masa tasan komai da yake ciki , amman tasan ko taki amincewa da shawarar nazafi me hali bazai fasa halinsa ba dan ba lallai idan ta fuskancesa ya fahimceta ba gashi har mugun halinsa yasa nazifi zarginsa akan bashi ne ya kawo Ibrahim duniya ba, da'ace shine ya kawo shi duniya tabbas duk son kudi irinsa nasa dole ya hakura ya rungumi rayuwar d'ansa dan bazai cutar da gudan jininsa ba wannan shine tmbyr da nazifi ya sha yi mata a tun sanda Ibrahim ya fara rashin lafiya ."
Cikin tsananin damuwa tace " wallahi shine mahaifinsa shine silar zuwansa duniya kawai dai haka rayuwarsa take yafi son kanshi akan kowa da komai, ta mike jiki a sanyaye ta shiga d'akinta a rikice Inda ta bar ib anan ta samesa kwance yayi shiru yana kallon sama d'akin tunanin tanweer yake yasan da lafiyarsa lau babu abinda zai zaunar dashi dole ta kowani hali ya dawo daita sai ga yadda Allah yayi dashi tashi ma baya iyawa bare akai ga magana duk wani kuzarinsa babu zuwa yanzu ya sadaukar da rayuwarsa adduar mutuwa yakewa Kansa ya huta da wannan rayuwar da yake ".
jin motsin shigowa d'akin yasa shi sauke idanunshi ya zubawa mata Idanunsa da suka rikid'e sukayi jazur , a kallon da yake mata ya fahimci bata cikin hankalinta da natsuwarta, ya cigaba da kallonta yana jiran yaji sautin muryarta ,itama kallonsa tayi dukkanin alamun sun nuna mata maganarta yake bukata ji, idanunta suka ciko da ruwan hawayen tausayinta dana yaronta ,ta zauna kusa dashi a bakin gado ta riko tafin hannunsa cikin nata hawayenta na diga .take hankalinsa ya sake tashi jikinsa ya kama rawa kamar mazari ya soma motsi da bakinsa alamun yana cewa wani abu amman babu hali .
a hankali ta fashe da matsanacin kuka tana kallonsa "na cuceka d'ana ,hakika ban maka adalci ba ,me yasa na auri mahaifinka gashi da kaina na zamo silar cutar da rayuwar d'ana ? na boye maka Mugayen halaiyan mahaifinka amman lokaci yayi da zan fayyace maka waye shi " duk wannan maganar da take acikin ranta take shima hawaye ne ke gangaro masa yana jin zafi da radadin halin da yake ciki da zubar hawayen mahaifiyarsa sai da tayi kukanta me isarta sannan ta zare hannunta cikin nashi tana shafa sumar kanshi "bari na gyara maka kwanciya ka kwanta kayi bacci inshallahu jibi duk yadda zanyi sai na bar gidan nan da Kai, bazan zuba Ido rayuwarka ta tagyayara ba, ta gyara masa kwanciya ta lullu'besa da bargo ta shiga bayi bayan minti biyar ta fito yana kallonta ta d'auki hijab dinta ta saka ta tsaya akan daddumar sallarta tare da tayar da sallah isha'i . "
bayan ta idar ta tashi ta fita zuwa kitchen babu kowa aciki kai tsaye ta shiga store din da kayan abinci yake , anan ta kira layin nazifi kira d'aya ya d'auka, ta fashe masa da kuka tana cewa"nazifi ka taimakeni tunda ka bar gidan nan na kasa samun natsuwa ,hankalina yaki kwanciya Ina ji ne kamar zan rasa Ibrahim dan Allah kasan yadda zamu bar gidan nan da Ibrahim daga gobe jibin da kace yayi min nisa dan bana son a bata lokaci dan a halin yanzu hankali yayi matukar tashi Ina ji ajikina kmr zan rasashi ne ,idan na rasa Ibrahim nima rayuwata tazo karshe zaka rasani ta k'arasa maganar tana kuka ".
" ki kwantar da hankalinki umma duk yadda kika ce haka za'a yi amman tafiya a goben akwai matsala saboda gbdy Shirin na jibi ne yanzu abinda za'a yi ki shiga d'akin ib ki soma had'a masa duk abinda kika san nashi ne me amfani inshallahu jibi zan zo da zarar dady ya bar gidan ,gobe idan zanzo zanzo da maganin bacci Koda zai zamo yana gida a jibi sai kiyi masa amfani dashi , bama anan zamu bar Ibrahim ba kasar ma gbdy zai bari na gama shirya komai tunda daman passport dinsa da naki zaku iya fita a duk sanda tafiya ta taso ".
"na gode! na gode !! nazifi Allah yayiwa rayuwarka albarka , yadda ka tsaya min kaima Allah ya tsaya maka bazan ta'ba manta hallacinka ba na gode sosai ".babu komai umma ai "yiwa Kai ne ban d'auki ib a matsayin amini ba kamar dan'uwa na d'aukesa Kuma wanda nake jinsa har cikin raina, Ina qunar ib Kuma zan iya masa komai idan ta kama zan iya sadaukar masa da rayuwata Allah dai ya bamu sa'a ."Ameen nazifi sun d'auki sama da awa suna tautaunawa Kiran alhj Tahir ne ya shigo har sau biyu yasa tayi masa sallama tana cewa "ka katse Kiran dady'nku na kirana ",to umma sai goben kenan , ya fad'a tare da katse Kiran ta d'auki Kiran alhj Tahir.
yana jin sautinta ya soma magana cikin fushi da zafin zuciya "kina Ina ne? sannan dawa kike waya haka tun dazu Ina kira busy busy ? "nida hjy zainab ne ,ta bashi amsa da hakan dan ta rasa me zata ce masa, ta godewa Allah ma da sunan yazo bakinta , naunayen ajiyar zuciya ya sauke "to ki fito ina falo "tace to gani nan zuwa .
Ta fito ta iske shi hakince akan d'aya daga cikin kujerun falon ta zauna akan kujerar dake fuskarta shi "me kuka tautauna da zainab din haka ? sai data zauna sannan ta fara magana "akan dai tanweer ne "
shiru yayi sannan ya gyara zama yana cewa " ko ta fad'a miki halin da'ake game da ma'aikatan nan dan yanzu na rasa gane kan lamarin nasu ?"eh to tace dai tanweer din ta kirasu cikin tashi hankali" a matukar firgice ya tashi daga rigin ginen da yayi ya zauna sosai yana dubanta a tsorace "uhm Ina jinki cigaba da bani labari sai data numfasa sannan ta cigaba" daga baya shima dan fashin ya kirasu tare da yi musu gargadi me karfi akan jami'an tsaro dake bibiyarsa idan suka cigaba da binsa zai kashe tanweer ta k'arasa maganar tana yin shiru.
"uhm to ita zainab din me tace ? Me kuwa zata ce ai tafi bukatar rayuwar diyarta nan dai tayita masa bayani kamar yadda hjy zainab tayi mata a wayarsu ta shekaran jiya ,jinjina Kai yayi kawai yana kallonta "Suma dai yanfashi nan da wasu kudin suka tambaya suka dawo musu da yarinyarsu cikin girma da arziki dan riketa da sukayi bashi da wani amfani hjy baseera tace" uhm " yace "eh mana to meye amfanin riketa da sukayi ?
duk abinda yace daga" eh! sai uhmmm take cewa a karshe ta tashi zata barsa "bari naje na kwanta. "tun yanzu ? ya fad'a yana duba agogon dake manne a falon. yanzu ne karfe goma tayi "eh yau duk ban zauna ba saboda masu shigowa duba jikin Ibrahim ko baccin ranar da nake dan yi yau ban samu nayi ba , ko akwai abinda kake bukata ne? "eh idan zan samu bakin shayi nake so "me zai hana zaka samu mana. mikewa tayi ta shiga kitchen ,cikin kankanin lokaci ta had'a masa har zata fito wani tunani yazo mata ta fito ta shiga dakinta ta d'auki kwayar tablet din da yake sa nazifi yana bawa Ibrahim ,ta fito ta markada ta zuba masa aciki shayinsa ta soma juya wa a hankali yadda bazai nuna ba "Kai ma kaji azabar da d'ana yake ji inshallahu kafin mu bar kasar Nan sai karfin jikinka ya ragu mugu kawai azalumi "
ta fito ta ajiye masa akan center table ta janyo gabansa alokacin yana kallon labarai ya d'auka ya kur'bi kad'an ya ajiye .
ita Kuma ta wuce daki tana shigowa Ibrahim ya bud'e idanunshi dake lumshe , a natse ta k'arasa Inda yake kwance ta Kai bakinta daidai kunnensa "Ibrahim d'ana jibi idan Allah ya Kai mu zamu bar gidan nan da Kai zuwa kasar Egypt domin duba lafiyarka tana gama fad'ar haka ta cire bakinta ya kura mata Ido yana bukatar qarin bayani "nasan Karin bayani kake bukata zanyi maka amman sai mun bar gidan nan .idanunshi ya shiga juya mata alamun bazashi koina ba, idanunta suka ciko da ruwan hawaye "idan har ban bar gidan nan da Kai ba mahaifinka zai yi sanadiyyar ruguza rayuwarka , idan har kana son ka mike bisa kafafunka ka taimaki tanweer ta dawo garemu dole sai ka bar gidan nan kayi nisa da mahaifinka ,zan maka bayani komai kamar yadda na fada maka amman sai mu bar nan , idanunshi ya lumshe mata alamun ya gamsu daita .ranar sam hjy basera bata runtsa ba ta zauna tana shirya duk abinda tasan zasu bukata har karfe d'aya saura sannan ta koma ta kwanta akan daddumar sallarta ."
****
Jaguwa ya gyara tsayuwa yana shafa qirjinsa da hannu d'aya sannan yana jin bayani amminsa daki daki akan matar data samo masa ,"ammi ki bar maganar wata hasera a yanzu , zanyi k'okari na kawo miki wacce zan aura ".ya fadi hakan ne ba dan zai Kai mata din ba sai dan ta rabashi da batun wata hasera .
a bangaren ammi ta katse shi da sauri "lokaci ya kure maka bazan sake baka wata dama ba dan naga alamun zuciyarka bata shirya amsar soyayyar kowace mace ba ,gara ni na shirya maka ga hasera nan ita zuciyata ta zaba maka Kuma ita zaka aura muddin Ina raye idan Kuma bujirewa zabina zakayi to sai ka sanar min ? ". Shiru yayi
tare da lumshe idanunshi a tsayen da yake dan amminsa ta rigada ta gama d'aure shi da maganarta "kayi shiru ko bazaka bi zabina bane nasani ? "
"Ban Isa ba ammi ,ban Isa naki bin zabinki ba amman ki canza min da wata ban da hasera" ya fad'a yana Jin wani sabon tashin hankali ya kusanto rayuwarsa "Amman Kaine kace duk wacce na zaba maka baka da ja ?sun d'auki tsawon lokaci suna tautaunawa a karshe yace ta bar maganar idan ya shigo karshen sati zasu sake tautaunawa akai ".
Bayan ya gama waya da ammi ya boye number ya kira mahaifin tanweer magana biyu yayi masa ya katse Kiran sannan ya kira number baba yana sheida masa zai maida tanweer gobe "bana ce maka karka kuskura ka maida yarinyar nan ba ?
"wannan yarinyar da kake tare daita a gidanka karka yarda ka rabu daita ko ka yarda ta matsa a kusa da Kai kmr yadda na fad'a maka a watanni da suka gabata ,
abinda bakasani ba ajikinta akwai taurari masu haske da karfin da zasuyi maka amfani akan aikinka ka barta a karkashika karka yarda ta bar karkashinka ".
"shiru jaguwa yayi yana tunanin abinda yake ta fad'a masa kenan kafin daga baya ya soma magana a sanyaye "bazan iya cutar daita ba sannan bazan iya amfani da taurarinta ba, idan da hali na zauna a yadda nake.
na samu duk abinda nake nema batare danayi amfani da taurarin kowa ba..".
"Wannan yarinyar dabam ce km ko ba yanzu ba dole zaka bukaci me irin taurarinta sai dai ba lallai ka samu ba dan haka ka barta kayi amfani da taurarinta ." bazan iya cigaba da zama da....."
"to ka aureta domin ta kasance a karkashin ikonka abinda ake so dai ta zauna tare da Kai ".
"Aure Kuma baba ?"
Mmn sudais
Mmn sudais💗💗💗💗💗💗
KUSKUREN BAYA
💖💖💖💖
💗💗💗💗💗💗
PAID BOOK
FREE PAGE
WRITING BY
AYSHA .A BAGUDO
WATTPAD @HAUESH
bismillahirrahmanirrahim
Wannan littafin na kudi ne mai bukata karanta shi ya tura 500 ta wannan account number din 1438775094 Aishat Abdullahi Access bank ,Idan a tura sai a turawa wannan number+234 703 534 8686alert domin tabbatar da an tura ko wannan number 08059623096 Idan Kuma vtu za'ayi sai a tura ta wannan number 08059623096 kada ayi vtu a number MTN domin sauraron littafaina a tuntubi channel dina ta hausa bakwai .
🅿️ 21
"Eh ! abinda nake nufi Kenan kuma nake bukata ka aikata, muddin wannan yarinyar bazata kasance karuwarka ba to ya zama lallai ka aureta Kuma acikin tsakankanin wannan lokacin ".
Cikin tsananin firgici da tsinkewar zuciya jaguwa yace " me yasa baba ? "mai yasa baza'a bar wannan maganar ba dan Allah ? " ni dai gsky a biyo wata hanyar banda wannan, tanwer tasan koni waye , tasan sana'ata fashi ne , nayi Imani Koda na fada mata zan aurenta bazata aureni da wannan sana'ar ba ya k'arasa maganar tare da yin shiru yana tunanin zuci "shi dai gaskiya komai za'a yi bazai taba auren tanwer da wata manufar ba ko cutar daita ba domin yana jinta ajikinsa tamkar jininsa ."
Shiru ne ya biyo baya na wasu mintuna kafin daga bisani baba ya numfasa kana ya soma magana a dake "Hanya daya ce zata maye maka wannan gurbin , ka nemi mace mai irin taurarinta ka ajiyeta akarkashin ikonka Koda bazaka aureta ba ka dinga saduwa daita saduwa irin ta aure idan kayi haka shikenan komai zai cigaba da tafiyar mana yadda muke so batare da wata matsala ba ."
"shiru jaguwa yayi yana kallon zara zaran yatsun kafafunsa masu tsananin kyau da sheki yana nazarin maganar baba, nan take gumi ya shiga tsatsafo masa a dukkanin ilahirin jikinsa, kwakwaluwarsa ta toshe zuciyarsa ta cunkushe guri daya , tunanin da yake ya tsaya cak ya Kasa cigaba da tunanin komai . sai daya dauki minti biyar tsaye batare da yasan madafar dafawa ba "amincewa auren tanwer Ko nemo mai irin taurarinta ya ajiyeta akarkashin ya dinga aikata zina daita "shi da yake neman yakice zina arayuwarsa sai ga baba na kokarin maidashi ruwa tsundum.
"Ya amince ne ko kuma ya fada masa a sake nemo wata mufutar ? sautin muryar baba ne ya dawo dashi cikin hankalinsa ta Inda ya cigaba da zayyano masa hujojinsa akan bukatar auren tanwer da yake son yayi Ko kuma ya shiga gari ya nemo mace me irin taurarinta idan ba haka ba nan gaba kadan za'a yi galaba akansa " .
duk abinda baba ya fada yasan yana da huja akan hakan kuma yasan ya fada ne domin ingata rayuwarsa daga sana'ar fashin da yake but shi baya jin zai iya ajiye tanwer a matsayin karuwarsa Ko aurenta domin samun wani biyan bukata daga gareta ". ya runtse idanunshi yana mai sake gyara tsayuwarsa yana jujuya maganganun baba yana sake fadadasu yana masu filla filla , gbdy komai ya tsaya masa.
ya sake neman natsuwarsa ya rasa , ji yake Kamar zuciyarsa zata buga tsabar shiga rud'ani tunanin matsalar dcp ,tanwer ,
Amminsa , yanzu Kuma ga matsalar baba da me zai ji?
"me ya kamata yayi ya samar ma zuciyarsa salama ? yana jin kamar yace babu abinda zai yi acikin umarnin baba wanda wannan shine Karo na farko da zai sabawa umarninsa a tun tsawon lokacin da suka dauka tare dan bai taba cewa ga abinda zaiyi ya mutsanta masa ba sai dai ya aiwatar . "
"tun yanzu ka fara tunanin shiga gari domin nemo me irin taurarin yarinyar nan ka ajiyeyata a matsayin karuwarka dan nasan bazaka taba aurenta ba tunda baka amince da auren yarinyar nan ba ."
Juya maganar baba yaketa faman yi acikin kwa kwaluwarsa , zuciyarsa ta dunkule guri daya yana jin Kamar ya daura hannu akanshi ya saka ihu ko yaji saukin zafin da zuciyarsa ke masa sai daya sanyawa jikinsa jarumta sannan yace "wacce irin alama ce zatasa na gane me irin taurarin tanwer ?
"Kenan kafin bukatar wata akan wannan yarinyar ?
"bazan iya cutar daita bane " ya fada yana furzar da iska mai zafi daga bakinsa, shiru baba yayi kafin daga bisani ya numfasa sannan ya cigaba da mgn "alamar da zaka gane me irin taurarinta , kana ganinta duk wata kafa ta gashi dake kwance ajikinka zata mike, take wannan zoben dake hannunka zai yi baki, abu na gaba tsuntsun dake ajiye a gidanka zai bayyana akanta wannan shine alamar me irin taurarinta amman fa bai zama lallai ka samu ba."
"zan samu ....." ina samun nasara akan komai dana saka gaba wannan Karon ma nasan zanyi nasara da yarda Allah "Ina maka fatan alkhairi da fatan samun nasara yana gama fadar haka yayi disconnecting din Kiran , jaguwa ya cigaba da tsayuwa agurun tare da lulu duniyar tunanin ."
bai dawo d'aki inda tanwer take ba sai wajen karfe d'aya da rabi na dare lokacin tuni tanweer tayi bacci a kasa tare da kankame jikinta guri d'aya saboda karfin ac d'akin yayi mata yawa , ya karasa ya tsugunna gabanta yana karewa jikinta kallo yana tunanin maganganun baba , ganinta yanzu kwance a gabansa yaji kamar ya amince da maganarsa sai dai take zuciyarsa ta dakatar da wannan tunanin dan haka yayi saurin kawar da maganar ya tsaida kwayar idanunshi akan fuskarta da tayi jawur alamun taci kuka .
a hankali ya Kai hannunsa yana shafa gefen fuskarta cike da tausayawa zafi yaji ya ratsa tafin hannunsa amman hakan bai hanashi Jin sanyi dadi a sansar jikinsa ba ,duk sanda zai kasance daita ya dinga jin irin wannan yanayin kenan ,ba ko wani irin yanayi bane illa kasala da tsananin sha'awarta haka zai dinga jin Kamar ana masa wanka da ruwan sanyi ."
Kallon fuskata ya cigaba dayi yana shafawa har zuwa kan tudun dukiyar fulaninta da suka dan bulluko ta saman rigarta wani irin zirrrrr yaji a gbdy ilahirin jikinsa kafin kace me jijiyarsa ta shiga harbawa da sauri sauri.
numfashi ya fesar yana jin kamar ya cire mata kayan jikinta ya soma sarrafasu "a hankali ya Kai hannunwansa zai ɗauketa firgigib ta bud'e idanunta ta watsa masa runannun idanunta tana sake kamkame jikinta waje d'aya ya matso sosai kmr zai shige jikinta tare da Kai bakinsa daidai saitin kunnenta ya kira sunanta cikin sanyayyiyar muryarshi mai tsananin kashe jiki da tsuma zuciya "tanweer !
Shiru tayi taki amsawa "idan bazaki bari na d'aukeki na kwantar dake ba ki tashi kije ki kwanta kar sanyi yayi miki illa " bata ce masa komai ba har sanda ta mike ta zauna shima ya matso kusa daita ya zauna yana shafa wuyanta zafi ne har lokacin ya sake ratsa tafin hannunsa yace " baki da lafiya ne ? sai da ta d'auki second biyar sannan tace " eh ! Ina dan jin zazzabi ne ,"sannu ya fad'a yana sake shafa gefen fuskarta "yauwa ta fad'a a sanyaye tana mai tsura masa Ido sai taga gbdy yanayinsa ya canza ba kamar da da yake mata Komai da gadara ba tausayinta ko tausayin Kansa ne ya maidashi haka bata sani ba ."
hakan ta dinga ji tausayinsa a ranta ya d'aukarwa Kansa muguwar rayuwa ,Allah ka shiryesa idan yana da rabon shiriya ta fad'a acikin ranta har karfe biyu ta buga jikinta da zuciyarta sunki saurara mata akanshi , tana son barin gidan tana tunanin matsayar soyayyarta agurinsa " Ina ma bashi da ta'bo komai da tabbas kowa zai tayata murna samun nagartaccen miji irinsa ya matso kusa daita sosai yana sake furta mata Sannu "nayi magana da mahaifinki zamu had'u dashi a gidan man royal stream gobe " tana jinsa amman taki cewa uffan ,ya kamo yatsun hannunta cikin nasa yana kallo farcenta masu kyau sai sheki suke a natse ya ɗauketa cak ya rungumeta tsam ajikinsa yana cigaba da kallon kyakkyawar fuskarta "zaki tafi gobe ki barni ?
ta lumshe masa idanunta alamun "eh! bai sake cewa komai ba haka bai sauketa akoina ba sai a tsakiyar gadonsa ya kwantar daita ya mata runfa da faffadan qirjinsa ya canza wutar d'akin zuwa mara haske yana mai lumshe idanunshi."
numfashi me zafi ta fesar qirjinta na sama da kasa a hankali ta Kai hannunta tana shafa sajen dake kwance a fuskarsa zuwa dogon hancinsa "zan tafi na barka me zaka bani wanda zan dinga tunawa da Kai ? ya bud'e idanunshi daya lumshe ya watsa cikin nata batare da yace mata Komai ba ,ya matso kusa daita sosai har tana Jin yadda qirjinsa ke bugawa fat fat kmr zai fasa qirjinsa ya fito, ya kwanta gefenta yana kallonta itama ta juyo suna fuskantar juna.
ya kamo yatsun hannunta ya jefa cikin bakinsa yana tsotsa a hankali yana cigaba da kallon kyakkyawar fuskarta acikin haske da bai gama haskake d'akin ba.
kallon juna suke cikin yanayi na tsananin soyayyar juna da buqatuwa da juna, sosai zuciyoyinsu ke bugawa da sauri sauri saboda yanayin da suke ji a sansar jikinsu "na tambayeka kayi shiru , shirunka na nufin baka bukatar na samu komai daga gareka ? ta fad'a tana shigewa jikinsa still bai ce mata komai ba ya janyo bargo mai taushi ya lullubesu acikin bargon ma suna manne da juna Kamar zasuyiwa juna numfashi .
sosai ta shige jikinsa "Adnan ......!
ta kira sunansa cikin kasalalliyar muryarta wani iri yaji a dalilin yadda ta Kira sunansa gbdy ta kashe masa jiki wani Abu yaji suna yawo a sansar jikinsa tun daga tsakiyar kansa har zuwa yatsun ka'fafunsa da kan jijiyarsa wanda bai taba ji akan kowacce mace ba sai akanta .
"Adnan kace min wani abu mana ka fada min abinda zaka bani wanda zai dinga debe min kewarka idan na tafi " still dai shirunsa ne ya biyo baya ta numfasa ", ni idan bazaka bani ba ka fad'a min abinda zan baka Wanda zaka dinga tunawa dani ,nayi alkwarin komai kace zanyi maka shi acikin a daren nan ."
Lumshe idanunshi yayi yana me sake shigewa jikinta yayinda jijiyarsa Ke sake shiga cikin garari da kaiwa kololuwar bukata da kyar ya fixgo magana " bana bukatar komai iya soyayyar da kika nuna min ma ta Isa "To ni me yasa baka sona alhalin kasan Ina sonka ? dan Allah Adnan ka soni kuma kar ka manta dani, dan ni Ina sonka da gaskiya ,ka rikeni aranka.
" ka rabani da abu me mahimmancin amman still zuciyata na sonka ban san wani irin so nake maka ba wallahi idan ka manta dani zan iya mutuwa dan bazan juri zama a duniyar nan babu Kai ba .
"wallahi Adnan tunda nake ban taba gani mutumin da ya shiga zuciyata farar daya kamarka ba, Adnan ka sace zuciyata da komai nawa dan Allah Adnan ka bani dama na shigo rayuwarka domin na canzaka sannan na zama abokin rayuwarka ."
Shi dai jaguwa jinta kawai yake yi har ta gama zubanta shi bai ce kala ba "adnan nasan kana jina ka shareni "Dan Allah ka min magana ko naji sanyi azuciyata I love you more than anything in this world ba karamin dadin kalamanta yaji ba sai dai yaki furta komai .
"don girman Allah ad ....." a sukwane ya toshe mata baki da bakinsa hannunsa Kuma ya hau shafa mata sansar jiki dashi sai daya tsotse mata baki tass sannan ya zare bakinsa yana cewa "bazan manta dake ba arayuwata , zanyi k'okari na dinga tunaninki sau biyu a rana ya fad'a cike da zolaya yana jan karan hancinta ".
"sau biyu kawai ?tayi mgnr a shagwa'be tana dukan qirjinsa ya kamkameta tsam ajikinsa yana busa mata numfashinsa "shikenan zan dinga tunaki akai akai , zanyi kewarki sosai .
dadin maganarsa ta sake narkar mata da zuciya , ta kai yatsun hannunnta tana yawo dasu akan fuskarsa tana jin tmkr su hade su zama abu guda .
Yayinda shi kuma ya kai hannunsa qirjinta yana mata tafiyar tsutsa yana ciza lips dinsa na kasa "taya ma zan iya mantaki a rayuwata ?yayi maganar a kasan ransa" kin jiyar Dani dadin da ban ta'ba ji ajikin kowacce mace ba ,Kuma nayi Imani bazan sake ji ba in ba Ina tare dake ba" ya kamkameta sosai ajikinsa kmr zai rabata gida biyu yana shafa ta yana Jin wani maganadisu sonta na shigarsa, yaji sha'awarsa data tafi tana Shirin dawowa gashi bazai iya aikata komai daita ba .
ya birkitota saman qirjinsa ta kwanta a saman lafiyayyen qirjinsa tana sakin numfashi "washhhh.. ! cike da shagwa'ba tace "ka Aure ni please" shiru yayi yana faman shafa bayanta "please Adnan ka daina wannan sa'anar ka aureni sam sana'ar nan bata dace da Kai ba "naji zanyi tunani akansa" "batun auren fa ka fad'a min zaka aureni ko bazakayi ba ? "surayya !
ya kira sunanta muryarsa a kasalance ta shige masa sosai batare data amsa ba, bata ta'ba jin wanda ya iya Kiran ainihin sunanta ba kamarsa "bazan iya abinda kike bukata ba a halin yanzu da zuciyata take cikin garari da tashin hankali Kiran da kikaga na fita na amsa Kiran ammina ne wai ta samar min matar da
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Chapter 36
Chapter 37
Chapter 38
Chapter 39
Chapter 40
Chapter 41
Chapter 42
Chapter 43
Chapter 44
Chapter 45
Chapter 46
Chapter 47
Chapter 48
Chapter 49
Chapter 50
Chapter 51
Chapter 52
Chapter 53
Chapter 54
Chapter 55
Chapter 56
Chapter 57
Chapter 58
Chapter 59
Chapter 60
Chapter 61
Chapter 62
Chapter 63
Chapter 64
Chapter 65
Chapter 66
Chapter 67
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 26 Chapter of 67