da Ido sai dai hannunsu bai ka ga jikinta ba suka hanata ta'ba kowacce mota a daidai lokacin su anas suka fito suka tsaya suna dubanta .
xagi ba kalar da tanweer bata musu ba da hausa da turanci Amman Babu Wanda ya kulata haushi ya isheta ta bar gurin mota ta nufi bakin get nan ma babu hali dan me gadi yaki bude mata get duk Inda tasan zata bi ta fita daga gidan babu hali ta shiga maseefa tana cewa " sai na bar gidan Kuma Babu wanda ya Isa ya hanani fita idan na bar gidan sai na sa ankamaku anyi muku hukunci me radadi,wallahi da Kun San Koni wacece a garin nan da baku tsaya bin umarnin wannan ba Kun hanani fita ba, ta juya ta Kalli Inda jaguwa yake tsaye jikin motarsa Idanunsa na kanta yana cigaba da kallon bakin tsiwa "zan nuna muku ko ni wace acikin garin nan tare da juya masa baya.
"Kashi Amman na tausaya miki wannna shi ake kira da power less" juyowa tayi cikin fushi ta Kalli Inda yake idanunta ya sauka akanshi.
yana nan tsaye sai dai zuwa wannan lokacin ya harde hannuwansa a qirji yana mata murmushin mugunta fuuuu ta nufosa cikin tsananin fushi da zuciya tace "zan nuna maka wannnan power din kasa Ido ka gani"tayi mgnr tana nunashi da yatsa "me zaki iyayi ?ba abinda zaki iya yi min ,ki daina takama da wannan dan matsayin da mahaifinki yake dashi dan baki da wani power da zaki iya min koma" .
ba bata lokaci ta cukumi wuyansa "zaka ga abinda zanyi ".
Yaransa suka bishi da kallo haka ma abokansa me gadi kam saurin kawar idanunshi yayi kamar bai ga abinda ke faruwa ba ran jaguwa yayi mugun 'baci sai dai bai ce mata Komai ba har sanda ta hau fad'a da maseefa da zaginsa da fada masa bakaken maganganun ,sai da tayi mai isarta sannan ta sakar masa wuya ta dukurshe ta zube kasa ta runtse idanunta wasu hawaye masu zafi suka zubo mata .
shi kuwa ya matsa gefenta ya tsura mata Ido ransa na quna kafin daga baya ya canza kallon zuwa natsana yayi taku biyu zuwa Inda take durkushe dafe da goshinta "sorry tanweer bazaki iya komai ba sai da kiyita ihu kina kuka kina zagina
just like a baby ,the great tanweer, kyakkyawar matashiya mai ji da
kudi yanzu ta zamo abar tausayi agidan nan , gidan nan fa ba yadda kike tunani bane dan ba haka kawai yake ba ko mahaifinki da karfin masu karfin garin nan zasu zo basu Isa su shigo ba, Ina tabbatar miki muddin kika bar gidan to nine na fitar dake amman rashin kunyarki da ihunki bazasu fitar dake ba cikin sauki ba ."
wani mugun kallo take masa tabbas da zata samu bindiga a halin yanzu da zata hakura da son da take masa
ta harbesa ta huta, hakan ne ma zai zame mata sauki a rayuwarta dan tasan muddin bai duniya zata hakura dashi , "amman bari na gwada miki karfina ai kina son fita ko?tayi shiru taki cewa komai sai hawaye dake zuba "Ammar bude mata get tuni
taga get ya bude "how dare you? ta fada tare da k'arasawa gurin me gadi ta d'aukeshi da mari "Kai har ka Isa na maka mgn Kaki bin umarnina kasan kuwa waye ubana a garin nan? "ubana shine minister of health na garin nan waye shi wannan daya ajiyeku ban da tantiri ?jaguwa ya matso gabanta ya mika mata roban ruwan faro me sanyi ",Sha ruwa sanyi tanweer kiyi aiki da kwakwaluwa " me yasa mahaifinki zai d'auki mataki akansu ?"anan basu san kowa ba sai sani , babu dokar kowa da zai yi aiki sai nawa ,gidan nan gidana ne mahaifinki bashi da wani matsayin bashi da power haka kema , shi wannan matsayin ko power din ki bari sai kin koma gidanku dan anan babu Wanda zaiyi respect dinki babu Wanda zai ga girmanki sannan babu Wanda zai bi umarninki sai nawa , nawa za'a bi kin san me yasa ?Yayi kusa kusa daita "kowa yasan matsayina, dan fashi ne dake sata wa kasa da kasa the CEO of armrobber's, armrobber's din daya yi suna da girma a fad'in Africa gbdya kowa yasan jaguwa wato Adnan amad gwoza anan wa yasan matsayin tanweer har ta bada umarni abi har ta kafa doka abi a zauna ?ke ba kowa bace sai diyar common minister of health da iya garin nan da wasu tsirarun garuruwa akansansa
sannan mutumin dake zaman banza
a offishinsa da suna yana aiki wa alumma mutumin da maci amana kasar ne , bai San komai ba sai shaye shaye da neman matan banza da bata rayuwar mutune wannan shine cikakken halin mahaifinki da kike takama dashi ,bari kiji da zai fito da boyayyen halinsa fili babu mutun d'aya da zai ga girmansa hatta ke kanki sai kin tsaneshi ,wallahi idan baki yi amfani da tunaninki kin kiyayeni ba kin daina zagina ba zan nuna miki asalin waye jaguwa, zan fito miki da true colour dina, zan yaga miki rashin mutunci ,zan mayar dake baiwa a gidan amadadin bautar da nake miki , sannan ki zamo daya daga cikin karuwaina nayi duk yadda nake so dake idan bukatata taso nayi ko sau nawa nake so yana gama fad'ar haka ya juya abunsa ."
ran tanweer yayi mata zafi ta dinga Jin zuciyarta kamar wuta magangunsa suka tsaya mata arai ta kasa motsi, ta bishi da Ido kawai
tana kallonsa ,lokaci na farko kenan da'aka fad'a mata bakaken maganganun da suka daga mata hankali Km akan masoyinta data fi qauna akan komai,sosai taji mgnr sun tokare mata zuciya Kuma ta kasa Koda motsi balle ta bud'e baki ta zagesa ko ta fad'a masa bakar mgn. shiru tayi tana mamakin abinda ya fad'a akan mahaifinta karyata hakan zuciyarta tayi sai dai Kuma ta rasa dalilin da zuciyarta ke wasi wasi akan maganarsa ."
Shi kanshi jaguwa yayi mamakinta Yana jiran yaji ta balbalesa da masifa da balai akan furuncinsa sai yaji shiru don haka byn ya dan yi nisa kad'an sai ya juyo yaga me takeyi, har yanzu tana zaune tana kallonsa yaga wani bacin rai atattare daita wanda bai ta'ba gani ba tayi sanyi sosai bazai iya karantar meye a kwakwaluwarta ba tuni yaji hankalinsa yayi matukar tashi Anya bai fadi magana dayawa ba kuwa akan dad dinta ? "Shi kansa yasan ya fadi abinda bai dace ya fad'a ba , jikinsa ne yayi sanyi ya Isa d'akinsa yana tunani hankalinsa ya tashi dan arayuwarsa baya qaunar ya batawa wani bare ita da yake jin duk saukar numfashinsa yana sauka da tunaninta ne ,yadda yaga yanayinta yasan ya ta'ba zuciyarta" me yasa na fadi abinda na fada "karka damu is a very good respond to her akan furucin bakinta km ya kamata tasan kadan daga cikin halin mahaifinta .
" amman Kuma karya zamo da gaske zata shirya daukar fansa akanka ? tsaki yaja dan me zakaji tsoro ko ka manta ko kai waye ? Yayi shiru na dan tsawon lokaci sannan yace "babu abinda zata iya ya kwanta akan kujerar kushin ya janyo pillow kujerar ya rungume a qirjinsa yace"tanweer you can't do anything coz na zamo wani bangare na rayuwarki ."
Tanweer ta koma d'akinta ta kwanta lamo akan kayan da tayi kaca kaca dashi sai dai tsabar zafin zuciya ta jima tana tunani wani lokaci hawaye ya zubo mata ta tsinci kanta cikin kewa ta dinga Jin kamar bata da kowa da komai a duniya a tattare daita haka ta yini kwance agurin ta Kulla wannan ta kwance har dare jaguwa yasa aka yi order abinci kala kala wanda yasan take so, ya nufo d'akinta Yana bud'ewa yaga wani duhu ya kunna wutar d'akin ya sameta kwance cikin yanayi mai ban tausayi ya matsa gareta ya tabata "tanweer "!
ya kira sunanta ai kamar wanda ya dana mata shoking din wuta tayi saurin mikewa ta buge masa hannunsa "ka kyaleni ka rabu dani kaji dadi burinka ya cika kasani cikin wani hali ,ka rabani da kowa nawa,kasani cikin damuwa hawaye ya zubo mata "ka rabani da masoyina ka rabani da dady ka rabani da komai hatta matsayina da mutuncina ka rabani dashi kana Jin wai Kai wani
ne shiyasa ka dauki kanka a wata tsiya to bari na fad'a maka sai dai idan ban bar gidan nan a raye ba amman wallahi sai na ......" shiiiiii ki Daina wahalar da kanki coz you can't do anything ".
dukkaninsu sukayi shiru suna kallon juna a zahirin gsky bai so ya fad'a mata abinda ya fad'a ba amman tunda ya fad'a babu abinda zai goge hakan, muryarsa can kasa yace"ga abinci kici ki km huce dan nasan baki ne babu abinda zaki iya yi ya mike ya juya yana cewa "ki tabbatar kin gyara d'akin ko ki kwana cikin datti ". kifi abincin tayi a kasa "baza'a ci abinci ba, gbdy ta zubar dashi tabisa da fad'a da tsawa bai kulata ba ya wuce ya tafi a wannan daren dukkaninsu babu wanda ya runtsa kowa da abinda ke ranshi ke sakawa jaguwa da bacci ya gagara ya tashi ya shiga d'akin anas kusan kwana sukayi suna Hira sai dai bai yarda ya Sako mgnr tanweer ba yayinda Zahra tayita Kiran wayarsa bai d'auka ba , wannan abu yayi mugu mugun d'aga hankalin zahra ta kwana da matsanacin fushi da bacin rai a zuciyarta da sake d'aukar burikan mugunta akan tanweer haka ma washegari bata hakura ba tayita kiransa bai d'auka ba shi kuwa duk kiranta yana gani amman yaki d'auka dan bai ga abinda zaiyi da kiranta ba ya cigaba da harkokin gabansa ."
A daidai wannan lokacin kuwa Zahra na can cikin tsananin tashin hankali tsaye cikin bakake kaya kunneta manne da waya cikin yanayi na tashin hankali take waya da blessing "matsalata daya yanzu arayuwa shine Adnan ."
"Na fada miki zaki samu Adnan zaki auresa ta kowani hali duk Wanda zai shiga tsakaninki dashi karshensa mutuwa ,mutuwace makomarsa dan haka ki kwantar da hankalinki mu gama da next target dinmu ki natsu karki rusa mana plan idan aikin boka yaki akwai makirci bare zai ci zan sake kaiki wani guri Ina tabbatar miki duk abinda yake takama dashi da asiri baya cinsa sai mun rusa, mun ruguza komai nashi yaji baya qaunar ganin kowa sai ke ."
"Shine abinda nafi qauna blessing ya zo da kanshi ko bai rokoeni soyayya ba ni dai yazo blessing bazan iya rayuwa babu Adnan ba "ki daina kaskanrar da kanki kina da komai da duk wani cikakken nmj zai soki akanshi kece kika fi dacewa da cancata dashi ba wacan tsinanniyar yarinyar ba, ya soki ya qaunaceki amman saboda rashin hankali da tunani me kyau irin nasa ya rasa Inda zai ajiye soyayyarsa sai gurin...." "excuse me blessing don't ever call him mad karki sake zaginsa idan kina cewa bashi da hankali da tunani ni Kuma da nake so shi fa ?don't don't try to insult him "am sorry kit Zahra ta katse Kiran batare da ta jira taji me blassing zata sake cewa ba ."
*******
Alhj tahir dake zaune yana jiran zuwn nazifi yace "ya'akayi son Kai nake jira anyi nasarar samun alluran kuwa da kwayoyin ?"kayi hakuri karka ga kamar Ina cutar da abokinka wallahi rashin tashinsa shine zaman Lafiya da kwanciyar hankalina sai da nazifi ya zauna akan kujera sannan yace "karka ji komai dady an samu da yarda Allah Kuma zai yi aiki ajikinsa sosai fiyye dana baya dan wannan maganin bincike ya nuna idan anyiwa mutun sau goma zai iya mutuwa dady ya matso gabansa "kar dai ya mutu amman Kuma idan mutuwar zata zame min hutu Allah ya bada ikon tafiya "inna lillahi wa inna ilaihi rajiun nazifi ya furta a ransa qirjinsa na bugawa da matsanacin karfi a sukwane nazifi ya jingina bayansa da abun kujera "dady nifa Ina ganin daga wannan maganin da zan kaiwa mumy bazan sake kawo komai ba nagaji da wannan aiki zuciyata ta kasa samun natsuwa kullum zuciyata na fad'a min Ina cutar da aminina, ruhina yaki samun salama wallahi bana iya runtsawa dama nasan dalilin da yasa kake son kassara rayuwar Ib Kuma nasan cewar ba cutarwa bace a rayuwarsa wallahi zan tsaya sai Inda karfina ya kare sannan zan tsaya naga komai ya tafi daidai ."
"kai dan Allah gafara can Sha Sha dady yayi hanzarin katseshi ta hanyar fad'ar haka "Ashe baka da hankali Taya kake tunanin zan fada maka dalilina ? karfi da matsayin da Ibrahim yake dashi acikin garin nan ne farkon jegon komai , muddin na bari ya tashi bisa kafafunsa komai zai iya faruwa dani, kasani Kai ma ko ka manta matsayinsa ne?bama haka ba Ibrahim nada karfin da zai iya komai akan cikar nawa burin dan haka
nazifi bazan barshi ya tashi ba Kuma bazan fada maka dalilina ba dan ko na fad'a maka bazaka fahimta ba ka dai qara min lokaci ka cigaba da aikin nan karshensa ma yazo ".
nazifi ya furza da wani huci Yana tsinewa alhj Tahir a zuciyarsa ya mike tare da yi masa sallama har ya kusan Kaiwa bakin kofa yaji muryar alhj Tahir "karka kuskura ka fadawa kowa wannan shiri dan bazan fad'a maka abinda zai biyo baya ba sai dai kawai ka tsinci kanka cikin tsaka me wuya abinda bazan so faruwarsa ba kenan dan har yanzu kana nan a matsayin d'ana" . gyada Kai kawai nazifi yayi ya fice .
Hajiya baseera zaune akan kujera me zaman mutun uku sai ga nazifi ya shigo hannunsa rike da leda wanda da gani kasan na asibiti ne dan a zahiri ake iya ganin abinda ke ciki ,hjy baseera na ganinsa ta saki fuska duk da zuciyarta cunkushe take da damuwar rashina lfyr Ibrahim ,
sosai tayi farincikin ganinsa tana qaunarsa tamkar yadda take qaunar Ib .ya dan rusuna cike da girmamawa ya gaisheta "Ina yi mumy ?"lafiya lau son ya fama da jama'a da kokari Kuma ?
"alhamdulillah mun godewa Allah ya Ib da jiki ? alhamdulillah Lafiya na ta samuwa ta nuna masa gurin zama da hannunta "ka zauna son "ya samu guri ya zauna yana cewa daga bangaren dady nake gbdy lamarinsa babu sauki a yadda yake kokarin son kassara rayuwar Ib,wallahi mumy abun na matukar bani mamaki haka nan sai na zauna Ina tunanin Anya kuwa mahaifinsa ne da yayi silar zuwansa duniya ?"mahaifinsa ne nazifi kama daina tantama shi mutun da son abun duniya ke sama da farincikin iyalinsa ".
runtse idanuwanshi yayi "dady na bukatar rayuwar Ib domin kuwa wadan nan magungunan da yake bukata a dinga bashi da allurai daidai suke da mutuwarsa dan watan wata rana za'a wayi gari babu shi ."
"Da naji wannan mummunar labari zanfi bukatar na bar gidan nan dashi sai dai ban san yadda zan bar gidan dashi ba batare da sanin mahaifinsa ba". ta k'arasa maganar cike da damuwa .
shiru suka yi na second biyar sannan nazifi ya cigaba da magana a tsanake "karki damu mumy daga yau kisa a ranki Ibrahim zai dawo rayuwa kamar yadda sauran mutanen suke yi "zan d'auki nauyin ib bama garin nan ba kasar ma zan bari dashi gabad'aya Cikin dakiyar zuciya hjy baseera tace "wannan hukuncin naka yayi daidai Kuma na gamsu dari bisa dari dashi wallahi , dan haka babu abinda zance maka sai godiya ,yadda kake son ka nisanta tsakanin Ibrahim da mahaifinsa ta k'arasa maganar tana Kuka sosai tmkr wacce aka Aiko mata da sakon mutuwar ta ko akace mutuwa Ibrahim zaiyi ".
"lamarin alhj Tahir akwai ban tsoro da rashin tausayi da Imani "sosai kuwa yanzu dai a sirrance zamuyi komai ta yadda bazai fargaba "Allah ya d'aura mu akansa Allah ya kawar da tunaninsa akanmu "Ameen mumy ni zan wuce duk abinda ake ciki zan kiraki a waya. "To na gode na gode sosai Allah yayiwa rayuwa albarka ya mike ya fice ."yana jinina girman alamrin dady ,gbdy ya gama ganosa Kuma yana tare da kwararrun hujojin da zai sa jami'an tsaro su tunhumeshi dashi idan bukatar haka ya taso , idan ta kama ya tsaya gaban alqali zai tsaya ya bada sheida domin kuwa mutumi kirki ake karewa da rufawa asiri irinsu dady kuwa sai dai a fallasasu duniya tayi Allah wadai dashi ."
***""
Da misalin karfe goma na daren ranar litini jaguwa ya shigo d'akin jikinsa sanye da kayan shan iska farare sol yayinda hannunsa ke rike da farar leda dake d'auke da roban takeway guda biyu wayam ya ga d'akin babu ita babu alamun ta jiki a sanyaye ya ajiye ledar hannunsa ya karasa ya zauna abakin gado a tunaninsa wanka take shiru har minti biyar ta wuce bata fito ba ya kira sunanta yana duba agogon dake d'aure da tsintsiyar hannunsa still shiru ya Kara five minute bai ji motsin saukar ruwa ba ya mike tsam ya Isa bakin kofar bayi yayi knowking still babu respond Kara knowking yayi no answer a hankali yaji zuciyarsa ta buga da sauri ya d'aura hannunsa kan handle din kofar ya murd'a yaji murfin a bud'e ya sanya kanshi cikin ya leka wayam ya gani nan ma babu ita yayi mamaki Inda taje ya fito a rud'e yana duba sauran dakunan gidan nan ma shiru babu ita ..
Wata uwar ashar ya saki ya wuce su anas ya fito zuwa haraban gidan da sauri da mugun sauri yanzu kam jikinsa ya fara bashi akwai matsala yana tafiya anas ,jubi,jabir ,har ma da kamil dake dingisa kafarsa suka biyosa suna Kiran sunansa amman bai juyo ba sai faman dube dube yake yana Kiran me gadinsa da sauri ya k'araso ya rusuna cike da girmamawa "ka budewa yarinyar nan kofa ne ?me gadi ya girgiza masa Kai alamun a'a , cikin fushi ya d'auke shi da mari "ka bud'e baki kamin magana zaka wani girgiza min Kai kamar kadangare "a'a sir ban budewa kowa get ba tun safe ma babu wanda ya fita daga gidan nan bayan Kai ".
ya Salam ya furta yana rike kugunsa da hannu d'aya ya shiga sintiri a haraban gidan ya bar me gadi dafe
da quncinsa "gidan ubanwa ta shiga ?wallahi idan banganta ba sai naci ubanka ya fad'a a fusace yana juyowa tare da nuna me gadi da yatsansa gbdy abokansa suka k'araso garesa alokacin d'aya anas ya dafa shi "wai meke damunka ne "ban sani ba duk banga amfaninku ba ace Kuna zaune tanweer ta fito baku sheida min ba "
"ta fito taje Ina ?"tun byn sallahr isha'i muke zaune a falo bana tunanin ta fito zo muje mu sake dubata tana ciki may be ko tana bathroom ne ya kamo hannun jaguwa ,ya fixge a fusace "bata nan na duba koina bata nan bata cikin gidan nan wallahi idan banganta ba duk sai na kasheku d'aya bayan d'aya cikin kankanin lokaci gabad'ayansu suka shiga tashin hankali anas ya basu umarnin nemota duk suka raba kansu suna nemanta shi kuwa jaguwa tuni ya dawo tamkar wani zarare shi kad'ai yasan irin tashin hankali dayake ciki "Ina tabi tunda me gadi yace bai bud'ewa kowa get ba ?ya d'aga Idanunsa da suka rikid'e suka canza kala zuwa katangar gidan da sauri ya girgiza Kanshi "muddin ta tsallaka katangar nan lallai zata mutu idan Bata mutu ba zata nakkasa gashi bayan gidan babu wasu gidaje sai kango .
ya fito a gigice anas da jubi suka biyosa suna cewa "Ina zaka ? "dan Allah ka natsu bazata iya tsallaka katangar nan ba , bai tsaya sauraronsu ba dan kwata kwata hankalinsa bai jikinsa Kai tsaye bayan gidan ya nufa yana haska gurin da wayarsa yana Kiran sunanta babu ita babu alamunta ya juyo
a harzuke yana masu wani irin kallo mai d'auke da rashin mutunci suna kallo ya dungule hannunsa, gbdynsu suka yi matukar tsorata shi kuwa anas byn tsoro har da kallon mamaki yake masa sai dai ya kasa ce masa komai wani irin kallo jaguwa ya cigaba da yi musu da jajayen idanunshi .."
💗💗💗💗💗💗
KUSKUREN BAYA
💖💖💖💖
💗💗💗💗💗💗
PAID BOOK
FREE PAGE
WRITING BY
AYSHA .A BAGUDO
WATTPAD @HAUESH
bismillahirrahmanirrahim
Wannan littafin na kudi ne mai bukata karanta shi ya tura 500 ta wannan account number din 1438775094 Aishat Abdullahi Access bank ,Idan an tura sai a turawa wannan number+234 703 534 8686 alert domin tabbatar da an tura ko wannan number 08059623096 Idan Kuma vtu za'ayi sai a tura ta wannan number 08059623096 kada ayi vtu a number MTN ,domin sauraran littafaina a tuntubi Channel dina ta Hausa bakwai.
🅿️18
....Anas ya Kalli jaguwa yaga gbdy yanayinsa ya sauya ,
dukkanin wani jijiya dake Kansa sun gama fitowa sunyi rud'u rud'u babu abinda qirjinsa yake sai d'agawa sama da kasa kamar numfashinsa zai bar gangar jikinsa .ya d'aga hannunsa sama zai naushi jabir dake tsaye kusa dashi yayi saurin matsawa baya, ya sauke hannunsa ya naushi iska kana ya zagayesu ya wuce cikin tsananin fushi, suka biyo bayansa suna fad'a masa tautausan kalamai masu sanyi "kayi wa Allah ka samu natsuwa inshallahu za'a ganta " bai kulasu ba ya shiga gidan kmar mayunwanci zaki yana haki ya rike kugunsa da hannu d'aya yayinda d'ayan hannunsa ke rike da goshinsa yana shafawa saboda saran da yake masa .anas da sauran mutanen dake zaune acikin gidan suka cigaba da duba ciki da wajen gidan ko Allah zai sa su ganta har Inda suka duba da farko sun sake dubawa babu ita babu alamunta, gabad'ayansu a matukar tsorace suke dan sun san muddin ba'a ganta ba sun zama abun zargi agurinsa me gadi yafi kowa shiga rud'ani , jikinsa banda rawa babu abinda yake ,da zarar zasu had'a Idanu da jaguwa zai yi saurin kawar da fuskarsa yana salati .
Tsayawa jaguwa yayi cak qirjinsa na wani irin luguden bugawa da matsanacin karfin gaske, ya tsaida idanunshi daidai Inda durom din ruwa yake wanda suke zuba shara acikinsa, haka nan yake Jin fad'uwar gaba me tsanani a yanzu da Idanunsa suka sauka akansa ,ahankali ya soma taku domin k'arasawa gurin , taku uku yayi sai ga anas ya k'araso da sauri "jaguwa !" ya kira sunansa cak ya tsaya yana sauraronsa dan a tunaninsa zai ce masa an ganta "munata wahalar da kanmu muje a duba cctv camera Ina da tabbacin zamu san inda take ."
wani irin juyowa jaguwa yayi da sauri tare da yiwa anas kallon second d'aya sannan da sauri ya soma tafiya cikin sauri kamar zai tashi sama ya nufi d'akin da camera yake , anas ne kad'ai ya biyosa daman Kuma daga shi sai anas ne suke shiga bangaren suna shiga d'akin anas ya kunna cctv camera bayan ya kunna yayi rewarning sai ga hotunan mutanen dake zaune a gidan ya soma bayyana .
a hankali suke kallo har zuwa sanda tanweer ta fito tana sand'a har ta fita zuwa haraban gidan har zata nufi get sai Kuma ta fasa ta Isa jikin window me gadi ta la'be tana dube dube da neman mafaka , cike da tsoro ta waigo bayanta nan taga alamun fitowar aliyu wanda shi sam hankalinsa bai je gurinta ba ganinsa yasa cikin sauri tasa hannunta ta bud'e durom din ruwa ta shiga.
wani irin naunayen ajiyar zuciya jaguwa ya sauke da karfin gaske sannan ya juya da sauri yana cewa "daman zuciyata da jikina sun bani naje na duba cikin durom din a she tana cikin ". ya Allah kasa wani abu bai sameta ba tafiya yake cikin sauri kamar zai tashi sama anas na biye dashi a falo suka wuce sauran abokansa da yaransa suma suna ganin haka suka biyousu cikin sarsarfa ya k'araso gurin ya bud'e duron din sai gata durkushe ta rufe bakinta da hannunta d'aya dan kar kukanta ya fito , gashi ta dungule jikinta guri d'aya tana haki bai san sanda yasa hannuwansa duka ya kamo kafad'unta ya fito daita waje ya rungumeta tsam ajikinsa yana sauke wahalalle numfashi . fuskata ya manna adaidai saitin zuciyarsa dake bugawa da karfin gaske , ita Kuwa haushi da bakinciki ne suka had'e mata a lokaci daya, ita da take ganin wa'adin zamanta ya kare a gidan dan har ta hango barinta gidan a yau din nan sai gashi ya rusa mata Komai .
a hankali ta d'auke kanta a daidai saitin zuciyarsa ta cusa cikin qirjinsa ta rushe da
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Chapter 36
Chapter 37
Chapter 38
Chapter 39
Chapter 40
Chapter 41
Chapter 42
Chapter 43
Chapter 44
Chapter 45
Chapter 46
Chapter 47
Chapter 48
Chapter 49
Chapter 50
Chapter 51
Chapter 52
Chapter 53
Chapter 54
Chapter 55
Chapter 56
Chapter 57
Chapter 58
Chapter 59
Chapter 60
Chapter 61
Chapter 62
Chapter 63
Chapter 64
Chapter 65
Chapter 66
Chapter 67
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 21 Chapter of 67