akwai masu lecture ɗin yamma dan haka sai sun jira su zasu haɗu su tafi gida gaba ɗayan su, suna daf da shiga gurin suka hango wata yarin daga can gefe ta kifa kai tana ta kuka, da ɗan tazara tsakanin su amma ba sosai ba suna sai iya jiyo sautin kukan ta, duk tsayawa sukayi tare da kallon junan su. sai kawai suka wuce basu ce komai, har suka shiga sukayi order ɗin abun da suke son ci sannan sukaci agun sun ma daɗe suna ƴar hirar su sama sama dan a ƙalla sunkai kusan minti ashirin a gun, kafin Beenish ta kalli agogon dake hannun ta ta miƙe da sauri tace kai Aunty Babba wlh munyi late muyi sauri Allah yasa SIR SURAJ bai shiga ba, kar ya hana mu shiga.
Da sauri duk suka miƙe duk da ba dukan sune zasuyi attending ɗin ba amma atare suka baro wajen har suna ɗan haɗawa da sauri,
Suna fitowa garin sauri suka ci karo da wata yarinya da sauri taja da baya mutyar ta cikin kuka tace dan Allah kuyi haƙuri ban kula ba kanta a ƙasa tayi maganar kamar zata kuma fashewa da sabon kuka, bata jira cewar su na tayi sauri ta bi gefen su, tana shigewa ta kuma fashewa da kuka tana toshe bakin ta dan bata so sautin ya fito,
A kusan tare suka juya suna bin bayan ta da kallo, duk sun kasa ɗauke idon su akan ta.
'Aunty Babba ce tace; "ku wallahi wataran ku kuke jawa kanku raini da shishshiginku yanzu me ya shafe ku a ciki idan ita da mahaifin ta ne fa ko kuma saurayi ko mahaifiya ku zakuzo kuji kunya,
Beenish ce tace ;Aunty Babba..! ta kira sunan ta cikin wata irin murya me kama da fara ta jin haushi, "Wannan wace irin magana ce ita ma mace idan kuma abun da kike zargi ba haka bane idan ma hakane shi mahaifin nata me yasa zai musguna matan da har zata fito waje da baƙin ciki Allah yabasa amanar ta bawai dan ya musgunawa ƴar sa, kinsan duk abun da iyaye zasuyiwa ƴaƴan su da har ya wuce suyi musu hukuncin da zasuyi shi a cikin gida wannan ba daidai bane, domin su ƴaƴa da kike gani amana ce da Allah ya bawa iyaye amma wasu iyayen basa aiki da hakan dan Allah banason kina sawa ranki irin waɗannan tunanin, yanzu da ɗaya daga cikin mu kika gani zakiyi tunanin wani abu, nasan zuwa kawai zakiyi kiyi ƙoƙarin jin damuwar sa, to yanzu ma ki ƙadarta ɗaya daga cikin mune kije kiji damuwar ta damuwar ɗan uwa musulmi damuwar kace domin duk daga abu ɗaya muka fito, kar muga ɗan uwan mu cikin damuwa muyi tunanin ai damuwar sa damuwar sa, yazama dole musa a ranmu taimakon duk wanda muka gani cikin wani hali na damuwa muyi ƙoƙari iya bakin iyawar mu ganin muntayashi warware masa inda hali musanya shi cikin farin ciki, bawai sai abun da ya shafe mu ba indai akan wannan fanninne idan ka taimaki wani kai kuma Allah zai ta make ka ne a duk inda kake kusa wannan aranku ba da ita kaɗai nake ba da gaba ɗayan mu nake.
Jikin Aunty Babba ne yayi sanyi dan tasan gaskiya ta faɗa mata yanzu da ace ɗaya me yake cikin wannan halin har yake fitar da kuka irin wannan da kana ji kasan ba ƙaramar damuwa mutum yake ciki ba, da a cikin sune sai inda ƙarfin ta yaƙare,
Ameela ce tace; maganar ki gaskiya ne Beenish musamman ma irin natannan ki duba fa kigani tun kan mushiga yake kuka kuma har yanzu bata gama ba wayasan ma tun loƙacin da ta farayi.
Allah sarki wallahi nima taban tausayi yaya kinga yanda idon ta yayi ja, cewar Babyn baby.
Zee tace ba tsayawa zamuyi muna kace nace ba, muje gashi kuma ku zaku shiga lecture kuje mu bari muje wajen ta ni da Ameela,
"A'a ku muje tare kawai, babu komai, cewar Beenish,
A tare suka jera suka koma cikin restaurant, hangen idan zasu ganta suka fara, can suka hango ta kuma kifa kanta akan table ɗin ga abinci a gaban ta da tasa aka kawo mata kuma ba iya ci zatai ba,
Da ɗan saurin su suka ƙarasa inda take duk zagaye ta sukayi suna kallon ta na ƴan sakanni, Beenish ce ta jawo kujera ta zauna daf da ita.
"Assalamu alaiki, Ƙawata...
A hankali ƴar matashiyar budurwar ta ɗago da jajayen idon da kumatun ta da suka kukkumbura kallo ɗaya zakai mata kagane ba ƙaramin kuka ta sha ba,
Tana ɗagowa zata buɗi baki kenan Beenish ta toshe mata bakin ta, tana girgiza mata kai alamar kar tayi magana, sannan ta sa hannu ta fara goge mata hawayen da ya gama wanke mata fuska, abincin da ta jawo sai ta fara zuba mata ruwa da kanta ta bata, ba musu yarinyar ta karɓa dan tana buƙatar ruwan amma takasa sha da kanta,
Tana gama shan ruwan ta buɗe plate ɗin abincin priderice sai cabage da aka ɗan zuba a gefe, spoon ɗin ta ɗauka tafara bata a baki da farko haka tace bazata ci ba, saida taga ta haɗe rai sannan karɓa, bata daina bata ba saida taga taci sosai har yafi rabi sannan ta kuma bata ruwa ta sha da kanta,
Har yanzu babu wanda yayi mata magana, saida Beenish ta tabbatar ta ɗan samu nutsuwa sannan ta miƙe tare da dafa kafaɗunta ta ɗago ta tsaye.
"Muje koh.., ta kalli sauran tana kamo hannun yarinyar, jale jale yarinyar ta shiga binta, abun mamaki takasa tanka musu da komai bare tayi musu taurin kai ko ta tambaye su ina zasu, kawai ta bisu, amma har yanzu bata bar sauke ajiyar zuciya ba,
Can wani waje suka nufa da ba mutane, sannan ta zaunar da ita ta zauna agefen ta, suma sauran duk zama sukayi, amma gurin bai ishe su ba, Babyn baby da Barazana a tsaye suka tsaya,
Cikin muryar rarrashi Beenish tace; in badamuwa zamu iya jin damuwar ki, me yasa ki kuka haka,
Take hawaye ya ƙara cicciko mata idon.
"No don't cry my dear, ni fa tambayar ki kawai nayi, ki faɗan kawai in Allah ya yarda zamuyi ƙoƙari gurin share miki wannan hawayen,
Shiru tayi ta kasa cewa komai dan tana tsoron faɗa musu tazo ta ƙara jefa kanta cikin damuwar da tafi wacce take ciki,
"A gida akayi miki, wani abun. Zee ta tambaye ta,
Girgiza kai tayi alamun "a'a"
"Saurayi, ƙawa, ƴan uwa, maƙota, waye daga ciki yasaki zubar da hawaye.
A hankali ta girgiza kai ƴar ƙaramar Muryar ta tace; babu ko ɗaya ta faɗa cikin sanyi jiki.
"Kinga look at me, give me your attention.
Kamar yanda Beenish tace haka tayi ta haɗa hankalin ta guri ɗaya, tana fuskantar ta da kyau,
"Yauwa my lovely sister, ina so kisa aranki zamu magance miki matsalar matuƙar bata fi ƙarfin mu ba, kar kiji tsoro duk wanda yake neman shiga rayuwar ki ki gaya mana, zamu tsaya miki, in kuma matsalar kuɗi ce ki faɗa mana nawa kike so, kar kiji komai nan duk ƴan uwan ki ne da yayyan ki da ƙannen ki, ki ɗauka duk ciki ɗaya muka fito kigaya mana damuwar ki baza mu taɓa cutar dake ba.
Hawayen da take riƙewa ne ya ƙarasa sauko mata, tayi saurin saka hannu ta share, sosai taji zuciyar ta tayi mata sanyi ko basu magance mata damuwar ta ba, tasan ta haɗu da waɗanda suka damu da damuwar ta,
Nagode da kulawar ku, ina cikin babbar matsala amma bana tunanin zaku iya magance min ita amma duk da haka zan faɗa muku, saidai kuyi min alƙawari baza kubari maganar nan ta fita ba, domin zaku ƙara jawo min wani bala'in dan Allah ku rufa min asiri kar ku faɗawa kowa wannan yazama sirri tsakanina daku kumin alƙawari.
"Hmmm gaskiya bazamuyi miki alƙawari ba saboda bamu san abun da zaki faɗa ba, zamu iya jure ko baza mu iya ba, kawai dai ki faɗa ai munsan daidai kuma bazamuyi abun da zai sa ki ƙara cutuwa ba.
Ɗagowa tayi tana kallon Barazana dake mata wannan maganar. Zuciyar ta sai raya mata take ta faɗa musu ko karta faɗa musu,
Hannun ta Beenish ta kamo tasaka cikin nata, tun kan tayi magana ma yarinyar tace; wani lectura ne a makarantar nan ya takurawa rayuwa ta sau uku yana dawo dani baya kuma yana sawa ina ta ƙara asarar kuɗi kuma mahaifana bama su hali bane, yanzu kuma yace idan ban amince dashi ba sai yasa an kore ni daga makarantar gaba ɗaya duk shekarun da nayi a banza, kuma yace idan nasake na faɗa sai ya lalata min suna ya ɓatawa mahaifina suna, yanzu haka daga gurin sa nake ya matse ni da ƙyar na gudu da office ɗin sa, na rasa yanda zanyi dashi har gida yake bina, yai tayi min bazarana da rayuwa ta.... tana kawai nan ta fashe da kuka tana faɗawa jikin Beenish dake gefen ta,
Gaba ɗayan su ransu in yayi dubu to ya ɓaci ɗaya bayan ɗaya, Beenish kam har idon ta saida ya kaɗa yayi ja saboda tsabar ɓacin rai, Barazana kam jikin ta ɓari kawai yake, Aunty Babba andunƙule hannu jira kawai take ta ɗagasa ta sauke sa akan bil'adama, Ameela kuma sai faman cije baki take ta miƙe tsaye tana zagaye agun, Babyn baby kuka kawai ta fashe da shi tana dan ita lamarin tsoro ma yabata,
A hankali Beenish ta janye ta daga jikin ta, ga mamakin su sai kawai ta kwashe ta da mari tana miƙewa tsaye, kowa saida ya saki baki yana kallon ta, dan basu taɓa kawo haka ba,
Da yatsa ta nunata cikin tsananin jin haushi tace; "kinayin irin wannan rayuwar shine har kika tsaya kika kasa gayawa kowa, kin gwammace aci mutuncin ki da na iyayen ki akan tonuwar asiri wani ƙaton banzan shekara uku kina fama da ƙunci a zuciyar ki, baki sa uwa baki da uba babu hukuma babu shugaban makaranta babu na gaba dashi, zaki zauna kina gani zaki kashe kanki a banza, wannan wane irin shirme ni, shiɗin annabi ne da zakina tsoron sa har haka ya isa yayi miki abun da Allah bai miki, duk da tsoron sa da kike nuna masa ai bai fasa yi miki komai ba, kuma bazai fasa ba, tunda kin maida shi mala'ikan ki, me yasa zaki zaɓi mutuwar ki... Hannu ta kuma kaiwa zata jawo ta, Barazana ta riƙeta tace; "Haba Beenish calm down man yanzu sai ki ƙara rikitata ai,
Huci kawai take zuciyar ta na tafar fasa ta daka mata tsawa tace; "Waye shi ya sunan sa uban waye ubansa acikin garinan, wane ɗan akuyar ne haka, waye...!!!!!
Cikin matsanan cin tashin hankali yarinyar cikin kuka da kiɗimewa, tace; SIR SURAJ NE...!!!!!!✍️✍️
[3/5, 11:47 AM] Yaya Azeema: *💦SU WAYE SU...!?💦*
*_(Who are they...!?)_*
_💦Story and writing💦_
💎
*🌬️Yaya Azeema😎*
______________________________
*_episode 11💧_*
💧💦محمدالرسوالله...!💦💧
Bissmillah.....✍️
___Cikin matsanan cin tashin hankali yarinyar cikin kuka da kiɗimewa, tace; SIR SURAJ NE...!!!
Cike da ɗumbin mamaki gaba ɗayan su suka bita da ido, jin sunan wanda ta ambata yasa su mutuwar tsaye dan saida numfashin su yaso ɗaukewa na wucin gadi kafin daga bisani sukayi saurin dawowa hayyacin su, a kusan tare suka ƙara maimaita SIR SURAJ..!suka faɗi sunan sa cike da al'ajabi,
Ai basu tsaya ƙara jin komai ba daga haka, a kusan tare suka ɗau hanya saboda daman sun san inda yake, yarinyar kuka ta saka musu tana roƙonsu dan Allah kar suje amma idan ƙasa tana magana suma zasuyi mata magana, saboda ba wanda yake jin me take cewa, a haka tai ta binsu tana roƙon su, amma babu wanda ya tsaya bare ya saurare ta,
Inda suka san yana ciki suka shiga daman su Beenish shine zai musu lecture yanzu har garin sauri suka haɗu da yarinyar dan haka yanzu already ya riga da ya shiga, ko sallama babu suka shiga kansu tsaye, yarinyar ganin shi yasa tayi saurin juyawa baya, zata gudu, Barazana ta cafko ta, tare da dawo da ita baya,
Beenish ce ta fara shiga da farko baisan da shigowar su ba, saida yaga Beenish a gaban sa, cikin shouting yace mata "How dare you? Get out of here.!! cikin ɓacin rai da masifar sa da ya saba yiwa duk wanda yayi ƙoƙarin shigowa bayan ya shigo, bare kuma har ka shigo masa kai tsaye without his permission zakaga yanda zaiyi disgracing ɗin ka a gaban mutane,
"Stop shouting at her!
Juyowa yayi ya kalli Babyn baby da tayi masa magana cikin ɗaga murya itama, bai gama fita daga mamakin taba, saida yaga sun haɗu su dukan su a gaban sa, suna jefa masa wani irin mugun kallo me cike da tsantsar tsana, zaro ido yayi tare da jin wata mahaukaciyar bugawar zuciyar sa, ba komai ya haddasa masa jin hakan ba, sai inda idanun sa suka sauka akan yarinyar dake tsakiyar su, ba ƙarya bai taɓa jin faɗuwar gaba irin na yau ba, ya tsorata sosai dan ko na agaya masa ba yasan asirin sa ne zai tonu, rasa inda zaisa ransa yayi duk da bai bari tsoron yayi tasiri akan fuskar sa ba, yana dai danƙare a zuciyar sa fal, amma a fuska baza ka gane hakan ba saboda mazewar da yayi,
"Meye haɗin ka da wannan yarinyar?
Jin tambayar yayi bazata dan bai kawo haka ba, baisan kuma mai zai ce musu ba,
"Get out of here I said, don't let me repeat it again, ya faɗa yana nuna musu hanya da yatsan sa,
Ameela ce ta tako zuwa gaban sa daf da shi, tana masa kallon up and down, ta haɗe hannayen ta a ƙirjin ta tana binsa da kallo, a hankali tace; "If not? what u will do? Eh why not ka ɗauke mu ka fitar damu tunda sana'ar kace, ɗaukan ƴan mata ba komai bane agun ka, kai da kake nema ta ƙarfi da yaji, to ga banza ta samu gamu nan mu biyar ras ka zaɓi wacce tayi maka, idan kuma duka zaka haɗa ba matsala bazan ga laifin ka, tunda kai bunsuru ne, nasan uwarka ma ba ɗaga mata zakai ba bare kuma dan ya da ƙanwa sun kasance guri ɗaya kowacce ma binta zakayi....
Beenish ce tayi saurin karɓar ta da cewa; "Bunsuru ai ba ruwansa da tantancewa indai har yabi uwar sa da ƴar cikin sa wace ma bazai bi ba, nan da za'a haɗa masa mu gaba ɗaya munyi masa kaɗan.
Runtse idon sa yayi jin munanan maganganun da suke faɗa suna dangan tasa da ɗan akuya,
Beenish ce ta jawo hannun yarinyar ta matso da ita gaban sa, jikin ta sai kyarma yake ji take kamar zai kuma kamata da kokawa a gaban su,
Wani irin mugun tsanar yarinyar ce ta kamasa dan gani yake duk ita taja masa wannan abun, zuciya ce ta ɗebe sa kawai ya kwashe yarinya da mari, kafin ya ɗauke hannun sa Beenish ta kwashe shi da nata, tana ɗaukewa Ameela ta taro sa da nata ta ɗayan ɓarin, marika huɗu suka sauke masa idan wannan ya mare sa ta ɓarin dama sai wannan yayi masa ta ɓarin hagu, kan kace me fuskar sa tayi shatin sahun hannun su abunka da farar fata,hular kansa har saida ta faɗi ƙasa santalelen kansa da yasha ƙwalƙwal yana sheƙi,
Gaba ɗaya gurin miƙewa sukayi masu ɗaukar hoto nayi masu ɗaukar video nayi, wasu kuma suna tafawa suna yi musu sawa, wasu kuma abun bai musu daɗin kalla ba saboda basu san me ya aikata ba,
Kunaya ce ta kamasa yana kasa ɗagowa baisan wane irin mataki zai ɗauka akan su ba, dan tunda yazo dunayi babu wanda ya taɓa ci masa zarafi da mutunci irin na yau,
"Beenish ce ta sa hannu ta ɗago da fuskar sa, tace; "Dan Allah kar ka fasa abun da kakeyi ka ciga ba, kuma kar ka barta da rai daga yau kar ka bari ta kuma kwana ɗaya a duniyar nan, wallahi sai mun saka dangin ka gaba ɗaya cikin hatsari sai kayi na damar zuwan ka duniya, kuma daga yanzu babu kai babu a cikin makarantar ka rubuta ka ajiye ka gama aiki a duk wata jami'a tunda kai burin ka ka tozarta wani to wallahi kai zaka tozar bazamu taɓa ƙyale duk wani macuci dake zalintar mutane sai inda ƙarfin mu ya ƙare, wawa wanda baisan ciwon kansa ba, kalle ka kamar mutumin kirki nan kwa jahilci ne ke ɗawainiya dakai, kana tunanin duk abun da kayi kasha banza,
Wata mahaukaciyar dariya ya saki kai bakace shine ya shiga wani yanayi ba yanzu, zagaye su ya fara yi yana cewa; kunyi babban kuskure jakar ƙwaƙwalwar ku ta tsara muku shirme, su waye ku da har kuka isa kusa inrasa aiki na, kunsan hukuncin da akeyiwa duk wanda yayiwa lectura rashin kunya ma bare har yasaka hannu ya dake sa, a yau zaku bar makarantar kun tafka babban kuskure a rayuwar ku da bazaku taɓa wanke kanku ba, sai nasa kunyi asarar duka shekarun da kukayi kuna karatu, kuma babu wata makaranta da zakuji kuyi karatu a ƙasar nan. ya ƙarasa maganar yana ƙara kwashe musu da dariyar mugun ta,
Mtsawww, Beenish ta saki wani dogon tsaki tana hararar sa, sannan ta juya ta kalli Aunty Babba, "Aunty Babba fitar mana dashi daga cikin gurin nan, dan bazan juri jin wannan banzar muryar tasa, yazo yana mana haushi a kunne, dan gwanda naji haushin asalin karen da naji ta jakin kare...
Dariyar da yake ce ta ɓace ɓat ta koma baƙin ciki fuskar nan tasa tayi murtuƙ kamar kunun kanwa ya kwana.
'Daman Aunty Babba ƙiris ake jira, nan taja babbar malin malin ɗin ta naɗe sa tare da hannayen sa, tayi masa riƙon maza (itafa indai ƙarfi ne idan kazo gurin Aunty Babba har da na siyarwa da akwai😂) dan saida yayi ƙoƙarin ƙwacewa amma sai yaji ƙam ta riƙesa, cicciɓar sa tayi tayi waje dashi me makon ta sake sa da taga wajen ba mutane sai kawai tasa ƙafa ta harbasa gaba, ya faɗi a gun, ko ta kansa bata bi ba ta koma ciki abun ta,
'Barazana ce ta kalli ƴan wajen cikin ɗaga murya tace wayoyin ku ƙasa kada wanda ya kuma ɗaukar wani abu anan,
Da sauri kuwa duk suka sauke wayoyin su,
"Beenish ce ta juya ta kalle su itama, cikin sanyin murya tace; "Nasan ba kowa bane ya gane me ke faruwa to zanyi muku bayani dalla dalla yanda kowa zai fahimta, kuna ganin wannan baiwar Allahr ta nuna musu yarinyar, sannan ta ɗora da basu labarin abun tundaga farko har ƙarshe, sannan tace muna buƙatar haɗin kanku domin wata ɓarnar ba a kashe ta saida wata ɓarnan, a cikin ku tsakanin ku da Allah wacce macen ce ta taɓa fuskantar haka daga cikin ɗaya daga lecturorin dake cikin makarantar nan kada wacce taji tsoro ku faɗa, ina so mu kawo ƙarshen wannan abun koda kuwa zai zama silar rufe wannan makarantar a shirye muke da mutsayawa kowa tare da haɗin kuwa,
Tafi kawai suka saka musu dan sunji daɗin wannan maganar tata, bayan gama tafin su, nan matan suka shiga fitowa abun mamaki saida a kasamu mata wajen goma sha biyar da abun ya faru dasu, waya suka saka da kansu suna yiwa ɗaya bayan ɗaya video suna faɗar abun da ya faru dasu da kuma sunayen lecturas ɗin, wannan tace ai yana yi lalatar da ita wanann tace itama bibbiyar rayuwar ta ake, wata kuma tace wani yayi mata barazanar idan bata yarda ba sai tazo fita zai dawo da ita baya, ko wacce dai da kalar abun da take fuskanta, a ƙala dai saida aka lissafo lecturori wajen guda huɗu da duk halayyar su ce, acikin su saida aka kuma samun wacce Sir Suraj yake yi mata irin yanda yakeyiwa ɗayar.
Bayan sun gama ne suka ce kowa zai iya tafiya, sannan kowa ya zauna cikin shiri zasu iya neman wasu, sannan yanzu zasu ajiye batun sauran malaman, yanzu iya akan Sir Suraj zasuyi,
Bayan fitar kowa daga gurin suka samu guri suma suka zauna, zasuyi tunanin ta inda zasu fara taro masa aiki, su saka a kore sa daga cikin makarantar kafin shi yasa a kore su dole suyi gaggawar yin wani abun.
'Wayar barazana ce tayi ring hakan yasa suka dakata da tattaunawar tasu,
Da sauri ta zaro wayar daga side bag ɗin ta, ganin me kiran yasata saurin amsawa, "tana ɗagawa tayi shiru tana ta sauraron abun da ake ce mata, can kuma sukaji tace; "Inna lillahi wa Inna lillahi raji'un" Ta faɗa tana shirin faɗuwa da sauri Ameela ta taro ta cike da tashin hankali suka shiga tambayar ta me ya faru, amma takasa basu amsa, sai hawaye kawai da ya fara gangaro mata, suma gaba ɗayan su sun ruɗe ganin ƴar uwar su cikin wannan yanayin,
Cikin kuka tace; "Sun kashe shi wallahi sun kashe shi saida sukaga yabar duniyar hankalin su zai kwanta, cikin garin mu yana cikin tashin hankali, akwai matsala, dole sai naje,
"Su waye su? waye aka kashe, me yake faruwa a garin? Sai tambayar ta suke amma takasa basu amsa sai sunbatu take musu,
Tsayawa tayi da ƙafarta tana maida wayar jaka, tace zan tafi, ku kula da kanku kar ku bari wani abu yasame ku, kar ku bari yayi galaba akan ku, ni zanje akwai wata matsalar acan dole sai naje, tana maganar tana goge hawaye, kuma a hakan so yake ta ƙarfafawa kanta ƙwarin gwiwa, tana gama maganar ta juya zata tafi, Beenish ta tari gaban ta tace;daman akwai abun da zai sameki da har zaki iya tsallakewa ki tafi ke kaɗai batare damu, mu kuma mu zuba miki ido ki tafi ke kaɗai, ba'a taɓa ba kuma baza'a taɓa ba, damuwar ɗaya daga cikin mu damuwar kowannen muce, dan haka tare zamu tafi babu inda zaki ke kaɗai.
Cikin marairaicewa tace "A'a kada kuyi haka idan muka tafi tare wannan matsalar kuma ya zakuyi da ita, akwai matsala idan muka tafi gaba ɗayan mu rayuwar mu zata kuma shiga garari bama mune abun ji ba, ita wannan yarinyar da kuma sauran yaran komai zai iya faruwa damu da su, gwanda ku tsaya kuyi solving ɗin wannan matsala, ni kuma in sha Allah zanyi ƙoƙarin ganin komai bai faru ba koda zan rasa raina, zan taimakawa wasu, dole sai naje,
"Zainab kar ki kuma magana anan gurin ki wuce muje zamuji da komai, nadan halin garin nan, basai kin ban labari ba, dan basu da imani muje kawai, babu abun da zai faru danan har muje mu dawo, cewar Ameela.
Babu yanda Barazana batayi da su ba akan su barta ta tafi ita kaɗai amma sunƙi yarda, dole ta amince su tafi taren......✍️✍️✍️
"Tofa wata sabuwa, ba'a kashe wata matsalar ba ga wata ta ɓullo, yanzu idan suka tafi to ya zasuyi, ga ƙudirin Sir Suraj akansu nasawa a kore su daga makaranta a yau.....
[3/5, 11:47 AM] Yaya Azeema: *💦SU WAYE SU...!?💦*
*_(Who are they...!?)_*
_💦Story and writing💦_
💎
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Chapter 36
Chapter 37
Chapter 38
Chapter 39
Chapter 40
Chapter 41
Chapter 42
Chapter 43
Chapter 44
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 8 Chapter of 44