masa gidan baya ya shiga yana cewa "hope kowannenku yayi shiri me kyau? " sosai suka bashi amsa motarsu na kokarin fita daga gidan Idanunsa ya sauka akan wani dattijo zaune a gindin bishiyar dake gefen gidansa nan take yace wa eku "stop ! ".eku ya tsaya nan take mutumin ya mike tsaye yana kallon motocin jaguwa masu shegen kyau da daukar hankali da hannu ya yafito me gadi ya k'araso da d'an saurinsa ya tsaya yana rusunwa "wacan mutumin fa me yake yi anan ? "wallahi oga gurinka yazo wai yana son ganinka tun jiya byn fitarka yazo nace baka nan shine dazu byn dawowarka sai gashi ya dawo na shiga domin nasar maka sky yace Kuna meeting shine na dawo na sheida masa ya dawo Koda karshen sati ne amman yace lallai sai ya ganka ."
shiru jaguwa yayi yana nazari sannan ya dan Kalli Inda dattijon mutumin yake tsaye cikin kod'ad'un kaya marasa fasali yana cigaba da nazarinsa ,a hankali ya fito ya soma tafiya har ya k'araso garesa , dattijon na ganinsa ya shiga rawar jikin "barka da fitowa ranka ya dade "barkanmu baba ya kwanan iyalin ?" Alhamdulillah duk muna Lafiya ,
jaguwa ya kad'a Kai sannan yace " baba fatan dai lfy kake son ganina ?"dattijon ya marairaice murya kmr zai yi kuka sannan ya fara mgn muryarsa na rawa gwanin tausayi "daman matsalace ke tafe dani gareka a wajen mutane na samu labarin irin taimakon da kake yiwa mutane ". jaguwa na jin haka ya sauke numfashi yana dubansa a tsanake " Ina Jinka baba wacce irin matsalar ce ?"daman akan yarona ne shekararsa biyar kenan da kammala karatunsa na degree sai dai yadda kasar nan tamu ta dawo yasa har yanzu yake gida zaune, duk Inda yaje apply din aiki sai ace sai ya biya kamin dubu dari biyar kudin office kafin a daukeshi gashi bashi da hanyar da zai samu kudin, ni ya kamata na biya masa ya samun aikin to ni din ma babu dan na abinci ma da kyar muke samu, dan Allah ka taimakeni kamar yadda Allah ya taimakeka ka samo masa aiki ko Kuma ka yarda ya kasance a karkashinka ya karasa maganar yana zubar da hawaye ."
jaguwa yayi shiru yana sauraronsa har sanda ya dasa aya "karkayi kuka baba inshallahu zan yi iyakar kokarina yanzu dai Ina kan hanya ne zani wani aiki amman ka dawo zuwa karshen sati da yaron inshallahu matsalarka tazo karshe dattijon ya soma k'okarin durkusawa jaguwa domin yi masa godiya, jaguwa yay saurin sa duka hannuwansa ya taresa "haba baba karka min haka mana " na gode d'ana Allah ya albarkaci rayuwarka , Allah yasa ka gama da duniya lafiya ,Allah ya jikan iyayenka idan sun rigamu gidan gsky, idan Kuma suna raye Allah ya Kara musu Lafiya mai amfani na gode na gode daman da gaske ana samun mutane irinka ?karka damu baba ya k'arasa maganar yana tsaida dattijon bisa kafafunsa ya Ciro dubu goma a aljihun wandonsa ya mika masa "ga wannan kayi kudin mota yana gama mikasa ya juya ya shiga mota suka bawa motacinsu wuta suka bar unguwar ,da sauri dattijon ya Ciro wata rubabbiyar wayarsa ya shiga neman number d'ansa domin yi masa albishiri ."
******
Bangaren minister of health kuwa gbdy hankalinsa yaki kwanciya kullum yana manne da hjy zainab yana rarrashi wacce kuka ya zame mata abincin ruhinta , yanzu ma zaune yake kusa daita yana aikin daya saba tare da babban amininsa alhj Tahir dake k'okarin shawo kanta "kada kiyi fushi da hukuncin Allah zainab wannan abu daya faru gbdy bai mana dadi ba sai dai bawa baya wuce qaddararsa Allah ya rigada ya qaddaro surayya zata fad'a cikin wannan tashin hankali bamu Isa mu canza mata qaddararta ba, fatan mu dai Allah yasa bata cikin tsanani cikin muryar kuka tace "na kasa jurewa dady dake hk take kiransa kmr yadda Ib ke kiransa " yau da mutuwa tanweer tayi na binneta da zan fi samun natsuwar zuciya amman Ina raye tanweer tana hannun 'yan fashin da ko labarinsu ba'a samu ba , taya kuke tunanin hankalina zai kwanta ?". Suma kiramu muji me suke bukata daga garemu sunki ta k'arasa maganar tana kallon saman falon hawaye masu zafin gaske na gangaro mata wanda zafinsu da rad'ad'insu ya wuce tunanin mai karatu .
"wannan haka ne amman duk da haka addua zamu taru muyi allah ya bayyanata cikin koshin lfy "amen ta furta a kasan makoshi tana cewa ya jikin Ib kuwa? kullum Ina sa ranar zanzo na dubasa mutanen dake shige da fice agidan nan zuwa jaje ke hanani fita ammn inshallahu zan samu lokaci na leko na dubashi .
"to jikinsa dai da sauki zamu ce Allah dai ya iya mana da iyawarsa dan rayuwar Ibrahim na daf da fuskantar matsala da Kuma qalubalin rayuwa ya kasa jurewa rashin tanweer "Allah sarki ib yana qaunar tanweer kmr yadda yake qaunar rayuwarsa inshallahu zata dawo har ma suyi aure ta k'arasa maganar tana sake matso ruwan hawaye sun dade suna tautauna wa akarshe minister ya kira cp yaji halin da'a ake ciki ,byn cp ya d'auki Kiran suka gaisa "wai ya ake ciki ne da batun yarinyata shirun fa yayi yawa zuciyata ta fara tsinkewa Ina Jin kamar Allah ya d'auki raina na huta ? na kasa jurewa rashin diyata da rashin kwanciyar hankalin matata ".naunayen ajiyar zuciya cp ya sauke sannan ya fara magana a natse"mun baza mutanen mu cikin gari yanzu haka mun fara samun improvement akan lamarin "to alhamdulillah Allah ya taimaka yasa aga yarinyata cikin koshin lfy "karka damu inshallahu komai yazo karshe ka kara mana lokaci kad'an "na gode na gode " sukayi sallama minister ya fuskanci hjy zainab tare da yi mata albashiri da abinda cp ya fad'a masa nan take farinciki ya mamaye zuciyarta shi kuwa alhj Tahir cikinsa ne ya duri ruwa gabansa ya shiga fad'uwa hankalinsa yayi kololuwar tashi .
babu shiri yayi musu sallama ya shiga motarsa direbansa ya ja suka kama hanyar zuwa gida ,yasan ya taro wa kanshi match tunda yayi sanadin da'aka d'auke tanweer wayarsa ya Ciro yanata Kiran number jaguwa ana ce masa akashe take har ya k'araso gida bai samesa ba , ya rasa yadda zaiyi da rayuwarsa yasan muddin su jaguwa sukazo hannu kashinsa ya bushe domin asirinsa ya tono ."
fitowa yayi da sauri daga cikin motar bai tsaya jiran direbansa ya fito ya bude masa ba kmr zai tuntsura ya shiga cikin gidansa gumi na karyo masa ta koina a sansar jikinsa kai tsaye bedroom dinsa ya shiga ya rage kayan jikinsa ya shiga zariya yana neman mafuta , yana tsaye hjy baseera ta shigo tana binsa da kallon mamaki dan ta kwana biyu bata gansa cikin yanayi irin haka ba "wai Lafiya ka shigo kamar wani kububuwa me km ya faru ? tsaki yaja yace "babu komai . "To daga Ina kake yanzu "?. daga gidan minister nake ya bata amsa yana fifita da hannunsa dan wani irin azababben zafi yake ji ta koina tana Jin haka na gane komai ta kama gabanta zata fita ya d'auki remut din ac yana kokarin qara karfinta tare da cewa "ya kuma zaki wuce ki barni ga dan iska kin samu kin tmbyeni na baki amsa kawai zaki juya ki kama gabanki "oh to ni me zanyi maka ?" zata sake magana ya d'aga mata hannu"jeki kawai bananason jin komai tunda babu abinda zakiyi shasha kawai ya fad'a a matukar fusace yana juya mata baya.
tabe baki tayi a ranta tace "ai Kai ne Sha Sha ,mutumin banza kawai da bai san ciwon kanshi ba aurenka ko hasara duk a tunaninka ban San halin da kake ciki bane byn na san komai a juri zuwa rafi dai wata rana tulun zai fashe juya tayi ta barshi tsaye yaji da damuwarsa .ta nufi gurin d'anta ta bashi maganin karfin jiki dan ta sha alwashin bazata sake yarda da tsarin mijinta ba hk kawai ta rasa tilon d'anta a banza, gbdy magungunan da yasa nazifi ya rubuta masa an siyo sai dai bata bashi ya sha ba wasu dabam ta bashi jikin ne dai nashi yaki daidai saboda an rigada an karya masa garkuwar jiki " .
*******
Sannu a hankali motarsu jaguwa ta d'auki titin airport suna gama Isa kowace mota ta samu guri ta tsaya a Inda jaguwa yayi umarni tare da saka fuskokin roba , motar da jaguwa yake ciki ne kawai ta Kai cikin mutane sosai. shiru yayi yana nazari da karewa gurin kallon da tarin mutane dake bin mutane ko suna bukatar canza kudi .facing cap dinsa ya cire ya juya ta baya ya cire glass din dake manne da idanunshi ya makala a goshinsa bayan kamar minti talatin ya ciza lip's dinsa na kasa da karfi ya fito rike da bindigarsa ak 47 yana gama fitowa ya fara sakin harbi kamar ruwa domin Kore mutane dake safa da marwa agurin , kafin kace me mutane sun rud'e tare da neman gurin 'buya bayan kmr minti biyar sai ga anas shima ya fito had'e da harbi nan ma sauran mutanen da suka rage suka tarwatse ya tsaya yana huci "iam bally the deadly one, mutun ya kama kanshi idan baya son ya bukunci lahira ."ya fad'a yana sauke numfashi .
jubi ya fito ya saita bindigarsa wani lungu Inda ya hango wasu mutane suna likensu sai dai bai yi harbi ba bisa umarni jaguwa dake duk suna Jin maganarsa sakamakon connecting din da yayi da wayoyinsu ya sauke numfashi yana cewa "as you can see am gentle man to the core , I don't take what's beyond my capacity disprit that iam not the one to be taking for granted , go and ask those how have done such before ya k'arasa maganar yana numfasawa tare da gyara tsayuwarsa eku remo ya k'araso ya tsaya gefen jaguwa rike da bindigarsa yana cewa ""Jaguwa ne da kanshi d'an mutuwa Kuma mutuwa ta dade da kar'basa amatsayin d'anta so everyone should run for his life "yana gama fad'ar haka ya koma gurin tsayuwarsa ya had'e da sauran yan'uwansa suka tsaita bakin bindiga ."
Shiru jaguwa yayi ya fuskanci office din da aka kwatanta masa jubi ya matso kusa dashi yana cewa " jaguwa let's move to his office jaguwa yace "da alamun bai nan jikina ya bani amman Kuma wannan lokacin anamdi ya bamu "to mu juya mana mu koma girgiza masa Kai yayi yana ciza lips dinsa na kasa "to ko zamu shiga office office ne muyi operation ?"no ya bashi amsa atakaice "okay ya fad'a yana gyara bindigarsa .gbdy gurin ya d'auki shiru ciki kuwa har da jami'an tsaro dake aiki agurin kowa nason rayuwarsa dan da ganinsu an san ba kananun yan fashi bane ."
Loakaci zuwa lokaci yake duba agogo dake d'aure a tsintsiyar hannunsa Bayan kamar minti talatin sai ga wata mota fara sol ta shigo gurin. tun da suka shigo tsoro ya kama na cikin motar sakamakon ganin gurin shiru babu motsin mutane jaguwa ya gyra bluetooth din dake manne da kunnensa "eku ga mutumin da muka zo dominsa nan ya shigo "okay boss I will do my duty .cike da matsanacin tsoro direban motar yaja burki yana k'okarin juyawa sakamakon ganinsu take eku ya harbi tayar motar .
tsayawar motar ke da wuya yaga mutane sun zagaye motar kamar almara sai ga jaguwa ya bayyana a tsakiyarsu direban yayi saurin kife kanshi akan stearing motar yana rawar jiki , jubi ya bude murfin site din baya Inda alhj aminu ke zaune ya fito dashi yayi cilli dashi gaban jaguwa ya tsaita kanshi da bakin bindiga "where's the money jikin mutumin na rawa yace "it's inside the car ya fad'a yana nuna motar "cheek ! inji cewar jaguwa".Anas da kamil suka nufi motar suka duba can byn second biyu anas yace "comform it's there "okay fine ,move move kamil ya fad'a yana ture alhj aminu " face the grand if you do nonsense i will kill you ,nan take alhji aminu yay sujjada gbdy ilahirin jikinsa na kyarma .
Suka jefa jakar kudin byn motarsu jaguwa ya shiga byn mota sauran dake shirin shiga sai ga jiniyar motacin police suna harbi ,ai nan take qarar harbi ya karad'e gurin police na harbi Suma suna yi kowa ya shiga mota har sun fara ja ya saura kamil ne bai samu damar shiga ba ya biyo motar aguje yayinda sauran yan'
uwansa ke harbin yansanda suna Kiran sunansa "km run kayi gudu mana suna miko masa hannu shi kuwa gudu yake da iyakar karfinsa yana k'okarin Isa ga motar gabad'aya suka mika masa hannuwansu suka had'a baki "zo kamil zo gamu maza mana kamil ka kara gudu suka fad'a hankalinsu a tashe .ganin halin da ake ciki yasa hankalin jaguwa yayi matukar tashi nan fa ya shiga bud'ewa police wuta daf da kamil zai shiga mota wani police yayi nasarar harbinsa a kafa wata razananniyar qara ya saki ya durkushe kasa cikin azaban ciwo tare da rike kafarsa "...
Mmn sudas💗💗💗💗💗💗
KUSKUREN BAYA
💖💖💖💖
💗💗💗💗💗💗
PAID BOOK
WRITING BY
AYSHA .A BAGUDO
WATTPAD @HAUESH
bismillahirrahmanirrahim
Wannan littafin na kudi ne mai bukata karanta shi ya tura 500 ta wannan account number din 1438775094 Aishat Abdullahi Access bank ,Idan a tura sai a turawa wannan number+234 703 534 8686 alert domin tabbatar da an tura ko wannan number 08059623096 Idan Kuma vtu za'ayi sai a tura ta wannan number 08059623096 kada ayi vtu a number MTN ,domin sauraran littafaina a tuntubi Channel dina ta Hausa bakwai.
🅿️14
.....Cike da zafin rai da zafin zuciya jaguwa ya soma k'okarin fitowa daga cikin motar yana gyara bindigar hannunsa nan fa hankalinsu anas yayi kololuwar tashi , anas ya rud'e yay saurin dakatar dashi ta hanyar Kai hannunsa qirjinsa "karka fita jaguwa , kaucewa yayi yana cewa "ku wuce kawai zanji da komai "dan Allah jaguwa karkayi wannan kasadar ". bai sake saurararsa ba ya soma harbi gumi na karyo masa , hakan yasa da sauri kowannensu ya cigaba harbi da iyakacin kwarewarsa ."
da mugun gudu jaguwa ya isa inda kamil yake durkushe rike da kafarsa yana cewa "km bani hannunka " , cikin tsananin tashi hankali kamil ya d'ago kai sai dai bashi da kuzarin da zai mika masa hannunsa " nace ka bani hannunka ya sake mika masa hannu shima kamil ya mika masa ya rike hannunsa gam cikin nashi yana cewa "taho km ka mike dan allah karka bari mu rasaka " kamil ya fara k'okarin mikewa adaidai lokacin da sky ya juya kan mota zuwa inda suke tare da yi musu tsakani da police officer's , cikin azama jaguwa yace " maza mike km da taimako allah jaguwa ya shigar da kamil cikin mota ai kuwa shigarsu motar keda wuya suka figi motar aguje nan motocin 'yansanda suka biyosu da mugun gudu suna harbi suna danna jiniya , haka suma bangaren jaguwa harbinsu suke , gudu sosai motacin jaguwa sukayi har suka yiwa police nisa a karshe suka daina hangosu ."
a matukar wahale suka k'araso gida jaguwa yay saurin fitowa daga cikin mota ya k'arasa da sauri ya bud'e kofar shiga cikin ainihin falon gidan , su jubi suka kamo kamil suna tafiya dashi a hankali kafafunsa babu takalmi dan tuni sun cire masa tun acikin mota ,Kai tsaye suka nufi hanyar falon jaguwa na mussaman dashi suna masa sannu, a hankali suka kwantar dashi akan wani k'aramin madaidai gado wanda daman an tanadesa domin irin haka ,kamil ya runtse idanunshi saboda azabar ciwo , cike da hanzari jaguwa ya nufi Inda first aid box dinsa yake ya d'auko ya dawo da sauri , eku ya janyo masa kujera ya zauna a gaban kamil yana masa sannu ."
jin motsin shigowar motocinsu da maganar wasu daga cikin yaransa sama sama yasa tanweer lalla'bowa babu takalmi a ka'fafunta tai hanyar babban falon gidan tana bin bango tana qarasowa bakin kofar falon ta tsaya a hankali ta bud'e kofar ta shiga bata ga kowa a falon ba, kasa kasa take jiyo magangansu , kawai ta nufi wani dogon korido Inda take zaton daga nan sautinsu yake fitowa , a hankali ta tsinci kanta acikinsu kowannensu cikin tsananin tashin hankali , jaguwa zaune a gaban kamil cike da tausayawa yana k'okarin cire masa harsashi . binsa tayi da kallon mamaki qirjinta na wani irin bugawa da matsanacin karfi shafa idanunta tai hade da runtsesu na second biyu sannan ta bud'e tana sake sauke idanunta akanshi wanda zuwa lokacin har yay nasarar ciro bulet din yana kallo sannan ya saka acikin farantin silver dake rike a hannun jubi, yayinda sauran ke zaune cikin tsananin tashin hankali gbdy idanunsu ya rufe babu wanda hankalinsa ya Kai Inda take tsaye ."
naunaye ajiyar zuciya suka sauke lokacin da jaguwa ya cire wa kamil bulet ita Kuwa tanweer zuciyarta ta shiga rawa had'e da tsinkewa ."me zata gani yau ? daman likita ne shi ko kuwa mafarki take ? yes wannan ba mafarki take ba shine tagani zaune ya cire bulet a kafar abokinsa, kasa tayi da idanunta tana kallon bayansa nan idanunta ya hango bindiga pestol soke a abayan wandon jaguwa ,nan take ta sake fita daga haiyacinta "bindiga ....! ta furta a kasan ranta " me Kuma yake yi da bindiga ? ya Allah karka sa abinda zuciyata ke hasashe akansa ya zama gaskiya dan bai cancanci haka ba " wani kuka ya kufce mata ta juya da sauri tana shesheka wanda hakan yasa gbdy suka d'ago suka ganta tana sarsarfa , cike da matsanacin firgici suka tsura ma jaguwa Ido dan jin abinda zai ce bai yi magana ba haka zalika bai nuna alamun damuwa atattare dashi ba , ya mike tsaye yana
furzar da numfashi tare da yiwa kamil sannu" ka kwanta ka huta kafin akawo maka abinci ya gyada masa Kai yana cewa" na gode abokina Ina alfahari da Kai ,nima haka ."
jubi ya dube jaguwa yana cewa "wallahi ban ta'ba shiga tashin hankali ba irin na wannan lokacin na tsorata matuka na sadaukar zamu rasa kamil "ba kai kad'ai ba inji cewar anas tafiya jaguwa ya fara a hankali suka biyosa a baya har gurin shakatawarsa "da'ace sunyi nasara akanmu zamu iya rasa rayukanmu gbdy". sai lokacin jaguwa ya motsa lip's dinsa "ina ai sai dai idan tawa ta kare sannan zaku iya shiga wannan hali amman muddin Ina tsaye akan kafafuna babu wanda zai yi nasara bare har mu rasa rayuka " ya karasa maganar tare da tsayawa cak ya rike karfen runfar dake kafe acikin gurin shakatawar , "hakika Nima na karaya inji cewar jabir " Karku ta'ba rungumar Karaya arayuwarku duk halin da zamu shiga karku karaya saboda rashin samun nasara ba namu bane ,a duk lokacin da naga Kun Karaya sai naga kamar tun asalin ku din ba jaruman gaske bane, sannan baku ne jarum da mukayi gasar mutuwa dasu ba ."
murmushi sukayi gbdy suna sauke numfashi "uhm wannan fa ba kamar gasar mutuwa bace ,gasar mutuwa kowa yasan mun saida rayukanmu ne dan biyan bukatarmu wannan fa ?"bayan sai da rai har da tozarci zamu janyowa gangar jikinmu idan muka tsinci kanmu a hannun jami'an tsaro ".anas ya karasa maganar yana dafa kafad'ar jaguwa "yanzu dai barkanmu allah ya k'ara karemu ." ameen jaguwa ya fad'a acikin zuciyarsa. "ka zauna kana bukatar hutu, jaguwa ya zauna akan d'aya daga cikin kujerun gurin yana lumshe idanunshi " me za'a kawo maka ka d'an sha ? ya girgiza masa Kai alamun bai bukatar komai , zama anas yayi kamar yadda sauran abokansa sukayi yana cewa "ya za'a yi da wannan yarinyar ta rigada taga komai , koma nace taji wasu abubuwa akanmu ? ,yana d'aya daga cikin abinda yasa kaga banason yarinyar nan agidan nan "."me taji ?."Ko me mu kace ?yay masa tambayar a dan kufule " idan Kuma taji taji kenan shikenan daman abinda take bukatar sani kenan tasan su waye mu " ya k'arasa maganar yana jan dogon tsaki tare da jin bakinciki da takaici, haka nan Kuma ya tsinci Kansa da Jin fad'uwar gaba mai tsanani ".
Koda tanweer ta koma d'aki ta kasa tsaye ta kasa zaune sai zariya take acikin d'akin ita kad'ai, ta saka wancan ta kwance , kwakwaluwarta ta shiga tunani mai zurfi, babu abinda zuciyarta bata kisama mata ba akansu , abu uku zuciyarta ta tsayu akansa shi din dan fashin ne ko Kuma jami'in sirri ,ko likita , idan ba haka ba me yake yi da bindiga ajikinsa ? ta kasa hakuri dan haka ta sake fitowa tai hanyar boys quarter nan fa hankalinta ya sake tashi ganin yadda yaran jaguwa ke fitowa da manya bindigu suna adanawa a maboyarsu ,mutuwar tsaye tayi har sanda suka kwashe komai suka d'auki katuwar jakar kudin da suka shigo dashi suka nufi hanyar Inda jaguwa yake tare da abokansa suna tautaunawa , cike da matsanacin tsoro ta biyo bayansu a tare suka k'araso ta ra'be jikin wata bishiya kasancewar yaran jaguwa suna gabanta yasa jaguwa da abokansa kasa ganinta ."
sky ya ajiye jakar kudin a gaban jaguwa yana cewa "boss ga kudin operation din ". operation ? ta furta a kasan ranta zuciyarta na tsananta bugu kamar zai fasa qirjinta ya fito waje , tayita tunanin abinda manufar operation yake nufi acikin ranta .
a natse Jaguwa ya d'ago idanunshi yana ciza lips dinsa na kasa sai daya d'auki minti biyar sannan ya gyada Kai , yay musu alamun su wuce suka soma k'okarin juyawa tana ganin haka tayi baya da sauri ta la'be dan karsu ganta , gbdy kwakwaluwarta
ta gama tabbatar mata da manufar operation fashi ne ".barin wannan bishiyar tayi ta dawo kusa dasu sosai ta sake makalewa a wata bishiyar ta kasa kunne daga Inda take boye take jiyo duk abinda suke cewa "mun gama da operation din yau yanzu dai a kasa kudin gida uku nasan inamdi na nan zuwa komai dare ya amshi kasonsa dan bashi da hakuri kmr alhj Tahir yake "kamar alhj Tahir ta maimaita sunan ?tunanin Inda tasan sunan take gbdy ta kasa tuno Inda ta ta'ba Jin sunan amman tabbas kwakwaluwarta na hasko mata tasan sunan Kuma na kusa da jikinta ne ".
ko gama rufe baki jaguwa bai yi ba sai ga inamdi da eku remo , inamdi ya mikawa jaguwa da abokansa hannu suka gaisa shi Kuma eku ya juya ya kama gabansa .
guri jaguwa ya nuna masa da hannunsa , ya zauna yana cewa "sannuku Kun sha da kyar lokacin dana ga police sun harbi d'aya daga cikinku naji tsoro matuka, hankalina yayi matukar tashi "sa'anar armrobber's akwai dadi akwai saida rai ,bancin kwarewa irin naka da yanzu kuna hannun police.
"inna lilli wa inna lillahi rajiun" tanweer ta shiga furtawa tana maimaiwa tasa hannunta duka ta rufe bakinta dan kar sautin kukanta ya fito "ya dai tabbata su din 'barayi ne ........? " wannan shine dalilin da yasa ya fad'a mata da tasan shi ko waye shi da bata kamu da soyayyarsa ba ?wayyohhhly Allah nah ! "wayyohhhly Allah Adnan me yasa? " me yasa ka zabi wannan sa'anar ? jikinta banda rawa babu abinda yake tana kallo aka kasafta kudin aka bawa inamdi nasa kason ya ciro wata karamar jaka a aljihunsa ya shiga d'aukar bandir din daloli yana zubawa cikin jakar har ya gama ya mike ya sake mimika musu hannu sukayi sallama ya wuce cikin sauri ."
A hankali ta dinga d'aga ka'fafunta tana takowa zuwa Inda suke zaune , jaguwa ne ya d'ago idanunshi suka sauka akanta, cikin tsananin tashin hankali da damuwa mara misaltuwa yake kallonta ,bakinta na rawa ta soma magana cikin firgici "daman 'yan fashi ne ku ?".ta fad'a tana kallonsu d'aya byn d'aya .a rud'e abokan jaguwa suka had'a baki gurin cewa" no mu ba 'yan fashi bane armrobber's ne" jaguwa ya mike a natse cike da bakinciki taji sirrinsu yayinda gbdy abokansa suka rud'e da ganinta har suka kasa bambamce tsakanin abinda tace da amsar da suka bata , fuskarsa a murtuke tamkar wanda aka aikowa da sakon mutuwa ya kallesu d'aya bayan d'aya kana ya soma mgn "babu bambamci da abinda
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Chapter 36
Chapter 37
Chapter 38
Chapter 39
Chapter 40
Chapter 41
Chapter 42
Chapter 43
Chapter 44
Chapter 45
Chapter 46
Chapter 47
Chapter 48
Chapter 49
Chapter 50
Chapter 51
Chapter 52
Chapter 53
Chapter 54
Chapter 55
Chapter 56
Chapter 57
Chapter 58
Chapter 59
Chapter 60
Chapter 61
Chapter 62
Chapter 63
Chapter 64
Chapter 65
Chapter 66
Chapter 67
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 14 Chapter of 67