binta da murmushi had'e da dariya.
wani bin kuma ta amsa mata ba mai tsawo ba.
Miemie taja ta tsaya ta d'an waro ido da damuwa ta ce
"FEERYAL karkiga yadda hankalina ya tashi da akace
an sace ki, ranar ko abinci banciba nayi ta kuka."
kafin FEERYAL tace wani abu suka hango su Ameerah sun fito daga side d'in Hajiya.
Miemie ta ce
"Yauwa tsaya gasu Ameerah can bari naga ko zasu gane ki taho muje."
ta janyo hanun ta suka karaso gurin su.
Tun daga can suka kafe FEERYAL da kallo suna son sanin wace bakuwa sukayi a gidan.
suna isowa inda suke Sumayya ta ce
"Wow see beautiful Miemie wannan fa? a ina kika zamo balarabiya haka."
"Dan Allah Sumayya baki gane ta ba?."
cewar Miemie tana dariya.
Ameerah ko hanci sama ta d'aga tana yamutsa fuska ita a rayuwar ta ta tsani taga wacce ta fita.
ta ce
"Sai wani rawar kafa kike ta ya za'ayi ta santa bata tab'a ganin ta ba, kasarsu ba d'aya ba."
"Laa Ameerah ke ma baki gane ta ba, Sahla Nabila kuma duk baku gane ta ba, to ku bani goron albishir na fad'a muku ko wace ce ita."
Miemie ta miko musu hanu tana dariya.
Sumayya ta zuba mata tafi a hannun tana fad'in
"To an baki."
su Nabila da Sahla dai murmushi sukayi.
Ameerah ko fuska ta yamutsa, ita haushin ganin yadda Miemie'n ke ta rawar kafa.
Miemie ta ce
"So surprised! FEERYAL ce."
Sumayya ta ce
"What!.
"Yes of course ita ce dai."
kai Sumayya ta girgaza tana kare mata kallo sai kuma ta ce
"Ba laifi."
Ameerah Sahla Nabila a tare suka bud'e ido da baki suna kallonta.
Ameerah ta ce
"Tabd'i jam! annoba ta kuma dawowa gidan mu,
wai ke baki da gidan uba ne kam sai dai ki rika yawo gidan mutane kina addabar rayuwar su,
idan da kin zauna lokacin muna yara yanzu kam baki isa ki zauna da mu ba, mayyar aljana,
mttsss dalla kuzo mu tafi,
akan wannan aljanar kika tsayar da mu har dawa ni wai Surprised aikin banza."
Nabila da Sahla suka ce
"Ai kuwa bara da bana ba d'aya ba ki karanta hakan da kanki."
Ameerah
ta janyo hannun Nabila da Sahla, da suke aikawa FEERYAL harara, Sumayya ta biyo bayansu sukayi gaba.
Jikin FEERYAL ya yi sanyi matuka.
Miemie ta bi bayan su da harara tana fad'in
"Ai ke kam Ameerah kin shiga uku sai ki hanata zama ai tun da ke kika gina gidan,
ku kuma kun bita kamar wata uwar ku, dalla rabu da su zo mu tafi FEERYAL suyi abinda zasuyi."
ta jata suka nufi sashin Ammah tana ce mata
"Karki wani damu da su."
cikin sanyin murya FEERYAL ta ce
"Hum Ameerah ke nan har yanzu dai bata sauya ba."
"Ai bazata sauya ba haka zata mutu da halinta,
kinga Sumayya tana da sanyin hali ita dai kawai zugi ke mata tasiri,
mance da su dalla."
ta d'auko mata wata hirar har suka wuce sashin Ammah.
Ammah na ganin ta ta rungume ta tana fad'in
"Oyoyo FEERYAL ke ce haka,
Allah sarki ya jiki ya abinda ya faru?."
FEERYAL tayi mirmushi tana gaisheta.
Miemie ta jata sukayi cikin d'akin ta bayan su. gaisa da Ammah.
hira sosai Miemie ke janta da shi ita dai murmushi sai dariya take binta da shi dan bata iya dogon hira irin haka ba.
sun jima sosai har wajen azahar sai da FEERYAL tace zata koma tayi wanka.
Miemie ta ce
"Kiyi wankan a toilet d'in na sai kije ki sa kaya."
ido FEERYAL ta waro ta ce
"To kaya fa bazan iya maida na jikina ba."
"Sai kisa nawa ba ga nawa ba, ko an ce miki kin fini kiba ne."
"Miemie muje dai ki rakani zan canza pad wajen awa uku yana jikina."
"To ai ina da shi shiga kiyi wanka bari na d'auko miki."
dole Miemie tasa ta shiga bathroom d'in ta tayi wanka ta bata pad da sabon pant ta saka,
ta fito ta samu ta ciro mata doguwar rigar abaya,
zata tafi da nata kayan Miemie ta ce ta barshi anan.
sannan suka fito ta rako ta.
Suna fita can suka hango su Ajeemal Faisal Zaraddin Shamsuddin, zasu shige side d'in su.
Miemie ta d'aga murya tana fad'in
"Kai-kai ku tsaya ku tsaya."
ta janyo hannun FEERYAL da sauri suka karo gurin su.
Faisal ya harare ta yana cewa
"Ke mu sa'annin ki ne da kike mana irin wannan kiran?."
Shamsuddin ya kai mata bugu a baki ta yi saurin kaucewa.
tana cewa "Wayyo Allah baki na, to ku tsaya kuji mana."
ya ce "Waye sa'anki."
Ajeemal ya ce "Ku kyale ta, mene ne Miemie?."
baki ta turo ta ce
"To ai bana so na kira sunan ku ne taji game d'in ya rushe,
yauwa kutsaya-kutsaya kuji in kun canka waye wannan?."
ta nuna FEERYAL sannan ta ce
"Ke ma in kinci su waye wad'annan fad'o min sunan su."
tayi maganar tana dariya da tafa hannu.
duk suka bi FEERYAL da kallo Zaraddin da shi dama ya kasa magana tun d'azu idanunsa yana kan ta gaba d'aya yawun bakin sa ya gama tsinkewa.
Ajeemal da ke ta juya kamannin nata cikin kwakwalwarsa, ya yi saurin janye idanunsa daga kallonta, jin yadda gaba d'aya kasala ke kokarin shigarsa.
Faisal kuwa cewa ya yi
"Nasanta mana balarabiya ce ai mun sani duka."
dariya ta kwashe da shi ta nuna Zaraddin da Shamsuddin da Ajeemal ta ce
"Kuma baku gane ko wace ce ba, to ke suwaye ne su."
tayi maganar tana kallon FEERYAL.
murmushi ta sake wanda ya sami nasar bayyan hushiryar da ke tsakiyar kyakwawan jerarrun hakorar ta,
yayin da kumatun ta ya lotsa dimples d'in ta ya bayyan.
ta kai yatsarta baki tana bin ko wannen su da kallo.
wani irin had'iye yawu Zaraddin ya yi yawani lumshe ido tare da jan numfashi a fili.
Dariya Miemie tayi ta ce
"Wai dukan ku baku gane ta ba, kema baki gane su ba? yee naci wina."
tayi maganar tana tsalle a tsakiyar su.
Ajeemal ya ce
"Ke Miemie wani irin shiririta ne wannan."
"Ya Ajeemal ku bani gari kawai FEERYAL ce fa,
FEERYAL baki gane Ya Ajeemal Ya Shamsuddin Ya Zaraddin Ya Faisal ba."
ido ta waro tana murmushi da bin ko wannen su da kallo, sai da ta fad'a sannan kamannin nasu na tun da yake zuwar mata ido.
suma d'in mamaki duk suka cika da shi,
wai FEERYAL ce ta zamo haka.
Zaraddin da yakuma hadiye miyau ya furta
"Wow! she is cute completely."
Shamsuddi da Faisal suka had'a baki wajen fad'in
"Haka kika girma FEERYAL."
nan ma murmushi ta bisu da shi batayi magana ba.
Ajeemal ne ya ce
"FEERYAL ya abin da ya faru ina tayaki jaje, ya karatu kuma,
au na mance wani rana Aunty take sanar min graduation naki, kinyi kokari fa kinfi su Miemie."
"Haba Ya Ajeemal sai kasa tayi tunanin bamuyi ba muma, tun yaushe mukayiwa secondary bye-bye, mun barwa yara."
hararar ta Faisal ya yi ya ce
"Wuce ki bar nan ke d'in mece ce."
hannun FEERYAL ta ja suka bar gurin da sauri tana dariya dan tasan zuwa anjima zata sami tsarabar mari.
Zaraddin yabi bayanta da kallo yana wani matse ido da latsar lips d'in sa.
Ajeemal ya d'an harare shi dan ya lura da yanayin da ya shiga tun d'azu, ya yi tsaki yana girgiza kai ya yi gaba abin sa suka biyo bayan sa.
Kan ka ce me gidan ya d'auki labarin FEERYAL ta dawo,
a bujajan Umma Karima ta d'auko kafa tayi sashin Mommy.
tun kafin ta zauna take cewa
"Hajiya Halima wai da gaske ne batunnan ko maganar yarannan ne kawai?."
"Ni ma yanzun nan su Ameerah suke sanar min kin san bazasuyi karya ba."
Umma Karima ta zauna tana fad'in
"Tabd'i jam wata sabuwa inji d'an caca!
aljana mayya annobar ta kuma dawo mana gidan."
ta saki dariya
"Hahaha lallai Hajiya Fatiya ba karamar 'yar wasa bace, sai da ta bari muka sakankance sannan ta shammace mu,
ta dawo da ita bayan ta hab'aka dafinta yagama kwari ta inda duk wanda ta kaimai sara zaiyi masa mummunar illa,
Fatima Fatima Fatima muzuba mugani waye zai cinye wasan!."
Mommy ta ce
"Ham tun da suka kawo min batun nan narasa a bin yi, yanzu ya kike ganin za'ayi Hajiya Karima."
"Yanzu ne za'a yi mai gaba d'aya ai ta farkar da mu daga nannauyar baccin da muke."
cewar Umma Karima tana girgiza kai.
Ameerah dake zaune sai cika take tana batsewa,
tun dataga FEERYAL, bakinciki kamar ya kasheta,
bata kaunar ganin wacce ta fita bare kuma a yabeta a gabanta.
ta ce
"Mommy amma dai zata bar gidan nan ko, dan wlh bazamu zauna da ita ba,
ta ya za'ayi ne ma kawayen mu suzo su ganta,
ina bazai yuwuba,
nifa duk yadda za'ayi Mommy tabar gidan nan."
"Ai barin gida ma yazama dole kwantar da hankalin ki d'iyar masu gida,
har wacce ta kawo tan ma wannan karon tare zasu bar gidan."
cewar Umma Karima tana gyara zaman ta.
Sumayya ta ce
"Wlh bakuga yadda ta girma ta zamo wata tsaleliyar budurwa ba,
ko gane ta bamuyi ba, ni na d'auka ma bakuwar balarabiya mukayi,
sai da Miemie ta ce mana wai ita ce,
wlh tafi da kyau gaskiya tana da kyau sosai kamar ita tayi kanta."
Mommy da ke ta aika mata harara tun da ta fara maganar ta ce
"Dalla rufa mana baki, kusheta kike ko yabon ta, ni fa watarana tantama nake akan ki dan naga kamar halinki na kamancece niya dana Ajeemal duk zan ci ubanku ai marasa ziciya,
wad'annan badun lokacin da na haifeku a take aka d'ago aka nuna min kuba da sai nace canza min ku a kayi."
Ameerah tabi Sumayya da harara tana jan tsaki ta mike tayi bedroom d'insu.
gaban mirror ta tsaya tana karewa kanta kallo.
sai kuma ta juya ta koma bakin gado ta zauna tana fad'in
"Aikin banza banga abin da ta fini da shi bama."
Yau kwanan FEERYAL uku a gidan.
kullum suna tare da Miemie ko a sashin Aunty ko a sashin su Miemie'n.
ko yanzu ma sun fito ne daga side d'in su Miemie zata rakata side d'insu.
Ammah ce ta kwallawa Miemie kira ta koma ciki,
kula mai d'auke da dambu ta mika mata ta ce
"Mikawa Hajiya wannan sai ku wuce."
ta amsa tana fad'in
"Hajiya mayyar dambu sai ya shake makogwaron masifar nan mu huta,
wata rana da kaina zan mata mara kayan had'e na kai mata taci ta shake."
"A bakin ki akaji ba a baki na ba, ke da Abbieh'n ku idan ya jiki."
Ammah ta fad'a tana juyawa ciki.
Miemie tayi waje tana cewa
"Allah sai na yi mata sai dai Abbieh yayi min masifa ko ya bige ni, mata kullum masifarta karuwa yake takusa mutuwa madadin ta rusuna amma sai gaba abin ta yake."
ta karaso in da FEERYAL ta ke ta ce
"Taho muje ki rakani na mikawa Hajiya dambun nan sai mu wuce."
FEERYAL tad'an waro ido ta ce
"Muje dai na jira ki a bakin get d'in ta."
"Dalla matsoraciya zo muje me zata yi miki, ai yanzu ta saduda, tun da ta amsawa Daddy ki zauna."
FEERYAL dai shiru tayi har suka karasa sashin Hajiya.
dan Hajiya tana daga cikin abubuwan da suka ki gogewa cikin kwakwalwarta na tun yaranta.
A parkour suka tadda Hajiya FEERYAL ta karaso a hankali kamar wacce kwai ya fashewa a ciki.
Miemie nayiwa Hajiyar magana ita hankalin ta na kan FEERYAL da ta d'an rusina tana fad'in
"Ina yini Hajiya."
Hajiya ta ce
"Ke Miemie wannan ba aljanar yarin yar nan bace?."
Miemie ta b'ata rai sannan ta ce
"FEERYAL sunan ta."
"Da gani ai ba sai an fad'a ba, dan ina ido biyu da ita naji tsikar jikina ya tashi,
haba kyan har ya kazanta hankali bazai d'auka ba,
ke tashi min a kai fita waje! kar na sake ganin ki cikin sashin nan,
ki zauna can sashin Fatima kafin a gama binciken ki koma can in da akayi gayyarki ba gidan d'ana ba, mayya aljana mai zubin aljanun ruwa."
Da sauri FEERYAL ta juya har tana had'awa da sassarfa tayi waje.
sai da tafi wajen get d'in sashin kafin ta tsaya.
Miemie ta dad'a b'ata rai ta ce
"Haba Hajiya ya zaki ce mata mayya kuma aljana, yanzu idan wani ya tsangwame mu haka kema fa bazakiji dad'i ba."
"To uwar ta ki karb'a mata, kefa Miemie tun da na datsa ayar tambaya a kanki, dan naga alama yarinyar nan bata barki banza ba,
kar na sake ganin ki da ita, kuma zanje na amso magani a soma miki dan da gani turen aljanu ta miki."
Miemie ta tura baki tana kunkune ta nufi kofar fita tana cewa
"Ni ba wanda ya isa ya rabani da FEERYAL, ba kuma maganin da zanyi in kin karb'o maganin sai kiyi amfani da kayanki."
tayi waje abin ta ta bar Hajiya tana ta masifa.
Bilkisu Saddiqa Rahama da Siyama kanwar Umma Karima da yanzu ta dawo gurin Umma Karima da zama,
suka fito daga sashin Umma karima.
Nabila da tayi fitowar karshe idanunta ya sauka kan FEERYAL da ke tsaye a bakin get d'in Hajiya.
da hannu ta nuna musu ita tana fad'in
"Yauwa kun ganta can ga FEERYAL d'in can."
duk suka maida dubansu gareta.
Saddiqa ta bud'e murya tare da yafaro ta da hannu ta ce
"Ke FEERYAL zo nan."
A hankali ta ke d'aga kafarta cikin yanayin ta na sanyi har ta iso inda suke.
dukkanin su suka bita da kallon tsaf,
Siyama ta yamutsa fuska tana fad'in
"FEERYAL d'in ke nan?."
Bilkisu ta ce
"Wai ita ce, bamu sani ba dai ko Aunty ta kuma d'auko wata ce tace ita ce ta da d'in data tsinto cikin ruwa,
dan lokacin da aka koreta a gidan nan tana ficiciya."
Rahama ta ce
"Ke kifa daina mana yawo a gida idan kuma kika ki dukan tsiya zaki ci, dan sau uku ke nan nake hango ki kina kai kawo cikin gidan nan."
Nabila tace
"Ah to gaya mata dai dan nan gidan ubanmu ne agola bata isa tayi abin da ta so ba,
ke daga yau ma duk abin da zakiyi sai kin nimi izin mu, har idan kina so ayi miki alfarmar zama na d'an wani lokaci."
Siyama ta bita da kallon banza tana wani yamutsa baki ta ce
"To dai kinji abin da masu gida suka fad'a, sai kibi a hankali domin ki cigaba da zaman alfarma, in ba haka ba kuma a koma in da aka fito."
Rahama ta ce
"Ai kuwa dama zaman alfarma take dan Hajiya ta fad'awa Umma Daddy ne ya nima mata alfarman zama dai-dai, kunsan 'yan kidnapping d'in nan wannan mai tawagar d'aukar amaryar nan sun d'auke ta da kyar aka kwato ta,
bayan ya gama bidirin sa da ita."
dariya suka kwashe da shi Siyama ta ce
"Kice ashe dai fanko ce tsaye a nan, kyalkyali daga waje ciki fanko."
FEERYAL na tsaye bata ce da su kala ba,
gaba d'aya tsoro ya rufe ta bata saba ganin haka ba,
tun bayan da ta sami 'yancin barinta gidan rabon da ayi mata irin haka.
Miemie da ta fito daga sashin Hajiya ta hango ta can tsaye dasu Bilkisu,
kugu ta rike tana kallon su sai magana suke suna nuna FEERYAL da yatsa.
itako tayi kasa da kai kamar mai d'aukar wa'azi,
a kufule ta nufo gurin su fuska d'aure ta ce
"Ke kuma FEERYAL me kike a nan? na fito ina ta duba ki a she kina tsaye anan, to muje."
Bilkisu ta ce
"Mu muka kirata muna mata kashedi ne, kar ta sake ta rika mana yawo a gida."
Miemie ta dube ta shekeke ta ce
"Kuma dai Aunty Bilkisu meye wani abin kashedi dan anyi ya wo a cikin gida,
waje ke nan kuke so muje murika yawo."
Rahama ta ce
"Bawai ke ba da ita muke."
"Har da ni mana Aunty Rahama tun da tare kuke ganin mu, idan bamuyi yawo a cikin gida ba waje kuke so mufita."
Siyama ta ce
"Ke Miemie ana gaya miki ba ke ba da ita ake."
"Dakata Siyama ba da ke nake ba da su nake, ban kira sunan ki ba,
Aunty Bilkisu Aunty Rahama Saddiqa Nabila,
ina ga acikin mu da ni da ku duk babu mai hurumin ikon hana wani yawo cikin gida, tun da babu wacce ta gina gidan a cikin mu,
Daddy ke da ikon yanke hukunci ba mu ba."
"Ke karkice zaki min rashin kunya dan tuntuni nake ganin take-taken ki."
Siyama ta fad'a tana nuna Miemie da yatsa.
Miemie ta wani dalla mata harara taja tsaki tare da jan hannun FEERYAL tana cewa
"Dalla zo mu tafi, sai naga wanda ya isa ya hanaki yawo,
ai agololin suna da yawa a gidan idan sauran suka daina ke ma zaki daina."
Sai da sukayi nisa da su Miemie ta harare FEERYAL tana fad'in
"Kin wani tsaya suna gaggaya miki magana baki maida musu amsa ba, in fad'a miki a gidan nan idan bakada baki anrika cin tuwo a kanka ke nan,
garama ki koya kiyi baki,
duk ba mutunci suke da shi ba, shi yasa nima bana ganin su da mutunci, Bilkisu da Rahamar ma albarkacin Ammah suka ci nake had'a su nan su da Aunty, amma ba dun haka ba duk da sunan su zan kira su, tun da basu rike girman su ba,
duk sun turewa shekara 27 ko uwar me suke d'auka a gidan suka kasa aure oho,
ita kuma wannan shegiyar Siyamar ba karamin haushi take bani ba,
an kasa auruwa a Kano an dawo Lagos ko za'a sami mashinshini,
wai a haka budurwace da kike ganin ta nan kamar bazawara,
da gani wannan ta kai shekaru arba'in
kanwar Umma Karima ce da bushasshen jiki ko ina a bushe ba soka."
FEERYAL dai murmushi tayi bata ce ko mai ba,
Miemie ko bata fasa mitar ba har suka shige sashin Aunty.........!
Mommyn Twins ce
🌺 *FEERYAL* 🌺
*NA*
*RASHEEDAT S DIRECTOR*
( _Book 1_)
*~Free page~*
*_Littafin na kud'i ne 500 account no 3170524141 Rashida Salihu first bank ka-ki tura shaidar biya ta WhatsApp number ta 08034690723*
*____________________________________*
*🌈🇰AINUWA 🇼RITER'S✍🏼*
*🇦SSOCIATION🤝🏻*
```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}```
https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation
*_domin shiga shafin mu na Bakandamiya danna nan_*👇🏻
https://bakandamiya.com/group/71/Kainuwa-writers-association
*____________________________________*
🅿️22
Suna shiga parkour suka tadda Aunty zaune,
Feeryal ta karaso ta kwanta kan kujerar da Aunty ke zaune tayi pillow da cinyar.
Aunty ta zame d'ankwalin kanta tana fad'in
"Me kitso anjima tana zuwa."
fuska ta kwab'e ta ce
"Ammie gyaran gashi fa zamuje da Miemie jibi."
"Wai haka Miemie? ko duk gudun kitson ne haka."
cewar Aunty tana duban ta.
Miemie ta gyad'a kai tana dariya.
Feeryal ta dubi Aunty ta marairaice fuska da fad'in
"Ammie ba kince za'a aske gashin ba."
Aunty ta dunguri kanta tana fad'in
"Baki da kaine, ama bar gyaran gashin a gyare yake,
maza akitsa kyan yau,
in anyi tsifa sai aje a gyara gashin."
birmima ta shiga yi a jikinta tana bubbuga kafa kan kujera Miemie sai dariya take mata.
Mai kitso ta zo da yamma, tana ganin gashin nata ta ce wlh bazata iya kitsa shi ba dan ya yi yawa.
Aunty ta ce ta gwada dai da kyar aka tuttuka akayi biyu,
karshe tsefe biyun akayi ta tafi,
Feeryal ko sai murna take dama bata son kitson har da hawaye da aka kama kan ana kitsawa...
Umma Karima ce ta fito tana gyara mayafin kan ta,
da alama dai shirin fita tayi dan ga jaka rike a hannunta.
a parlour ta tadda 'ya'yan nata duka kowa na sha'anin gabansa.
Siyama ta mike tana fad'in
"Aunty Karima fita zakiyi ne?."
"Eh fitan gaggawa ce ta taso min bazan jima ba zan dawo, wai ina Nabila ce?."
bata rufa baki ba Nabila ta shigo tana kananun magana.
"Ke kuma da wa kike?."
uwar tata ta fad'a tana duban ta.
ta ce
"Ni da wancan direban naki Sule mana Umma, d'an rainin wayo wai kullum ya ganni sai jira yake ni na fara gaishe shi har na wuce bazai haishe ni ba,
shine yanzu nazo zan wuce har da ce min wai ban gaishe shi ba,
kajimin fa d'an rainin wayo,
ni da gidan ubana yazo cin arziki yace ni zan rika gaishe shi ba shi zai gaishe ni ba,
kaf ma'aikatan gidan nan su ke gaishe mu ba mu muke gaishe su ba,
hatta Baba Ilu mai baiwa fulawa ruwa shi yake gaishe mu ba mu muke gaishe shi ba,
na gaya masa na rantse watarana sai na d'auke shi da mari,
kuma zan gayawa Daddy sai ya bar gidan nan,
ni ban san me yasa kiko son tukin wannan kazamin buzun ba ma Umma, to wlh
ya yi a bakin aikin sa dan wlh sai na sa Daddy ya kore shi."
Umma karima ta ce
"Ke dalla tafi can, ko da wasa naji batun nan a bakin Daddy'n ku sai na sab'a miki,
kaf direbobin gidan nan banga diriban da ya kai Sule iya tuki ba,
tukunna ma ina direba na ne ba naku ba,
ko da wasa na sake jin kin masa rashin kunya sai na sab'a miki,
kiyi wa kowa rashin mutunci banda Sule dan shi mutumin kirki ne,
babu ruwanki da shi na gaya miki ke nan,
ni bari na tafi, ke Siyama bana ji kince anjima zaku fita da saurayin ki ba."
"Eh Aunty Karima yanzu ma mukayi waya ya ce min yana zuwa."
Umma Karima ta ce
"Wai har haka kika bashi dama ne Siyama karfa ya b'ullo da batun aure ya b'ata mana shiri."
"Ah haba ina ai shi wannan d'an hirar rage zafi ne kawai,
yaushe zan bashi dama ga dahir a kasa."
"Yauwa to yanzu naji batu zanje na dad'a jin nasarar da take tinkaro mu,
wai ke Bilkisu har yanzu Bilal bai kiraki ba?."
Bilkisu ta mara baki tana gyara zaman ta idanunta a kan wayar da take chatting ta ce
"Tun da ya tafi Japan sau biyu mukayi magana, yanzu ko na kira sa ma wayarsa baya tafi,
ni bazan ma kara niman sa ba in ya gadama ya neme ni,
ni na sami wani ma yana ma zuwa anjima."
"Dalla tafi can yaushe zaki jira har sai ya neme ki, kiyi ta nimansa har wayarsa ta shiga,
zan sami Daddy'n ku muyi magana a d'aura auren kawai a kaiki can Japan d'in a wuce gurin,
karki sake ki kunyata ni gaban kawaye na,
ni dana gama fad'a nima 'yata zatayi aure a kasar waje,
yanzu ki kawo min wani batu zanje har gida na sami maman Bilal d'in bari na je na dawo."
Ta fice waje tana sambatu.
burin ta ace itama d'iyarta tayi aure a kasar waje kamar yadda d'iyar Mommy Farida itama ta yi.
ta nufi parking lot d'in ta,
a jikin motarta ta dadda Sule direba yana gogewa yana magana.
yana ganin ta ya wani washe baki yana fad'in
"A'a hajiya barka da fito wa."
"Barka dai Sule yi sauri muje bar goge motar nan,
da wa kake surutu haka?."
fuska ya d'an had'e ya ce
"Da waccan yarinyar mana Nabila yanzunnan ta gama gwazamin rashin mutunci."
"Rabu da ita da'alla sai hakuri kasan har yanzu Nabila yarinya ce, kuruciya ke damun ta."
ya ce
"To ai shike nan adai rika gwada mata babba babbane,
yauwa ba dai gurin wancan Mali'n zamu ba, tun kan muje ki zazzage masa bakin jaka duka ina bukatar kud'i fa."
"Kai ka fiye korafi Sule, yaushe-yaushe ne na baka naira dubu d'ari biyar, kayi yaya da su wai kana nufin har ka kashe su,
a karshen watan da ya karen nan fa Alhaji ya baku albashin ku,
da abin da kowa zaici a gidan sa na tsawon wata guda,
yabaku baiyi da sati ba na baka kud'i dubu d'ari biyar d'in nan da karin kayan abinci,
matan ka d'aya da 'ya'yan ka uku me kakeyi da kud'i haka."
"Haba Hajiya kya tambaye ni abin da nake yi da kud'i,
kud'in haya na biya na siyi abinci na turawa tsoffi can Nijar, kin ga ko ai kud'i sun kare."
"Ni Sule kana bani mamaki, banga ammafin sai da gidan da Alhaji ya raba muku da kayi ba,
ko wani ma'aikaci yana zaune a gidan da aka bashi cikin rufin asirin shi, babu ruwanshi da batun wani kud'in haya,
amma kai ka tashi ka d'au gida ka siyar babu kud'i babu gida,
gashi kana kan damuwar kud'in haya."
"To ya ya za'ayi kinsan dai lalurar jinyan iyaye ce ta sani sai da gidan nan,
a ni ma min alfarma Alhaji ya kuma bani wani,
amma kafin nan dai ki bani wani abu a gurin ki kada muje ki juye masa kud'in duka."
Umma Karima ta shige mota ta zauna gaba shima ya shige mazaunin direba,
yana cigaba da fad'in
"Hajiya matsuwa ce adai bani wani abin."
ta zuge jaka ta ciro d'aurin 'yan dubu d'ai-d'ai guda biyu ta damka masa tana fad'in
"Ga wannan 200k ne sai ka lallab'a, bari mu dawo zan kara maka,
sannan zanyi wa Alhaji magana za'a kuma baka wani gidan,
yanzu dai muyi sauri ina da babban matsala so nake na ga Mali cikin gaggawa."
ya ja motar suka fice daga side d'in ta suka nufi babban get suna fita gaba d'aya a gidan ya juyo yana fad'in
"Ace wai ina gidan nan a karkashin Hajiya Karima,
sakani na da jirgi wai sai dai gani da ido idan na kai masu shiga cikin sa airport,
haba Hajiya wai ina batun tafiya ta makka ce ta kwana."
"Wannan shekarar zan biya maka hajji shike nan."
ya washe baki
"Shike nan fa Hajiya kin gama min ko mai wayaga Sule a hajji."
ya sheke da dariya.
Tafiya mai nisa sosai sukayi da ya kai awanni hud'u kafin suka shige dajin boka Mali.
sai da sukayi tafiya kusan na awa guda daga bakin dajin zuwa cikin dajin kafin suka faka a ginfin wata katuwar itaciya.
Umma Karima ta fito
All Chapters
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 19 Chapter of 20