Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
layi duk da tana da wata shi bai san tana da waya ba kuma kudin shine na shago. Yau ta bashi kyallen shadda,gobe leshi jibi atamfa ko material masu tsada tace suna da biki. Itama haule ko yaushe nafiu yana hanya gurin amso omo, sabulu da madara. Wannan lamarin yana ma2kar bata ran ikilima shi yasa koda haule xata dake tane sai dai ta dake ta amma bata xuwa amso mata sabulu ko wani abun. Lokacin da yar tata ta dao sai ta shaida mata cewa ga hukuncin da babanta ya yanke. Nfsa tace sunyi ta banxa don ba dai dani ba to ko kudin gaisuwar safina dubu 50 ne bare ni in ba a kawo min 100 ba ai sai dai nima a bani 50 din,amma dubu 5 sai kace dan tsako. Haule tace ashe kin fara hankali yanxu kyale shi 2nda ance sai kin gama makaranta ki karta mishi rashin M har yayi xuciya ya daina xuwa sannan kiyi ta dora mishi nauyin abinda bashi dashi duk abinda kika sanyafi karfin shi shi xakice ya sai miki. Nfsa tace ki bar shi sai mun karya shagon kema ki dinga aikawa kina amso sabulu da omo haule tayi dariya tace xan ko dinga aikawa. Hakan ce ta kasance,tashin farko ta sake bijiro masa da ba2n waya jiki na bari ya siyo mata har da layi duk da tana da wata shi bai san tana da waya ba kuma kudin shine na shago. Yau ta bashi kyallen shadda,gobe leshi jibi atamfa ko material masu tsada tace suna da biki. Itama haule ko yaushe nafiu yana hanya gurin amso omo, sabulu da madara. Wannan lamarin yana ma2kar bata ran ikilima shi yasa koda haule xata dake tane sai dai ta dake ta amma bata xuwa amso mata sabulu ko wani abun. *** Rayuwar ikilima abin sha'awa ne ga duk wani mai hankali yarinyar tana kara2 sosai yanxun ne take aji 6 na makarantar primary islamiyya kuwa suna ajin sauka ga kuma hadda tana xuwa yanxun haka tana da haddar izfi 30. Mutane da dama yan layin su ma sun manta da kamannin fuskar iklima saboda ko yaushe koina xata sanye da babban hijabi da kuma nikabi ga safa. Malamansu na islamiya koyaushe suna yin alfahari da iklima usman tana da zazzakar murya shiyasa duk lokacin da xa ayi gasar kara2n alkur'ani da wasu makaran2 iklima na daya daga cikin masu gasa kuma tasha xuwa musu ta daya. Yanxun ma da ake shirin yin na kananan hukumomi itace suka yanke shawarar turawa don haka mahaifinta malam usman na alfahari da ita kuma duk lokacin da taxo mishi da wani bukata game da makaranta yana biya mata. Haule kuwa tana kallon iklima a wawiya yar kauye shiyasa ma basu cika shiri ba kullum tana ckin yi mata fada duk da cewar biyayyar da take mata nfsa bata mata ga uban aikin gidan duk ita ce ke yin shi. Ita kuwa nfsa yanxu tana ma2kar juya mahmuda duk sun karya shago har sai da ya saida mashin dinsa ya kara jari amma ina suma 2ni sun tafi. Wannan al'amarin ya 2nxura mahaifin shi in da ya kira shi ya tsare shi da son ya sanar daa shi inda ya kai kudin 2nda ba abinci yake saye yana ci ba ba kome ba. Shiru kawai yayi bayan ya gama mishi fadan ya sake bashi kudin amma kafin watanni 3 suma sun kare. Kai hatta kannanshi haushinsa suke ji domin su sun san gindin nafsa ya tare, shi kuwa burin shi ya faranta mata, ga nfsa kuwa yanxun wata sabuwar rayuwar take fantamawa haka nan cikin xuciyarta koyaushe kara son mahmud takeyi sai dai har yanxun bata gama yanke xata aure shi ko ba xata aure shi ba domin duk lokacin da wani yaxo gurinta ba mahmud ba takan samu kanta da jin kunci amma in mahmud ne ko ta daure masa fuska xuciyarta ta kan sanyaya tare da jin nishadi. Xuwa yanxun ta gama yarda mahmud ne kawai farin cikin rayuwar ta sai dai matsawar bai samu aiki ba to ba2n autan su yasha ruwa kenan. Iklima ta shga ckin ma2kar farin ciki ta samu haule tana firar doya ta xauna tare da cewa mama yau dai mun gama jarabawar mu ta sauka sai walima ya rage mana,iklima 2nda wani malami ya taba yi musu nasiha kan cewa babu kyau yaro yana fadar sunan mahaifin shi ta daina kiran sunan haule. Haule tace na mki murna kinga kin huta da wannan ziritin xuwa makarantar kome ruwa kome sanyi, iklima ta dubi haule mama kara2 yanxun muka sa kafa, haule ta taba baki ai sai kiya tayi kin ga ni ban iya abinda kika iya ba tashi ki hada min murhu,cikin sauri iklima ta tashi ta cire hijab da nikab ta shiga kitchen. Ckin kwanakin Alhaji ibrhm ya kira mahmud ya saka shi gaba da fada a gaban hajiya uwa uwargdan shi yace uwa yanxun ki duba mahmud shagon sa ya sake lalacewa da ina xaton yana da hankali ashe ba haka bane dubu dari shida na xuba mishi kayan sun narke,mashin ya saida na sake bashi dubu dari3 suma sun rushe to me yakeyi da kudin? Hajiya uwa tace kasan mahmud da kyauta, Alhaji ibrahim yace daina gaya min wannan ba2n don yana da kyauta sai ya rabar da kayan?nifa nafi xaton cewa mata yake nema...da sauri mahmud ya dubi mahaifinsa, hajiya uwa tace haba Alhaji kada kayi masa mummunan xato ba halin mahmud bane. Alhaji ibrahim yace to caca yakeyi kenan? Hajiya tace babu ko daya ka dai daure ka kara mishi, Alhaji yace Allah ya tsare ni nayi rantsuwa baxan kuma bashi ko sisi ba kuma baxanyi kaffara ba tashi ka fita ka bani wuri. Mahmud ya dubi mahaifinshi yace kamin afuwa yanxu xan gyara, Alhaji yace kada ma ka gyara tashi ka fita,mahmud ya nike tare da cewa Allah ya huci xuciyarku, Alhaji ibrahim yaja tsaki tare da cew sakarai batun aure kaki har kasa sana'a itama kaki to ni yanxu na xuba maka idanu. Ckin daknshi ya shiga yana ta ziri2 yana kai kawo shi kanshi ya sani ya cancanci fada kai har duka ma gata dai mai suna gata mahaifinsa ya nuna masa ya sani duk cikin yayan mahaifin nasu ya fi son shi maimakon ya mu2nta kanshi ya jawo kannanshi ya lura dasu don wata rana in babu mahaifinsu shine xai zama mahaifin nasu. Ya kasa gyara kanshi duk dalilin son nafsa to anjima xayaje ya sameta ya gaji hakanan in ba xata aureshi bane ya hakura alabasshi son nata ya kashe shi. Bayan sallar ishai ya aika aka kira mishi kabiru don ya tsare mai shago. Mahmud yayi kyau ckin bakin wandon jeans da jar t-shirt mai gajeran hannu,ya fesa mayan turarenshi sunshine ya saka takalmanshi ya fita. Yana tsaye nafiu ya fito mahmud ya kira shi nafiu ya gaida shi sannan yace yaya nafisa suje biki bata nan yce jeka xan je in dao shagonshi ya koma sai tara saura ya kuma nufar gdan tare da adduar Allah yasa ta dao. Yana tsaye iklima ta dawo haddar dare bata san shi bane yace malama kin dawo? Cikin natsuwa ta nufo shi don ta shaida muryarsa sallama ta masa sannan tace ya nafisan bata nan ne ko baka samu dan aike ba ne? Yace daxu naxo wai sunje biki shine na dawo yanxu, iklima tace to bari in shiga sai na 2ro ta ta tafi tare da cewa sai da safe shi ko da kallo ya bita yarinyar ta samu yabo a kafatannin unguwan su tana da ma2kar nutsuwa shi kanshi ya manta kamannin fuskarta, ina ma haka nfsa take? Koda dai shi yana son mace wayayya, nfsan ce ta katse mishi 2nani da cewa my sweet ga alama yau kana son ganina ance ka xo dazu wallahi mun je biki ne. Baice kala ba,ta kai hannu xata kama nashii su xauna sai ta 2na yanxunnan sa iya yin rigima kan hakan don haka sai ta fasa tace mu xauna mana my sweety darling. Ya xauna sai dai ta lura fuskarshi babu annuri tace wai shin yau me yake faruwa? Yace ni dai gaskiya na gaji yau naxo ne muyi ta ta kare, tace name? Yace na aure, bakya duba uxuri na sai naki ni kuma na fada miki ina bukatar mace kusa dani ni ba maxinaci bane gashi mahaifina ya kosa inyi aure. Tace to yanxu me kake nufi da ayi ta ta kare?cikin xafin rai yace na shirya rabuwa dake domin na kasa gane kanki ta raxana tare da xare idanu,mahmud xaka iya rabuwa dani? Taci gaba da magana muryarta na rawa,dama kenan ba son gaskiya kake min ba?ta mike xata tafi tana cewa shikenen nagode. Kukan ya kwace mata sosai,da hanxari ya mike ya cafko hannunta lokaci guda kuma yace a'uzubillahi tare da sakin hannun ta. Yasha gabanta baki fahimce ni bane nafsa ba nufina in bata miki rai ba,nafi son ko xamu rabu muy rabuwar mu2mci ta sake fusata barni na wuce in yaso son naka yayi ajalina dama na jima ina zargin ba sona kake yi ba. Nan take ya daburce ya shiga lallashinta,kuka takeyi rurus da kyar ya shawo kanta tayi shiru. Ckin sarkewar murya irin ta wanda yaci kuka tace mahmud dama akwai ranar da xataxo kayi 2nanin barina? Yace come on beby nace mu wuce gurin ko? tace a'a mahmud kasan son da nake maka kuwa?wallahi gara na rasa raina da na rasaka,me xaisa ka dinga baraxanar rabuwa dani? Ya sake matsowa kusa da ita xuciyata ke gaya min cewa xaki yaudare ni, raina xaya fi kwanciya idan mukai aure in na xama naki kema ki tabbata tawa ni1. Ta sauke ajiyar heart wallahi na fika son in ga wannan ranar,to kayi hakuri mana 2nda baifi wata shida mu gama ba. Yayi shiru yana 2nani itama 2nanin take yi nata naxarin in ma xata aureshi to xata cigaba da huldarta da wasu alhazan,to kuma bata ba shiga katon gda da ka2war mota?sai yaushe kenan ta cika burinkanta? Ya katse ta da cewa shikenen zan kara daurewa tace nagode masoyina don ma in na baka wata shawara baxaka yarda bane yace fadi mana in xata amfane mu. Tace xata amfane mu sosai mana,yace ina jinki. Tace 2nda aure xamuyi an riga an baka ni in ma kana jin xaka takura sai inxo dakinka mu dinga rayuwarmu tamkar ma'aurata...ya katse ta da cewa A'uzubillahi kina nufin muyi zina?tace to an riga an baka ni shi ne zina? Yace ke daina furta wannan kalmar mara dadin ji duk wanda yace miki don an baka yarinya ba a daura aure ba ya kusance ta ba zina bane to ki ce masa karyaa ne. Nafsa ko an kai sadakina gdanku ba xan take ki ba bare ba a kai ba,ni aure nake son inyi mai tsafta na sunna ba jafwalgwalo ba, sannan in haifi yaya suma wasu can su lalata min su don haka take duk wanda yayi zina da yar wani haka xa ayi da tasa,nfsa shawararki bata yi ba ke a duk lokacin da irin wannan 2nanin ya bjiro miki kice a'uzubillahi,ya mike tashi ki shga gida sai da safe ta kasa tashi,ya tsuganna menene kuma? tace duk abinda nace sai kace banyi daidai ba ni banga wani laifi ba kowa fa ba matsala don muna hulda. Ya fusata kina da hankali kuwa,kin san me kike fada?to gurin Allah ba karamin laifi bane. Sannan xaki iya samun ciki me xaki ce da iyayenki?me xaki ce da mutan unguwa?me xaki ce da ubangijinki?sannan me xaki ce da dan koi yar?kinga dai na farko cikin da akayi auran sunna ni xan dinga doki kema haka dangina ma haka haka danginki. Sannan yaron xai tashi ckin dangin mu kowa na sonshi. Amma in muka yishi ta hanyar zina ke a boye ba kwanciyar hankali danginki basu san a sani,dangina ma kila su karyata suce ba nawa bane,nima in naga xanji kunya in zuke ince ba nawa bane,yaro in ya taso gori gurin yaran unguwa a karshe ya rsare ki don ki fito mishi da ubansa ga dinbin zunubi gurin Allah. Kin gane nufina? A sanyaye tace na gane kuma haka ne. Yace yauwa nafisata nafi son in bareki daga leda. Gabanta ya fadi ta mike tare da cewa to sai da safe,yace mu kwana lafiya kiyi mafarkina kinji?tace to,cikin sanyin jiki ta nufi cikin gida. Lamura sun dagule mata,mahmud yasan cewa 2ni wasu suka bare ta a leda?kenan in bai same ta a ledar ba xai gane?lokacin da ta shiga gida mahaifinta ya fito bayi yace sai yanxu kika shigo?nifa ban son doguwar hirar nan 2n ana fadin gaskiya har karya ta shigo ciki. Jeki taso Danlami ya rufo gidan,daga yau kada 10 ta kuma yi miki a waje. Nfsa dai tace to ta shge dakinsu ta samu iklima tana kara2n Al"urani,ta fada gurin kwanciyarta ta shiga 2nani gashi kuma iklima ta dame ta sai dai tasan koda wasa baxa tace mata tayi shiru ba domin idan baban su yaji xata kwana da tabon duka. Iklima ta gama kara2nta tayi addua ta kwanta,nfsa ta dube ta iklima ina cikin damuwa kin sanni in xance na cina bana iya rikewa labari xan baki ba shawara nake nema ba. Iklima tace ina jinki don tanaso su dinga hira amma nfsa taki hakan. Nfsa tace yau mahmud yaxo min da wani shirme wai xai rabu dani,iklima tace saboda me?nfsa tace in ban yarada munyi aure yanxu ba kai ba2n ya girgixa ni bai san irin sonsa da nake bane. Iklima tace to yaya nfsa banga amfanin xaman haka ba 2nda bakya xuwa makarantar ba sai kuyi auranku ba?ta katse ta da cewa nace ba neman shawara nake ba. Iklima tace na manta ne,nfsa tace duk sonda nake masa kuwa banjin xan aureshi a haka inje babu lafiyayyan abinci bare sutura. Iklima tace da kinyi bu2lci,nfsa tace a,ai in na auri wani din na wawuro sai naxi muyi aure kin san ni burina babban gda da babbar mota. Iklima tace yaya nfsa kwadayi fa shi ne mabudin wahala,ba kyau bawa yana kallon na saman shi. Manzon Allah(S.A.W) yace duk wanda bai gode kadan ba ko ya samu mai yawa ba xai gode ba,don haka in kin raina arzikin mahmud ko kin samu babban gda da babbar mota baxa ki gode ba,xaki hari wani abinne. Sannan Allah ba xai bar cin amanar da kikayi wa mahmud ba ku dubi yanda yake dawaiyniya damu cikin gidannan,sutura...nfsa ta katse ta da cewa malama kiyi min shiru kin cika min kunne an ce miki irin rayuwarki xanyi kullum a lullube shi yasa gashi har yanxu baki da saurayi. Iklima tace ba shine a gabana ba sai da safe,ta kwanta tare da jan mayafinta ta bar nfsa tana ta masifa tare da yi mata gore gore. Washegari da ta sanar da haule yanda sukayi dashi haule tace nifa bana ma so kina wani zancan mahmud wannan ai an gama babin shi 2nda yanxu bashi da ko taro shagon ma ya tsiyace. Nfsa tace shiyasa yanxun duk wanda yaxo fita xanyi ko a gaban shi ne,haule tace yauwa yarinya mai tsada kyan ki babban gida da babbar mota Hajiyar Allah. Nfsa tace amma ikli dana bata shawara wai irin nima yaruwa sai ta shiga zuga ni tare da kawo min hadisai,haule tace nace ki daina shiga harkarta iklima me ta sani na rayuwa?nfsa tace ai babu kari. Ana gobe su iklima xasuje gurin gasar kara2,malam yunus yana kara musu bayani musamman saboda shigar da xasuyi yace ba2n hijabi fa tabbas kowannan ku yasa kalan na makaranta,suka ce to banda iklima wadda babanta bai sami dari taran saya mata yadin ba. Bayan malam yunus ya sallame su ita ta tsaya bayan sun tafi ta dube shi,malam ina ganin kila ni baxan samu xuwa gasar ba yace saboda me?cikin mata dake muke takama,tace babana bashi da kudi yayi duk yadda xa yayi ko bashi bai samu ba so kaga bani da hijabi kenan. Yayi shiru sannan yace je gida ki kwana dai da niyar xuwa. Da dare yaro ya shigo yace wai ana sallama da iklima,nfsa tace inji wa?ko dai nfsa?yaro yace haka ni dai yace min. Haule tace iklima kixo kinyi kasuwa,suka sheke da dariya,ta taso ta saka hijab da nikab,nfsa tace kai shegiyar yarinyar nan ra'ayi ya miki yawa tadin ma kin rufe fuska gashi sai uban kaurin hayaki kike yi,iklima batace kala ba ta tafi,sai dai nata 2nanin kila yan ajinsu ne,ga mamakinta sai taga malam yunus ta gaishe shi cikin girmamawa ya amsa ya miko mata leda; to iklima ga hijabi don Allah ki shirya da wuri sannan ki sake duba littafanki,tace na saka dawaiyniya malam yanxun ban san ma me xance da babana ba sai ko ga baban ya taho tace yauwa gashi nan xuwa. Malam yunus ya gaishe shi sannan tace baba wannan malamin mu ne ya sai min hijabinne ka ganshi baba yace to to Allah ya saka maka da alkhairi naso kwarai in sai mata hijabin amma Allah bai bani iko ba,malam yace ba komai shi xaya tafi nan sukayi sallama. Washegari 2n safe su ikli aka shiga yin aiki da ta san itace me yin shi don kada ta makara koda ta gama ta shiga shiri dama koda ta dawo daga kiran malamin su ta nuna ma su haule hijabin tsaki suka ja,ta shirya tsaf suka dau hanya. MABUDIN WAHALA 1***4 Kusan duk wanda ya halarci taron gasar iklima ta burgeshi da zazzakar muryarta. Haka nan ta amsa duk wasu tambayoyi da akayi mata babu gyara karshe dai itace taxo ta daya don haka ta samu damar xuwa gasa ta jihohi wadda za ayi a jihar sokoto. Murna gurin ta da babanta da yayyenta maxa sai ka gani,nfsa kam baki ta taba,haule kuwa cewa tayi ni dai 2nda ban ga kudi ba ba a birgeni ba,nan ko ta samu kyautan litattafai harda kudi wadanda aka gayyata sun bata amam sau ta mika su ga babanta 2n a can tace kada ma ya sanar da su haule. Shi kam dadi gurin shi da yake ji har kwalla sai da yayi,lokaci da take kara2n kusan dukkan mutanan da ke gurin shi mata albarka suke yi tare da cewa mahaifanta sunji dadi. Hakanan makaranta sun sake ji da ita tare da kaf kaf da ita musammamln malam yunus wanda ya fito ya nuna mata son da ya jima yana yi mata,yaki nunawa ne kawai don yana malaminta,itama ta aminta dashi don dama ko yaushe burinta Allah ya bata saurayi mai ilmi,mai tsafta kamar malam yunus. Matan ajinsu sun sha nuna masa so amma sam shi baya ko sakar musu fuska,ko yanxun da ya fito da son da yake ma ikliman yace mata wannan sirrinsu ne haka nan baya so yan makarantar su sani don haka in sunxo makaranta duk abinda zai ma sauran daliban itama haka yake mata kai ko dukan duka aji baya tsallaketa don haka babu wanda ya gane sai dai in yaxo tadi yace tayi hakuri duka da ya mata daxun shima yaji zafin a jikin shi. Babanta ya aminta da shi dan haka yana xuwa tadi sau daya a sati kuma minti 30 yake tafiya. Nfsa kam dariya take yi ma iklima wai ta rasa wanda xata aura sai malami,ita dai bata kula ta ba,haule ma ko yaushe yazo sai tayi mita. *** A kwana a tashi babu wuya a gurin Allah su nfsa anyi jarabawar fita lokacin iklima tana js2 kuma wannan lokacin ne suke ta shirin tafiya gasar kara2 ta kasa. Nfsa kam ko a dakin jarabawa sai kallon silin da cixon biro,to bata yi kara2n ba balle tasan me xata rubuta lokaci na cika aka amshi takardun suka fita amma saboda tsabar karya da salo har da buga kalanda da memo tare da yin party wai an gama secondary school. Ta gayyato kawayanta yan karya tare da samari da kuma wasu maxan da take kiran su abokanta,mahmuda ma yaje sai dai xuciyarsa tana cike da mamakin inda nfsa ta samu kudin yin wannan shagalin da kuma 2nanin ina ta roro wadannan kawayan?shi kan shi gurin da akayi partyn yasan dubu30 ake kamawa don haka ya kosa a tashi don ta amsa masa tambayoyin sa. Yanmatan da suka halarci gurin gaba daya ba kawayanta na kuruciya cikin su daga mama zee sai safina sune kawai ya sani,su kuwa yanmatan sai zundan nfsa sukeyi suna mata dariya wai wannan talakan tilis din take so sai dai dayawansu sunce kyawun dirinsa gami da kwarjininsa ne ke rudinta. Bayan an taso ya wuce gda yaxo da dare bata nan dole sai washegari shima din ya ritsa ta ne ta caba ado zata fita,nan take ko ta daure fuska gami da ce mishi ita fa unguwa xasu je ana jiranta ne. Yace ina kenan?ta zafga mishi harara da manyan idanunta masu kara tsuma shi, cikin taunan cingam tana kas- kas dashi tace sai kaji?yace to ni kuma naxo da magana,tace lafiya?tana girgiza kafadu in ta dame ka maganar ka zo da dare. Ya bita da kallo cikin irin tafiyarta tamkar ana mata kida ranshi bace ya juya shi kanshi yana jin haushin kansa irin cin kashin da take masa ya kasa watsi da ita. Yaxo bata dawo ba sai kusan tara yana zaune har xata wuce yace nfsa ta dubi inda yake taja tsaki sannan ta iso sai da taxo kusa dashi sannan tace naci yace to ki gaya min in kin daina sona ne in hakura tace don ina sonka sai kuma ko yaushe kana like a kofar gidan mu? kaga nifa na soma gajiya da wannan tadin,yace to kinga dai 2nda yanxun kin gama kara2n sai na 2ro ta katse shi da cewa ka 2ro ina?ai wlh baxan yi auren da nasani ba auran da iyayena xasu saida akuya ta dawo tana ci musu danga ba yayi shiru can ya mike yace to shikenan Allah ya hada kowa da rabonsa cikin isa da izza tace amin. Lokacin da ya isa gida ko ganin gabanshi bayayi kafin wani lokaci zazzabi ya rufe shi sai dai yasha alwashin koda son nata xaya xama ajalinsa ne sai dai ya mu2. Ita kuwa ta shiga gda tana murnar ta yarda kwallon mangwaro ta huta da kuda,cikin ranta tace ana harkar arxiki waka ba2n tsiya yanxun da haka kudi ne cikin jakarta naira 20K saurayin mama zee ya basu 40K ita da safina suka raba kuma cikin masu sonta da xasuyi fatin nan daga mai 100K sai mai 50K amma shi ko ko taro,dakin haule ta shiga ta samu baban su bai shigo ba don haka ta zube mata kudin suna kirgawa suna farinciki tana kuma sanar da ita yanda sukayi da mahmud,taji dadi sosai tare da sa mata albarka. Sai dai me?lokacin da taje kwanciya sai zuciyarta ta bijiro mata da son mahmud din tare da kawata mata suffofin shi kyawawan lebunan shi masu jan hankalinta,nan take ta birkice taji baxa ta iya rabuwa da shi ba 12 na dare 2ni an rufe musu gida ta sadada ta bude ta fito ko gyale babu ta isa kofar dakin shi cikin sa'a kofar tana bude ne 2nda ya shigo ya fada kan katifa bai samu damar tashi ya rufe ba ta 2ra ta shiga sannan tayi sallama.ovels BOOK MABUDIN WAHALA 1***5 Bai jita ba duk da ba barci yake yi ba idanunsa suna kallon silin ta xauna gefen katifar tare da cewa mahmud yayi firgigit ya kalle ta ya tashi xaune cikin daurewar fuska. Me kika zo yi kuma?tace hakuri naxo baka na sani ko cikin mafarki ban isa ince xan barka ba kai dai dinnan kaine i love you so much don Allah kayi min afuwa yanxun muyi maganar auranmu, ya mata banxa nan ta shiga kuka wiwi ganin daren kara yi yake yace to na hakura tashi ki tafi tace to zo ka raka ni tsoro nake ji,yace to sai dai ki kwana don bazan fita ba,ga mamakin shi sai gani yayi ta matso tare da cewa dan matsa mini,da sauri yace in matsa miki kiyi me?tace in kwanta da asubahi sai na koma gida lokacin baba na ya tafi masallaci,ya mike tsaye duk da zazzabin da yake damun sa muje in rakaki don nasan hakkin addini na har kofar gda ya kaita sannan ya dawo,taxo xata shiga daki babansu ya fito daga bayi yace ke nfsa xo nan daga gidan uban wa kike?tace na'am a bayi zan shiga yace karya kikeyi ina daga bayi ina jin motsinki kina rufe gida ya nufi gindin murhu ya suri itace jikinta sai bari yakeyi yace zo nan, ta soma bashi hakuri yace inda kika fito karfe daya kawai xaki fada min tace kirana akayi mahmud yace karya kikeyi mahmud ko goma baya kaiwa ya matso ya cafketa ya shiga aza mata itace ta shiga kurma ihu dukkan mutaan gidan suka fito . Haule tana ta cewa don Allah me yarinyar nan tayi maka kake dukanta?yace duk wanda ya matso nan xan targada shi ya jibge ta son rai da kanshi ya hakura ya kyaleta ya shige daki haule tazo ta kama ta ta nufi dakinsu da ita iklima ta kauce ta basu hanya sai kuka take. Haule na lallashi a hankali don kada ya jiyo su danlami suka wuce dakin su itama iklima taxo ta koma makwancinta tana kallon su, haule tace wai me kika masa ne?ckin muryar wanda yayi kuka ya gaji tace kirana fa kawai akayi na fita shi ne ya zi ya hau ni da duka,haule tace mugunta ce irin wadda ya saba ki barshi Allah zai saka miki. Iklima tace haba mama yaya uba zai hukunta yarsa kice... Ta jefa mata fulo akai rufe min baki yar iska,iklima taja abin rufarta tayi musu shiru tana jina su suna ta aibata mahaifin nasu har dai bacci ya kwasheta bata ma san lokacin da haule ta fita ba. Washegari kasa fitowa nfsa tayi,tayi dankam ta doku ranar kam babu yawo sannan bata daina kuka ba shi ko mahaifin lokacin da haule ta dawo daki fada ta yayi da fada sannan yace ya gaji aurar da ita zayayi sadaka, da sahe kuwa ya tashu danlami yace maza ya kira mishi mahmuda,ya isa dakin mahmud yayi sallama ya amsa tare da cewa shigo,suka gaisa danlami yace baban mu ke neman ka yace to kace masa ina zuwa. Tafiyar danlami ba dadewa ya isa gidan sai ga nafiu ya dawo siyan sugar yace baba yana nan?yace yana nan, mahmud yace kace ina jiransa a nan,shigar nafiu ba jimawa baban ya fito. Mahmud ya zube yana gaidashi baba yace ka 2ro min manyan ka yau,mahmud yace to. Haka kuwa akayi ya samu mahaifinsa ya shaida masa sakon surkin nasa, Alhaji ibrahim yace ka kuma shirya auren ne yanzun?ko ko dai wani shirmen zamu kuma zuwa muji? mahmud yace Alhaji ina jin ba2n auran ne dan ta gama kara2n,yace shikenan zan masu Alhaji mustapha magana. Lokacin da waliyan nashi suka je sun gana da malam usman yace maganar aure ne ta taso suna so wannan satin ne ko za asa wata daya? Sun mika sadaki 10K sannan zasuji daga bakin mahaifin yaron da shi yaron in sun shirya shikenan. Lokacin da sukazo ma Alhaji ibrahim da wannan ba2n yace a kira mishi uwargida hajiya uwa yace kinji ba2n auran mahmud suna so mu tsaida lokaci shi sakaran ma bance ya tanadi kome ba,tace a kirashi dan abinda yake dashi sai

Chapter 3 of 20