*_episode 44💧_*
💧💦محمد لرسول الله...!💦💧
*Duk me son littafin su waye sudaga farko zuwa inda aka tsaya da kuma 💅sarki sameer💅 complete, yayi min magana👉08124226526*
Bismillah..✍️
A hankali ya shiga zare glass ɗin dake idon dan ya ganta da kyau ita ɗince ko kuwa ƙarya idon sa yayi masa, Ido cikin Ido sukayi suna kallon juna, yayin da hannun ta ke cikin nasa a murɗe...
Duk da dukiyar da take jin ta, amma yanzu ganin sa haka saida taji tsoro ya shige ta, dan atake zuciyar ta ta shiga bugawa, da sauri ta janye idon ta, ta mayar dashi kan hannun ta da ya murɗe, duk da a tsorace take da shi amma saida ta kuma dakewa ta shiga ƙoƙarin ƙwace hannun ta, shikam ƙara tamke fuskar sa yayi ganin tana ƙoƙarin ƙwacewa yasa ta kuma yi murɗe hannun sosai wanda yafi na da, ƙara ta saki da ta fi ta ɗazu, dan taji zafi sosai, juyawa tayi tabi yanda ya murɗa hannun ko zataji sauƙi amma tana juya shima sai ya kuma murɗa hannun ɗayan ɓarin, da sauri tayi ƙasa zata tsugunna sai ya kuma murɗa hannun sama dole ta dawo ta tsaya, tuni idon ta ya cika, da ƙwalla, murɗa shi ya sake yi akan nada saida yaji yayi ƙara sannan ya tura ta da ƙarfi, ta gaba ta kifa fuskar ta ta daki ƙasa, kasa tashi tayi saboda zugin da taji hannun ta yanayi kamar ma ya karye, da ƙyar ta iya miƙewa zaune tana tashi zaune ya kuma sa ƙafa ya tura ta sannan cikin tsawa yace ta tashi ta kwashe abubuwan da ta zubar masa, ai bata san loƙacin da ta fashe da kuka ba, ta kuma ɗagowa da ƙyar tana kallon hannun ta data ga kamar rawa yake, ashe da gaske dai karya mata hannun yayi, tabbatar da karyewa hannun yayi yasa ta kuma ƙara sautin kukan ta, ga hancin ta ta fara zubar da jinin haɓo sakamakon bugawar da tayi da fuskar, ga fuskar tayi dumu dumu da ƙasa, sai ta zama abar dariya abar tausayi.
Zagayowa yayi ta gaban ta, yana kuma cewa ta tashi ta kwashe masa abun da ta zubar,
Ƙara sautin kukan ta tayi tana cewa "wayyo hannun na, wayyooo hannuna ya kare.
Nan hankalin waɗan suka dawo gurin bayan gama harbin, hankalin su ya karkata kanta, da sauri wasu suka nemi zuwa gun amma sojan da yake agurin ya hana su, dan shi daman ba inda yaje yana gurin kuma duk yana kallon abun da ya faru.
Daga nesa wasu suka tsaya duk suke kallon ta cike dason jin abun da yafaru, itakam sai faman kuka take tana wayyo hannun ta,
Shi kam ko ajinkin sa, daɗi ma yaji da ya ganta a wannan yanayin, sosai zuciyarsa tayi fari, tsugunnawa yayi a gabanta kamar abun arziƙi zaiyi, amma sai ya cire hular kanta, yakama gashin ta, da ƙarfi ya damƙa ya shiga jijjiga mata shi, idan ya girgiza shi gaba da baya, sai ya girgiza shi gefe da gefe, har wani cije baki yake yana girgiza ta da ƙarfi, Allah sarki ita kuma sai dai ta kuma fashewa da kuka dan bata da ƙarfin da zata iya dakatar da shi, saida yagama wujijjiga mata kai ya hargitsa mata ƙwaƙwalwa dan har saida taga duniyar na juya mata, tana ganin mutane hurhuɗu, yana sakin ta kuwa ta kuma faɗawa ta baya dan bazata iya zama ba, ranshi fari tass ya tashi duk halin da take ciki amma haka ya kuma ce mata yabata minti biyar ta kwashe abubuwan ta kawo masa, yana faɗa mata haka ya juya, ya koma inda ɗayan sojan yake,
"Kallon ƴan gurin yayi yace "ina sauran a haka kuke shirin zama sojojin daga jin harbin binduga shine duk zakuyi wannan haukan, so this is the first time da ku kuma yin wannan abun If not I will punish you akan wannan abun, jin abun da yake cewa dan da ƙarfi yake maganar yasa waɗanda suka ɓuɓɓuya a wasu guraren suka shiga, fitowa, duk gurin su suka dawo zuciyoyin su na ɗarɗar,
Ameela da Fashion ne ƙarshen fitowa suna daga bayan sojan dake gurin, a hankali Barazana take tafiya,kamar ɓarauniya dan gaba ɗaya a tsorace take har yanzu, har sunyi gaba, RK ya ce "ke!
Fashion daman ƙiris take jira tana jin wannan tsawar ta kwasa aguje saima ta rasa inda zata dosa duk tabi ta kiɗime, saida taba wasu dariya suka shiga a hankali, Ameela kam juyowa tayi itama a tsorace, tana juyowa suka haɗa ido, duk da wani abu baitaɓa haɗasu ba, amma saida taji gaban ta ya yanke ya faɗi, bata san loƙacin da ta zaro ido ba cike da tsoron ganin sa, kana kallon ta zakasan a mugun tsorace take.
Bayan wata mota dake gurin Barazana taje ta ɓuya gabanta nata dukan uku uku.
RK da mugunta ta gama cika masa ciki, yana ganin su ya gane su, hakan yasa yabi Barazana inda yaga ta tsugunna, a hankali yake takawa har yaje gurin sai ya zagaya ta bayan ta, yana tsaye a ba ceyan ta, yaga ta daddafe motar tana ɗan tashi a hankali da niyar ta leƙa taga babu wanda ya biyota, tana wannan leƙen RK yaɗan dafa ƙafaɗar ta, ihu ta saki tana juyowa a tsorace, tozali da fuskar sa yasata ƙamewa dan numfashin ta ne ya ɗauke gaba ɗaya, saida yayi saurin girgiza ta, sannan ta dawo hayyacin ta tana kuma sakin ihu zata kuma guduwa, ya damƙi hannun da ƙarfi ya shiga janta sannan ya saki hannun ya shiga tura kanta, kamar zata kifa haka yake turata har suka ƙarasa gurin, Ameela kam na inda ya barta mamaki ya ƙamar da ita agun,
Duk ihun da Beenish take dake gurin ɗan tazara da tsakanin su, gashi kuma basa cikin hayyacin su yasa duk babu wanda ya hankalin sa yakai ga jiyo sautin muryar ta.
Yana kawo ta gurin ta ya koma inda yake ya tsaya yana haɗe rai tare da cire p-cap ɗin kansa yana miƙawa sojan gefen sa ya riƙe masa, cikin ɗaga murya ya ce "oya get ready, then, prepare to move out and hold the line!
Saurin gyara tsayuwar su sukayi kowa na saita kansa inda aka saka shi, yanda sukayi tsayiwar layin farko su bakwai sai na tsakiya shida ɗayan gefen ma seven, Barazana dai da Ameela a rikice suke har yanzu musamman ma Abu da jikin ta har karkarwa yake.
Ameela ce ta samu ƙarfin halin duddubawa taga ina Beenish amma har ta gama duba ko ina bata ganta ba acikin gurin, hankalin ta ya kuma tashi ta shiga tunanin ina take to, kode tayi wani wajen loƙacin da suka gudu, sai bayani yake musu amma hankalin ta gaba ɗaya baya gun sai dube dube take.
Gurin babban guri ne haka nan aka sa kowa yabi layi zasuyi gudu su zagaye sa sau goma,
RK yace "kuyi dividing ɗin kan ku into 4 groups, any group zai zama we have 5,5 members,
Group 1 suka fara ware kansu mazan uku uku mata kuma zai kama bibbiyu amma wani group ɗin sai dai asaka maza huɗu mace ɗaya, kasancewar su, matan su bakwai ne idan suka raba kansu a huɗu wani group ɗin bazai samu mace ɗaya ba, su kuma mazan suma idan suka raba kansu gida huɗu ɗaya zaiyi ragowa saidai ya shiga cikin group ɗin da yake da mace ɗaya,
Saida suka raba kannasu sai suka ga group ɗaya maza huɗu ne kawai babu macen ɗaya da zata shiga cikin su, tunawa sukayi da inda take nan suka kalli gurin sai suka ga bata gurin, ɗaya daga cikin matan da suka shiga group ɗaya da Ameela ta tambaye ta, ina ƴar uwar su da ta gansu tare, tayi maganar ƙasa ƙasa da sukaɗai suka san me suke cewa, karkaɗa mata kai kawai Ameela tayi alamun bata san inda take ba itama, daman itama so take ta samu damar da zata tambaye ta gashi kuma ita tafara tambayar ta,
RK ne yace "group A u can start!
Ɗayan sojanne ya irga musu 3, su kuma acikin minti ashirin ake so sugama zagayewar, ɗayan group ɗinne suka fara yi, sannan group B wanda Barazana ke ciki, suna suka fara nasu, tun a zagaye na biyu Zee ta zube agun, dan daman ba iyawa take ba, kaɗan kaɗan takeyi, babu wanda ya kula ta saidai suka gama, sannan RK yace nasu baiyi ba, sai sun sake nasu, haka Zee ta ja musu saida taga ya tunkaro ta sannan ta tashi taci gaba dayi, da ƙyar ta iya gamawa, tana gamawa ta zube a ƙasa tana maida numfashi dan ji take kamar numfashin ta zai ɗauke, group C ne suka fara group ɗin su Beenish, suna gamawa na ƙarshe zasuyi nasu, zasu fara kenan RK ya dakatar da su, cike da rainin hankali sai kace baisan me ya faru ba, yace "ina cikon group ɗin?
Ɗayane yace "Sir tana cen gurin ɗazu yanzu kuma munga bata gurin, bin gurin yayi da kallo shima kansa yayi mamakin rashin ganin ta agun, amma bai bari mamakin ya bayyana ba, kawai yaba su go ahead ɗin su fara sunayi yana kallon su amma zuciyar cike take da tambayar ina tayi daga gurin ko wane ne gangancinne ya yi masa shishshigi ya taimake ta, batare da sanin sa ba.
Suna gama nasu aka kuma basu wani horon na tafiya akwance, babu wanda bai gajiba sannan aka sallame su suje su huta kafin a juma su ƙara fitowa wani horon, yana gama sanar da su ya juya yabar wajen, ɗayan sojan ma bayan sa yabi.
Sukam yawancin su kasa tashi sukayi daga gurin Zee kam in banda kuka tanayin Allah ya isa babu abun da take yi, dan ita ko takan rashin ganin Beenish bai dameta ba,
Ameela ce ta ce "ke kam dan Allah kiyi shiru wallahi kar ya dawo ya jiki, yauwa ke wai ina Beenish ne, kowa fa yace bai ganta, kamata yayi ma mu tashi mu duba inda take.
"Wallahi babu inda zani tama ɓatan ina ruwana ai duk ita tajawo mana wannan bala'in da masifar ko me ya same ta ai ita tajawa kanta, wallahi Allah ya isa na Beenish Allah bazan yafewa yarinyar nan ba abubuwan da take min na zalinci, sai zuba take tana share hawaye, idon yayi ja tsabar jigatuwar da tayi.
Ameela bata kuma ce mata komai ba, dan tasan komai zatace ba sauraron ta zatayi ba, ita da wata mace, tayiwa magana tace dan Allah ta rakata su zagaya gurin ko zasu gano ta a wani wajen.
Tafiya sukayi suka bar Fashion a gun tana ta faman zubar da hawaye tana goge wa da hannu.
Fita sukayi daga gurin suna ta zagayen neman inda take.
RK sosai abun shima ya basa mamaki dan har saida ya kasa jurewa suna cikin tafiyar ya tsaya tare da kallon, ɗayan sojan,
yace "ko yaga inda yarinyar nan tayi daga gurin da take?
Jinjina masa kai yayi tare da cewa "eh naga wani soja ya ɗauke ta akafaɗa saidai banga fuskar waye ba.
Haɗe rai yayi yace "why u shouldn't tell me?
"To ai banga wani abuba wataƙil ko ɗata daga cikin masu kula da lafiyar sune yaganta a cikin halin shiyasa ya ɗauke ta.
Kawai kallon sa yayi yana jinjina kai yayi gaba, yabar sa, a ransa yana ayyana cin mutuncin da wanda yayi masa wannan shishshigin ko waye bazai ƙyale sa ba.
Can cikin wani guri ya dosa, inda masaukin su yake, cikin zafin nama yake tafiya saboda ya matsu yaje ya cire kayan jikin sa zafi yake ji.
Yana shiga tundaga falo ya shiga ɓalle botiran rigarsa, hakannan yaji ransa duk adagule, saboda zafin da yake ji, a galon ya jefar da rigar tasa, ya ɗaga singilet ɗin sa itama ya cireta yana daf da shiga ɗaki ya shiga cire belt ɗin sa ya fara cire wandon ƙasa, yana shiga ɗakin ya ƙarasa cire sa, ya doshi banɗaki, ya daɗe yana wanka kafin ya fito daga banɗakin ɗaure da towel, idon sa ne ya sauka kan gadon sa, a ɗan firgice ya kuma waro idon sa dan ganin sa da kyau, kamar mutum yake gani a kan gadon akwance, matsawa yayi kusa da gadon.
Da ƙarfi yace "what...!!!!
Cike da mamaki yake binta da kallo ganin yanda ta kwanta ɗaiɗai tana sauke numfashi, hannun ta kuma naɗe da farin abu ta miƙar dashi gefe...✍️✍️
_Ba yawa sorry 😔 amma da babu gwanda ba daɗi ko inji masu iya magana._
*Duk meson na saka shi a group ɗin Su waye su yayi min magana, ta wannan number 08124226526 iya littafin su waye su, dan Allah kar wanda ya min magana akan meman wani littafin, ko yace min in saka sa a group ɗin littattafai, to wallahi duk wanda yayi min magana bazanyi reply ba, sbd an saba yi min irin haka Ni ga abun da nace amma sai wasu si ta tambayata in tura musu littattafai dan Allah ku daina bana so ba littattafai nake turawa ba nawa kawai nake turawa*
_Ƴan facebook kuma kuyi searching ɗin su waye su hausa novel group kuyi join akwai a ciki tundaga farko har inda aka tsaya, dan ba kullum zanna posting a kowane group ba_
[4/25, 12:52 PM] Yaya Azeema: *💦SU WAYE SU...!?💦*
*_(Who are they...!?)_*
_💦Story and writing💦_
💎
*🌬️Yaya Azeema😎*
(THE WRITER OF 💅SARI SAMEER💅)
________* 08124226526*_______
*_episode 45💧_*
💧💦محمد لرسول الله...!💦💧
*Duk me son littafin su waye sudaga farko zuwa inda aka tsaya da kuma 💅sarki sameer💅 complete, yayi min magana👉08124226526*
_Bismillah..✍️_
_____Cike da mamaki yake binta da kallo ganin yanda ta kwanta ɗaiɗai tana sauke numfashi, hannun ta kuma naɗe da farin abu ta miƙar dashi gefe.
Kamar wanda mayan ƙarfe ya zuƙo haka ya ƙarasa gaban gadon yana kuma zaro ido yana kallon ta da kyau, jinjina kai yayi cike da ƙara tabbatar wa kansa ita ɗin ce.
Cikin zafin ya ware tafin hannun sa, ya ɗalla mata duka a gadon baya, a firgice Beenish ta buɗu idon, amma tama kasa tantance me taki kuma daga kuma a ina take, bata gama tunanin me ya faru da ita ba, RK ya damƙo ƙafarta ya shiga jawo ta daga kan gadon, da sauri ta tashi zaune tana ƙoƙarin ƙwacewa amma ya hanata, ɗayan hannun me lafiya ta miƙa tayi sauri ta riƙe zanin gadon nan ya tattare ya biyo hannun ta sai tayi sauri ta riƙo wani guri a jikin fuskar gadon, yana janta amma ta riƙe fuskar gadon ƙam, saida ya kuma tattaro ƙarfin sa, yayi mata wata irin fusga, bata san loƙacin da ta saki jikin gadon, gaba ɗayan ta ta taho zata sillo ƙasa, ganin dai da gaske so yake ya faɗo da ita ƙasa ahaka yasa tayi saurin riƙe towel jikin sa ƙam, hakan yasa shi dole ya dakata da jan da take masa.
Cikin mamaki ya ɗago yana kallon cikin idon ta, itama kallon nasa tayi, kowa kagani fuskarsa kamar tsohon kunun da ya kwana, kowa ya haɗe rai tamau kamar babu wanda ya taɓa yin dariya acikin su kowa zuciyar sa ta farfasa take ji suke kamar su cinye junan su a haka.
Cikin ɓacin batare da ya ɗauke ido daga kallon da sukewa junan su ba, yace "Are You mad? Kina haukan ne, sakar ni!
Itama cikin haɗe ran tace "kafara sakina tukunna in bahaka wallahi kana kuma jan ƙafata zan ja abunnan, tayi maganar tana ɗauke idon ta daga kansa ta mayar dashi kan hannun dake kan towel ɗin.
Da ɗayan hannun sa ya ɗora kan hannun nata zai murɗe amma yanda ta riƙe towel yasa dole ya sake ta dan yasan koya ya motsa mata hannun zata iya kunce masa towel ɗin dan yajisa ma sako sako kamar ya kusan kuncewa, amma taurin kai ya hanasa sakin ta dan bayaso yayi abin da take so.
Wata tsawar ya kuma daka mata yace "ki sake kafin inkashe ki a ɗakin nan kuma wallahi na kashe banza, ke wace irin mahaukaciya ce, uban me ya kawo ki ɗakina, idan ma iskancin kine ya motsa to ki fita waje ki nemi irinki, banza mahaukaciya ƴar iska, ki sake ni nace!
Tunda ya fara wannan maganar ta kafe shi da ido tana aika masa da kallon tsana, ji tayi zuciyar ta kamar ta ɓula waje ta fito, tunda take babu wanda ya taɓa yi mata kalar wannan zagin shiyasa ranta yayi ƙololowar ɓaci.
Itama cikin tsawar da taso ma tafi tashi tace "kai dalla Malam dakata! Kaine babban mahaukacin wanda baisan darajar mata ba, kuma wallahi wallahi idan baka sakeni ba kana kuma wani motsi anan sai naja towel ɗinnan sai kafi jin daɗin kirana da ƴar iskar da kyau, mugu kawai azzalumi ga babban haukanan kanayi, in ba hauka ba mezaisa ka yin wannan daƙiƙancin bakaga halin da nake ciki ba amma dake ba Allah a ranka kake shirin ka jawo Ni ƙasan gurin ba ruwan ka da me zai faru idan na faɗo ɗin, to wallahi ka sani baka isa kayi min duk abun da kaga dama ba, dan ba jakar ka bace ni.
Idon sa har ƙanƙancewa yake saboda tsabar ɓacin rai, bakin sa ya shiga taunewa kamar zai fasa su, hannun sa kuma dunƙule su, har karkarwa suke, ita kanta taji hakan a hannun sa da ya riƙe ƙafar ta, daman a tsorace take jin hakan yasa ta kuma tsorata saidai bata bari ya bayyana ba, saima ƙara wurga masa kallon banza me cike da tsana da take watsa masa, itama kuma tana ƙara riƙe towel ɗin da kyau yanda de tasan bazai kunce ba, dan barazana ce kawai itama bazata so taga ƙato gaban ta hakaba.
Gashin kanta ya damƙa da mugun ƙarfi wanda hakan yasa tayi saurin sakin sa tana dafe kan zata cire hannun nasa, amma ina takasa, take hawaye ya shiga sauko mata, tayi saurin gogewa dan bata so ya gani ya kuma raina ta, a haka ya miƙar da ita tsaye, bata daddara ba ta kuma saurin ɗora hannun ta kan towel ɗin da tasan nan ne kawai mafitar ta, ta daidai inda ya ƙulle ta ɗora, cikin ɗaga murya tace "mugu ka sake ni kaina ciwo yake, kuma wallahi saina ja abunnan, tana faɗa ta shiga alamun kamar zata kunce ɗin, da ƙarfi ya sake ta yana turata baya, yana turata towel ɗin ya fara kunce cikin sauri ya riƙo sa yana maida shi maɗaurin sa, juyawa kawai yayi cikin sauri ya nufi wajen wardrobe ɗin sa, Allah Allah yake ya shirya shi kaɗai yasan me zaiyi mata yau, dan saina lahira yafita jin daɗin, sai ya koya mata hankali ta shiga taitayin ta sai ya sanya mata tsoron sa tunda yaga kamar bata tsoron sa.
Tura tana da yayi yasa Beenish ta faɗa kan karyayyen hannun ta, azaba ta sakata sakin ihu, amma tuna abun da zai mata idan yagama yasa tayi arowa kanta jarumta cikin hanzari ta miƙe tana saukowa daga kan gadon ga hawaye duk yagama wanke mata fuska, ɗayan hannun tasa ta riƙo hannun me karaya, da sauri ta nufi ƙofa tana satar kallon sa, ganin ya juya, yana ɗauko kaya.
Buɗe ƙofar tayi a hankali, ta fito daga ɗakin, bata san loƙackin da ta sauke ajiyar zuciya ba, cikin sauri ta kuma nufar ƙofar falon zata fita tajiyo Muryar sa yana cewa "idan kika sake ki fita daga falon nan sai nayi gunduwa gunduwa da namanki, yana maganar yana dosota.
Da sauri ta buɗe ƙofar tana cewa "ashema na cika mahaukaciyar idan na tsaya, tana faɗar haka ta fita shi kuma yana ƙarasowa tana fita, tsayawa ya saka ya ƙarasa saka rigar da ya riƙo a hannun sa, dan wando kawai ya saka, yaga bata ɗakin hakan yasa ta ɗauko rigar ya biyo ta.
Yana gama saka rigar ya fito waje saidai harta ɓace baigan taba, haushi yaji ya kuma cikashi, sojojin gurin ya shiga balbalewa da masifa yana tambayar su ina tayi kuma waye ya kawota nan part ɗin, cikin sauri ɗaya yace "Sir babu wanda ya fito yanzu, tun ɗazu dai da Moohad ya kawota ta fita bai kuma dawowa ba kawai dai yace mu kula da gurin da kyau idan munji kukan ta ko ta fito tana buƙatar wani abun mu bata kafin ka dawo, ai sojan nan na rufe bakin sa yasakar mar wawan naushi a baki sai kace shi yayi masa laifin, yana naushin sa ya caƙumo wuyan sa yace "how dare you uban wa yace kubar wasu ƴan iska su shigar min part, baka da hankali ne kake min wannan bayanin da bakin ka, yanzu jakar nan ta fito amma kace bakuga kowa ba, ni zaku munafurta ta ina tabi inba tanan ba?
Da sauri sojan ya shiga basa haƙuri yana kakarin amai dan ya shaƙeshi da yawa, sakin sa yayi yana yin kan sauran ragowar biyun dake gurin suma duk saida suka samu rabon su, sannan kamar zarrare ya doshi inda aka sauki su Beenish, yana tafiya yana ayyana irin abun da zaiwa mata da ita da Moohad, dan jin Moohad ne yasa yaji ransa ya kuma ɓaci dan me yasa zai kaita part ɗin shi, meyasa baikaita nasa part ɗina, me yasa yake masa shishshigi a rayuwar sa, zaiyi maganin sa amma, yana tafiya yana zayyana abubuwa a cikin ransa, kana kallon fuskar sa kasan ba lafiya.
Beenish na ganin ya tafi tayi saurin fitowa daga bayan ƙofar ashe tana fitowa taga wasu sojojin sai ta koma da baya tana leƙawa taga yana saka riga sai tayi sauri maƙale abayan jikin labule har yagama ya fita bai san da ita ba,
Tana fitowa wani soja yayi saurin tarar ta yana cewa yanzu Sir RK yazo nemanki, Abdul je ka kirasa gatanan mukuma mu tsare ta kayi sauri kar yayi nisa.
Kuka Beenish ta sakar musu tace "dan Allah kuyi min rai kar ku kirashi na roƙeku wallahi zai iya kashe ni idan ya ganni baida imani kuma ni bani na kawo kaina ba nan gurin hasalima bansan gurin sa bane wallahi da zangayawa wanda ya kawo ni bazan zauna, amma dan Allah ku rufamin asiri kada ku kirashi, ku kira wannan ɗin da mukazo tare yazo ya taimaka min ya fitar dani daga gurin nan in ba haka ba, wannan azzalumin sai yaga ya nakasani zai rabu dani gwanda in bar nan gaba ɗaya.
"Babu inda zaki kina nan damu sai kin zama cikakkiyar soja me dauriya ba me tsoro ba, ki rage wannan tsoron nasa da kike ki barni dashi yanzu zo muje nakaiki part ɗina idan kin warke kya fito.
Juyawa tayi tana kallon Moohad da yana zuwa yaji tana wannan maganar, ƙarasowa yayi tare da kamo hannun ta, yace "muje"
Binsa ta shiga yi batare da ta kuma cewa ko uffan ba, har sun ɗanyi
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Chapter 36
Chapter 37
Chapter 38
Chapter 39
Chapter 40
Chapter 41
Chapter 42
Chapter 43
Chapter 44
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 38 Chapter of 44