ta zame mata abin kallo.
Maryam ta janyo ta tana fad'in
"Zo muje kici abinci ki rakani gidan wata kawata."
cikin zakuwa ta janyo ta suka fito.
A parlour suka sata gaba sai taci abinci tad'an ci dai ba laifi dan ita ba ma'abociyar cin abinci da yawa bane,
yogurt da cake sune abin cin ta.
Sosai suka rika janta ajiki a wunin ranar harta saki jiki da su.
taga soyayya da kauna da kulawa kamar zasu goya ta.
Alhaji Tahir Abbas yana gida bai fita ba saboda zuwan FEERYAL, ya kira Aunty video call suka sha hira tamkar suna tare.
bayan sun gama waya da Aunty Maryam ta mike tace tazo suje ta rakata.
Hajja Umma ta ce
ta bari sai gobe yanzu yamma ta yi.
Da daddare ma a parlour'n sama suka yada zangon su, sai da suka kai karfe 12 suna hira kafin Abba ya ce suje su kwanta.
Washegari Maryam ta ja FEERYAL sukayi gidan kawarta a nan unguwar su.
suna shiga gidan da
Haulat kawar Maryam d'in suka fara cin karo.
Haulat ta kasa amsa sallamr da Maryam takeyi.
ta kurawa FEERYAL ido.
"Ke dalla ina sallama kinyi shiru bazaki amsaba."
"Wow wannan fa a'ina kika samota, ko ba'in turawa kukayi?."
Haulat ta fad'a tana nuna FEERYAL tana ware idanunta sosai a kanta.
"Ni dad'i na dake hauka ke kam baza'a yi miki surprised ba ana miki zaki iya mutuwa, d'iyar Aunty Faty'n Lagos ce."
"Ke da'alla serious Maryam kar ki shigar da ni, wannan dai ba bahaushiya bace, da gani ruwa biyu ce baturiya balarabiya."
"Da gaske d'iyar Aunty Faty ce jiya ta zo, kin wani barmu a tsaye komu koma ne kin wani tsare ni da tambayoyi."
"Yi hakuri taho mushiga ciki wlh ganin ta ne yasa ni shiga yana yin nan, zo na rike hannunki ya sunan ta?."
Haulat tayi maganar tana ruko hannun FEERYAL.
"Ya salam ashe ana ganin irin su a zahiri ba a TV ba."
dariya Maryam tayi ta ce
"Wlh ke da a kauye kike bansan ya zaki kare ba."
"Ke dai Maryam barni nafad'i gaskiya ta, wlh yarinyar nan so beautiful, ta tafi da ni gaba d'aya."
Haulat na rike da hannunta suka shige parlour'n su.
Maryam ta zauna tana dariyar Haulat da gaba d'aya ta rud'e da ganin kyan FEERYAL.
a gefen ta ta zaunar da ita tana rike da hannunta bata sake ba, ta dubi Maryam tana faɗin
"Wai dan Allah kuma da gaske d'iyar Aunty Faty'n Lagos ce, ko dai abokin kasuwan cin Abba ne yazo da 'yarsa daga wani kasan,
yanzu wannan 'yar Alhaji Abubakar Fiya ne?."
fuska Maryam ta had'a ta ce
"Abin da na saba miki, kin ga tabon sa a goshi na ai, karya ba."
"Allah baki hakuri kawata, lallai kuwa babu ko shakka kwanciyar hankali ma yana karawa mutum kyau, d'iyar Alhaji Abubakar Fiya jika ga Tahir Abbas ai abin bana wasa bane, sai dai ita wannan kyan nata na daban ne tamkar ta had'a jini da larabawa ko turawa,
watakila Alhaji Abubakar Fiya ya had'a jini da su, duk da cewa Aunty Faty ma badaga nan ba a kyau."
Maryam ta sakar mata hararar wasa ta ce
"Yauwa yanzu kika gyara kalamanki ai muma dai kinsan muna da kyau, har da namu kyan ta d'auko makoyi ne dai yafi gwani."
"Lallai kuwa yarinya kin fito a dai-dai d'iyar Alhaji Abubakar Fiya jikan Tahir Abbas."
"Sai kin kiramin sunan uba, kiji dad'i ina Haulat banson cin fuska."
"Suna da inkiya ba cin fuska bane."
dariya duk sukayi.
Maryam ta ce
"Wai ya naji gidan shiru ne, Momma fa?."
"Unguwa suka tafi dukan su,
sun je gidan tsohuwar ta, yanzu haka sai yamma su dawo,
ni ma dama zan gama ne na bisu can d'in,
tun da kunzo muyi hira kawai."
nan suka cigaba da hira wanda rabi da kwatan hirar duk akan FEERYAL ce.
Haulat taki barin su su tafi tana ta jansu da hira.
ita dai FEERYAL da ido kawai take binsu, hakan nadaga cikin dabi'ar ta rashin magana da yawa, bata daga cikin yara irin masu yawan surutun nan.
Har kusan azahar suna gidan sai da Hajja Umma ta kira Maryam a waya ta ce ta dawo mata da jikarta yanzun nan, kafin suka tafi.
Washegari kuwa gyaran gashi Maryam ta d'auke ta suka tafi.
suna shiga shagon kallo ya dawo kansu.
daga nan suka wuce gidan Aunty Zainab yayar Aunty da take binta.
FEERYAL taga kauna a gidan ita da 'ya'yanta kamar zasu goyata, har Aunty Zainab tace a bar mata ita tayi mata kwana biyu.
Hajja Umma ta ce
maza-maza a dawo mata da ita.
Duk in da Maryam zata je da ita take zuwa duk wanda ya gansu tare kuwa sai ya tambaye ta a ina ta samo ta, idan ta ce dasu d'iyar Aunty ta ce suyi ta shan mamaki.
Wad'an da suka san Aunty'n nata kuwa da mijin da take aure sukan gaskata hakan a take, dan sanin ko waye mijin Aunty'n nata.
dan cewa suke kud'i zai iya komai wata kila akwai dangantakar nesa da kud'i ya iya janyo sa.
ma'ana ya na da dangi da suka shafi wata kabilar ba hausa ba, wan da har ya kaiga samun d'iyar da ta yiyo kamarsu.
Satin FEERYAL guda a Abuja a ka samar mata makaranta ta fara zuwa.
Lagos
Tun da Ajeemal ya sami labarin barin FEERYAL gidan gaba d'aya yaji ba dad'i.
Miemie ma har kuka tayi ta kaurace wa sashin kakan nasu, ko wani abin tab'awa Ammah ta bata ta kai wa Hajiya, sai dai ta je ta kaiwa Ameerah ko Sahla ko Nabila ta ce su kai mata, inji Ammah'n ta.
Ajeemal ne zaune a parlor'n Mommy yana cin abinci.
Mommy na hakimce a kan kujera tana kallon TV.
su Ameerah da Sumayya suka shigo da uniform a jikin su dawowan su daga school ke nan.
tun kan su karaso parlour'n Sumayya ta ce
"Mommy kiji wai Ameerah zata zana paper a primary 5, na ce ta bari next year muma sai da muka kai 6 kafin muka zana, wai ba wanda ya isa ya hanata, dan taga kawayen ta sunce zasu zana this year."
baki Ameerah ta murgud'a mata cikin tsiwa ta ce
"Sai na zana sai ki hana ai ina ruwanki da ni 'yar sa ido."
Mommy tayi saurin cewa
"Ina ruwan ki da ita Sumayya in tace zata zana,
kinsan dai Ameerah ba jahila ba ce kwakwalwar ta na ja,
ko a primary 4 take tace zata je JS kinsan dai zata iya ko, babu abinda 'yan JS d'in zasu nuna mata."
Ajmal daya bi Ameerah da harara ya ce
"Mommy wannan ce me kwakwalwar, dan baki tab'a zaunar da ita bane, in banda rashin kunya babu komai a kanta,
ai mai ƙwaƙwalwa sai FEERYAL yarinyar akwai ilimi har mamaki basirar ta yake bani."
da sauri Mommy ta katse shi ta hanyar buga masa tsawa
"Rufamin baki ita FEERYAL d'in kanwar uwarka ce ko kanwar uban ka,
sai taje can ta karata da kwakwalwar ta mara amfani dan da uba ake ado, mun jefar da kwallon mangoro mun huta da kuda,
kada ka sake ambata min sunan mayyar aljanar can,
ni harma na mance da ita,
shine bari ka tuno min da ita kana so ka b'ata min rai,
to kafita idona na rufe kada na sake jin sunan 'yar nan a bakin ka, bare har ka danganta min ita da 'ya'yana!."
Kai ya girgiza ya ce
"Allah baki hakuri Mommy."
ya mike ya d'au plt d'in abincin sa ya yi waje.
ta bisa da harara tana fad'in
"Ai ba'a barka banza ba, sai na mike tsaye a kanka."
Zaune Daddy ya ke cikin parlour'n sa yana kallon labarai a TV, kira ya shigo d'aya daga cikin wayoyin sa da suke zube kan table d'in gaban kujerar da yake kai.
Dr Omar sunan daya bayyana kan screen d'in wayar kenan.
ya janyo wayar tare da picking na call d'in,
ya kai wayar kunne tare da yin sallama.
da sauri cike da girmamawa Dr Omar ya amsa sallamar yana d'aurawa da fad'in
"Barka da warhaka ranka shi dad'e, ya gida ya kokari ya ji da jama'a."
"Alhmdulillah, Dr Omar ya aikin ya masu jiki?."
"Alhmdulillah gashi nan muna ta fama kam sai godiyan Allah, guri ya kacame, Alhaji dama akan batun mu na rannan ne na kuma kiran ka, Allah yasa dai ban matsa da yawa ba,
a gafarce ni dole ne yasa ni hakan,
dan Allah Alhaji a taimaka a sake mana magana da Dr mu asibiti tana bukatar sa."
Daddy ya gyara zama tare da sauke idanunsa kan kofa. inda yajiyo muryar Aunty da ta shigo da sallama kana ya ce
"A'a wai har yanzu bakuyi magana da shi bane, dana ji shiru ai na d'auka kun rigada kunyi magana."
"Kwanaki munyi magana da shi har ya amsa min kan cewa zai dawo, to ganin shiru sai na sake tuntub'arsa da batun,
to dai har yanzu ban sami kwakkwaran amsa a gurin sa ba, kasan mutumin namu sai ana had'awa da lallami, idan ya baud'e bazamu iya karkato shi ta dad'i ba,
yanzun nan muka fita mitin all Doctor's gaskiya na fahimci irin gudunmawar da zamu samu 100%
idan yana cikin mu, gaba d'aya mitin d'in nan a kansa ya kare, na tayaya zamuyi ya dawo cikin mu,
kwanaki munyi taro a government house mai girma Gwamna da kansa sai da ya tambaye sa,
a ranar ma sai da na kirasa na sanar masa,
sai dai is not serious ni nasan baya bukata dama can ni nayi ta tirsasa masa,
da bibiyar sa har hospital d'in sa,
kafin ya yarda ya fara zuwa general hospital,
ni da kaina na shigar da takardun sa badun yaso ba,
dan Allah Alhaji a samana baki cikin lamarin muna bukatar sa."
Daddy ya jinjina kai ya ce
"To ba damu insha'allah zamuyi magana da shi."
Dr Omar ya yi ta masa godiya kana ya yi masa sallama ya kashe kiran.
Daddy ya maida hankalin sa kan Aunty data karaso ta zauna gefen sa.
ta tsiyaya masa had'in lemun da ta had'a da kanta cikin kyakkyawan cup, ya yi sanyi kuwa amma ba sanyi mai cutarwa ba,
ta tad'ago ta mika masa.
ya gyara zamansa da kyau ya karb'i cup d'in yana binta da murmushi sannan ya ce
"Nagode Ammie'n FEERYAL."
murmushi tayi masa tana rufe ragowar lemun.
Ya kai cup d'in bakinsa ya kurb'i lemun ya lumshe ido yana jin dad'in sa na rasa cikin bakin sa.
kana ya bud'e idanun nasa a kanta ya ce
"Ya yi dad'i sosai fa, kunyi waya da FEERYAL yau kuwa? nayi ta gwada lambar hajja Umma baya tafiya, Alhaji kuma ya ce min yana Kano yau sai gobe sai koma."
"Kafin na zo nan munyi waya da ita a wayan Maryam, nima na kira wayan Hajja Umman bai tafi ba, Maryam take ce min wai FEERYAL d'in ce ta cinye cajin wayar nata da game."
dariya Daddy ya yi ya ce
"Da kyau mana, gobe zansa a kai mata sabuwar waya,
sai tayi ta buga game ta barwa Hajja Umma nata."
Murmushi Aunty tayi tare da mikewa tsaye, tana jin kewar d'iyarta, damma kullum suna tare a waya suna kallon junan su ta video call.
Daddy ya yi saurin fad'in
"Ina kuma zakije Fad'imatu?
ki zauna mana ki tayani hira."
"Daddy ka shanye lemun nan duka akwai wani a fridge zan karo maka, anjima ka shigo kaci abinci dan naga alamun kafara jin yunwa."
tayi maganar tana son kawar da nasa batun, dan tasan yanzu haka Umma Karima tana hanyar zuwa side d'in nasa, dan itace da shi, kuma tana da tabbacin taga shigowar ta, dan takan aje 'ya'yan ta a hanya suna mata gadi.
tayi saurin nufar kofa tun kafin ya dakatar da ita.
Aiko tana sa kai sukayi kicib'us da Umma Karima.
kallon tuhumar me ya kawo ta sashin baran kwanan ta ba Umma Karima ta bi Aunty da shi.
itako batama bi ta kanta ba tayi gaba a binta,
tana jin miyagun maganganun da Umma Karima take aika mata su bata ko waiga ba.........!
Mommyn Twins ce
🌺🌺 *FEERYAL* 🌺🌺
*NA*
*RASHEEDAT S DIRECTOR*
( _Book 1_)
*~Free page~*
*_Littafin na kud'i ne 500 account no 3170524141 Rashida Salihu first bank ka-ki tura shaidar biya ta WhatsApp number ta 08034690723_*
*____________________________________*
*🌈🇰AINUWA 🇼RITER'S✍🏼*
*🇦SSOCIATION🤝🏻*
```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}```
https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation
*_domin shiga shafin mu na Bakandamiya danna nan_*👇🏻
https://bakandamiya.com/group/71/Kainuwa-writers-association
*____________________________________*
🅿️16
Rayuwa mai shud'ewa, mai tafi a sanu a sannu.
bayan wani lokaci mai tsawo....
rayuwa mai kyau da tsafta FEERYAL take gudanar da shi yanzu, babu tsangwama bare kyara,
tsantsar kauna da soyayya mai had'e da kulawa Abba da Hajja Umma da Maryam da duk wasu danginsu suke nuna mata.
in banda su da suka san wace ce ita babu wani baren da yasan asalinta,
abinda kowani bare ya sani shine ita 'yar Hajiya Fatima ce kuma d'iyar Alhaji Abubakar Fiya jika ga Tahir Abbas.
Sannu a sannu FEERYAL nakara girma da wayo ya yin da kyawunta ke dad'a karuwa yana tsole idon duk mai kallonta, wanda hakan yake son zamowa barazana a rayuwar ta.
dole Alhaji Tahir Abbas ya samar mata da security bayan direban da yake kaita makaranta ko kaisu unguwa idan zasuje da Maryam.
security na tare da su sabo da harin da wasu fitsararrun maza suke kawo mata.
Lagos
Da misalin karfe 1 da rabi na dare.
(Zero Club)
baka jin ko mai sai tashin sautin kid'an daya karad'e ciki da wajen Club d'in.
maza da mata ne a cakud'e, suna ta tikar
rawa cike da fitsara suna rungumar junan su.
gaba d'ayan su 'ya'yan manya ne, 'ya'yan masu kud'i masu fad'a aji.
Wasu kuma suna zaune suna ta aikin bushe-bushen shisha ya yin da 'yanmata ke makale a jikinsu, suna ta badakalar su.
Zaraddin dake zaune ya baje kafa,
ya yi doguwar mika, kana ya aje mabusar shishar dake rike a hannunsa yana aikin busawa,
ya janye budurwar dake rungume da shi, tana ta aikin shafa shi.
ya mike yana duban agogon dake daure a hannunsa kana ya ce
"Beb zan shiga gida 2 saura yanzu nasan sunyi ta kiran wayoyi na ma suna mota."
mikewa tayi ta sakalo hannayen ta a wuyansa ta narke murya tare da kashe masa ido irin na gogaggun 'yanmatan bariki.
"Din wai yaushe ne zaka waye kana babban yaro ace kamar kan nan wai har yanzu ba'a dai na sama ido a gida ba,
me zai hana mu kwana a nan kawai."
hannunsa ya tura cikin rigarta yana wani sakin murmushin gefen baki, sannan ya zaro hannun ya d'an ture ta a jikin sa.
Da sauri ta dad'a matso shi tsoron ta d'aya kada ace yarabu da ita ke nan, dan tun d'azu ta lura da kallon da yake ta bin wasu sabbin 'yanmatan da suka shigo d'azu.
Ziyad ya mike ya yana fad'in
"Ke yayan Dad d'in sa fa dodo ne mugun tsaro ne da shi, kinsan kuma duk iskancin mu munajin maganan nagaba."
Zaraddin bai kulasu ba ya sa takalminsa ya nufi hanyar fita.
Da sauri Ziyad ya bishi yana fad'in
"Din kar ka mance gobe ne fa Birthday party Neela, kar mu kuma jin kunya a gaban su Bash,
irin na birthday Seena 1 ko 2 million ya kamata mu rike mushiga filin nan da shi."
kai Zaraddin ya gyad'a yana shigewa cikin motar sa.
dai-dai lokacin da Seena budurwar da suke tare da shi d'azu ta karaso.
ta bud'e gefen mai zaman banza ta shiga ta zauna.
"Din muje mu kwana agidan ku, yau bazan iya kwanan nan ba, baka nan."
ido yad'an tsura mata sai kuma ya juyar da kansa ya yi wa motar key yana cewa
"Fita Seena an fad'a miki nafara hauka ne, ki koma gidan ku kije ki kwana a can."
zata kuma magana yabuga mata tsawa
"get out please."
kina dad'a tsayar da ni dare yana da d'a yi."
Ta bud'e ta fita tana tura baki, taso su kwana tare koba a nan ba ko a gidan nasu ne.
yaja motar a guje yafiya a Club d'in yana maganar zuci
"Yanzu haka wancan tsohon yana nan idanunsa biyu ka dawo yasoma tuhumar ka in da ka fito, mtsst."
yaja tsaki yana kara gudun motar ya d'au hanyar A.A FIYA STREET.
Yana isa bakin get d'in gidan su, ya yi hon har sau biyar ba'a bud'e masa get ba.
a kufule ya fito daga cikin motar, ya tab'a karamar kofa yaji ta a kulle.
rai b'ace yashiga bubbugawa da karfi.
security suna ji basu ko kalli kofar ba, duk da suna da tabbacin Zaraddin d'in ne ya dawo, dan shine yake dawowa a'irin wannan lokacin ko fin irin lokacin ma.
tun da karfe goma na daren al'a'dar Daddy ne sai yaje ya duba matasan gidan shin kowa ya dawo kafin ya je ya kwanta.
bayan ya duba yaga kowa na nan shine kawai baya nan har wajen karfe 12 yakuma zuwa da kansa ya duba yaga bai dawo ba,
ya sanarwa security idan ya dawo kar su bud'e masa kofa tun da ba yau ya saba yin hakan ba.
Zaraddin yakai minti goma tsaye yana buga kofa, babu security daya taso bud'e masa.
dogon tsaki ya ja, ya juya ya koma motar sa ya d'au wayoyin sa da tun zuwan sa Club d'in rabonsa da d'aukar su.
nan yaga missed calls sun cika wayar.
na Ajeemal ya fara cin karo da shi, sai na Dad da Mom d'in sa.
a karshe kuna 1 missed call na Daddy.
Tsaki yakuma ja
"Sai kace mutum zai b'ata sun wani cika min waya da kira."
ya dannan no d'in Ajeemal.
har kiran ya yanke bai d'aga ba, yakuma mai da kiran har ya kusa yankewa kafin ya d'aga.
A b'angaren Ajeemal kuwa kiran wayar ne ya tashe sa daga bacci.
ya janyo wayar tare da d'aga kiran cikin muryar bacci ya yi sallama batare da duba mai kiran nasa ba.
jin ya d'aga Zaraddin ya ce
"Ajeemal zo kasa wad'an nan banzayen security su bud'e min kofa, nakai 20min a tsaye suna jina ina hon sunki bud'ewa sai kace gidan uban su!."
Ido Ajeemal ya mustsike cike da jin bacci ya mika hannu ya kara hasken Night Shining Bulb in da ke kan bedside, ya dubi agogon dake like jikin garun d'akin karfe 2 har da mintuna 15 ya ce
"Zaraddin har this time kana waje baka shigo gida ba?."
"Dalla kazo ka bud'e min kofa ko ma meye kabari na shigo ciki tukun."
kai Ajeemal ya girgiza ya janye blanket d'in da ke rufe a jikin sa ya sauko a gadon yafita ya nufi bakin get.
Kasancewar tazaran da ke sakanin babban get da side d'in nasu, sai da ya yi tafiya mai d'an tsawo kafin ya isa bakin get d'in.
A zaune a waje ya tadda security guda biyu, da alama hon da bugun kofar Zaraddin d'in ne ya ta sosu.
Ajeemal ya ce
"Ku bud'e masa get ya shigo."
suka ce
"Alhaji ne ya ce kada a bud'e masa ko da ya dawo."
Ajeemal ya ce
"Kar ku damu ku bud'e masa babu komai."
nan d'aya daga cikin su ya karasa ya bud'e get d'in.
Zaraddin ya ja tsaki ya dannu hancin motar da gudu kamar zai d'auke security'n.
ba shiri ya matsa gefe.
ya d'an tafi can ya tsaya Ajeeml ya karaso ya bud'e d'aya gefen ya shiga yana binsa da kallon tuhuma.
Zaraddin ya d'auke kai ko a jikin sa ya ja motar zuwa side d'in su.
gudun kar Ajeemal ya tsare shi da surutu ya sauka da sauri ya je ya bud'e get d'in side d'in su ya dawo ya shiga motar suka karasa parking lot d'in su,
ya gayara parking gefen motocin su Ajeemal d'in.
yana kashe motar ya fita.
Ajeemal ya bi bayan sa, har suka shige parlour'n su.
yana kokarin shigewa bedroom d'in sa Ajeemal ya ce
"Zaraddin yanzu abinda kakeyi kana kyautawa kan ka ke nan,
har wani irin dad'i zakaji karaba dare a waje baka dawo gidan iyayen ka ba, ba wani aiki kake ba bare ace aiki ne ke tsaida ka ka kai har dare irin haka,
ya kamata kayiwa kanka karatun tanatsu, ka dai na abunda kake yi d'in nan, babu riba cikin ta sai fad'uwa,
har sau nawa na kiraka a waya baka d'aga ba,
karigada ka san Daddy kullum sai yazo ya duba duk muna nan ko ba ma nan,
d'azu yazo baka nan karka mance shekaran jiya ma yazo baka nan, kuma na fad'a maka,
madadin ka kiyaye shine ka sake aikatawa."
"Kai bafa wani guri naje ba mittin muke da abokai na."
"Aiki kuka somayi kai da abokan naka da kuka zauna yin mittin, wace irin aiki ce arasa lokacin yin mittin sai tsakar dare, maita ce ko sata shine dai nake da tabbacin ake yin sa a tsakiyar dare,
wlh Zaraddin kayi wa kanka fad'a nadai fad'a maka."
hararar Ajeemal ya yi ya ce
"Idan ina maita ko sata ku zaku fara sani, dalla karabu da ni malam kaje ka kwanta."
Hayaniyar su ne ya tashi Shamsuddin da Faisal, suka fito daga d'akunan su.
dai-dai lokacin da Zaraddin yake shigewa cikin bedroom d'in sa.
Shamsuddin ya dubi Ajeemal ya ce
"Ka tsaya b'ata lokacin ka a cikin daren nan dalla rabu da shi, yaje ya yi ta yi tun da hakan yafi masa."
Faisal ya girgiza kai yana fad'in
"Bansan me ke damun Zaraddin ba, d'azu da naga wannan abokin nasa Ziyad d'an gidan Ministan nan nasan cewa da in da suka kulla zuwa yau,
wlh wannan Ziyad d'in ba mutumin arziki bane, baima kamata ace wani d'an gidan nan yana harka da shi ba, har ma a gansa yana shigowa cikin gidan nan."
"Ba shi yaja ba duk wani kare da doki sune abokan sa, yaran da suka fi karfin iyayen su, sai abin da sukaga damar yi suke yi."
ce war Shamsuddin, yana hararar kofar sa.
Zaraddin ya leko yana fad'in
"To munafukai idan kun gama sai kuje ku kwanta,
ni nayi kwanciya ta abina."
ya turo kofarsa ya rufe.
"Zaka gamu da Daddy gobe ai."
Shamsuddin ya fad'a ya juya ya shige bedroom d'in sa.
Faisal da Ajeemal ma suka wuce nasu d'akunan.
Washegari tun karfe 9 da rabi na safe Zaraddin ya tashi ya nufi sashin Daddy.
kamar yadda suka saba ko wacce rana da safe karfe 10 suke bin kan iyayen nasu duk su gaishe su.
acikin su kuwa shine mai lattin zuwa gaisuwa, yakan kai goma da rabi wani binma har 11, idan yagama baccin gajiyar yawon daren sa kafin yafita zuwa gaishe su.
sai gashi yau yariga kowa zuwa sashin Daddy.
A parlour ya tadda shi fitowar sa daga bedroom kenan, yana kokarin zama Zaraddin d'in na shigo wa.
ya karaso tsimi-tsimi kansa a kasa, ya zauna kasan carpet kusa da kafar Daddy.
cikin kwantar da murya ya shiga gaishe sa.
Daddy ya zuba masa ido batare da ya amsa gaisuwar tasa ba kana ya ce
"Ina ka kwana Zaraddin?."
da sauri ya d'ago ya ce "A ina na kwana kuma Daddy a gida na kwana wlh."
"Karya ka ke har karfe 12 ina tsaye da kafafu na ina jiran dawowar ka, har nayi bacci baka dawo gidan nan ba."
da sauri ya mike yana cigaba da marairaice murya ya saka gwuiwowin sa a kasa kamar mai niman gafara yana wani kwantar da kai
"Wlh wlh Daddy a gidan nan na kwana Ajeemal ma shaida ne, shi ya zo yasa security suka bud'e min kofa,
nafi awa uku a waje tun 11 da wani abu nake bakin get suka ki bud'e min, sai da na kira sa kafin yazo yasa suka bud'e,
ni Daddy ina zanje na kwana batare da izinin ku ba idan ina son zaman lafiya da sanyawar albarka."
Shiru Daddy ya yi yana kallon sa, shi dai a sanin sa sai da 12 tayi jiya kafin yaje ya ce da security kada su bud'e masa get. amma gashi shi yanzu yana fad'in
wai tun 11 da wani abu yake bakin get.
gaba d'aya Zaraddin ya marairaice tamkar iya gaskiyar sa yake fad'i.
har kuwa Daddy ya yarda yake ganin wata kila basuji hon d'in sa bane yasa basu bud'e da farko ba, bayan kuma yaje yace dasu idan yazo karsu bud'e shiyasa suka ki bud'e masa daga baya.
Daddy ya ce
"To naji amma dai kasan dokan karfe goma ne kowa ya kasance a gida ko, duk abinda kuke ku bari ku dawo gida,
duk abin da kake koma mene ne ka barshi ka dawo gida, kada ka kuma ketare karfe goma daga yau na fad'a maka."
"To insha'allahu Daddy bazan karaba jiyan ma akasi aka samu, a gafarce ni."
Daddy ya jinjina kai yana cewa
"Tashi ka je, kadai kiyaye kaji na gaya maka."
Zama ya gyara ya tsunkuyar da kai yana d'an sosa bayan keyar sa.
Daddy ya dube sa yana fad'in
"Ya akayi kuma?."
dad'a tsunkuyar da kai ya yi yana shafo keyarsa sannan ya ce
"Am dama Daddy wani d'an kud'i ne nake da bukatar su."
Sallamar da su Ajeemal sukayi ne ya katse shi daga abin da yake son fad'a.
Daddy ya amsa suka karaso suka zazzauna kasan carpet suna gaida Daddy'n.
ya amsa yana tambayarsu sun tashi lafiya?.
duk suka amsa da lafiya lau.
Suma zaman suka gyara da alamar akwai abin da ke tafe da su.
Daddy ya dubi Zaraddin ya ce
"Uhum ina jin ka Zaraddin me ke tafe da kai?."
Zaraddin yabi su Ajeemal da kallon kasa-kasa duk ya harare su kana ya muskuta ya ce
"Da ma Daddy kud'i
All Chapters
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 14 Chapter of 20