da saje sai da daga kasan gemunsa yana da gemu kaɗan da ya fito masa shima baki silif da shi gwanin ban sha'awa. Sannan yana cikar sumar kai, mai yawa baƙi silik da ke shan gyara sosai.
Yana da faɗi daga saman sa jikinsa kuma duk a murɗe ne sakamakon training.
baƙinsa mai kyau ne tunda har shining ya ke yi, idanuwansa matsakai ta ne, sai dai yana da karan hanci dogo da bakinsa dai dai misali.
Ƙaramin firizan dake falon ya je ya buɗe ya ɗauki ruwan gora ya kafa kai yasha fin rabi, sai ya rufe firizan ya kuma ijiye ruwan a saman firizan ya Juya yana tafiyarsa na zafzaf ya koma cikin ɗakin da ya fito.
Ya jima aciki kafin ya sake fitowa wannan karon hannunsa ɗauke da wayarsa ya fito ɗayan kuma hannunsa ɗauke da kujera fara ta roba, ya zo ya kafata acikin falon ya zauna yana harɗe kafafunsa waje ɗaya.
Tun yana salla ya ji ana ta kiran wayarsa, tunda ya ji kiran yaƙi ya kare ya zargi mutane guda biyu
Ko Bintu ko Mu'azzam.
Sune suke yi masa mahaukacin kira rututu ko bai so ba sai ya ɗauka in bai ɗuka ba, ba za kuma su fasa kiran ba.
Wannan karon ba Bintu ba ne ɗaan uwanta ne Mu'azzam, sai da yaga kiransa sannan ya tuna ya ce masa sun zo kano buga wasa, kenan yana can yana tunanin in sun gama buga wasa zai shigo wajensa.
Shuru ya yi yana wani tunani, Mu'azzam kamar mai hankali kamar kuma ya girma ammh bai daina abun yarinta ba, shi fa bai ce masa zai zo ba ballantana ya ce yana jiransa ne, kawai daga sun je buga wasa sai a ga ya ce za shi wani waje? Kamar wani yaro ƙarami.
Yana wannan tunanin kiran Mu'azzam GADDAFI DANJUMA ya shigo cikin wayarsa kamar yadda ya yi masa Saving.
Sai da ta kusa katsewa ya ɗaga kiran bai yi mgana ba.
Dagacan bangaram Mu'azzam ya ce"Kana ina ne? Ai kace min tun a jiya za ku gama wasan ko?
Sai da ya lumshe ido sannan ya buɗe kafin cikin muryansa ta kai tsaye ya ce"Eh mun gama.," Mu'azzam yace"Suwa suka ci?
Kai tsaye ya ce"An ci masu gida."
Mu'azzam ya ce"Good Ajin Jihata nasan za ka yi musu cin cikin gida ne."
Mirmishi ya yi ba tare da ya yi mgana,
Mu'azzam ya ce"Yaushe za ka taho?
Yau saboda kai na dawo daga office da wuri fa"
Daman yasan za'a rina cikin dakushe muryansa ya ce"Na taho ina? daman nace maka zan zo ne?
Da sauri Mu'azzam ya ce"Ban gane ba? Kana ina ne?
Kai tsaye ya ce"Ina gida"
Mu'azzam baki ya saki kafin ya ce"Wani gida kuma?
Aji ya ce"Wani gida gare ni?
Mu'azzam ya ce"Mallam sidi ko anguwan Arawa ko Tunfure?
Cikin Kosawa ya ce"Mallam Sidi tushe na ne, anguwan Arawa kuma nan ne gidanmu, Tunfere kuma muhallina ne, ina Tunfere yanzu haka."
Cikin ƙarin Mamaki Mu'azzam yace"What! Gombe?
Sai ya juya yana kallon matarsa Hibba tana ta kai da kawo tsakanin Kitchen da falo domin shiryama ɗan uwansa abincin tarba ammh wai yana faɗa masa yana Gombe.
cikin jin haushi ya kira sunanshi.
"MANSOOR..!"
"MU'AZZAM.!"
Shima ya ambaci sunan shi, cikin takaici Mu'azzam ya ce"Tun safe da na faɗa ma Hibblove za ka zo wlh ta kasa zama waje ɗaya tayi maka girke girke yafi kala uku, akwai sarewa na faɗ mata ba za ka zo ba? ya za ta ji? Kuma don Allah ya kake son mu yi da abincin?
Kai tsaye ya ce"Ku yi ta ci har sai kun gaji, ni ban ce maka zan zo ba, faɗa maka kawai na yi mun shigo kano buga wasa, wa ya ce ka je ka faɗa ma matarka na ce zan zo? Mun yi haka dakai tsakanin ka da Allah Mu'azzam? sai Mu'azzam ya kasa mgana cikin ajiyar zuciya ya ce.
"Baban Inna."
"Ɗan inna."
Shima ya maida masa, daga haka Mu'azzam ya saki huci kafin ya ce"Ai shike nan." Sai kuma suka katse kiran a tare, mirmishin gefen baki ya yi kafin ya jinjina kai yasan yanzu za'a kai ƙaransa wajen Inna , yau in ya je anguwan Arawa ya san zai sha faɗan bai kyauta tunda bai je ya ga Mu'azzam ba.
Har zai sauke wayar sai kuma wani tunani ya faɗo masa da sauri ya kunna data ya shiga Facebook searching ya shiga ya saka sunan Karamci Tv.
Sai ga jerin shirye shiryensu ya bayyana, da ga vadion ma kafin ya shiga fuskarta ne cikin mirmishi tare da loɓawar dimple ɗinta Daga kasa ya ga daga ɗora vadeo 1hr ago har an masu kallo 2k comment kuma 1k.
Ƙankancewa Idanuwansa suka yi, ƙaramin tsaki ya ja kafin ya fita daga wajen gabaɗaya, ya koma ya na hura iska daga cikin bakinsa, sai ya ji kamar cikinsa ya ɗauki zafi rau ita kanta isar bakin nasa ma zafi take fitarwa.
Duk iya ƙokarinsa na kar ya kara komawa sai da ya kara shiga ya kuma danna hannunsa ya yi cliking ɗin vedeo.
Daman suna ɗora duka shirye shiryensu ta shafinsu dake facebook wato karamci Tv.
Tausayi ne ya kaishi ko nace rabon yau ya yi kwanan bacin rai da bakinciki, fuskar ta tar take kamar ko yaushe babban abun jan hankali daga gareta zaƙin muryanta.
Iya tsara kwalliya da shiga mai kyau da tsari yanzu ɗin ma wani leshi ne ajikinta mai kalan blue mai duhu da pich, ta yi ɗinkin doguwar riga fitted ta saka mayafi pich mai raga raga na ya yi, sai kuma ɗaurinta mai taken Zahra Buhari, kunnuwanta da hannayenta gold ne hatta ko zabban hannunta ta yi ƙayatacciyar kwalliyarta ta saka kalan jan bakin da ta ke yawan Amfani da shi mai kalan kalan deep blue ja ja kuma, in ta yi dariya sai fararen hakoranta su kara haska kyakyawan farar fuskarta su bayyana tare da hakorin makkanta shima yana kyalli sai ya kara mata kyau da kwarjini.
Fatima Mimi kyakyawa ce ajin farko acikin mata, daga saman kanta kwantattacen gashi da kana gani zaka fahimci tana da sumar cikar gashi.
Hancinta dogo da ƙaramin bakinta wanda saman ya yi tudu kaɗan ga cikar naman lebe, sannan fuskarta tana da ɗan faɗi kaɗan ƙaramin jiki gareta da ya dace da kyakyawan suranta.
Shekarunta ya fi ba ma mutane mamaki, ammh tarihinta bai ba su mamaki ba saboda daga ganinta yar manyan mutane ce, ko daga yanayin shigarta da yadda take hawa kaya masu tsada da yarari.
Tsabar yadda ya ke jin zuciyarsa na wani fat! fat! Kamar zata faso kirjinsa ta fito ya sa ya sauka daga vadeon sai dai rawan da hannunsa ke yi ne ya sa ya faɗa comments section bai sani ba, nan ya ga abin da ya kusa tarwatsa masa tunani da zuciyarsa gabaɗaya.
"Adadin mutane nawa ne suke kallonta?
"Maza nawa ne suke jin ta na burgesu?
"Maza nawa take ba ma sha'awa? Maza nawa take ɗaukan hankalinsu da kyan suranta da kwalliyarta?
Tambayoyin da suka cika masa zuciya kenan, lokacin da ya ga comments ɗin maza rututu.
Yawanci suna faɗin jikinta ya ɓoye shekarunta, sai masu faɗin.
"Mimi mai kyau ki na burgemu"
"Dimple bbym Tauraruwar karamchi"
"Ni dai ina son ki Hajiya Mimi, kin iya kwalliya da ado."
"Ni kuma ina son yanayin turancin ki, zaƙin muryan ki na tafiya damu."
"Ina son dariyan ki Mimi,kin haɗu kin haɗu kin ga ji da haɗuwa."
Gabaɗaya sai yaji jikinsa na rawa jiyoyin kansa suka mike raɗau zufa kawai ke keto masa kamar an watsa masa ruwa, ya dunkule hannunsa na hagu ya ɗaga zai naushi fuskar wayarsa sai wata zuciyr ta ce" Mansoor kana da dalilin yin hakan ne?
Ka manta sharaɗin da iyakar dake tsakanin ka da ita? In ma maza dubu ne zata burge su ji sha'awarta bai kamata ya dame ka ba"
Sai kawai ya koma ya sauke hannunsa ya na sakin huci a fili ya furta."Hakane bai kamata na damu ba, ita ɗin banza ta je ko mazan duniya za ta aura ma bazai damu MANSOOR AJI ba, ba zai dame ni ba."
Ya ke faɗa yana kara ma kansa karfin gwiwa, dalilin da yasa wayarsa bata sha naushi ba kenan, sai ma tashi da ya yi ya koma ciki.
Bedroom ne mai ɗauke da cafet da katifa sai kuma hanger mai Dlɗauke da kayansa na sawa, sai takalma ga su nan zube a gefen dakin duk an warwarsa su.
Kwanciya ya yi saman katifar kwanciyar sama ya hard'e hannayensa yana kallon rufin ɗakin wayarsa kuma ya kasheta gabaɗaya.
Vya daɗe yana kwance kafin ya samu barci sai bayan la'asar ya tashi ya yi sallah key ɗn motarsa ya ɗauka ya fita. Sai da ya buɗe get din ya fita da motar sannan ya dawo ya rufe ya koma ya shiga motarsa ya fita.
Abinci ya je restaurant ya siyo da ruwa da lemun maltina kowanne katan, dag anan gida ya dawo ya ci abincin. Farar shinkafa da miyan naman rago. Bayan ya natsa anan tsakiyar falon ya fara training ɗin sa.
Yana sama ya na kasa zufa ya ke yi ammh bai dakata ba har aka kira sallar mangariba.
Sannan ya tsaya ya koma ɗaki ya yi alwala ya sauya kaya zuwa manya kaya na shadda mai ruwan kasa harda hula saboda ya rufe sumar kansa tabbas in Baba ya ganshi da sumar nan sai ya yi masa faɗan rashin yin aski.
A mashin wannan karon ya bar gidan sai anguwam Arawa, a masallacin layinsu ya tsaya ya yi mangariba.
A masallacin ya haɗu da su Baba ɗanlami da Baba Sani. Sun rigashi fita daga waje shi kuma sai da ya gama addu'o'in shi sannan ya fito.
Daga nesa ya hangesu tun da akwai hasken inji a bakin masallaci.
Shi kuma yana fitowa matasan anguwan suka yayyameshi suna masa kirari da sunansa.
Wato Ajin jihata.
Shi kuma ya ba su hannu suna musabaha, suna mgana sai da ya yi mirmishi kuɗi ya lalubo aljihunsa ya diɓo baisan adadin su ba, ya mika ga wani daga cikinsu ya ce su raba a tsakaninsu.
Suka saki Ihu suna faɗin"Allah ya taimaki Ajin jiharmu da ikon Allah sai ka ɗauko mana Kofin duniya."
Mirmishi kawai ya yi musu ya wuce zuwa in da ya kafe mashin ɗinsa, kusa da mashin din su Baba Ɗanlami ke tsaye suna kuskus.
Suna ganinsa suka fara washe masa baki suna fad'in"A'a Mansoor ne an dawo garin kenan?
Baba Sani ke wannan rawan bakin mganar kallo ɗaya ya yi masu kawai sai ya ɗaaga musu hannu yana Fadin"Barkan ku da dare" Daga haka ya hau mashin ɗin sa ya tada kuma ya bar wajen da sauri.
Baba Ɗanlami ya rike baki yana kallon kaninsa Muhammad Sani.
Kafin ya yi mgana Baba Sani ya kaɗa kai ya ce"Eh lalle wato dai shi wannan Agolan yaron bazai taɓa sauya halinsa ba ko?
Baba D'anlami ya ce"Uhm ka gani dai, yaron nan fa ya raina mu ba mu ci darajan ya zo gabanmu ya gaishemu ba sai dai kawai ya ɗaga mana hannu yana faɗin barkan ku da dare kaamar wasu sa'aninsa"
Ya karishe faɗa yana kwaikwayon yadda Mansoor ya yi musu mgana.
Baba sani ya ji ciwon abu fiye da kullum maganar gaisuwa ba ta dameshi ba daman ai sun saba in dai yaron nan ne bazai taɓa ganinka ya ce maka ina yini ba? Sai dai barka da safiya in da safe ne in kuma da rana ne yace barka da rana.
In kuma da yammah ne yace barka da yammah in dare ne yace barka da dare.
Ba za ka taɓa cin darajan ya ce maka ina yini baba wanne ba? Ai shi bai san wannan tarbiyan ba, ko yara ne suka ce masa ina yini? Sai dai yace barka yaro kamar ya gagari kowa. Shi abin da yafi damunshi suna ganin shi su san za su samu kuɗi sun tsaya ya zo su yi masa maula susan in ya tashi ba ka kuɗi ba kaɗan ya ke ba ka ba babbar kyauta yake yi shi.
Baba Ɗanlami ne ya katse shi da faɗin"Kuma duk Yaya Ɗanjuma ne ya sangarta yaron nan komai akace ya yi sai ya ce ayi hakuri maraya ne, amana ne a hannuna ku tayani rike amanar yaron nan Sani don Allah."
Baba Ɗanlami ke mgana yana ƙwaikwayon mganar yayan nasu Ɗanjuma.
Baba sani ya yi ajiyar zuciya kafin ya ce"Ai fa ga shi nan Agola yazo yafi masu gida arziki da samun ɗaukaka, kaf ƴaƴanmu ba wanda ya kai yaron nan nan samun duniya." Baba Ɗanlami ya ce"Kai ina rabaka an ce Ƴan ƙwallo kudi suke samu mahaukata ma kuwa, kai daga yanayin gyaran da ya yi ma gidanmu zaka fahimci yana da kuɗi ga yadda ya gyara ma Meri ɗakinta kamar na wata yar boko, ni fa Auwalu ke gayamin a kungiyar da yake buga kwallo shi ne shugabansu ko Kaftin ne ake kiranshi da turanci na dai manta, ammh maganar gaskiya yaro nan ya sha kwana shi ya sa ya ke mana kallon haɗaarin kaji."
Baba Ɗanlami ya ja gauran numfashi kafin ya ce"Mu tafi gidan Sani, duk tsiyarsa bai isa ya sallami Yaya Ɗanjuma mu bai sallame mu ba"
Baba sani yace"Kwarai kuwa."
Haka suka jera suna tafe suna mganganganu Baba sani faɗi yake yi"Har Yaya Danjuma in ka lura ya fara famkama a anguwa shi wai adole Agolan da ya rike ya samu duniya, ba ka ga ko wamzanci yanzu baya zuwa ba sai da ya yi mana mgana ba."
Ɗablami yace"Wlh na lura ko jiya sai da muka yi mgana da Gaje ta ce sai fankama yaya Danjuma yake yi, Meri kuma daman kasan halinta dariyan hakori ita a dole ɗanta ne mai arziki a gidan Wanzamai gabaɗaya."
"Ka daina fa danganta shi da gidan Wanzamai, ka ce Agolan gidan wanzamai kuma bai fi ƴayanmu ba sa'an rayuwa kawai ya samu su ba su samu ba, ni fa kamar na ce ko Yaya Danjuma na shige shige ne, ka duba fa duka ya'yansa sun samu duniya yanzu Mu'azzam fa babban Ɗan sanda ne yana kano in ya tashi zuwa kaga motar da yake zuwa da ita da shi da matarsa da ɗansu gwanin sha'awa ga kayan abinci da yake zuwa da shi cikin alfahari Meri ke rabawa sasa sasa ita adole ya'yanta masu arziki."
Baba sani ya faɗa bayan ya katse Baba ɗanlami.
Dukkansu a tare suka kalli juna kafin su ja gwaron numfashi.
Suka cigaba da tafiya da sauri sauri suna kuma tafe suna zagin Yaya Ɗanjuma da matarsa Meri da ya'yanasu Mansoor da Mu'azzam.
****
Har cikin gida ya shiga da mashin ɗin sa Mariya na cikin ɗakin Magajiya taji karan mashin da sauri ta fito da ya ke Sashen magajiya ke Farko kafin na Inna Merin
sauran sasan kuma da ya gyara gidan sai ya fitar musu da kofar su ta can, shashen iyayen sa kuma ya fitar musu da tasu kofar daga kudu.
Yana kokarin kafe mashin ɗin sa ya ji muryan Mariya ta na faɗin"Yayanmu sannu da zuwa."
Ta faɗa cikin muryanta mai sanyi, sai da ya kafe mashin ɗin sannan ya dago yana kallonta tana tsaye tana ta yi masa mirmishi.
Akwai wutar nepa hasken farin kwan lantarkin dake waje ya haske masa ƴar farar fuskarta. Cikin rashin sakewa ya ce"Yauwa."
Daga haka ya wuceta dai dai lokacin da magajiya ta fito daga makewayi da buta a hannunta. Sai ya shigeta zai shige koridon Maman Mu'azzam shi ya sa bashi da mafita sai sun haɗu.
Bai tsaya ba yana gota ta sai ta ji yana faɗin"Barka da dare Magajiya."
Ta juya ta na kallonsa cikin harzuka da ɗaga murya ta ce"Ji min wulakamci da reni, in ba za ka iya kirana da suna Mama ko Umma ba sai ka sakaya sunana ka ce Maman Auwalu ko maman Mariya ammh ba ka rika kirana da sunana Magajiya gantsal ba, wannan dai sam ba tarbiyan ba ne."
Ta gama faɗa ta na faman hararan bayanshi, shi dai bai ko juyo ba mamaki ya cikasa to me take son ya kirata?
Ya ga dai ko ƴa'yanta da ta haifa ma tun yana ƙarami ya ji suna gatsa sunanta Magajiya kuma bata damu ba sai shi don yau ya kirata da magajiya sai ta ce ba tarbiya ba ne?
Yana wannan tunanin yaji ta na fadin"Har kina wani fita kina gaishe shi don ubanki to ni nan uwarki ban ci darajan ya ganni ya ce min ina kwana ba, na kara ganin kin gan sa yazo kin fito kina yi masa dariya ki gani in ban falla miki mari ba."
Bai juyo ba ammh ya san baki Mariya ta tura kafin ta ce"Kai magajiya Baba fa ya ce yayanmu ne."
Daga murya tayi kafin ta ce"Karya ne wlh, Agola ne ba ɗan gida bane, ba ku haɗa komai da shi ba."
Ya ji sanda ta furta kalmar agola, adai dai lokacin ya yi sallama ƙofar ɗakin Maman Mu'azzam. Inna Meri uwar Mansoor Innar Mu'azzam.
*Janafty*
*1rd, March 2023*
*Post on 04 August 2024*
Follow this link to join my WhatsApp group: https://chat.whatsapp.com/FpA4NvQPg3XIRUQOgytNh5
*IDAN AN CIZA..!*
*Wattpad:Jamilaumar315*
*Arewabooks:Jamilaumarjanafty*
*Mallakar:Janafty*
*SADAUKARWA GA HAJIYA AISHA AHMAD IYA.*
*MADALLAH DA SURAYYA DEE, ALLAH YA CIKA MIKI DUKA BURIKAN KI NA ALHERI YA BA KI SANYIN IDANIYA AMIN.*
*FATAN ALHERI GA AMINIYATA AISHA MUHAMMAD ALTO(SISINAH), ITA ƊIN TA DABAM CE A WAJENA. NA GAISHE KI*
*NA GAISHE DA IYAYEN ƊAKINA*
*ZAINAB INUWA(AUNTYSIS)*
*HAJIYA LUBABATU MUSA*
*KHADIJA SALISU YUSUF(UMMINA)*
*HAJIYA HABIBA ABUBAKAR IMAM*
*ANTY ZAINAB ABDULWAHAB*
*HAJIYA HALIMA ƊALHA SHEHU.*
*ANTY HADIZA MAHE MUHAMMAD*
*ANTY SALAMATU ABUJA.*
*ANTY FADILA KABIR*
*ANTY FIDDAUSI KABIR*
*FATAN ALHERI NAGODE*
*INA GAIDA MARUBUTA, KARAMCINKU ABUN YAƁO NE. ALLAH YA ƘARA BASIRA ƳAƳAN BAIWA AMIN.*
*Page 2*
A tsakiyar falon ya ci karo da Inna Meri tana tsaye ita da Walida, ya yi sallama suka amsa gabaɗayansu. Tun kafin ya buɗe baki ya fara gaishe da Inna Walida ta yi zaraf ta ce"Yayanmu barka da dare"
Saboda sanin halinsa yanzu tana cewa ina yini sai yace bai ga yinin ba, sai dai ta ce masa barka da dare. Cikin mamakin ganinsu a tsaye ya ce"Barkan mu lafiya na gan ku a tsaye, Innanmu lafiya kuwa?
Inna Meri wata bakar dattijuwa kallon farko za ka yi mata ka fahimci ta fito daga shiyar sokkoto ne, sannan ta haɗa jini da Arawa, saboda gefen bakinta dama da hagu ga zanenta na Arawa nan ɓaro ɓaro ya bayyana duk da ko ta na baƙa na iya ganinsa. Sannan sai alokacin na fahimci in da Mansoor ya ɗauko tsawon sa, Inna Meri doguwa ce sosai mai kaurin jiki kuma.
A shekarunta iyakarta 56 zuwa da bakwai a duniya ba ammh yanayin jikinta bai nuna wahala ba sosai tana sanye da hijabi ne a jikinta hannunta kuma casbaha ne, daga gani ta idar da sallar mangariba ne tana lazimi. Cikin yanayin maganarta ta ce"Tun da naji Kwakwazon Magajiya na ce to Baban Inna ya shigo gidan" Mirmishi ya yi ba tare da ya yi mgana ba, Walida tayi saurin shimfiɗa masa darduma sanin halinsa bai son zaman kujera duk ko da irin tuma tuman kujerun alfarman dake mamaye da falon na inna Meri ko wata amarya albarka. Cikin natsuwarsa ya zauna itama Inna Meri sai ta samu daga gefensa ta zauna saman cafet mai taushi dake malale a cikin ɗakinta.
Cikin yalwataccen fara'an da ba a raba fuskarta da shi ta ce" Tun fa ɗazu muke ta duban hanyan ka ni da Babanku muka ji ka shuru." Daman yasan tuni labarin dawowarsa ya zo musu tunda Mu'azzam ya ji labari. Kansa na kasa ya ce"Innarmu kun yi mgana da Mu'azzam ne?
Cikin jimami ta ce"Ya kirani kamar ya yi kuka Baban Inna ba ka kyauta ma ɗan Innna ba gaskiya, me ya sa ba ka je ka duba ɗan uwanka ba?
Kai tsaye Ya ce"Inna wasa muka je bugawa kamar kuma wani mace sai a ganni daga zuwa wasa ina faman biye biye
Inna Meri ta ce"To menene? ba wajen ɗan uwanka za ka je ba? ya ce matarsa ta kasa zama waje ɗaya saboda zuwanka maganar gaskiya Baban Inna ba ka kyauta ba."
Ba ya son jan mganar ya sa Ya ce"Shike nan ki yi hakuri Innarmu, Ina Baba ko a masallaci ban gan sa ba?
Inna Meri tace"Tun ɗazu abokinsa Mallam Hashimu ya kirasa kan dai zaman da ake yi akan auran ƴarsa maigado shi ne ina ga har yanzu ba su kai ga matsaya ba."
Cikin mamaki Ya ce"Auran ya mutu ne?
Tana gyara zama ta ce"To abin dai nasu sanin gaskiya sai Allah ita ta ce ya saketa shi kuma ya yi rantsuwan bai furta mata saki ba sun dai yi sa'insa har ya dake ta"
Mansoor ya yi shuru bai yi mgana ba, yana ji Inna Meri ta cigaba da ba sa labarin yadda akayi jin ta kawai ya ke yi hankalinsa na wani wajen kuma.
Walida ya ke hangowa ta cikin uwar ɗakin Inna Meri ta na karatu sai dai baisan me ta ke karantawa ba. Ya buɗe baki zai kwala mata kira kenan Inna ta riga sa, tana fitowa ta kalleta tana faɗin"Ke mara wayau baki kawo ma yayan naku ko ruwa ba?
Da sauri Ya ce"Ba na jin kishi Inna".
Kallonsa ta yi kafin Ta ce"To abinci fa?
Kai tsaye Ya ce"Inna zan ci tuwo ammh ba yanzu ba sai na kusa tafiya."
Daga haka ta girgiza kanta kafin ta ce"Shike nan kun dawo oafiya ko? Ina fatan an samu nasara? Cikin sakin fuska ya ce"Lafiya lau Innarmu, an samu nasara in sha Allahu."
Nan Inna ta cigaba da kwararo addu'o'i yana amsa mata da Amin Amin. Walida kuma tsalle ta buga tana faɗin.
"Yayanmu kun ci ƴan kano kenan? eyye na ji daɗi daman yau a makaranta ana ta labarin ƙwallon da aka buga tsakaninku da yan kanon"
Kallonta ya yi lokaci ɗaya yana hararanta kafin ya ce"Ke ba karatu ki ka je yi makaranta ba labarin kwallo yake kai ki kenan ko?
Ta na jin haka ta yi sum sum ta wuce ciki Inna Meri ta ce"A'a ƙyalemin Auta, ita ke bani labaran ƙwallon naku ni kasan ba gane abun na ke yi ba, ranar ma a tibi ta ga an nuno wasu ta ce min Innarmu wata rana za ki kalli Baban Inna acikin tibin na ce Allah ya nuna mana."
Yana Mirmishi ya amsa ma ta da Amin.
Hira suka cigaba da yi Inna Meri na faɗa msa ta yi waya da mutanen mallam Sidi sun ce ya ji ma bai je ba Goggonsa yalwa har ta yi rashin lafiya kwanaki.
Yana duba agogon fatan da ke hannunsa ya ce"Zan je Inna ba na samun zama ne, ammh zuwa karshen watannan zan ga abin da Allah zai yi."
Inna Meri ta ce"Ya dai kamata ko ba ka kwana ba, Mu'azzam yafi ka son zumunci yanzu haka duk zuwan da zai yi garin nan sai ya leka wajen yan'uwan mahaifiyarsa ya gaishesu ka ga hakan ai yafi da ace mutum kwata kwata baya zuwa." Kai tsaye ya ce" Hakane Inna zan kokarta in sha Allahu."
Wayarsa a ka kira yana ganin Coach ne ke kiransa ya ɗaga suka gaisa nan ya ke faɗa masa gobe da safe suna da morning Training, da kai ya amsa mishi sannan ya sauke wayar dai dai ookacin da ya ji gudu da dariyan yara daga koridon shigowa shashen inna Meri kafin ya yi mgana ya ji Inna na faɗin"To ga shugabanin yan kiriniya nan sun dawo." Kafin ma ya samu zarafin mganar sun faɗo ɗakin da gudu sauran kaɗan su ture Mansoor dake zaune.
Sai da ya daka musu tsawa sannan suka fahimci yana ɗakin.
Sai suka natsu sum sum suka koma bayan inna Meri suka tsaya suna fiki fiki da ido kamar za su yi kuka.
Inna Meri ta juya ta kallesu kamar tayi dariya sai kuma ba ta yi ba.
Ta jawo Hassan jikinta shi kuma Hussaini ya lafe a bayanta.
Cikin sigar lallashi ta ce"To sojojin Inna ba ku gai da kawun ku ba."
Daga jikinta suka hadɗa baki wajen faɗin.
"Kawu ina yini."
Kai tsaye ya ce"Barka da dare ake cewa ina yini ba gaisuwa ba ce kun ji ko?
A tare suka ɗaga masa kai, yan biyu ne masu tsananin kama da juna.
Inna Meri ya kallah kafin ya ce"Daga ina suke Inna? kuma wa ya kawo su?
Inna Meri ta mikar da Hassan ta na ce musu su shiga ciki wajen uwarsu Walida, sum sum suka wuce suna tafe suna taɓa juna ba Halin su yi mugun wasa yanzu kawun su ya za ne musu jiki su san Halinsa ai tunda a ɗakin Inna Meri suka yi yaye, bai damu da kankantarsu a lokacin ba, da sun fara ma Inna kukan banza in da
All Chapters
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 2 Chapter of 26