Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
sae da aka yi Azahar snn ya shigo dakin da leda a hannunsa, ya ajiye ledan ya karaso gabanta ya durkusa yace "me yasa xa ki kwanta kan tiles?" bnxa tayi masa ta dauke kai, bae kuma tanka ta ba ya gama hada drip din da ya siyo ya makale shi snn ya mike yana kallonta yace "kina jin yunwa koh wife?" yi tayi kmr ba da ita ya ke ba, ya karasa kusa da ita ya dagota, ta sakar masa kukaya dauketa, duk ya ji ta fayau ba nauyi ya kwantar da ita kan gado ta mike xaune da sauri cikin kuka tace "bana so, ni ka kyaleni" murmushi yyi yana kallonta yace "to me nayi maki, ni kawae bbyna xan kara ma lfya fa?" Ta kuma fashewa da matsanancinkuka tana kallonsa, ya jawota jikinsa a hnkli yace "tosbda me kike son mu yi kisa wife?" Cikin kuka tace"sbda bna son cikin, kullum sae inyi ta jin amae, ko ina ya dinga min ciwo?" Khaleel yyi murmushi yace"toh shknn xan cire maki amma da sharadi," ta dago manyan idonta tana kallonsa, alamar ya gaya Mata sharadin, jin yyi shiru yasa a hnkli tace "na mene?" Yace "xan gaya maki anjima da daddare, ynxu dae ki bari in sa maki drip din don ki ji kwarin jikin ki kafin a cire cikin" wani irin kallo tayi masa sae kumata saka kuka tace "ka tsamman ni yarinya ce, wae nixaka ma wayo koh, to bana son drip din wllh, kuma da kaina xan je a cire cikin, don ba kai kke wahala ba shi yasa kke son ka mun wayo" kallonta kawae Khaleel yake can ya mike ya fice daga dakin. Bae kuma dawowa dakin ba har aka yi sllhn la'asar yana xaune falo da Al-ameen suna tattaunawa, Khaleel ya girgixa kai yace "he won't ever get me, bana ma son in je in kara bata masa rae" Al-ameen yace "kai dae ka gwada tukun Khaleel, dad naka fa na da saukin kai, parent dinta ne suka harxuka shi hka" Khaleel yace "OK I will do as yhu said, ita kuma natadad din fa ya xa mu yi da shi? Ya dau xafi da yawa" Al-ameen ya girgixa kai yace "may b idan ya ga grand child dinsa xuciyarsa xae yi sanyi, ko kuma idan gskya ta bayyana, amma kar ku je gun sa ynxu gskya" Khaleel yace "cikin da take cewa sae na cire mata ma" Al-ameen yace "ka share ta kawae, haukakke xa ka cire mata ciki, nd lastly Khaleel idan xa kaji ta nawa ka mayar ma da Najeeb duk abun da ya baka daxu, he is a crook, though u won't get dat now sae nn gaba idan komae ya bude, but sae in har xa ka ji ta nawa, idan taimakon ka yake son yi don me bae yi tun da ba sae da ya ji kana gidana, get this plss... Yhu went to birthday on dat vry day, u got drunk, ya maido ka gida ya kai ka har cikin dakin ka, sae ga shi washegarin ranan an ga takardan saki cikin drawern ka, kuma idan ba mantawa nayi ba jiya da kke bn lbri kace shi yace Fateema ta ba ka magani cikin drawern idan ka tashi, y will ur common sense nt make yhu understand somethin in here?" Shiru Khaleel yyi yana kallon abokin nasa maganan sa na karshe na masa yawo a ka, girgixa kai yyi a xuciyarsa yace "No! Najeeb baxae min hka ba, never! No he cant." Al-ameen sae kallonsa yake don for sure yasan Khaleel ba dauka xae yi ba, can ya tabe baki yace "no big deal, watarana in fact ba sae ma watarana ba vry soon gskya xata bayyana" Khaleel dae bae ce masa komae ba, Al-ameen yace"in ka ga xa ka iya tsayawa gidana gashi ku tsaya damatarka don gobe xa mu koma Zaria, I took a wk leave, nd tomorrow is makin it a wk, in kuma ka ga kafi son gidan Najeeb din ne fine," Khaleel dae bae ce komae ba Al-ameen ya dauki wayarsa da ake kira ya daga, mikewa Khaleel yyi ya nufi sama, ko kadan bae ji ddin xargin da Al-ameen ke ma Najeeb don a tunaninsa dat will be d lst thin da Najeeb xae masa a rayuwa" amae ya tar da Ashnaah ke yi a bathroom kmr xata amaye hanjin cikinta, ya karasa da sauri ya durkusa kusa da ita cike da tausayinta yana mata sannu, kuka ta fashe da, ya mike ya shiga gyara mata jiki snn ya fito da ita daga bayin, kwanciya tayi nn da nn baccin wahala ya dauketa, sae da daddare ya samu ya lallabata ya sa mata drip din bayan ta dan sha kunun da Maryam tayi Mata, hka ya kwana ranan yana gadinta da daddare don duk motsin da xata yi a kan idon sa, sae Asuba drip din ya kare ya cire mata, snn yyi sllh ya samu ya kwanta. Karfe goma saura na safe Al-ameen yace da Khaleel xa su koma Zaria, Khaleel ya kasa ce masa baxae xauna gidansa ba ya amsa da xae xauna kawae duk da bae yi niyar xama ba, dubu hamsin Al-ameen ya basa ya rike, Khaleel ya ki amsa yace ae yana da kudi enuf, nn kan centre table Al-ameen ya bar masa ya fice daga falon, Maryam ta so suyi sallama da Ashnaah amma har lkcn bata tashi ba, tace "in ta tashi ka ce mata sae mun yi waya doctor, kuma plss ka kula da ita da kyau, cikin nn na wahalar da ita wllh, da xa ka ji ta nawa ma kace momy ta samo maku yar dattijiwa da xata dinga kula da ita ta dinga mata duk abinda take so tun da na ga kunu ma kawae take iya sha" Khaleel yace "In'sha Allah Maryam, tnx a lot we re grateful" har bakin motarsu ya raka su, sae da Al-ameen ya ja masa kunne kan kar ya kuskura ya bar Najeeb ya kara xuwa kofar gidan snn suka wuce, shi dae Khaleel murmushi kawae yyi ya komacikin gida yana tunanin ynda xae tunkari dad dinsa, yasan ma ba sauraransa xae yi ba, yana shiga daki ya tar da wayar Ashnaah na vibrate ya dauka yana kallon mai kiranta, momy ya gani, yana rike da shi har ya katse ya ga miscals din da yawa kuma duk na momynta ne da Ashfah, kira aka kuma yi ya juya yana kallon Ashnaah da ke ta bacci, ya fara tunanin ya daga ko kar ya daga. ~Dr Khaleel~ By Khaleesat Haiydar102....Sae da wayar ta kusa katsewa snn Khaleel ya daga, shiru yyi da farko don ya rasa ta inda xae fara mgnan, jin momyn ta ambaci sunan Fateema yasa ya bude baki da kyar yyi mata sallama, shiru momy tayi daga daya bangaren, sallaman ya kuma yi momy ta amsa wnn karan, dukar da kai yyi kmr tanaganinsa ya gaisheta, momy ta amsa ta kuma yin shiru, rasa me xae kuma cewa yyi, can yyi saurin cewa "Amm bacci take momy, idan ta tashi xa ta kira" Momy tace "OK ngd" sallama yyi mata ta kashe wayan, Khaleel ya sauke ajiyar xuciya ya ajiye wayar ya xauna gefen gado yana kallon Ashnaah, wayarsa ya shiga ring ya daga yana kallonme kiran ya ga umminsa ce, ya daga tare da mata sallama suka gaisa, Ummi tace "Fateema fa? Ya jikin nata?" Yace "Da sauki Ummi, bacci ma take" Ummi tace "to Allah ya sauwake, dama Rukayya ce tace tana son xuwa, shine nace bari in kiraka ka fada mata inda kuke" Khaleel yace "to Bari in kirata Ummi" Ummi tace "toh shknn, ka gaida fateeman idan ta tashi" sallama suka yi ya katse kiran ya shiga neman layin kanwartasa don yi Mata kwatancen inda su ke. Yana ajiye wayar kiran Zeenat ya shigo wayar kuma, dagawa yyi suka gaisa tace "dama ina son xuwa in duba Fateema ne doctor" Khaleel yace "OK bbu damuwa, lemme sendyhu address" Address din gidan Al-ameen ya tura mata, Karfe sha daya Rukayya ta iso gidan ta kira shi, Khaleel ya fito ya tare ta su ka shiga gidan a tare, falo ta bar abincin hannunta da Ummi tace ta kawo ma fateema ya nufi sama da ita, a stairs yake tambayar ta ko dad dinsu na nan, tace "ya tafi Abujajiya," yace "OK, me kika kawo a kula" tace "waina ce da miya" Ashnaah na xaune suka shigo dakin, ta daga kai tana kallon Rukayya, Rukayya ta karaso inda take ta xauna gefen gadon tace "sannu, ya jikin?" Ashnaah tace "da sauki" Rukayya tace "to Allah ya kara lfya" mikewa tayi ta fita daga dakin don ba sabawa suka yi ba ta koma falo, Khaleel yace "Ummi ta kawo maki waina xa ki ci?" Shiru tayitana kallonsa, nn da nn ta ji sha'awar wainan sae dae tana tsoron kar ya sa ta amai, kmr xata yi kuka tace "nima bn san ko xan ci ba" murmushi yyi ya mike ya fita dakin, sae ga shi ya dawo rike da plate din wainar da miya a wani bowl, dauke kanta tayi dasauri ya karaso yace "baxa ki yi amae ba wife, dan kadan xa ki ci" a hnkli ta dago kanta tana kallon abincin, ya sakko da ita kasa yace "toh ci kadan ba da yawa ba" ta dan leka miyan ta dauke kai tace "ni hka xan ci bbu miya" yace "to dauka ki ci" daukan daya yyi ya kai mata baki ta karba ta shiga ci a hnkli,tun da ta fara laulayi sae ranan ta sa abinci baki, wayarsa ya dauka jin ana kiransa ya ga Zeenat ce, ya dauka tace ga ta a kofar gida, Rukayya ya kira yace ta je ta shigo da ita, Ashnaah tace "wacece?" Ya ajiye wayar hannunsa yace "Zeenat ce xa ta xo gaishe ki wae" ta hade rae tace "me ya same ni?" Yi yyi kmr bae ji ta ba, sae kuma yace "momy ta kira kidaxu kina bacci na dauka" Ashnaah tace "wace momy" ya daga manyan idonsa yana kallonta yace"ur mum" shiru tayi tana kallonsa, a hnkli tace "me kace mata?" Ba tare da ya kalleta ba yace "na ce kina bacci" wayarsa ya dauka ya mika mata yace"gashi ki kirata" ba musu ta karbi wayar a sanyaye, ya mike ya fita daga dakin, bugu biyu momy ta dauka, Ashnaah tayi mata sallama tare da gaisheta, momy tace "kina lfya fateema? Ya jikin?" Ashnaah tace "da sauki momy, kin kira daxu ina bacci" momytace "ehh, kina dae cin abinci koh?" Ashnaah ta gyada mata kai tace "ina ci momy, Ashfah fa?" Momy tace "dama ita ce ke damuna tana son xuwa gun ki, shine nace Bari in kira in gaya maki ki tura mata address" a sanyaye Ashnaah tace "Abba fa momy?" Momy ta dan yi shiru snn tace "baya nn, yana Abuja" Ashnaah tace "toh xan turo mata address din ta nmbrta" sallama suka yi Ashnaah ta ajiye wayar Khaleel, jikinta a Sanyaye, duk lkcn da ta tuna kalaman Abbanta na karshe a kanta sae ta ji hnklinta ya tashi, bata fatan Allah ya dauki ranta bata yi reconcile da Abbanta ba ya yafe Mata, da koh ta bani a rayuwa, hawaye ne ya shiga sakko Mata, dai dai nn Khaleel ya shigo dakin, karasowa yyi inda take da sauri ganin hawaye fuskarta da damuwa yace "me ya faru wife, momy ta ji haushi na daga kiranta koh?, am vry srry I won't do dat again" girgixa masa kai tayi tana hawaye a hnkli tace "bata ce komae ba, Abbana nake tunani" Khaleel ya dan sauke ajiyar xuciya yace "kar ki damu wife, wataran sae lbri, kuma In'sha Allah duk xa mu gama da iyayen mu lfya" gyada masa kae kawae tayi, yace "to share fuskar ki, kin ga Zeenat taxo gaishe ki" lkci daya Ashnaah ta hade rae tace"wae gaisuwar me xata xo ta min," Khaleel yyi shiru snn yyi murmushi, Ashnaah tace "bana son gaisuwar, ta wani xo wajen ka ta fake da cewar ni taxo gaisarwa meye hadi na da ita, ina ta san ni ko kuma na Santa, kawae ta xo wajen ka ta wani ce ta xo gaishe ni" fashewa da kuka tayi, Khaleel ya danne dariyarsa yace "Haba bby meye abun kuka a nn, ba sae in bar gidan ba idan ta gama gaishe ki ta yi wucewarta" Ashnaah ta galla masa harara ya mike yana dariya ya fita, bin sa tayi da kallo lkci daya ta ji haushin kanta, share hawayen fuskarta ta shiga yi a hnkli, y will she show she cares dat much abou him, he is d cause of everythin she is goin through, me yasa son sa ya shigeta lkci daya bayan duk wahalan da ta sha a hannunsa, girgixa kai tayi ta tura wainan gabanta cike da jin haushin kanta, dae dae nn Zeenat ta shigo dakin da sallama rike daflask a hannunta da ledan fruit, Ashnaah ta sunkuyar da kai da sauri, Zeenat ta karaso gabanta tana murmushi tace "sannu Fateema, ya jikin" Ashnaah ta kasa yi mata abinda tayi niya, ta dago kanta ta dan kirkiri murmushi tace "da sauki, Alhmdllh," Zeenat ta ce "toh Allah ya kara lfya, ga kunu na yo maki" Ashnaah tace "to ngdd Allah ya saka da alkhairi" Mintin Zeenat goma a dakin ta mike tace "xa ta koma" Ashnaah ta kuma yi mata gdya snn tace bari ta rakata falo, duk ynda Zeenat taso tayi xamanta ta bar rakiyan kn yadda Ashnaah ta yi suka sauko har falo, Zeenat na kallon Rukayya dake kallo a falon tace "doctor fa Rukayya?" Rukayya tace "ya fita wllh" Ashnaah na jin hka ta juya ta nufi sama, Zeenat tace "to idan ya dawo ki ce masa na tafi" Rukayya tace to, snn suka yi sallama ta fita, sae a snn hnklin Ashnaah ya kwanta ta koma sama, Karfe biyu saura Rukayya tayi ma yayanta da Ashnaah sallama ta wuce gida. Da yamma Karfe hudu da rabi Khaleel ya sa Ashnaah ta shirya suka tafi can gidansu tun da Abbansa na Abuja. Suna gidan har kusan Karfe shidda sae ga Abba ya dawo daga Abuja, ba karamin tashi hnklin khaleel yyi ba don bae taba xaton dawowan dad din nasa a lkcn ba, toh da wani idon ma xae kalli mahaifin nasa, da ma bae shigo da motarsa cikin gidan bne, ita kanta Ummi bata so dawowan mai gidan nata ba a lkcn sanin ita kanta sae ranta ya baci, ae kam hka ya faru don ko da ta je yi masa sannu da xuwa shareta yyi, ta bar masa dakinsa kawae, tana dawowa bedroom dinta Khaleel da ke xaune ya rike kansa ya mike da sauri yace "Ummi xa mu tafi" Ummi ya galla masa harara tace "tana baccin xa ku tafi" ya juya yana kallon Ashnaah da kebacci tun shigowar su gidan, a hnkli yace "tashin ta xan yi Ummi" Ummi tace "bbu inda xa ku sae ta tashi" kasa mata musu yyi ya koma ya xauna, ita kuma ta ci gaba da abinda take, a hnkli yace "xan iya xuwa gaida dad Ummi" girgixa masa kai tayi ba tare da ta kallesa ba tace "A'a kar ka je" bae kuma ce mata komae ba har aka kira sllhn Magrib snn ya mike ya shiga bathroom dinta yyi alwala ya ce ya tafi masallaci, Khaleel bae nufi masallacin da yasanxae hadu da dad dinsa ba, kuma ana idar da sllh ya dawo gida don ma kar su hadu bakin gate. Da kyar ya iya cin shinkafar da Ummi tayi masa ranan bayan ya dawo daga sllhn isha, Karfe takwas da kusan rabi Ashnaah ta tashi, Ummi ta kawo mata kunun da tayi mata, ta mike ta nufi bayi ta kuskure bakinta snn ta dawo ta dauki kunun tana sha, Karfe tara Khaleel ya shiga dakin rukayya yace ta duba masa falo ko dad na nn don xa su koma gida ne, ta dawo tace baya falo, komawa dakin umminsa yyi yace da ita xa su wuce gida, Ashnaah ta Mike ta dauki hijab din da Rukayya ta bata ta sa snn suka yi ma Ummi sae da safe, Ummi tayi masu Allah ya kiyaye suka fita daga dakin tana gaba yana biye da ita a baya, ido hudu Khaleel yyi da dad dinsa da sakkowansa falon knn yana cin fruit a kan centre table, Khaleel ya dauke kansa da sauri ya kasa ci gaba da tafiyar ya tsaya stairs din karshe, Ashnaah ta juya tana kallonsa, ita ma jikinta yyi sanyi, ta karasa falon a sanyaye ta isa inda dad din yake ta durkusa kasa ta gaishesa kanta a sunkuye, dago kai yyi yana kallonta, ya ajiye fork din hannunsa yana dan murmushi yace "lfya lau, kun xo lfya?" Ta dago Kai tace "lfya lau Abba," dad yace "to madallah, ashe kuna ciki nayi xaton kun tafi ne" ta girgixa kai tace "ba mu tafi ba" Dad yace "to yyi kyau, ya jikin naki?" Tace "da sauki Abba" yace "to Allah ya sauwake, ko xa ki ci kankanan ne in dibar maki" tayi murmushi tace "Aa nagode Abba" dad yace "A'a baria debar maki dae" murmushi ta kuma yi bata ce komae ba don sae taji kankanan ya bata sha'awa, dad ya dauki wani plate ya shiga deban mata kankanan snn ya sa mata toothpick ya mika mata, akunyace ta karba tare da yi masa gdya, yace "tashi ki koma kujera toh" kin tashi tayi ta shiga cin fruit din nn inda take, sae ta ji ina ma Abbanta ne hka, tunanin hka ya sa kwalla ya taru a idonta. ~Dr Khaleel~ By Khaleesat Haiydar 103..... A hnkli Ashnaah ta daga kai a sanyaye tana kallon Khaleel da ke tsaye har lkcn, suna hada ido ya dauke kansa, Dad kam ci gaba yyi da shan fruit dinsa, Khaleel ya juya ya koma sama da ganinsa kasan jikinsa yyi sanyi, a hnkli tayi ta shan water melon din har ta kusa shanyewa bata ji ya isheta ba, dad yace "yaushe ku ka xo?" Ta daga kai tana kallonsa tace "daxu da yamma" yace "shine xa ku koma ynxu?" Shiru Ashnaah tayi bata ce komae ba, dad yace "ku bari sae da safe ku tafi" kai kawae ta gyada masa, ya dauki wayarsa ya kira driver yace ya shigo falo ya samesa, ko minti biyar ba ayi ba drivern ya shigo dad ya ciro dubu biyu ya mika masa yace "kankana masu kyau xa ka siyo mata" kunya ya kama Ashnaah don ko kadan bata lura da har ta shanye kankanan gabanta gaba daya ba, da sauri tace "A'a Abba ni na koshi" Dad yace "bari dae ya karo maki ki kara" bata kuma cewa komae ba, dad ya canxa tasha xuwa news ya maida hnklinsa. Bayan minti sha biyu drivern ya dawo rike da ledan water melon, ya ajiye ma Dad kan center table, ya mika masa canjin dubu daya yace "na ga dayawa oga" dad yace "to rike canjin kai ma sae ka siya ka sha" gdya yyi ya fita daga falon, dad ya mike da kansa ya nufi kitchen ya dauko wuka da plate ya dawo ya dauki kankanan daya ya yanka snn yyi slicin dinsa kan plate din ya dauki toothpick ta saka ya mika ma Ashnaah da ke ta kallonsa, a kunyace ta ce "lahh Abba ni ya isheni fa" Dad yace "A'a ki dae kara" karba tayi tayi masa gdya kuma, har kusan Karfe goma da rabi Ashnaah na xaune falon da dad, ta dae ji ta fara jin bacci ta mike tana kallon dad tace "Abba bacci nake ji" yace "to tafi kiyi kwanciyar ki," ledan sauran kankanan ya mika mata yace "ga shi ki tafiya da sauran, Wanda aka yanka kuma ki saka a fridge" gdya tayi masa ta karba snn ta dauki plates din da tasha fruit din da nasa da wukan ta kai kitchen, tsaf ta wankesu ta ajiye snn ta fito ta kuma yi masa sae da safe ta nufi sama ina ma Abbanta ne hka da ta more rayuwa, dakin Ummi Ashnaah ta nufa, ta tarda Ummi xaune suna kallo da rukayya, Ummi tayi mata murmushi tace "sae ynxu" Ashnaah tayi murmushin ita ma, ta ajiye ledan hannunta xa ta xauna kasa Ummi tace ta dawo kan gado, ta xauna gefen gadon, Ummi tace "yana can dakinsa in kina jin bacci ki tafi ki kwanta kar ki takura kanki" Ashnaah ta sunkuyar da kanta tace "to ga fruit Abba ya siya min" Ummi tace "to kin gode" mikewa Ashnaah tayi ma Ummi sae da safe xata fita daga dakin Ummi tace "to kin bar fruit din" Ashnaah tace "A'a na sha da yawa Ummi, na koshi" Ummi tace "to dauka ki kai ma Khaleel" bbu musu Ashnaah ta dauki fruit din snn ta kuma yi mata sae da safe ta fita ta nufi dakin Khaleel, a hnkli ta tura kofar dakin ta same shi durkushe kusa da fridge dinsa, gabanta yyi mugun faduwa ganin abinda ke hannunsa yana dubawa, tasan baxae wuce expire date yake dubawa ba, yana ganin ta ya mayar da sauri ya fiddo ruwa, ta dauke kanta ta ajiye ledan hannunta ta nufi kan gado, ya bi ta da kallo yace "yhu re back wife" kai kawae ta gyada masa ta kwanta gefen gadon ta juya masa baya kmr bata son mgna rufe fridge din yyi ya dawo kusa da ita ya xauna yace "jikin ne wife?" Girgixa masa kai tayi da kyar tace "bacci xan yi" yace "OK wife, amma bari ki fara shan drugs dinki" girgixa masa kai tayi da sauri tace "amae xan yi" bata jira cewarsa ba ta juya masa baya, mikewa yyi ya dauko blanket ya rufa mata, ta lumshe ido kmr me bacci, gefen gadon ya xauna ta daya side din yana danna wayarsa, har kusan sha daya Ashnaah bata yi bacci ba amma bata bari ya gane ba, mikewa ta ga yyi yana kallonta, ta rufe idonta gaba daya kmr me baccin gske, fridge ta ga ya nufa ya bude ya fiddo kwalban daxu yana kallonsa rabon sa da shan giya tun ran da ya sha a birthday, ganinsa yasa yaji kmr ya shekara goma rabonsa da sha, Ashnaah taji kmr tayi masa mgna amma ta kasa sae taji hawayen takaici na sakko mata, budewa taga yyi ya koma bakin gado ya xauna ya kai bakinsa ya shiga sha, ko second talatin ba ayi da kai shi bakinsa ba ta ga ya cire da sauri, juyawa tayi tana kallonsa don yasan ma ba bacci take ba, ya ajiye kwalban hannunsa kasa gefensa ya rike kansa, mikewa taga yyi da hanxari ya nufi bathroom ta bi sa da kallo, amae ta ji ya shiga yi, ko motsawa daga inda take bata yi ba, amae ssae yyi a bayin, daga karshe ya fito da kyar bae bari sun hada ido ba ya nufi can gefen gado ya kwanta ba tare da ya kalli kwalban da ya ajiye kasa ba don ko ganinsa ma bae son yi, nn da nn bacci ya daukesa. Ashnaah tayi murmushi ta mike ta dauki kwalban taga har ya kusa rabi, bayi ta shiga da shi ta toshe hanci don ko warin bata son ji, ta tuttular da giyan snn ta dawo dakin ta bude fridge ta fita da sauran ma gaba daya duk sae da ta tuttulesu a bayi hancinta a toshe snn ta wanke bayin da kyar don duk tayi weak, wanka tayi da ruwan dumi ta fito da kwalaban ta ajiye su dakin tayi kwanciyarta da xanin jikinta, nn da nn bacci ya dauketa ita ma, can cikin dare ta farka ta dalilin aman da ta dinga ji, ta mike xaune da kyar ta jingina jikin gadon xuciyarta na tashi, juyawa tayi tana kallon Khaleel taga baccinsa yake, mikewa tayi ganin aman na neman taho mata ta nufi bathroom da sauri, ta durkushe ta shiga kwararo aman, hkn ya farkar da Khaleel

Chapter 24 of 29