Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
abinda kike so ba" nafisa ta ce"ina tsoron kada in fada zina ne,kin san zuciya bata da qashi" hajara ta gyara zama tace bari in wayar maki da kai. Sai da ta sake gyara zama tare da numfasawa sannan ta ci gaba da magana a nutse. Ni hajara tunda na taso na kasance mai son hulda da masu kudi,duk da iyayena masu karamin karfi ne.Lokacin dana zama budurwa duk kyau baya sharaba ne,saurayi in ba shi da mota bana fitowa,cikin haka muka hadu da alhaji kabiru lokacin na zo abuja tare da wata amarya makociyarmu dana rakota biki.Muna haduwa ya soma yi min barin kudi,nan fa na ce naga miji.Lokacin ina (SS3) ai ko tuni na saki makaranta muka yi aurenmu.An kashe kudi kamar tsiya,don duk unguwarmu a keffi ba a taba shagali da barin kudi kamar na bikina ba,tunda aka kawo ni mijina baya kula ni har kusan wata na yi masa magana sai yace min ba shi da lafiya kamar dai naki din nan. Muna nan zaune a haka saboda kudin da nake samu wata rana naje wani super market siyayya sai naga wani dan saurayi mai kyau nan take naji sha'awar shi don haka sai nace masa suna da motar kai ma mutane kaya gida? Yace in an siya da yawa ba. Na ce shi nake son fa ya kai min don na kula yana da nutsuwa.yace sai dai in ma Ogansu bayani. Ta dubi nafisa ta ce kina fahimta? Nafisa ta ce,"eh" hajara taci gaba da cewa na yi ma ogan nasu bayani sai yace ba damuwa. In gaya miki Nafisa nan nayi ta lodar kaya aka cika mota. Muna zuwa suka yi ta saukewa suna shigar min dasu to dama da cikon kudi na ce ya zo ya karba,ni kadai ce lokacin Alh kabiru yayi tafiya. Yana zaune falo nace mashi ya sunansa? Ya ce bello nace ina zuwa bari in kawo mai kudin ko? Na yi dabara na kulle falon nan koma daki na cire kayana na fito.(Wa iyazubillah) Ya tsorata ya tashi zai gudu amma kofa a kulle nace mishi ka nutsu ka biya bukatata zan baka ko nawa kake so tace in takaita miki Nafisa sai da na dire mishi dubu dari sannan ya yarda. Daga nan muka saba da bello har kwana yana zuwa yayi,Na ce ma 'yan aikina kanina ne. Nafisa ta ce Alh kabiru kuma bai gane ba? Hajara tayi murmushi bai gane me ba? Ai kin Allah daga baya har kudin da zan ba maza yake bani kuma cikin Ummi ina zaton na bello ne. Alh kabiru shi yayi komai saboda ba ya so danginsa su san baya da lafiya,ya ce min zasu yi masa dariya amma cikin Abba ban san na wanene ba,tunda lokacin na samu samari da yawa" Nafisa tai zugum cikin matukar al'ajabi, sannan tace, "km har yau kina hulda da maza? Tace "sosai ma, ynxu da likafa ma tayi gaba ina xuwa dubai sarin kaya, kin san ina da shago nima inda na dora bello yana kular min dashi, can nake holewata da duk namijin da yai min, jm in gaya miki dk abokansu hk suke basa amfani da matansu". Nafisa tace "dk aboknsu fa kika ce? Hajara tace Eh, gashi km suna dayawa, kowanne matar shi hoto ce. Amma bai damu tabi wani ba. Hk nan suna rike yayan da dk matan suka rero a waje". Nafisa tace "kai nidai bazan iya aikata zina ba da aurena. Wnda nayi da ma ina neman gafara. Hajara tace gara ma ki huta in ba hk ba kya tsufa dn shi ba sakinki zai yi ba hakanan in kin haihu zai fi sakar miki kudi fiye da ynzu. Nafisa tace ni mamakina ma ace dk group dinsu basu da lfy, to ya akayi hk? Hajara tace su dai suka sani, ke dai kiyi hrkar gabanki". Tnda nafisa taji wannan batun, hnklnta yai mu2kar tashi, data dawo gda ma sai tufka take tana warwarewa amma da yake son abin dunia ya rufe mata idanu ta kasa tsaida tunaninta ga ynda zata br gidn alhji jamilu, tafi maida kai ga tunanin ynda zata samu wanda zasu aikata laifin. Yau satinsu 1 da tarewa, dk da bb abnda ya shiga tsakaninsu na auratayya, suna mu2nta junansu. Mahmud a ganinshi iklima bata da matsala illa rashin iya kwalliya da salon mata gurin jan ra'ayin miji, sai dai zuciarshi tana yawan shaida mishi cewa kada yayi saurin yanke mata hukunci, ya bari zama yai zama. Ita kuwa nata gefen tana fassara mahmud a mu2m mai saurin fushi, miskili. Sai dai yana burgeta gurin kula da ibada, da km tsafta ga iya sa tufafi, uwa-uba kasancewarshi mai yin komai cikin kuzari, hakan na birgeta. Ya shigo da sallama hannunshi rike da leda ta tashi da sauri ta aje fiqhun da take dubawa,ta amshe shi tare da cewa "sannu da zuwa ka dawo lafiya?" Ya fadada murmushinsa ya ce"lafiya lau ya ki ka yini?" Ta ce fyn. Ya murmusa tare da baba muke fa,zai zo nan muka hadu na taso shago. Tace "yana ina yanzun?" Yace yana zaure (soro).ya dauki tabarma ki zo ku gaisa. Da sauri ta sako dogon hijabinta ta dauki jug da ruwa da kofi ta nufi zaure gefen tabarma ta zauna cikin fara'a tace sannu da zuwa Baba nayi miss naka. Cikin shagwaba tayi maganar. ***Ya murmusa sannan ya dubi mahmud wanda ke tsugune gefe ya ce,Malam mahmuda ya ya harkokin? Ya ce lafiya lau Baba. Iklima ta gaida mahaifinta tare da tambayr nafiu bai zo ba. Yace kasuwa muke zuwa dashi,daga can yake zuwa makaranta in sun taso ma can yake wucewa. Haka nan lokacin islamiyya. Iklima cikin damuwa ta ce Mama fa? Yace tana gidanta. Yayi saurin kauda maganar da cewa iklima kuna lafiya ko? Ya dubi mahmud "lafiya lau muke" yace maigidan naki shima lafiya? Ta dubi mahmud din shima ya kalle ta suka murmusa. Ta sunkuyar da kai tace lafiyan shi lau Baba, yace to madalla. Mahmud zai mike yace zauna,da farko zan soma da yi muku nasiha da kuyi hakuri da juna,ku kashe ku rufe tsakaninku Allah yayi muku albarka da abinda zaku haifa. Mahmud yace Amin sun gode. Yasa hannu cikin aljihunshi ya ciro kudi sababi yan 500 yace bismilla kirga min wannan mal. Mahmud. Mahmud ya amsa ya kirga su dubu hamsin. Ya sake ciro wasu yan 100 ya mika mashi ya gama kirgawa dubu ashirin. Yace to kinga abinda yayi saura cikin kudin gida da aka samu,gidan naira miliyan biyar da dubu dari tara an saida mota sannan na bawa mutane dangi da makota duk sun sa albarka.malaman kuma duk an basu. Sannan neman taimakon da masallacin makarantarku ke yi mun saka maki dubu dari sadaka. Iklima tace nagode baba,to kai ma ka dau wani abu, ya ciro 30k yace gasu nan na dau 30k Allah yayi muku albarka. Suka ce amin. Ya dubi mahmud gida kuma yana matsayin nata ko bayan raina nasa an rubuta takardu da sunanta. Nan take ta hade fuska, baba ni fa kai na bawa kyauta naka ne. Yace a'a iklima hajji dai naje Allah yasa munyi karbabbiya amma gida fa naki ne za dai mu zauna mun huta haya. Ta dubi mahmud don Allah Yaya kasa baki. Mahmud yayi murmushi sannan yace kiyi hakuri da yanda baba yace in kin lura da bayanansa sun riga sun gama komai,ta karyar da kai gefe tare da cewa shi kenan.ya mike tsaye,to ni zan tafi. Tace Ba ka fa sha ruwan gida na ba.yauwa baba ina ku ke samun abinci? Ya yi 'yar dariya,saye muke yi. Tace baba don Allah kayi duk wani kokarinka don mama ta dawo, yace ta ki iklima yaya zanyi da ita? Su su hamza ma tuni sun zo min da batun wata mace da mijinta ya rasu,'yar jalingo ce,sai dai sun ce bata haihuwa amma tana da matukar hakuri.iklima tayi kici-kici da fuska,to yarda kayi Baba don Allah? Yace iklima su hamza kannaina ne amma ba zan watsa musu kasa a ido ba,dole nayi aure ko don girki yanzu da haka ranar juma'a za'a daura auran. Sune suka biya sadaki.iklima ta tabe baki sannan tace shi kenan Baba sai an kwana biyu. Yace to iklima a dai yi hakuri naga ranki bai so ba. Suka fita da mahmud ita ko sai data koma daki sannan lamarin auren mahaifinta ya dagula mata lissafi. MABUDIN WAHALA 2**3 Harara haule ta zabga mata "nayi kama da matar babanku ynxu? Ta xaro idanu "ba danginsa sun aura mishi daidai shi ba? Na wuce da ajinsa". Ikilima tayi dim. Sannan tace ki daiyi naxari mama, ki dawo sbd ke da baba baxaku taba samun kamar juna ba, mu yaya kuke so muyi? Haule ta sake xabga mata harara tare da cewa in kika cikani xan tashi na zane ki ba ruwana, laifina ma kike gani? Shi ya sake ni ko ni na saki kaina? Haka nan bani da kmr nafisa dk cikinku km dk wnda yace bayason nafisa nima makiyi nane Iklima tace,mama dukkanmu muna son Ya nafisa,matsalarsu da Baba ni ce na kasheta da na auri wanda Baba ke so.shi kenan tazo kawai ta ba Baba hakuri ke kuma dama a cikin musulunci in mutum ya saki matarsa saki daya ko biyu in dai bata yi idda ba yace ya maida ta to ta maidu kuma kinga tuni baba yace ya maida ki. Tace,"ban koma ba me shegen tsarin tsiya,yaushe aka haife ki da har zaki ce min musulunci yace kaza? Ni ai kin san tuba nayi da zaki ce min a cikin musulunci. Iklima tace yi hakuri. Yaro ya shigo da sallama,haule tace kai wa kake nema ne ka shigo min gida ba notice? Kazamin yaro dube shi dan talakawa kawai. Iklima ta zaro ido tana kallon mahaifiyarta. Yaron yace wani ne a waje yace iklima tayi sauri ko ya tafi. Tasan mijinta ne don haka tace ma yaro "kaje kace gani nan zuwa.Haule tace ke da waye? Tace mahmud ne ya ce in gaisheki. Ta ja tsaki,shine yaja tunga a waje ko ya shigo,ina ruwana dashi? Har yake zai tafi. Mota ya siya ya kawo ki? Tace a'a a kafa ne. Haule ta sheke da dariya "ba dai kinji kin gani ba,haka zaku kare rayuwarku. Kowa yana abin arziki ban da ku. Iklima tace mun tafi mama.amma kiyi nazarin maganganuna.tace nace miki fa ba zan yi ba koda baban naku yace ya maida ni ban koma ba.iklima ta wuce ranta a bace. Mahmud ya dube ta kin shanya ni. Tace,yi hakuri. A gidansu ya barta gidan yai mata kyau,matar baban nasu mai tsafta ta amshi iklima hannu biyu. Ta sauke abinci ta zuba ma iklima,Nafiu ya dawo makaranta yana tamurnar ganin ikilima. Daga ganinshi ka san yana samun kulawa tsaf dashi.da suka yi sallah tace da iklima tsefe kai in maki kitso. Iklima tace kan nawa ma a tsefe yake. Nan kuwa matar baban nasu ta yarfa mata kitso kanana yayi kyau.Tana ta godiya tace ina ma zan samu wadda ta iya lalle da ta zana min. Matar baban ta ce "Nafiu in kasa kayan islamiyyar shiga nan makota ka gani yarinyar nan naja take ko wa? Nafiu yace eh sunanta Naja tana yin fulawa sosai bari na kira miki ita Ya iklima. Tace to. Naja kam ta zana mata fulawa mai kyau ta biya tana ta yabawa. An soma kiran sallar magriba,babansu ya shigo. Cikin murna take mishi sannu da zuwa shima da fara'a.yace iklima ke ce? Ta ce,"eh,ai nan na yini" yace lafiya dai ko? Ya ya ba kije gida ba? Tace zai zo mu tafi yace min. Baba yace,to madallah,hakan ya yi kyau dama baki san uwar taki ba,itama tana taso nafiu ya rakota bai san gidan ba,tace" to baba da kai baka raka ta ba? Yace bari muyi sallah sai na zo mu gaisa sosai. Iklima tana lura da duk yanda matar Baban nasu ke gudanar da lamuranta. Bata tsinke ba sai da taga yanda take karrama babansu gami da girmama shi.lokacin da tazo ma kayan baban ta samu tana wankewa dana nafiu,tun daga mam ta san cewa ko mamansu ta dawo dole ta gyara zamantakewar su in ko ba haka ba sai dai ta zama yar kallo. Don shi namiji dan son tarairaya ne da kula komai tsufansa. Tunda ta taso ko babansu bashi da lafiya bata taba ganin mamansu ta wanke mishi kaya ba,sannu da zuwa kuma in kaga ta mishi to ta hango leda a hannunshi cike da cefane. Bayan sunyo sallah sun dawo nan suka zauna suna ta hira tare da cin tuwo miyar kuka.sai bayan isha'I sannan mahmud yazo.Sun gaisa da su baba sannan suka tafi. Baban yana ta sa musu albarka. Mahmud ya yaba kitson da lallen sosai har sai daya biya kudin da aka yi su. Zaman su kam ba laifi suna kula da juna zuwa yanzun iklima tana ganin bata da kamar mahmud,sai dai shi yana ganin akwai abubuwa da yake so mace ta ringa mishi ita kuma bata iya ba.don haka nashi ganin rashin wayewarta ce matsala in ba haka ba sai yace tayi. Nafisa tana tsaye bakin kofar motafta tana kallon yaron, matsahi yana loda mata kayan da ta siya a cikin boot yayi mata kama sosai da Mahmud dinta, illa manyan ido da Mahmud din ya dan fi wannan saurayin, hatta sajensu daya ne.. Yace an gama hajiya. Ta dybe shi da murmushi. "Ya sunanka?" Yace "Timo". Ta sake dubanshi "Kai ba musulmi bane?" Yace " a'a". Tace "kayi kama sosai da musulmai" yace "haka mutane suke cewa." Ta ciro yan dubu dubu guda biyar ta mika mishi. Ya yi ta godiya, ta shiga mota ta tafi. Cikin kwanakin shedaniyar zuciyarta ta gama saka mata yanda zata shawo kan Timo, amma tana tsorin Alhaji Jamilu ya sani ko ya gani, sao dai Allah ya sa shima irin mijin Anty Hajara ne ko ya gani ba ruwanshi. Ta a cikin wannan tunanin a lambun shakatawarsu sai ta hango wadansu samari biyu za su shiga falonsu. Ta yu kura da nufin yi musu magana, idonta ya sauka akan Alhaji Jamilun, shima ya tasanma shiga falon, ta koma ta zauna tana mamakin yanda samari ke yin safa da marwa a cikin gidan, matsawar yana gari, koda yake yace mata aiki yake samar musu. Ta jima tana tunani, sannan ta mike ta shiga ciki. Falonshi ta nufa don ta manta ma yayi baki, da baza taje ba tunda y sha sanar da ita cewa in yayi baki ta daina zuwa don yana da kishi.ta shiga falon kanta tsaye, wani irin nishi ta jiyo daga dakinsa.. Gabanta yana faduwa ta nufi dakin ta tura. Numfashinta ya dauke tare da fadin "innalillahi, A'uzu billahi! Me zan gani?" Ta fada ta tashi zata fita da gudu, yace da na tsayen, "riko min ita" wanda ke tsayen ya cafko ta sannan ya ce "kulle kofar ka cire key din. Nafisa ta zube tana wani irin kuka, a gabanta ya aikata alfasha da dayan, dukkansu da ya gama sai da yasa wani farin kyalle ya kwashi wani abu a al'aurarsu, sannan ya duko wannan jakar tashi ya ciro daurin yan dubu dai dai ya basu dubu dari dari, sannan ya zira jallabiyarsa suka yi sallama tare da ce masa sun gode. Ya juyo yana kallonta "leke lekenki na tsiya ya sa kin leko abinda yafi karfinki, to bakinki kanin kafarki.". Ya jawo wata dirowa ya ciro bindiga ya nuna mata, "zan iya karar da danginku kaf da wannan in na samu labari gurin wani, haka nan zan kashe duk wanda kika gaya na wannan sirrin ko da uwarki ce. Sannan bazan taba sakinki ba, taimako daya zan miki in kinga wanda kikeso ki kawo shi ki kwana da sbi ba matsalata bace." Cikin kuka tace "kaji tsoron Allah ka tuna zaka mutu ka tuna da kwanciyar..." Ya dauketa da wani makahon mari har ta gigice. Yace "baki da hurumin yi mun wa'azi, kudi kika gani kudi kika aura, kudin kuma nake baki." Cikin kidima tace "kudin ludu?" Yasa kafa ya shure ta sannan ya take ta da kafsrshi "in kin sake magana sai na karar da numfashinki." Shiru tayi don tayi mutukar tsorata da shi. Ya jata ya fitar da ita daga sasanshi ya yar tare da cewa "ina jaddada miki ki iya bakinki." Ya fita abinshi. Ta ja jiki ta nufi dakinta, kan gado ta zube. Ina ma ace iyakarshi bai da lafiyar ne kawai ba wannan mummunan kazamin laifin yake aikatawa ba. Lallai tayi mutukar da ta sani a rayuwarta, yau tga lidi da idonta, abinda take jin labarinshi. Ranar kwana tayi kuka, daga bisani ta dangana. Washegari ta nufi gidan Anty Ajara tana kuka, amma ta kasa gaya mata abinda ya faru saboda mijinta ya gargadeta. Amma ga mamakinta sai taji anty hajara tace "na jima ina sa ido ki zo min da wannan kukan amman sai yau" Nafisa ta dube tq "ban gane ba" anty hajara tace "nutsu in ganar dake." Nafisa ta share hawayennta tare da jan hancinta tace "ina jinki." Hajara tace "Duk mazanmu sirrinsu kenan na siyasarsu da harkokinsu. Shine yasa basa iya amfani da mata sai dai ludu, ko bashi kika gani ba?" Nafisa tace "Wa'iyazu billahi! Na shiga uku!" Hajara ta bata rai, "ke don Allah dakataa min, a zamanin nan in dai kika ce kwadayi ne to fa sai kin ga haka. Babbab gida kike so da babbar mota, kin samu. Don haka dole ki jure ki zauna da shi, in ma kin nutsu in ma baki nutsi ba, tunda kika ga sirrin shi dayan biyu ne, ko ko zauna dashi ko ki rasa baki, in har an barki da rai kenan. Zaki daina magana kwata kwata don kada ki tona sirrin. Nasan ya fada miki ko mahaifiyarki baya so t sani ko?" Ranar kwana tayi kuka daga bisani ta dangana.washegari ta nufi gidan anty hajara tana kuka amma ta kasa gaya mata abinda ya faru saboda mijinta ya gargade ta. Amma ga mamakinta sai ta ji anty hajara tace na jima ina sa ido ki zo min da wannan kukan amma sai yau. Nafisa ta dube ta"ban gane ba? Anty hajara tace nutsu in ganar da ke, nafisa ta share hawaye tare da jan hancinta tace ina jin ki. Hajara ta ce duk mazanmu sirrinsu kenan na siyasarsu da harkokinsu,shine yasa basa iya amfani da mata sai dai ludu ko ba shi kika gani ba? Nafisa ta ce"wa'iyazu billah,na shiga uku" hajara ta bata rai,ke don Allah dakata min a zamanin nan in dai kika ce kwadayi ne to fa sai kin ga haka. Babban gida ki ke so da babbar mota kin samu. Don haka dole ne ki jure ki zauna dashi in ma kin nutsu in ma baki nutsu ba tunda ki ka ga sirrin shi yanzun dayan biyu ne ko ki zauna ko rasa baki in har an barki da rai kenan.zaki daina magana kwata kwata don kada ki tona sirrin. Nasan ya fada miki ko mahaifiyarki baya so ta sani ko? Nafisa ta daga kai,hajara ta ce "to kiyi ceton ranta don yanzun duk lamuranki za'a sa ido a kansu. Nafisa tayi kuka har ta gaji har dare sannan ta koma gida. Da yake itama shedaniyar kanta ce kafin sati shedan ya gama toshe mata basira. Hajara tazo har gida ta sake yi mata famfo,alhaji jamilu ya sake sakar mata kudi tare da bata damar yin hulda da dukkan namijin da take so har yake ce mata har da masoyinki mahmud in kina so. Tana mamakin yanda yasan mahmud masoyinta ne. Ranar nan fa har dawainiyar da mahmud din yayi mata sai da ya fada mata,wannan ya nuna mata Alh jamilu yasan komai nata kenan kuma yana bin diddigin duk inda taje. Nafisa bata yanke shawarar bin wani namiji ba duk da tana son timo,albarkacin kamannin shi da mahmud.cikin dan lokaci Hajara ta fita da ita cikin sauran matan abokansu idanunta suka kara budewa da ganin yanda matan ke fantamawa da kudi.wata rana sun je birthday party din yar Alh hashimu abokin su Alh Jamilun ne shima.matarsa laila irin fulanin nan ne mai kyau. 'Ya'yanta uku,Nafisa tace da anty hajara "yanzun wannan ma ba yar Alh hashimu din ba ce? Hajara ta ce duk wanda ki ka gani cikin grp din nan ba yayansa ba ne.Sai dai yan kadan daga ciki masu yara yan shekaru sha biyar zuwa sama.to manyan yayan su ne kafin su shiga kungiyar,amma duk wanda ya shiga to fa shi kenan. Nafisa tace mamkin da nake ji ki ga suna ta ji ya'yan. Hajara tace iyi to ai hakan shi ne rufin asirinsu shi yasa ki kaga suna kiran yan jarida don su nuna ma duniya cewa suna da ya'ya ba za'ayi musu wani zato ba. Lokacim da taro ya ragu sai matan abokan suka hadu suna ba juna labarin lamurransu. Nafisa sai raba ido tana sauraron abubuwan tamkar almara.Sima ce ta ce,hajara zuwana dubai din nan naji dadinsa,sauran suka ce kun samu kaya kenan? Sima tace,yaushe ma ni nabi takan kaya? Tun a jirgi idanuna suka kyallo wani bawan Allah zuciya kuwa ta kwadaita dashi duk na kasa sukuni shi kuma daga ganinshi kamili ne sai Allah yasa (hotel) daya zamu sauka dashi.da dare na dan fito shan iska sai ko na hango shi yana zaune kan wata kujera irn mai lema din nan na nufi gurinshi da biyu.na isa da sallama cikin mutunci na zauna na tambaye shi yace bismilla zauna mana. Sima tayi yar dariya tare da cewa,kun san abinda ya kara birge ni da wannan mutumin? Suka ce"a'ah. Tace ina danna waya tamkar me neman wani abu shi ko iyalanshi ya kira. Hankalina na gurinshi suna ta hira a bashi yaransa suka gaisa sannan suka ci gaba da hirar soyayya da matarsa. Yana gaya mata I miss u,I luv u,I need u da sausaran hirarrakinsu na miji da mata. Sai naji zuciyata ta kwadaitu dashi,tashi nayi naje dakina ina ta shiya yanda zan has kanshi don daga ganinshi kamili ne. Tace can na dawo na same shi zaune har lokacin wayar yake nace "bawan Allah don girman Allah zo ka min taimako wani abu a dakina ba zan iya fitar dashi ba. Ya dube ni kamar zai ce ba wani kwaron da zai shiga nan(hotel)din amma ganin yanda na rude sai ya biyo ni. Muna zuwa na nuna masa cikin bedroom yana shiga na kulle kofa na jefar da dan key din na cire kaya na bishi daidai lokacin da yake cewa banga komai ba." Juyowar da zai yi na rungume shi tare da samun sa'ar bakinshi na saka nawa,ya yi kokarin kwacewa amma shidan ba raggo bane ya dafa min,in gajarce muku nan muka aikata wannan laifin sai da komai ya kammalu ni ina murna don mutumin ya kai namiji shi kuma sai naga yasa kuka wai na cuce shi shi bai taba aikata zina ba.N WAHALA 2**4 Laila tayi tsaki,don kalaman kawai? Hajara tace maganar gaskiya laila mace yar son soyayya ce,mu kuma duk cikinmu wacece zata ce mijinta ya taba ce mata I luv u tun bayan aurensu? Kowace tace ina,gaskiya ita sai tayi wata bata ganshi ba. Hajiya Samira tace,sai dai inji yana ce ma katti in suna aikata laifin amma ba ni ba.Nafisa Sabon shiga tace,ni kuma wanda nake so yanzun an aura masa kanwata na rasa yanda zan shawo kanshi ya dinga debe min kewa ta basu labarin yanda alamuranta suka faru ta kara musu da cewa "ita in tayi yunkurin aikata laifin sai kuma ta tuna da mutuwa da hisabi sai ta fasa. Nan suka yi caa a kanta suna bata labarinsu Marsy tace kudi zaki sakar masa ga ki da kyau ai baki da matsala. Laila tace ki daina tuna mutuwa kafin ta zo kin tuba.(Kamar sun san sadda mutuwar za ta zo) sima tace sannan ga wani sirri ki dinga yawaita aikin alkhairi in kin ci sa'a sai ya shafe zunubin ki. Nafisa dai cikin zuciyarta tace bamu isa mu yiwa Allah wayo ba,don ya san abinda ke cikin zukatanmu amma a fili sai tace hakan zanyi. Koda suka dawo gida zuciyarta sai mamakin labarurrukan matan abokan Alh Jamilu take yi. Ta tuno sa'adatu da tace ita mijinta kullum zai kawo wani ya yi dashi a gabanta sannan in sun gama sai ya umurci saurayin ita kuma yayi zina da ita,a haka tana da yara uku bata san wanene asalin baban yaran ba. Wa'iyazu billah. Nafisa dk tmkr cikin mafarki take ji da ganin abubuwn, ta roki alhji jamilu iya roko kan cewa ita wlh bazata iya wannan rywr ba, don Allah ya saketa zata rufa asirinshi, amma sai ya bata tsoro cewa ta iya bakinta inta matsa mishi za a batar da ita. Alhji jamilu yaje gidansu hajara ya samesu suna dinner, ya zauna shima za shiga sahu. Suna ci suna hira, yace hajara kin kasa saka tawa matar akan hanya, sai damuna takeyi. Alhji kabiru yace "na zata an wuce wannan babin. Hajia hajara tace taurin kanta yai yawa, amma ka sani ne kabiru, ka kai yara gidanku sai ku shirya mana fita waje ko dubai ne, nasha muku alwashin in mun dawo zaka ga canji. Suka ce shikenan. Alhji jamilu yace ma nafisa ta shirya zasu fita dubai ita da hajara su dan siyo takalmansu na sawa da turaruka. Tace, to. Hajara tasan lbrin timo da nafisa take gaya mata cewar yayi kama da masoyinta, dn hk ta same shi ta xuba mishi kudi tare da mishi bayanin abnda take so yai mata. Cikin kwanakin suka kammala shiri, a airport suka hadu dasu timo, nafisa tai mamakin ganinshi su da wani saurayi. A zatnta tafiar su daban sai taga sun hau jirgi tare sun sauka tare. Ashe ma dakinsu daya ne. Nafisa tace ma hajara meyasa wadannan suke biye dasu? Hajara tace tare muke, su dan taya mu shakatawa. Har nafisa ta soma fada, hajara tace ma timo sai fa yayi aikinshi sannan zata cika masa kudinsa. Nan ko ya iske nafisa a bayi tana wnka, ya soma yi mata kaxaman wasanni shedan ya rura wutar suka taru suka kifar da dan guntn imanin dake zuciar nafisa, hr ta soma ganin wautarta da taso taki. Shaidan ya kawata mata zinar hr taji bb rywr data kai wannan sugar. Tir! Allah ka tsare mana imanin mu. Cikin kwanakin nafisa ta xama gwaska, sati 3 sai taga tamkar kwana 3. Da suka dawo kam alhji jamilu yaga bambanci, ynxun ta sake ta daina kunci da takura kanta cikin daki. Sannan ba ruwanta da batn harkar nashi zunubi. Timo kuwa har kwana yakeyi a gidan. Harka ta balle tuni ta sake kullewa da matan abokanshi tana daukar wasu darussan. Allah ya tsare mu. Iklima suna tsakar gida suna aiki da makota da dangin me jego, daya matar gidansu ta haihu yau aikin kunu. Tana sanye da riga da zani da hijabinta na xaman tsakar gida, iyakarshi gwiwa. Suna xaune ne suna tace kullin kunun, wasu suna kicin gurin ruwan kunun. Sai zancenta suke wai waccan amaryaryar haka take yini da hijabi? Wata tace tnda akayi haihuwar nake xuwa amma ko yaushe da hijabi. Maman ummi daya matar gidan kenan tace a ynda kuka ganta din nan hk take. Sam bata xama sai da hijaba, sai kace wani abu tafi mu. Wata tace iya yine. Suna ta dai tsegun- gumansu ita kam bata ma sani ba. Mahmud ya shigo da sallama ta

Chapter 9 of 20