Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
KOSHI MUNA DA MAGUNGUNA DA ZUMA 3 IN 1 KIBA BRST HIPS TA CIKO MIKI KU INA KIYI FRESH MUNA DA KWAYOYI MUNA DA GARI DUK MASU CIKO JIKI NE KIYI DUM INA MASU FAMA DA MATSALA BRST KU TSUHU YAFI SON YAGA NONO A TSAYE DUK MAI MAGANIN DA TACCE MIKI ZATA BAKI MAGANIN NONO KAI TSAYE YAYI MIKI KARYA CE MAGANIN BRST SAI KIN SHA ADADIN WANDA ZAI MIKI SBD DUK CIKIN GYARAN JIKI NA BRST YAFI WAHALA YI INA MASU FAMA DA MATSALA SANYI MUNA DA MAGANIN SANYI ORIGINAL INA MASU ZAMAN BANZA BABU SANA'A KINA KONE DATA KI GA BANZA WURIN TSEGUMIN KALLON STATUS DIN WASU GA DAMA TAZU MUNA HAR GIDA GA WAYAR HANNUN KI KI MALLAKE MOTA MILLION 8 HAR FIYE GA ALBASHI GA RIBA GA KYAUTA KAYAYA KI 08066726866. Follow this link to join my WhatsApp group: https://chat.whatsapp.com/JMpd8nXr7TIDD3ILDXh64z *Page 5* _Monday 5rd March, 2022. Gidan Talabijin na Karamchi_ *10:04am* A shashin al'amuran labarai na yau da kullum na gidan talabijin mai tashe a jihar gombe. Wani shashi ne mai girma a gidan talabijin ɗin mai ɗauke da babban falo tare da ofisoshin manyan ma'aikatan bangaren. Irin su news manager, editer da sauran su shi kuma babban falo mai ɗauke da kowani rukuni kamar an ƙawayanta ma kowa bangaransa ne. Kowa kuma akwai ƙaramin teburinsa da kayansa a kai sai kujeran inda kake da muhallin ijiye komai naka, daga gefe akwai ɗan aninin da ke nuni da  sunan mai wajen. Daga can kusa da office ɗin new manager wajen zaman Broadcaster ɗin gidan talabijin ɗin ne, daga gaba can kuma waje zaman camera man tare da reporters ne, da kuma ɗalibai masu sanin makaman aiki wato yan Intern.   Dole bayan sun haɗa rahottnni da kuma labarai wato bayan camera man da reporter sun gama aikin su kenan akwai bukatar editer ya duba ya kuma ta ce sahihancin labarin. Bayan ya gama dubawa kuma sai news manager ya duba ya cire kalmar da ya ga ba ta dace ba, dole dai sai an bi matakai kafin labarai ya kai ma masu kallo ko masu saurare. Kuma abuin da mutane wasu ba su sani ba, labaran da ake karanta su a gidan talabijin live ne, ko da an mai maitashi to sake karan tashi aka yi ba recording ba ne. Sannan broadcaster zai iya zama reporter, amma ba kowani reporter ke iya zama Broadcaster ba, kamar yadda Salim Bunza ya kasance a gidan talabijin na karamchi Reporter ne, sannan kuma shi ɗin Broadcaster ne.    Mimi ce kaɗai ce ta kasance Broadcaster kaɗai kuma a tsarin gidan talabijin ɗin su biyu ne Broadcaster ɗin Kowani na karanta oabarai sau hakwai a sati tunda kwanaki bakwai sai tsarin ya kasance kowa ya na yin adadin rabin kwanakin da zai kasance a sati. Tun da safe da yammah ne,  su ma suna shan wahala kwarai tunda suna da tsare tsare kafin ma a fara ɗaukan labaran live a haska ma mai kallo. A kwai bukatar camera man tare da masu makeup tunda abu ne da duniya zata ri ƙa kallo a matsayin majigin gani da ido akwai bukatar gyara ga mai karanta labaran.   A can baya kafin Mimi ta fara aiki da su wata Cindera ce ta yi aiki da su yar Lagos ce, komawa ta yi garin su ya sa ta saki aiki da Karamchi a tsarin su,  suke ba da kayan sawa in da zaka karanta labarai amma zuwan Mimi ta ruguza wannan tsarin ta ce ita da kayanta zata rika amfani tunda kuma yar ma su da shi ne daga ganinta kasan ba tsiya a jikinta kuma ta na da kyau ga iya ɗaukan wakan da kwalliya sai suka amince da tsarinta.   Abu ɗaya ake yi mata kafin a fara ɗaukan live shine makeup man ya gyara mata fuskarta ya ɗan kara mata hoda shikenan. Duk da ba ta daɗe da fara aiki da su ba ta zama tauraruwa a gidan talabijin Karamchi saboda fuskar Mimi, ta kasance mace mai fara'a da farinjini manyan mutane sun sha kawo ziyara suna mai ya ba mata. Sannan ga zaƙin murya ga turanci da ya zauna a bakinta, wanda in ta juya harshe sai ka rantse bata taɓa jin yaren hausa ba.   Daga office ɗin editor ta fito zuwa mazauninta in da ƙaramin oaptop ɗin ta ya ke da sauran tarkacenta ta ja Kujera ta zauna ita kaɗai ce a bangaren sai daga nesa kuma sauran reporters ɗinsu ne ke nuna ma ƴan inten wasu abubuwan. Salim Bunza sai dare ya ke da karanta labarai bai riga ya shigo ba tukunnah. Sanye ta ke da doguwar rigar atamfa mai adon zanen golding a jikinta ta sanya mayafinta mai raga raga a saman wuyanta da ya ji sarka mai kyau da yarari, hannunta sanye da zabbunanta na zinare guda biyu kafarta sanye cikin wani bakin Booth ɗin takalmi kalan na mata. Saukakkiyar kwaliya ce a saman fuskarta amma kallo ɗaaya zaka yi mata kasan ko ba ta yi kwalliya ba ita ɗin mai kyau ce. Ta zauna kenan wata matashiya daga cikin ƴan inten ta zo kusa da ita cikin girmamawa lokaci ɗaya tana faɗin. "Barka da aiki Anty Mimi."   Ta juyo Cikin fara'a kafin ta ce"Yauwa Safina kina bukatar wani abu ne? Safina ta karisa kusa da ita tana nuna mata takardan hannunta lokaci ɗaya tana fadɗn"kan wannan ne, ina bukatar karin bayani." Cikin kwarwaarta kan abin da ta karanta ta fara mata bayani har sai da ta gamsu. Cikin jin daɗi ta ce"Na gode Sosai Anty Mimi"   Gyaɗa  mata kai ta yi cikin irin mirmishinta kafin ta ce"Kar dki damu aikina ne." Cikin jin daɗi  Safina ta wuce wajen ƴan'uwanta kamar daman ita su ke jira sai aka zagayeta ta fara kora musu bayanin da Mmi ta kora mata yanzu. Ta na kallonsu a cikin ranta tana jin wani iri, dama ita ce dama dama ace zata iya maida hannun agogo baya. Su ɗin ta san ba su da wata matsala a rayuwarsu ba kamar ita da ciwon dake ckin zuciyata yake taso mata ookaci bayan lokaci ya hanata sukuni ba.   Ajiyar zuciya ta sauke lokaci ɗaya  tana buɗe jakarta da ke kan desk ɗin dake  gabanta, ta dauko wayarta ta na latsa hasken wayar sai ta ga Missed call har guda uku da sauri ta ja ta duba, sai ta ga Mommy ce ta kirata bata gani ba. Da sauri ta yi kokarin nemanta sai ga kiran Mommy ya shigo kamar yadda ta yi mata saving acikin wayar. Da Sauri ta ɗaga kiran cikin fara'a kafin ta ce" Barrister Murjanatu Soron ɗinki" Mommy daga can bangaren Ta ce. "Na'am, Fatima kabir Dabo." Sai Mimi ta saki dariya kafin ta ce"Mommy mun ta shi lafiya?  ya Abi ya tashi? Annuri na bayyana a saman fuskarta Ita fa Mommy yar ba ruwanta ne.Sunan kowa da sunan uban shi take yi masa saving a wayarta har Korafi ta taɓa yi mata ita kuma ta ce sunan su ne cikakke ko suna kyamatar sunan ne? Mimi tace a'a Mommy ta ce to ba za ta sauya ma kowa ba, to ba ma su kaɗai ba kowa haka ta ke yi masa saving acikin wayarta. "Lafiya kalau muka ta shi, Habibi ne ma tun jiya ya(e ta kiran sunan ki shi ne nace bari na kira ki na faɗa miki.."   Mimi na dariya ta ce"Allah Sarki Abi Mommy ba shi wayar mu gaisa" Mommy ta mika ma Abi wayar dake kwance a kan gado sai dai ta saka masa filo ta kara masa daga bayansa kansa ya ɗan ta sa sama. Cikin yanayin Muryan sa da ta sha jinya ya ce"Mimin Abi." Da sauri Mimi ta ce"Na'am Abin Mimi ya jikin ka? Abi ya amsa mata da cewa yaji Sauki ya karishe da faɗin "Honey tana kula dani sosai na gode mata Allah ya yi mata albarka." Mimi ta amsa da Amin Amin. Sun gaisa cikin fara'a da tambayan aiki ta ce gata ma a wajen aiki. Cikin yanayin muryansa ya ce"Mimi ki yi hakuri da rayuwar nan kin ji ko? Mimi ta amsa da cewa" In sha Allahu Abi Allah ya baka Lafiya." Abi ya amsa mata da Amin kafin ya ce" yaushe za ki zo? Da sauri ta ce"Abi kana son ganina ne? Abi ya gyaɗa mata kai kafin ya ce"Eh ina son ganin ki, ki zo in kin samu dama." Mimi ta amsamai da faɗin" In sha Allahu Abi Allah ya kara maka lafiya da tsawon kwana." Ya amsa mata dai dai ookacin da Mommy ta shigo bedroom ɗin ɗauke da Mug a hannunta damn tana bashi wayar ta fita zuwa Kitchen.   Tana zuwa kusa da shi ta sauke mug ɗin hannunta saman Side drower ɗin gadon dai dai ya na miko mata wayar ta amsa ta na karawa a kunne ookaci ɗaya tana faɗin. " later lokacin karya wan Habibi ne." Mimi ta ce"Mommy sai an juma." Daga haka suka yanke kiran a lokaci ɗaya Mimi ta bi wayarta da kallo tana ɗan Mirmishi, Abi da Mommy kenan sai ta tuna shekaru a can baya in ran Abi ya ɓaci Murjanatu ya ke kiranta kai tsaye Honey sai lokaci bayan lokaci. Amman yanzu komai ya sauya tsarin rayuwar da komai shi ya sa rayuwar nan duk babu tabbas a cikinta. Yau fari ne gobe kuma baki, in yau ka ji daɗi gobe kuma akasin sa zaka shiga.   Tunani ta shiga yi, tunanin wani irin nema Abi yake yi mata, ko da yaushe tsakaninsu ban hakuri, ita kuma har acikin ranta ba ta taɓa rike Abi acikin ranta ba komai ya yi mata shi uba ne kuma duk abinnda ya yi domin ya inganta rayuwarta ne, ba taɓa fushi da shi Saboda abijbda ya faru a baya ba, Tana kaunar Abi domin mahaifinta ya wuce sauran mahaifa ya kuma yi mata gatan duniya nan, abin da ya faru wani kaddaren al'amari ne daga Ubangiji da bawa bai isa ya kauce ma faruwarsa ba. Hankalinta ya yi nisa ba ta san Rukky ta shigo ba, sai kawai ji ta yi ta saita dai dai kunnenta  ta ƙwala mata kira.   "Mimii..!."   Firgigit ta yi gabanta na faɗuwa domin ta ji tsoro sai ta ci karo Rukky da ta na mata dariya cikin jin haushi Mimi ta ce"Rukky Why? Kin bani tsoro  ba ki ji yadda kirjina ke faɗuwa ba" Rukky na dariya ta zauna saman desk tana kallon Mimi kafin tace"Tunanin wa kike yi ne da ba ki san shigowa ta ba? Mimi ta lumshe ido kafin ta buɗe tana faɗin" Me ya faru? Domin daga ganin bakin ki akwai mgana." Rukky ta ce"Maganar dai da muka fara ta waya, ki zo mu tattauna yadda zamu shirya bikin Bibi."   Mimi ta kalleta a karkace kafin ta ce"Saboda ita Bibi ba ta da ƙawaye? mu fa yayye ne Baby ina ruwan mu da tsara biki wannan ai sai ƙawayenta." Rukky ta ce" Bibi ta ce mu tsara komai kinsan fa ba ta da wasu kawaye, sai wasu yan makarantar su kuma kinsan yadda zamu tsara al'amarin ba kamar su ba." Mimi ta yi shuru kafin ta kara mgana Rukky ta shagwabe fuska ta na faɗin" Haba mana Hajiya Mimi ta."   Mirmishi ta yi kafin tace"Yaudara! Zan shigo gidan sai mu yi mgana." Rukky tace" Yauwa ko ke fa? yaushe to za ki shigo ? Ko yau kawai ki jirani na tashi sai mu tafi tare." Mimi ta taɓe baki kafin tace"Yau daga nan ina komawa gida zan dauki Hajiya mu je gidan Daddy kinsan Mama ta kwanta asibiti jiya aka sallamo ta sau ɗaya naje na duba ta shi ne yau zan kai Hajiya mu kara dubata." Rukky ta jinjina kai kafin tace"Shike nan Allah ya ba ta lafiya." Nan suka cigaba da hiran su Rukky na faɗa mata yadda za su tsara Bikin ya yi kyau sosai. Mimi na dariya tac e"Kina ta tsare tsare Baby, shin angon nan zai fitar da kudaɗe ne masu yawa ya baki? Rukky tace"Ba ma dolen shi ba, ai na yi mgana da shi yace ba matsala akwai abokansa da suke tunanin ɗaukan nauyin yin dinner, mu dai nan kamu kaɗai Ummi tace zata ɗauki nauyi." Mimi ta gyaɗa kafin ta ce"Good! Allah ya nuna mana ookacin da rai da lafiya."   Rukky ta jima har sai da aka kira wayarta sannan ta bar wajen Itama Mimi bata jima ba ta kwashi tarkacenta ta shiga office ɗin manajansu ta kai masa takardun hannunta suka yi mganar da za su yi ta ce mai ita ta tashi sai gobe da yammah tunda sai karfe bakwai din gobe take da karanta labarai amman zata shigo zuwa la'asar. Daga nan ta fito ta yi sallama da sauran ma'aikantan bangaren su. Ta fita zuwa babban falon da ke ma'aikan ana mata mgana ta na amsawa da sakin fuska. Na Misau ta hanga yana ta hira da wani ɗan siyasa acikin shirin Nageria a siyan ce. Daga masa hannu ta yi ta cikin gilashin da ya raba wajen shi kuma sai ya jinjina mata kai. Ko bangaren su Rukky ba ta biya ta fita zuwa haraban wajen ta kunna motarta bayan ta ijiye jakarta a kujeran mai zaman banza ta zagaya ta shiga bangaren direba ta zauna da bismillah a bakinta. Sannan ta yi ma motar key ta juya ta fice daga gidan talabijin ɗin megadi na faɗin a sauka lafiya Hajiya." Itama sai ta ɗaga masa hannu cikin fara'an da ke saman fuskarta. Bata da chanji ne acikin jakarta sai dai gobe in ta dawo. Mimi mai kyauta ce abun hannunta baya rufe mata ido in tana da shi ta ba ka in bata da shi ta ba ka hakuri.   Gida ta koma ta iske Hajiya ta yi barci sai Baaba Uwani kaɗai a gida tana ta zirga zirga sannu da gida ta yi mata sannan itama ta shige cikin ɗakinta. Kaya ta sauya zuwa masu sauki na gida sannan ta haye gado ta kwanta ta na motsa jikinta domin tana jin jikinta duk gajiya ya saukar mata. Har ta kwanta sai kuma ta mike ta isa kan Dressing mirror ɗin da ke ɗakin ta buɗe jakarta ookaci ɗaya ta ciro wayarta ta koma ta kwanta. Faceebook ta shiga ta sauya Account ɗin ta na Asali na Fatima Kabir sulaimam Dabo(Mimi).Zuwa wanda ta buɗe na sirri da suna MIAJ Kuma account ɗin  bai da suna ko wani bayanan da za'a iya gane ko wani jinsi ne. Da ɓoyayyen account take bibiyan Aji kuma da shi ne ta tura masa friend request tun shekaru huɗu da suka gabata kuma ya karɓeta sannan tana following ɗin GOMBE UNITED nan t ke ganin wasu abubuwan   Tun da shi ba chart yake yi ba, ta sha masa sallama bai taɓa buɗewa ba ballantana ya amsa ta ba, sai dai ta na bibiyan shi ta hanyar club  ɗin sa. A nan ne ma ta samu hoton sa da ta kai aka yi ma babban elegerment, anan take ganin in suna da wasa da garin da suka je anan kuma take ganin irin cigaban da ya samu bayan rabuwar su. Ba za ta taɓa manta lokacin tana Kano tana Master ɗinta ba , ta taɓa haɗuwa da ɗaya daga cikin abokansa mai suna Nasir. A bakin shi ta fara jin Aji yanzu ƙwallo yake yi, ta daɗe ta na mamaki sai da ta gani sannan ta tabbatar. Shiga ta rika yi hotunan da Club ke ɗorawa yawanci na yan wasan su ne, har akwai hoton da aka ɗauka da Aji tare da Coach ɗin su ookacin da ya yi singing contract  da su.   A nan take samun ganin rabin ranta ta kuma kalle shi son ranta, komai nashi na nan a yadda ta san shi sai dai yanzu ya rage fara'a sannan fuskar nan a kimtse kamar wanda ke cikin bacin rai, ya kara dai girma tunda shekaru sun ja, wani hoto da ya yi mata kyau sai da ta ɗauke shi. A Studion  ne aka ɗauki hoton yana sanye a blue din kayan kwallo a jikinsa ya duka kamar zai taso daga sujjuda zufa duk ya cika fuskarsa a wannan hoton ta ga dariyan shi. Har ga fararen hakoransa nan sun bayyana. Kamar kuma a wani gari ne da suka je kwallo, sai da ta duba rubutun ƙasan Hoton ta ga an saka. Kaduna da date din sannan an Rubuta Captain Aji baka dariya sai ka kada masu gida. Itama sai da ta murmmusa a sanin da ta masa a baya yana dariya. Sai dai ta san masifaffe ne, abu kaɗaan sai ya harzuƙa sa ya fara masifa. Ga zuciya da kafiya in ya kafe akan abu baya sauya ra'ayi. Tana kai hoton da ta ɗauka wajen da take adana hotunan sirinta ta furta a fili" Ko yanzu ya daina faɗa? Ko wasu hallayansa ne suka sauya bayan mun rabu?   Sai ta kasa ba ma kanta wannan amsar, sai kawai ta kashe data,  ta sauka daga kan Account din ta kashe wayarta ta sauke a gefenta ta koma ta kwanta tana sauke numfashi. Ya jima ta na ta tunane tunane kafin barci ya kwasheta. Ba ta tashi ba sai da Hajiya ta shigo tana buga mata kafa da cewa an yi azahar. Sannan ta iya tashi a kasalance ta shiga tiolet tayi alwala ta zo ta yi sallah sannan ta fita fallo ta iske Baaba Uwani da Hajiya suna hira. Kirchen ta nufa tana faɗin "Baaba me kika girka mana yau? Baaba Uwani ta ce"Alala Hajiya ta ce tana jin ci yau, shi na yi." Mimi ta daka yar tsalle kafin ta ce"Kai Hajiyata Allah ya saka ki a gidan Aljannah, kamar kin shiga raina daman na ce sai weekend na zauna nayi Alala na kwana biyu ban ci ba." Ta faɗa tana shiga kitchen ɗin cikin farinciki.   Hajiya na mirmishi ta ce"Daman nasan kina so, rashin samun zama ya sa ba ki yi mana mun ci ba, da Uwani take tambayata abin da za a dafa na ce ta yi mana Alala kawai." Ta na jin maganar Hajiya daga cikin madafin , miyanta har tsinkewa yake yi sanda ta ga alalan gwangwani da manja. filet ta samu ta zubo guda huɗu ta saka yaji kaɗan mai daɗi da Yaddiko da aiko ma da Hajiya ta kuma tsiyayi soyayyan manja a gefe. Ko da ta fito falo mirmishi kawai take yi cikinta na wani yamutsawa.   Gefe ta samu ta zauna kan cafet ta yi bismillah ta fara ci loma daya biyu ta ɗago tana kallon Hajiya dake kallonta kafin ta ce"Hajiya ke ba za ki ci ba ne? Hajiya na yar dariya ta ce"Sai ya sha iska zan ci kar na ci da zafi ya lalatamin ciki." Mimi ta ce"Hmm hajiya da zafi ya fi daɗi." Baaba Uwani ta saka dariya tana faɗin" Binta ko na saka waigi ne? Mimi ta jinjina kai kafin ta ce"Baaba na manta kafin ki saka waigin haɗomin da ruwa wayyo daɗi Hajiya." Ta ke faɗa tana cin alalanta tana santi Hajiya da Baaba Uwani na yi mata dariya. Baaba Uwani ta tashi ta ɗauko mata ruwa mai sanyi da kofi ta kawo mata. Mimi na ta buga santi suna ta mata dariya tas ta Cinye ta sha ruwa kafin ta ce"Baaba Uwani Allah ya yi albarka ya sa a gama da duniya lafiya."   Baaba Uwani na dariya ta ce"Amin Binta." ta mike ɗauke da filet ɗin hannunta tana faɗin"Baaba Uwani cikin Albashina  na wannan watan kina da dubu goma cash tukwaicin Bintan Hajiya ne." Baaba Uwani ta ɗaga hanci ta rangaɗa guɗa kafin ta ce"Ina godiya uwar ɗakina Allah ya saka da alheri Allah ya tsare gaban ki da bayan ki Allah ya rabaki da sharrin makiya da mahassada, Allah kuma ya bama  babanki lafiya." Mimi na gabda shiga madafi ta ce"Amin Amin Baaba Uwani da kika yi min addu'an  Allah ya ba ma Abi lafiya kamar na ce na ƙara miki wata duban goman"" Ta faɗa ta na yar dariya Baaba Uwani ta kara karkacewa ta yanka wata guɗaa kafin ta ce"Gaba salamun baya salamun yar lelen Hajiya da ba kamarta  Allah ya kara arziki da wadata Na gode kwarai" Hajiya na gefe da cashaba a hannunta tana ja cikin mirmishi ta ce"Da kin kara da addu'an Allah ya kawo ranar auran Binta da wuri wuri da na cike miki kudin sun zama dubu hamsim"Baaba Uwani na jin haka ta yi zaman dirshan gaban Hajiya tana faɗin"Allahu Akbar Uwar marayu, kin goya na gida kin goya bare, ai ban gama addu'an ba, tana tafe Allah ya nuna mana auran Binta Allah ya bata miji nagari kyakyawan kamarta mai kyan hali da mutumci kamar ita.." Hajiya na dariya ta ce"duk da kin makara na dai ƙara miki dubu goma." Baaba Uwani ta ɗaaga hannu alamun jinjina kafin ta ce"Allah ya kara nisan kwana Hajiya, Allah yasa ki dade a duniya kina goya marayu irin mu." Hajiya ta ce"Uwani ai duk sona da duniya sai na mutu na barta ballantana ai bazan iya rama shekaruna na baya a duniya ba, ke dai Allah yasa mu cika da kyau da Imani." Uwani ta amsa mata da Amin Mimi ta fito ta na taɓa cikinta lokaci daya tana faɗin. " Hajiya mu bar tafiyar mu gidan Daddy sai anjuma lokacin cikina ya sassaɓe" Hajiya ta kaɗa kai kafin ta ce"Daman ai sai rana ta yi sanyi." Baaba uwani na gefe ta ce"Hajiya nima ina son zuwa na duba mai jikin." Hajiya ta ce"Ba matsala duk sai mu tafi tare. tashi ki zubomin alala ya kara wucewa kafin na gama lazimi." Baaba Uwani ta mike ta na faɗin "Angama Uwar marayu." Mimi kuma dakin Hajiya ta shige ta je ta kunna talabijin. Tunda bayan falo akwai wani talabijin ɗin a ɗakin Hajiya. Mbc Bollywood ta saka sai ta ga a wani Film ɗin da ta ke matukar so mai suna HIKCHI FiLM ɗin Rani murkarji ne.  Cikin jin daɗi  ta gyara zama ta cigaba da kallo.   Ba su samu tafiya gidan Daddy ba sai bayan la'asar, gidansa na anguwan Abubakar Habu Hashidu Estate ne, Hajiya na gidan gaba Mimi na driving Baaba uwani na gidan Baya. Sanda suka je gidan sun iske Jaheed ya zo garin tunda mahaifiyarsa ce Mama sai Amaryanta da suke kira da Anty. Gidan Alhaji Hamza Sulaiman Dabo gida ne na rayuwar yan boko, kowa kuma abin da ya ga dama shi yake yi shi ba mutum ba ne mai zama ɗan siyasa mai jama'a, kuma ba shi da takura da matsawa rayuwar boko zallah kawai iyalansa ke gudanarwa. Ko da suka shiga ɗakin Mama Jaheed suka iske kwance kusa da Maman kamar zai koma cikin cikinta. Ga kanwarta nan a cikin ɗaakin amman bai saka shi ya fita ba. Ya juya yana ta magana a waya sai da yabji mganar Mimi da Hajiya ne ya yanke wayar da ya ke yi ya juyo ya na sakin Mirmishi ya ce"   "Hajiyata Amaryata."   Hajiya ta balla masa harara tana faɗin"Ni ai ba na mijin da kai, tafi can soloɓiyo kullun kwance ɗakin uwa kamar wani jariri, ke Hansa'u hala nono kike ba shi ne? Gabaɗayan su ka fashe da dariya shi kuma sai ya hau shafa kansa. Mama ta ba ma Hajiya wajen zama na saman kujera guda ɗaya da ke cikin bedroom ɗin ta. Kanwarta mai suna Hajiya Turai ta kada baki ta ce"Ai Jaheed jin sa ya ke kamar Yaya bata yaye shi ba." Mama ta yi dariya ba ta yi mgana ba, saboda ita macece mai kaunar ya'yanta haka zaka ga ko masu auran in suka zo Jikiko su hau jikinta iyayensu su kwanto kan Jikinta. Ita Anty ma ba ta taɓa haihuwa ba sai dai suna zaune lafiya sai dai kishi na halitta.   Bayan an gaisa da yambayan jki Mama ta ce ta samu sauki, Hajiya ta ce"Sannu! Allah ya kara lafiya.' Ta amsa da Amin Jaheed kuma kusa da Mimi ya koma ya zauna kamar zai shige jikinta ta yi saurin matsawa kusa da Hajiya Turai daman a gefen gadon ta zauna a kusa da ita. A cikin kunnenta ya yi mata raɗa" Me na yi miki ba ki ɗaukan wayata? Mimi ta kalleshi ta na masa inkiya da su Mama sai kawai ya ɗaga murya yana faɗin" Mama ga Mmin ba kin ce za ki yi mata mgana ba? Mama ni fa Mimi ta ce ba ta sona me na rasa mene ne bazan yi mata ba in mu ka yi aure?   Ya faɗa cikin yar shagwaɓa Mimi kunya ya kamata sai ta yi saurin tashi, Mama kuma idon Hajiya ya sa ba ta yi magana ba sai Hajiya Turai ce

Chapter 7 of 26