na commissionan ƴan sanda kana yin abun da bai dace bane da har kake expecting ɗin zamu ɗauke maka yaro, idan kana tunanin haka ai kai jami'in tsaro ne me kare haƙƙin jama'a ko waye bare kuma ace an taɓa naka ai kamata yayi kayi gaggawar ɗaukar mataki amma har ka ɗauki masu laifi a motar ka kayi driving ɗinsu batare da ka ɗauki ko wane irin mata ki ba, wannan ai abun kunya ne baka cancanci muƙamin kaba, da masu sharar gida ka dace ta yanda zaka zama marar gata akuya da kare su ɗauka sannan......
Ameelaaa...!!!
Ya daka mata tsawa tare da cewa; "fice min daga mota right now......
Dariya ta kwashe da ita harda tafawa tare da cukwikwiye masa riga tana sauya kalar fuskar ta zuwa ai nahin yanda ya santa.......✍️
Please ayi maleji ba yawa.
*(Duk me son in saka shi a group yayi min magana ta number ta a WhatsApp, dan Allah idan kasan ba karantawa zakayi ko zaka tambaye ni wani littafin to kar kayi min magana Please 🙏08124226526)*
*(ƴan facebook kuma da basa WhatsApp kuyi searching ɗin SU WAYE SU HAUSA NOVEL GROUP kuyi join anan zan ringa posting kullum amma idan kana wani group ɗin zaka iya ganin sa saidai baizama lalle kagani kullum ba kuma ba ajere ba.)*
[3/5, 11:45 AM] Yaya Azeema: *💦SU WAYE SU...!?💦*
*_(Who are they...!?)_*
_💦Story and writing💦_
💎
*🌬️Yaya Azeema😎*
______________________________
*_episode 9💧_*
💧💦محمدالرسوالله...!💦💧
Bissmillah.....✍️
Ameelaaa...!!!
Ya daka mata tsawa tare da cewa; "fice min daga mota right now...!
Dariya ta kwashe da ita harda tafawa tare da cukwikwiye masa riga tana sauya kalar fuskar ta zuwa ai nahin yanda ya santa.
Stop shouting at me before inyi maka a bun da baka tsammani na rantse da Allah ka kuma ɗaga min murya anan gurin sai ka gane shayi ruwa ne, har Ni zaka cewa in fitar maka a mota, Ni zaka kora daga motar ka, akan wani ɗan iskan ɗanka, kasan ba tsoran uban kowa muke ba, da idan mu muka ɗauka zamu ɓoye, mu ɗauke sa mu ɗorawa kanmu kaya, ai mutum nayi mana zamu ci ƙaniyar sa jikin mutum yagaya masa basai anɗau loƙaci ba, bare ma kuma shi yayi kaɗan muyi dashi saidai muyi da Baban sa ko Baban Babban sa... Tana faɗar haka ta sake sa tana watsa masa harara tare da buɗe murfin motar ta fita tana banko masa ƙofar kamar zata ɓalle ta, dan har saida yaɗan razana kaɗan da jin ƙarar ƙofar, hannu ya dunƙuli ya kaiwa sitiyarin ɗin motar duka yana me sakin ƙara kalmar ta ta ƙarshe ba ƙaramin tasiri tayi ba a zuciyar sa, maganar ta dake shi sosai, saidai tayi da Baban Baban sa, lalle Ameela dole ta gama rainasa, amma idan sun san wata basu basan wata ba, zai ɓullo musu ta bayan gida zasu gane basu da wayo.... Haka yayi ta kunce da warwara shi kaɗai saida ya kai tsawon wani loƙaci a haka kafin ya iya tayar da motar yabar wajen zuciyar sa cike da ta ƙai ci.
*Ameela*
Can inda take tunani ganin su ta nufa cikin wani restaurant dake gefen inda suka tsaya, tana shiga kam ta hango su suna kwasan waku, ita ma ƙarasawa tayi tayi join ɗin su daman plate ɗin ta yana gurin hana jiran ta dan haka ta hau ci kawai tana basu labarin yanda sukayi da commissionana, har suka gama cin abin cin suka tashi daga gurin tare da biyan kuɗin suka bar wajen.
Washe gari.....
Kamar kullum yauma haka suka shirya suka tafi makaranta duk wanda ya gan su sai yayi mamakin ganin nasu domin ana tunani yanzu suna sale a ƙulle amma kuma ko kwana basuyi ba a gansu sun dawo makaranta, amma saidai gulmar tasu dan babu wanda ya iya tunkarar su bare ya tambaye su yaji ya akai suka dawo.
Suna shiga duk suka rabu kowa yayi nasu department ɗin su.
"Kai amma fa sun burge ni wallahi amma ina tunanin ta ina zan fara yi musu magana karfa su wulaƙan tani kasan ba ɗauka zanyi ba kar a zo a samu matsala, ganin neman gira a rasa ido.
"Faheema bama abun da zai faru ni inaji ajiki na ba abun da zasu yi miki zasu karɓeki hannu bibbiyu saidai kawai kar ki bari su san ko ke ƴar waye sannan karki rinƙa zaƙe musu da yawa ki bisu a sannu sannu nasan zasu kaɓe ki amma fa sai kinyi haƙuri kin daure zamu samu abun da muke so.
"Tom yaya zandai yi kawai saboda kai, amma fa gaskiya ba komai zan jura ba zandai gwada mugani Allah dai ya rufa asiri kawai komai ya tafi yanda kake so, amma zanbi waɗancan ukun da naga sun shiga can dan naga kamar zasufi sauƙin kai musamman wannan me red kayan nan, (Beenish)
Jin wacce ta faɗa har saida ya ɗan lumshe idon sa jin kamar ra'ayin su yazo ɗaya dan shima yafi jin Beenish ɗin a cikin ransa, cikin zumuɗi yace; Yauwa nima na fahimci zata fi sauƙin kai, ita ce wacce tayi kukan nan har na nakaita office ɗina,
"Okay tom bari in wuce saura 3 minutes mu shiga lecture any way idan na fito ma haɗu zan duba inda suke zama, tana faɗar haka ta buɗe motar ta fito, shima fitowa yayi cikin sauri, nan sukayi sallama kowa yayi nasa guri....
*$$$$$$$$$$$$$$$$$$$$$$*
*ƊAN IJJI'S HOUSE*
Alhaji ɗan ijje ne zaune a falon sa shida matayen su kowannen su yayi rafka uban tagumi tunda aka ɗauke Bilal komai ya tsayawa Alhaji ɗan ijje dan ya ɗorawa ɗan so bana wasa ba, ko abinci yaƙi ci, saboda baya cikin kwanciyar hankali, musamman idan ya tuno hoton ɗan nasa da aka turo musu ana mishi barazanar kashe shi yana cikin mawuya cin hali ga bindugu da suke saitin sa, gashi ance indai yana so ɗan sa ya dawo sai ya tura musu billoin talatin da biyar zasu bada ɗan shi kuwa yana tunanin ta ina zai fara basu kuɗin nan duk da yana dashi amma sunyi yawa, idan ya basu karayar arziƙi zata iya kamasa, saboda sai yacire rabi za kwata na kuɗin sa,
Miƙewa yayi daga inda yake a zaune yana ɗan tafiya kaɗan kaɗan yana tunanin mafita gurin wazai je ya taimaka masa, su haɗa kuɗin nan in yaso sai ya ci gaba da neman wasu ya haɗa ya biya,
Hajiya Khattume ce tace; Alhaji, ni kam in baka wata ƴar shawara mana, me zai hana kayiwa tsohon governor maganar mana nasan zai taimaka maka bazaiƙi baka wani abun ba, mussaman idan yaji halin da kake ciki, ina ganin ko bai baka ba zai iya sawa a binciko duk inda suke ko ɗan sane zai sa a gaba kadan dai ɗansa ba wasa zai iya lalubo su kuma idan ya lalubo su bazai musu ta daɗi ba, ko jin sunan shima a cikin lamarin zai iya sawa su tsorata su dawo dashi batare da sun cutar dashi ba, amma kayi tunanin kaga meye mafita,
Shiru yayi yana nazarin maganar ta kuma ta wani fanni yaji daɗin wannan shawar ta ta, "Gaskiya ne maganar ta hanyar sa kawai zan samu Bilal in ba haka ba nasan sai na shiga wani hali wallahi gaba ɗaya kaina ya ƙulle nama rasa wane kalar tunani zanyi a kai in samu mafita, take wani irin farin ciki ya lulluɓe sa kamar ance masa Bilal ya dawo, saboda murna baisan loƙacin da yaje ya mannawa Hajiya Khattume kiss ba a gaban Jannat, rufe ido tayi kawai tana watsa masa hararar da baisan tana yi ba, kuma ko inda take bai kalla ba, ya kuma juyawa yana ta farin ciki ya fice daga gidan dan yace baiga ta zama ba sai ya gansa a gaban tsohon governor hankalin sa zai kwanta.
Yana fita Jannar ta daka tsaki tare da miƙewa daga gurin tabar wajen, Hajiya Khattume kam binta da kallo tayi kawai tana jinjinawa lamarin ta, yanzu sai ta ƙullace ta ɗan wannan abun da me gidan yayi mata a gabanta sai kace ita tace yayi mata, itama taɓe baki tayi haɗi da maƙe kafaɗa, a fili tace to ba mijina bane koma me ya min, ita ma gurin tabari ta nufi hanyar kitchen..
*$$$$$$$$$$$$$$$$$$*
*COMMISSIONA*
Can ofishin ƴan sandar ya koma tare da gargaɗi kowa da jan kunne akan abun da suka gani game da abun da yafaru tsakanin sa da ƴan matan, ya hana kowa ɗaga maganar da gargaɗi me ƙarfi, yace duk wanda yasake maganar ta fito a bakin aikin sa, hakan kwa babu wanda yayi gigin tunanin zai bari maganar ta fito, haka yagama jan kunnen su sannan ya nufi asibiti inda aka kwatar da ɗan da suka ɓallawa hannu.
Tunda ya shiga asibitin ake gaida shi saboda sanin matsayin da yake dashi, Saida sukaje bakin ward ɗin sannan sauran ƴan sandan suka tsaya abakin ƙofar ɗakin da zai shiga, shi kuma ya ƙarasa shiga.
"Yana shiga ya tsaya yana kallon su yaron ne a zaune ga hannun da aka naɗe masa da bandeji, sai wata mata dake basa abinci a baki, bisa ga dukkan alamu kamar mahaifiyar sa ce dan suna ɗan kama da ita, sai wata yarinya dake tsaye a gefen su, itace ta ɗago ta kalli mahaifin na su, dan duk basu san da shigowar sa ba, da sauri tace; Abba hakan yasa mahaifiyar tasu sa da ɗan saurayin suka ɗago suna kallon bakin ƙofar.
Saida ya sauke ɓoyayyiyar ajiyar zuciya sannan ya iya takawa zuwa inda suke, gaida shi sukayi gana ɗayan su, sannan matar ta ɗora da cewa; "Abban su ya akayi da yaran da aka kama, ina fatan dai za'a ɓallawa yarinyar da ta ɓallasa su kuma sauran ayi musu hukunci me ƙarfi da zai hanasu ƙara yiwa wani haka bare kuma zuri'ar da ta shafe ka.
Yarinyar ce tace; "Gaskiya dai Abba dan bazamu barsu dan ko anyi musu hukunci in suka fito sai na kuma ɗaukar wa yayana fansa dan bazan ƙyale su ba nima,
Maganar mahaifiyar tasu bata dame sa ba kamar yanda yaji batun ƴar tasa, tunda ta fara maganar yake binta da kallo yana jinjina kai a ransa yana ƙara maimaita kalmar ta ta kusan ƙarshe, fansa, fansa sai na ɗau fansa zagayawa yayi ta inda take sannan ya riƙo hannun ta, ƙasa yayi da murya sannan ya ce; Kinsan dai meye aiki na, ko kuma duk ne ɗaukan hukunci da kansa shima me laifi yake zama dan haka kar na kuma jin wannan furucin a bakin ki, ɗaukar hukunci a dakan ka ya saɓa shari'ah bare ma kuma an riga anyi musu hukunci kizo ki ƙara ɗauka, kinga nema zaki zama me laifi, ko kina so kema a sakaki a sale?
Da sauri ta girgiza kai tana tutturo baki dan ranta baiso ba da dakatar da ita ɗin da yayi, amma duk da haka ko bata ɗauki mataki ba sai tasan abun da zatayi musu batare da kowa yasan itace tayi ba.
Shi kuma yayi mata hakane saboda halin su da yasani yasan ko hauka suke bata isa ta iya ɗaukar fansa a kan su ba, kawai zata kuma jefa sa cikin matsala ne tsakanin sa da su, shiyasa gwanda yayiwa tifkar hanci tun wuri baya so familyn sa su saka ƙafar wando ɗaya da yaran nan dan mugayen mutane ne riski ne da su, shi baima san me ya kawo su garin ba, baitaɓa tunanin zasu zo har inda yake ba, gashi kuma suna ƙoƙarin takura rayuwar sa....
"Abban su.!"
Matar ta kirasa hakan ya katse tunanin da yake, zuba mata ido yayi yana kallon ta batare da yace komai ba.
Cikin yanayin damuwa sosai tace; Wai har yanzu ba a gano inda suka kai min Zaid ba haka zamu zauna muna zuba, ya kake so inyi da rayuwa ta wancan sun ɗauke sa wannan sun karyasa wai me hakan yake nufi meye haɗin su da ƴaƴa na, me suka tsare musu da zasu ringayi min haka ta kara sa maganar ta ɗan matsar ƙwalla, cike da damuwa.
Dafe kansa yayi da yaji ya fara sara masa dan shi tunanin sa ya fara tsayawa da matsayin da komai amma wasu suna ƙoƙarin maida shi ƙaramin mutum, saida ya shaƙi iska sannan ya furzar da me zafi yana cije baki, sannan ya ce; ba haka bane kar kiyi tunanin laifin kine ko laifin su, shi wannan laifin sa ne tunda shi yaci zarafin ta tunda ya mare ta shiyasa suma sukayi masa haka, shi kuma Zaid basu suka ɗauke sa ba, yaran basu isa ɗaukar mutum ba, kawai dai basaji idan an taɓa ɗaya daga cikin su, amma ɗaukar Zaid baida alaƙa da su, wasu ne daban suka ɗauke sa kuma kinga ai bashi kaɗai aka dauke ba harda ɗan gidan Alhaji ɗan Ijje, zai iya yiyuwa sunyi mana hakane saboda sunga muna dashi ko kuma abokan adawa dan kana rayuwar ka baka shiga ta kowa ba amma zaka tsokane wa wasu ido da basu da burin da ya wuce suga sun ƙuntata maka rayuwa, amma dai kiyi haƙuri har yanzu ana nan ana bincike matsalar kuma daman basuyi waya ba bare abi diddigin inda suke saidai muyi ta addu'a Allah ya kare su a duk inda suke daga shi har ɗayan, Allah ya bayyana mana su.
"Ameen tace yana ƙara goge hawayen da ya cika mata ido taf,
"Kai kuma na dawo gare ka ya maida kallon sa gare shi, sunkuyar da kansa yayi saboda duk tsiyayar da yake tsulawa baya bari mahaifin sa, yasani saboda yana jin tsoron sa,
"NA'EEM" kar kayi tunani bansan me kake ba rabuwa nake dakai kawai idan baka shiga hankalin ka sai nayi maganin ka, ni da kaina zan kuma ɓalla ɗayan hannun, akan kawai ta bugeka bata sani ba, dan me yasa zaka ɗaga hannu ka mare ta wannan ai shashanci ne da shirme, daga yau bakai ba su ka fita a harkar su kar naji wani abun ya kuma tasowa magana ta ƙare ankashe ta tun ɗazu kaji ni?
Jinjina masa kai yayi alamun eh amma a ransa ba haka bane dan acike yake dasu baya jin zai iya rabuwa dasu.
Shima mahaifin na sa daɗi yaji aransa dan yana ganin kamar ya kawo ƙarshen abun dan bayaso maganar taci gaba da tafiya.....✍️
🫣🫣🫣🫣 Wlh kunyar ku nake ji kuyi haƙuri in sha Allah zan faran ta muku a satin nan dan har weekend ma sai nayi muku sorry please
[3/5, 11:46 AM] Yaya Azeema: *💦SU WAYE SU...!?💦*
*_(Who are they...!?)_*
_💦Story and writing💦_
💎
*🌬️Yaya Azeema😎*
______________________________
*_episode 10💧_*
💧💦محمدالرسوالله...!💦💧
Bissmillah.....✍️
*Alhaji ɗan Ijje*
___Tun yana kan hanya ya kira number sa yasanar masa da zuwan sa, dan haka tun kan ya ƙaraso aka sanar da masu gadin gidan, bai wani tsaya ba yana zuwa suka basa hanya, ya wuce ciki, gida ne tafkeken gaske me girman gaske wanda yaci uwar na Alhaji Ɗan Ijje a girma da haɗuwa da komai, wajen gidan da cikin gidan duk cike yake da matakan tsaro sun zagaye ko ina na cikin gidan, wasu harda bindigu a hannun su irin zabga zabgan nan,
Motar sa na tsayawa a wata farfajiya, wani daga cikin masu tsaron gidan yazo da sauri ya buɗe masa ƙofa, yana fitowa wanda ya buɗe masa motar yayi yana yi masa iso yana nuna masa inda zaiyi, sai kuma wasu mutum biyu a bayan sa suna mara masa baya, saida sukayi tafiyar kamar minti 3 sannan suka ƙaraso bakin wata ƙofa me ɗan faɗi suka buɗe suka shiga wani dogon corridor suka kuma miƙewa ba wata tafiya me tsawo sannan sukayi kwana tun anyi kwanar sauran biyun suka tsaya daga gurin da ɗayan suka ƙarasa bakin wata ƙofa nocking yayi sannan ya matsa daga gurin tare da juyawa ya matsa can nesa dashi,
A hankali a ka buɗe ƙofar wata mata ce ta buɗe tare da sunkuyar da kai ƙasa tace barka da zuwa bismillah ta faɗa tana basa hanya, shiga yayi tare da yin sallama ta amsa masa, tare da barin wajen, cikin tanƙameman falon ya ƙarasa ya samu ɗaya daga cikin luntsuma-luntsuman royal chairs ɗin da suka gaji da kyau ya samu ya zauna, babu kowa a falon sai kan center table ɗin da aka cika da kayan marmari, shiru yayi yana ɗan bin falon da kallo duk da ba wannan ne loƙacin da ya fara shigowa falon ba, saidai kuma duk shigowa sai ka samu abun da aka sauya a cikin falon,
"Ahh wata sabon gani ashe talaka na ganinka, Mas'ud baka da kirki wallahi mutuncin ka kaɗanne"
Dariya Alhaji ɗan Ijje yake yi irin tasu ta manya ta masu kuɗi, yana jinjina halin sa da irin waɗannan maganganun nasa, shi dai a kwai sa zolaya...,
Mutumin shima fuskar sa ɗauke da murmushi a kan kyakkyawar fuskar sa ya ƙaraso inda yake zaune yana miƙa masa hannun alamar suyi musabaha da sauri Alhaji ɗan Ijje shima ya miƙe yana miƙa masa sukayi musabaha, sannan Alhaji ɗan Ijje ya koma ya zauna shima mutumin kujera ya samu ya zauna yana fuskantar sa.
Alhajin Allah kana nan abunka ka manta damu kaci mutuncin abota wallahi duk da bansan dalilin ka na juya mana baya ba,
Alhaji ɗan Ijje ya ɗan sosa kai sannan yace; "Hmm ai kune Alhazai wane mu muna gefe, siyasa ta ɓoye ku, ya shirye-shiryen zaɓe kuma?
Saida ya ɗanyi jim kamar bazai ce masa komai ba, sai kuma can yace;zaɓe alahamdulillah, tunda kai ka guje mu me zai hana yanzu ka ƙara fitowa takarar ina tunanin yanzu baza a kuma samun matsala ba kamar da, saboda ada ɗinma laifin kane amma da tuni kasan kai zaka ci amma ka juya mana baya amma......
Hannu Alhaji ɗan Ijje ya ɗaga masa tare da cewa; dan Allah mubar wannan maganar tunda de komai ya wuce, yanzun ma ɗan wani abune ya kawo ni idan zai samu fa amma ba takura idan kuma da matsala shima abarsa.
Shiru yayi kamar yanda ya buƙata amma aransa baiji daɗin hakan da yayi masa ba, ko ba komai yakai wani matsayi da shi bai kai ba duk girman abotar da ke tsakanin su bai kamata ya ɗaga masa hannu ba a loƙacin da yake magana, amma duk da haka me makon ya nuna masa ɓacin ransa saima murmushin girma irin nasu na masu kuɗi da ya sakar masa yana me ɗaukar glass cups ɗin da aka kifesu akan plate juyo dasu yayi sannan ya ɗauki flaks ɗin tea ya tsiyaya a ciki sannan ya ɗauka ya miƙa masa, ba musu ya amsa,
Shima ya ɗauka yayi saida ya ɗan sha sannan ya ajiye, ya ƙara maida hankalin sa gare sa, sai yaga ya riƙe cup ɗin kawai bakai bakin sa ba,
Murmushi ya kuma yi har haƙoran sa na fitowa ya ɗan jinjina kai, sai kawai ya ce; "Ɗan Ijje inajin ka me yake tafe dakai kasan babban abune tunda har aka iya neman alfarma ta nasan ba ƙaramin abu bane,
Ajiye cup ɗin yayi sannan ya ɗago yana kallon sa ido cikin ido ya ce; "ALHAJI KAMAL" banaso wannan abubuwan su ringa faruwa na fahimci kamar kana min magana me harshen damo to ni bada wata manufa nazo gurin ka ba, akan ɓatan ɗana ne da akayi kidnaping shi da ɗan gidan Commisiona, shiyasa nazo inji ko kana da wata hanyar da zamu bi gurin gano inda suke ko kuma kasa ɗan wajen ka cikin lamarin tunda ku kuna faɗa aji, ba kamar mu ba.
"Jinjina kai yayi bayan jin abun da yafaɗa duk da yasan maganar amma tunda har yazo da kansa dole zai taimaka masa"
"To abokina nima komai na faɗa da wasa nake ma, daman naji maganar tun aranar amma yanzu gaskiya ni bazan iya cewa komai ba game da inda za'a same su, saidai ku ƙara haƙuri a cigaba da addu'a da neman inda ake tunanin zasu kasance daga nan zuwa nan da sati biyu ranar da za'a fara taron ƴan majalissu ranar MAHEER zai dawo Nigeria idan ya dawo sai a miƙa masa case ɗin nasan duk wanda ya ɗauke suma idan sukaji labari zasu dawo dasu in sha Allah.
Ajiyar zuciya ya sauke duk da baya tunanin zai iya jura har zuwa sati biyu besaka ɗansa a idon sa ba baisan halin da yake ciki ba dan yana jin kamar kafin loƙacin zasu iya cutar dashi, "Allah ya yarda dan wallahi abun yaban tsoro kuma da wasu mata ake zargi saboda sunɗan samu saɓani tsakanin su dashi a danger to shine ake zargin ko su suka ɗauke su to amma commissionana ya kirani yace ya kamasu kuma basu bane dan yana da tabbaci akansu yayi duk binciken da zaiye har ƙulle su yayi a sale amma ya gane basu ɗin bane kawai dai sun taka sahun ɓarawo ne,
"Ƴan mata kuma daman banda abunku ku rasa wazaku zarga sai mata me mata zasuyi dashi dan kawai wannan ɗan abun da ya faru a tsakanin su, nima naji labarin su bandai gansu ba, amma tunda naji labarin nasan baza su aikata ba, kawai dai yanzu abun ayi haƙuri a jira kiran su dan nasan dole zasu kira suce suna buƙatar wani abun mukuma tanan za'a samu damar cafke su.
"Nima abun da nake taso kenan naso su kira inji me suke so, amma shiru shiru har yanzu basu kira ba"
"Abokina kar ka wani damu babu abun da zasuyi musu, kunsan ku masu kuɗi daman sai kunyi haƙuri da irin waɗannan abubuwan da ƴan baƙin ciki zasuyi muku...
Ɗan hararar wasa yayi masa ya ce; "Idan mu masu kuɗi ne ku kuma sai akiraku dame, ai irin ku zasu farayiwa kafin mu koh ya ƙarasa maganar yana ɗan yin ƙaramar wasa ta alamun zolaya.
"Shima murmushin yayi sannan yace; mu da ko rabun ku bamuyi ba ina wasu kuɗi anan..... Nan dai sukai ta tsokanar junan su kamar kananun yara saboda abotace tun ta yarinta, shiyasa idan suka haɗu suna mantawa da sun girma, a haka suka ɗau loƙaci ne ɗan tsawo suna tattaunawa cike da tsokana har suka gama yayo masa rakiya bakin ƙofa sannan suka rabu.......
*$$$$$$$$$$$$$$$$$$*
*R, K, D, UNIVERSITY KANO*
Kamar yanda suka saba haɗuwa idan sun fito daga lecture yanzu haka duk sun haɗu su duka biyar ɗin amma ba gida zasu ba zasu wuce su farayin lunch saboda a cikin su
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Chapter 36
Chapter 37
Chapter 38
Chapter 39
Chapter 40
Chapter 41
Chapter 42
Chapter 43
Chapter 44
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 7 Chapter of 44