi ya fi yi ma mazan matan ma wata sai ta yi shekara bata ganshi ba tunda ya fara harkan ƙwallon nan. Kuma sun fi sakewa da Mu'azzam Mansoor daman shi tuntuni sun ɓata garinsu a wajensa mata ba ta isa ta tare shi da wata mgana ba.
Jummai ke ba da labarin a anguwarsu wani gidan ɗan majalisa yana raba tallafin kayan abinci da suka je bin layi sai da ta yi faɗa da wata mata. Hibba na zaune ta ce"Kai yaya Junmai dambe a titi ba girman ki ba ne."
Bintu ta yi dariya kafin ta ce"Baki san Yaya Jummai ba ne shi ya sa."
Hibba sai kawai ta kaɗa kai ta ce Allah ya kyauta wayarta mai tsada ta ɗauka ta tura ma Bobo ɗinta sakon tana Jiran sa zai zo ya kaita gidan su ne yau can zata kwana.
Daman auran zumunci ne tsakaninsu da Mu'azzam ɗiyar kanwar mahaifiyar Mu'azzam ce aka yi haɗin zumumci.
Yanzu can bolari zata fara biyawa babban gidansu kafin ta wuce tudun wada gidansu.
Sai ya ce mata yana tare da Mansoor in sun gama gashi nan zuwa. Amina ta kalleta kafin ta ce"Kun fasa tafiya can tudun wadan ne? Sai ta girgiza kai kafin ta ce"Ya ce yana wajen Yaya Mansoor in sun gama zai taho."
Bintu na jin an ambaci sunan shi ta yi saurin cewa"Baban Inna, uhm ban faɗa muku abin da ya yi min ba?
Nan ta shiga ba su labarin faɗan da yaje ya yi mata a gaban kishiyarta da mijinta.
Cikin takaici Binta ta ce"Ni ba abin da yafi ban haushi sai cewan da ya yi sai ya yi biji biji da ni na kara mgana a wajen."
Jummai ta ce "Kan uba, shi fa daman masifaffe ne, har yanzu bai daina masifarsa ba." Halima ta ce"Ya rage masifa amma ya kara ninka bakar zuciyarsa."
Hibba na jin su ta na dariya sau ɗaya ya taɓa zuwa gidanta na kano sai dai su hadu in sun zo garin nan. Ta san shi tun suna yanmata tunda suna zuwa gida nan.
Ita dariyansa ne ba ta taɓa gani ba, Kamar baya son zama acikin mutane ne.
Nan aka buɗe caftan Baban Inna ana ta gulmansa.
Hibba na saurare tana dariya farar mace ce doguwa mai kyau da ita ga gashi da ka ganta ka ga bafullatan gombe.
Suna cikin mgana Inna Meri ta leƙo tana faɗin " Duk ina jin ku, ku gama za ge min Babana na gode."
Sai gabaɗaya suka saka mata dariya har da Jummai tana faɗin"Ni dai inna ban da ni kar ki hanani tsaraban Mu'azzam"
Domin jummai akwai son abun duniya zata iya kwantar da kanta saboda abun duniya.
*An samu kuskure a page 1, in da na ce Mimi ta karanci Mass communication Faculty of Sciences, kuskure ne zan ce ne a faculty of Social Sciences*
*Janafty*
*IDAN AN CIZA..!*
*Wattpad:Jamilaumar315*
*Arewabooks:Jamilaumarjanafty*
*Mallakar:Janafty*
*SADAUKARWA GA HAJIYA AISHA AHMAD IYA*
MMN MUJAHID KAYAN MATA AND SUPPLEMENT
SHIN KINA DA LABARIN MACCE MAI GYARA DABAN TAKE GA ZUCIYA MIJIN TA
MUNA DA KAYAN MATA MASU ZAFI NA BUGAWA GA JARIDA
HAJIYA TA KUDI DA KUDI AKE NEMAN SU
INA MASU FAMA DA MATSALA RAMA BA GABA BA BAYA KINA ZAUNE ANA KWATANCI DAKE KINA CI BAKI KOSHI MUNA DA MAGUNGUNA DA ZUMA 3 IN 1 KIBA BRST HIPS TA CIKO MIKI KU INA KIYI FRESH MUNA DA KWAYOYI MUNA DA GARI DUK MASU CIKO JIKI NE KIYI DUM
INA MASU FAMA DA MATSALA BRST KU TSUHU YAFI SON YAGA NONO A TSAYE DUK MAI MAGANIN DA TACCE MIKI ZATA BAKI MAGANIN NONO KAI TSAYE YAYI MIKI KARYA CE MAGANIN BRST SAI KIN SHA ADADIN WANDA ZAI MIKI SBD DUK CIKIN GYARAN JIKI NA BRST YAFI WAHALA YI
INA MASU FAMA DA MATSALA SANYI MUNA DA MAGANIN SANYI ORIGINAL
INA MASU ZAMAN BANZA BABU SANA'A KINA KONE DATA KI GA BANZA WURIN TSEGUMIN KALLON STATUS DIN WASU GA DAMA TAZU MUNA HAR GIDA GA WAYAR HANNUN KI KI MALLAKE MOTA MILLION 8 HAR FIYE GA ALBASHI GA RIBA GA KYAUTA KAYAYA KI
08066726866
Follow this link to join my WhatsApp group: https://chat.whatsapp.com/JMpd8nXr7TIDD3ILDXh64z
*Page 6*
Mu'azzam bai shigo gidan nan ba sai bayan la'asar Hibba har ta gaji da jiransa, sanda ya shigo har lokacin Jummai tana bangaren Inna Meri ba ta tafi ba daman Mu'azzam ɗin take jira ko za ta samu kuɗi a hannunsa.
Tsaraba kuma sauran wanda ya rage na bangaren Inna Meri ta raba gida biyu ta ba ta rabi, daman dankali ne sai wake da garin rogo, sai siga da ya kan zo da shi a raba ma yan gida da makota.
Turamen zani guda biyun da ya zo da shi yace ɗaya Inna Meri ɗaya kuma Magajiya kuma an kai mata nata amman a inda Mariya ta sauke kayan kallon banza ta yi musu ta kauda kanta nan suka kwana kuma ba ta kauda su ba, ballantana ta ga abin da ke ciki. Ita babban bakincikin ta ita ce mace ta farko da ta auri Danjuma a matsayin saurayi da budurwa tun ya na matashin sa, amman yau daga karshe ita ce koma baya a cikin gidansa. A ce har wata banzan bassakwata ta zo ta fita matsayi aciki gidanta da tun tana da kuruciya take cikin shi. Sannan karin takaicinta gabaɗaya inna Meri ta siye kowa na gidan da kirkinta, sannan ƴaƴan gidan masu kuɗin duk ta tattare su a ɗakinta ita sai abin da ta raba ta aiko mata da shi.
Ai in da gaskiya acikin lamarinta Mu'azzam ɗan Danjuma ne, ba ita ta haife shi ba in ta rike kayan da AGOLAN ɗanta ya kawo mata tana kan daidanta, amman na wajen Mu'azzam ko na wajen Amina ko Halima ba ta da hakki a kansu tunda ba ita ce uwar su ba, Magajiya duk ta manta lokacin da uwarsu ta rasu da Ɗanjuma ya ce ta rike su tsalle ta da ka ta ce ba za ta iya rike ƴaƴan wata ba. Itama nata sun isheta duk ba ta duba wannan ba sai yau da suka zama wasu take tunanin ba a yi mata adalci ba.
Tana tsakar gida tana jajjagen kayan miyan abincin dare da za ta ɗora Mu'azzam ya shigo gidan cikin shigan kananun kaya gefe ɗaya key ɗin motarsa wata bakar Jeep katuwa ne a hannunsa yana tafe yana kaɗawa shi fari ne sai dai bai kai Mansoor tsawo ba da ka ganshi ka ga Baba Danjuma saboda suna bala'in ɗibar kama da shi sosai.
Cikin ladabinsa ya gaisheta kamar yadda ya saba shi dai ta na amsa masa cikin sakewa ba kamar ɗan uwansa da ta ce gaisuwan reni yake yi mata. Har ya gota ta zuwa bangaren Inna Meri tana kallonsa ji be sa yadda ya zama kato ya yi kiba saboda ya samu duniya. Kwallah suka cika mata ido, kaf ƴaƴanta ba mai jin daɗi a gidan auran sa, har gwara ma Zuwaira akan Jummai ita Jummai ai kullum a gida a ke ba ta, ba ta kawo ma uwa ba. Sai dai ta bi ta karɓe Auwalu ne Namiji babba shi kuma ya ƙi karatu sai yanzu take jin haushin yadda ta zura masa ido ya ƙi makaranta in da yau ya yi karatu da Meri ba ta isa ta rika mata famkama da kudin su Mu'azzam ba, su ma ai da karatun su ke takama, ba za ta manta yadda Danjuma ya rika fama da shi akan karatu ba ya ki yi, Ita kuma ta ɗaure masa kugun yin abin da ya ga dama ga shi nan daga karshe sai buga bugan gini ga shi ya yi aure ya tara Iyalai shima fama yake yi da kansa. Saddiqu ne bai yi aure ba har yanzu ya na can garin Ikko ya na neman kuɗi amman sai ya shekara bai zo ganin gida ba sai dai a waya sai sako da ya ke yi musu wani lokacin, shima ba sosai ba tunda Auwalu ya fi shi tausayin iyaye shi kawai domin ba shi da shi ne.
Mariya ce ta rage a gabanta ita kuma ai ba ta ɗawainiyarta daga karatu har bangaren Surutu ƴaƴan Meri sun ɗauke mata wannan bangaren kuma duk abin da take so suna yi mata ko jiyan ta ganta da hijabi sabo da takalmi ta zo ta na nuna mata da cewa matar Mu'azzam ta kawo mu su ita da Walida, ta san suna kokari amman bakin cikinta ace ƴaƴan Meri ke taimaka mata to na yaushe kuma in taci ta sha su ne, tunda yanzu Ɗanjuma ba kasafai ya ke wanzanci nashi ba, ba kuma kamar a shekarun baya da ya yi suna tunda abun na su na gada ne ba haya ba.
Duk da tuntuni bala'in magajiya ya sa aka raba girkin bangaren har yau har gobe kayan abinci biyu a ke rabawa, ita rabi Meri rabi ciki har ta san ma sauran ƴaƴanta
Kuma har gobe komai in Inna Meri ta dafa sai ta aika mata da shi sai dai in taki ci, ta bar shi nan Mariya ta ɗauka ta cinye. Har ta gama jajjagen ta tunanin yadda rayuwa ta zo mata ba yadda ta yi tsammani ba da gawayi yanzu suke amfani ta fito da murhun gawayin tana kakkabewa dagacan shashen ta jiyo muryan Inna Meri na faɗin.
"Ɗan Inna ba za ka tsaya ka ci abinci ba?
Ɗanwake Walida ta yi saboda kai."
Ta na jinsa ya ce"Sai na dawo Inna, in na tsaya yamma za ta yi."
Ƙaramin tsaki taja. Tana jin wani irin takaici a kasan ranta, Mariya ta ke jira sai ta mata bugun tsiya Jummai ma tunda ta shige har yanzu bata kara lekowa ba kyafci ta yi ita kaɗai ta na girgiza jikinta daga gani za ka san Magajiya ta iya bala'i sannan cutar hassadan dake damunta ne ya sa har gobe ta kasa ganin alherin ƴaƴan Meri ne suka lulluɓe rayuwarta. Ta koma ɗaki kenan taji fitowarsu da mganarsu zuwa shashenta ta ji muryan Jummai na faɗin " Mu'azzam ka taimaka min yara nan duk ba sa zuwa makaranta daga bokon har islamiyan an kore su." Ba ta ji dai me ya ce ba ta dai ji Jummai na ta godiya kamar zata kwanta masa, baƙinciki ya kara cikata ita da ya kamata ya'yanta su ba da, su ne yau za su koma yan maula suna roko a na ba suna godiya.
Muryan Hibba taji kamar za ta shigo ɗakinta yasa zaraf ta ɗaga labule ta fito sai suka ci karo da juna cikin shirinta ga Walida rike da ƙaramar akwatinta sai Mariya dake dauke da Junoir, gabaɗayan sune har da Bintu da su Amina suma cikin shirin fita kila duk tare za su tafi ko kafin ta samu damar mgana Hibba ta rankwafa cikin ladabi tana Faɗin " Sai anjuma Magajiya yau a Tudun wada zan kwana sai jibi in sha Allahu."
Kadahan kadahan ta ce"Allah ya kaimu, ku gaida gida."
Mariya ta kallah cikin jin haushinta Mu'azzam kuma ya fice lokaci ɗaya yana fadin"Ku fito mu tafi in na kai ku daga can zan biya wani waje ne."
Amina ce ta bi shi tana faɗin" Kai Mu'azzam ka ce mu zauna kenan ba za ka dawo da mu ba?. Sun fita can waje suna magana su ma su Binta sai suka rufama musu baya, Mariya ta kallah da ke shirin bin su a fusace ta ce"Ke ina za ki je?
Cikin tura baki ta ce"Za mu raka Anty Hibba can ne, Yaya Mu'azzam zai dawo damu a motar sa."
Wani irin harara magajiya ta sakar mata kafin ta ce"To ki fita ki gani,wlh sai na yi kasa kasa dake acikin gidan nan"
Daga haka ta duka tana zuba gawayi acikin murhun dake gabanta lokaci ɗaya tana kara sakin tsaki, Mariya ba ta da yadda za ta yi dole ta fita waje ta mika ma Bintu Junior ta ce Magajiya ta hana ta zuwa, ba wanda ya damu sanin halin Magajiya duk wanda ke rayuwa a gidan wanzamai ba ma acikin gidan ba har makota su san wacece ita a haka ma ta rage a shekarun baya in ta fara bala'i da masifa sai makota sun ji acikin gida kuma sai su Gaje sun cika tsakar gida suna bata hakuri, abin da ba a taɓa ji ba shine nuryan Inna Meri tana tanka mata daga ita har Baba Danjuma masu hakuri ne da kau da kai daga sha'aninta.
Da Mariya ta dawo haka ta rika jaraba tana zaginta, Inna Mari
All Chapters
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 8 Chapter of 26