Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
ce ta tashe ta. Yace ta zo sasanshi. Kwance ta same shi wai zazzabi. Ita ce tayi ta kula dashi har ya dan murmure.daga baya kuma abokanshi suka ba shi shawara ya fita waje a duba shi da kyau. Tare suka shirya tafiyar sai dai kafin su tafi sai da ta yo ma haule waya ta shaida mata mijinta ba shi da lafiya,ita da su danlami suka je sannan suka tafi.wani bala'I duk da rashin lafiyar dake damunsa wai haka kartin ke shiga wurinshi suna aikata kazamin aikinsu. Da tace ya bari ya warke yace ai sharadi ne kullum sai sun aikata haka ko da baka da lafiya sai kayi kuma sai anyi maka. Wa'iyazubillah,wannan ai rayuwar dabbobi ce kai ko kare bama kare ba ko alade mafi muni da wulakantuwa dai kenan namijin su baya bin namiji. Ya samu sauki ya yi sarai suka dawo kowannansu ya ci gaba da aikata laifinshi.zuwa yanzun nafisa ta juku da kudi,kasuwanci ana ta yin shi ba kama hannun yaro,bokaye suna cin nasu rabon. Hakika zuciyar nafisa ta kamu da ciwon som dunoya wanda ya mantar da ita ibadarta da addininta. Ko ramadan ne yanzun gani take yi talauci ke sa yin ibada,sharholiyarta ce kawai a gabanta.tabi namijin da taga dama ga kudi. Haule kuwa likkafa ta yi gaba,hajj da umra ba sauki duk anje ga hakoran makka an zubo sama biyu kasa daya. Da ta hango ka tun daga nesa zata soma washe baki,duk ko wanda yace mata haule bai hada da hajiya ba sai ta mishi rashin mutunci. Malam usman ne kawai ke taka ta son ranshi don da zata yi mishi salo zai warware ta.yauma minna ta dauko su nafisa,suna zaune falon haule suna dambe da kaji da kalolin juice sai ga iklima tayi sallama,daga skul take ta zo su gaisa da haule dama ta tambaya. Nafisa ta hada rai,iklima ta isa gurin ta tana cewa,tuba nake 'yar uwa,wlh ina nan sai dai ki ganni kwatsam. Nafisa tayi dan yake tare da cewa ki sha zamanki,ai duniya yawa ne da ita.a bariki ma ana samun yan uwa.suna can wlh sun ishe ni zumunci. Haule ma fuska daure ta amsa gaisuwar iklima,ta sakko khalil ta mika ma nafisa tare da cewa,to ga dan naki. Nafisa tace,a'a bar shi bari dai in ganshi a hannunki,wa ya biyo? Don ni bana daukan yara babu pampers. Iklima tayi sororo,nafisa ta dubi yaron tace,um kama da ke ne wannan yaron. Haule tace,ubansa ne ba kya ganin wannan dakwa-dakwan idanun kaman na kare an danna shi a kwata? Nafisa bata ji dadin haka ba, ita ce ya dace ta haifi yaron nan da mahmud ba iklima ba. Ta kauda kai tana jin zafi a ranta,wai shin dama haka so yake da dafi? Har boka tace ma tana so ta daina son mahmud amma duk da irin surkullan da ya mata ta kasa daina sonshi. Iklima ta maida danta baya ta goya duk da tilin naman dake gabansu ba wanda yayi mata tayi,har ga Allah kuma ranta ya biya.tace,zan tafi. Suka ce sauka lafiya. Ta fito tana waiwayan naman amma duk da haka suka share ta, tayi murmushi tare da cewa,Allah ka kai bawa kan arzikinshi. Da ta koma gida ranar ko abinda zasu ci ma babu sai da dare yaje gidansu ya amso mata tuwo. Nafisa ta nufi gidansu safina, ta samu safinan tana bcci da kyar ta tashe ta suka rungume juna tace shegia nafisa kinzo dunia a sa'a, dubi ynda kike kara zama don kin gama shan kwana. Naga wasu fitinannun shaguna da kika sake budewa. Tai daria sanna tai juyi a tsakar falon tace, kin sanni tn ina karamata burina kenan, inji ance nice wance inji ana lbrina gurin kudi, in na wuce a bini da kallo. Safina tace kin samu Allah ya amsa. Nafisa tace matsalata daya ynzu a dunia ita ce son mahmud, wai yaushe wannan balain ze rabu dani ne? Duk namijin da ze hada shimfida dani sai dai in dinga raya ina tare da mahmud, sannan zan samu nutsuwa. Hawaye ya soma zuba dg idonta in sonsa ya motsa min sai inga zan iya rbw da daular da nake ciki don na zauna dashi. Na kashe kudi a cire min son shi ya gagara. Safina samo min mafita, nabi duk hanyoyin da zanja shi jikina ko da mu dinga rayuwa ne, na kashe kudi gurin bokaye abin ya faskara. Safina ta kama hannunta zuwa dakin bccinta, ta xaunar da ita bakin gado ta jawo wani kwali dg kasan gadonta cike da kwalabe tace ga magunguna abokan shawara, da kin juye 1 cikin ruwa mai sanyi zaki manta dashi, in ma baki manta dashi ba zata gaya miki ynda zakiyi. Nafisa tace wannan ina ce magungunan tari ne? Safina tace, tabdi kawata shan wannan shine zai sa ki kara hadewa. Zaki bani lbri. Daga ranar nafisa ta zama yar maye, sai shaye-shaye. Tir da wannan rayuwar. Albashin ikilima na taimakonsu matuka, dk da hk ba a wadace suke ba. Sai dai wadatar zuci, batayi girman kai ba tana amsar wankin jama'a tanayi ana biyanta, yace shi bayaso tace yai hkri rufin asirinsune. Hakan ya hkra. Matan gidansu ma suna bata ta musu dk da yan habaice habaicen da suke mata na cewa ta like a gindin namiji, dk abnda take nema bata tsinanawa kanta wata tsiya, in dai namiji ne ze koya mata hnkl. Share batnsu tayi ta cgb da harkar gabanta. Kullum son juna suke karayi. Mahmud yakan ce ya yarda wani hani ga Allah baiwa ne, ya tbbta da nafisa ce suke cikin wannan halin dk son da take mishi da tuni ta tada balli, amma ikilima bata taba bata ranta ba dn yace bb, sai dai tace Allah ya kawo. Annabi yayi gskia daya ce, "na hore ku daku auri mai addini". Sallamar ta kasa karewa, dk matan gidan basu nan sai ikilima ita kadai. Ta zura babban hijabi ta fita, maza 2 ne tsaye kofar gidan, cikin kakkausar murya tace Alaikumus salam, wa kuke nema? Suka ce mahmud. Tace ya fita lafia? Suka ce lfy lau, dayan ya ciro wata letter ya mika mata gashi inyazo ki bashi. Ta amsa ta juya farar takardar sannan tace to. Ta koma ciki ta ajje. Bai dawo da wuri ba don sunyi aiki a wani gida ba'a biyasu ba,suka yi ta jira har magriba sannan yazo yace suyi hakuri sai gobe. Rai bace ya shigo amma ta tare shi da sannu da zuwa,ta gabatar masa da ruwa cikin fara'a yasha tace na ganka wani iri gajiya ce? Ya dube ta,mun sha aiki yau muna sa ran kudi amma bamu sa mu ba, na biyo ta gidanmu in zo miki da tuwo muna cikin gaisawa da su hajiya uwa sai naji yara suna a kara musu tuwo aka ce ya kare sai a dibar musu cikin na Alh. Ta saki murmushi.don wannan kada ka damu,na samu wanki yau gashi nan na dafa mana taliya. damuwata daya ta murje ce kai kuma baka son taliyar fulawa. Yace,in kin ji ana cewa ana cin kaza ba'a cin kaza duk cikin hali ne. Yanzun kuwa ba mu da hali. Tace,bari ka gani,nayi ta tayi kyau tamkar ba ta murji ba. Ta zuba mishi ya soma ci. Sai da ya koshi ya sha ruwa sannan yace yau kasar nan jama'a suna cikin wani hali iklima. Yau ne na yarda da batunki da kike cewa aiki tare da ba'a samu kudin nan ba(ban gane nan ba sosai)kuka ya saka yace 'ya'yansa bakwai kuma babu abinda zasu ci yanzun haka da ya fito ko na rana babi. Karo-karon kudi aka mishi ya auni garin rogo. Iklima tace,Allah sarki,gaskiya mutane suna cikin wani hali an jefa kasar tamu cikin masifa,an talauta mu. Yace,rashin dace ne dashugabanni na kwarai tace haka ne,sai dai mu ma mu gyara halayenmu don kamanninmu kamannin shuwagabanninmu in mun canza Allah zai dube mu.Suna ta zuba sam ta manta da batun takardar nan da aka ce ta ba shi. Alh kabiru yana ta kai kawo a cikin falon,tamkar karya yake ganin result da Dr ya bashi,shine yake dauke da HIV? Zawo ne fa kurum,to likitoci biyu asibitoci biyu kuma kwararru sun tabbatar mishi lallai gaske ne,ko da yake zai koma gurin likitan farko don ya bashi shawarwari zai dinga shan magani ba kowa bane zai iya gane cewa yana da ciwo ba. Ya kuma ci gaba da shagalinshi kowa ma ya samu tunda shima sa mishi aka yi,hakan kuwa ya yi.Samari sai ayi hattara masu aikata laifin luwadi,irin su Alh kabiru masu dauke da ciwo suna da yawa ga kuma zunibi saboda girman zunubin da kazantarsa in ana aikata shi duniya sai ta girgiza da za ku ji hukuncin mai laifin kuma sama za'a hau bene a jeho mutum. Allah ka kare alummar musulmi. Shi kuwa Alh jamilu wani maruru ne dan karami ya fito mishi daga matsugunna sai damun shi yake yi,ko zama ya kasa. In ya taba yana jin shi amma nafisa da yace ta duba mishi tace ba ta ga komai ba. Don haka bai yi kasa a gwiwa ba yayi asibiti.ashe tsutsosi ne suke dam a gurin tsugunnon,likitan yace aiki za'a masa. Ko gida bai yo waya ya shaida ma nafisa ba,yace ayi mishi. Sai da aka gama sannan yayi ma nafisa waya ta zo sai dai wata sabuwar matsalar tunda aka yi aiki baya rike kashi duk abinda yace sai dai ka ganshi satata da ya yi dan nishi,haka nan suka nufi egypt inda aka yanki cinyarshi aka yi masa ciko.sannan likitocin suka gargade shi da ya daina bari ana taba shi a gurin.Ma'ana a daina mishi luwadi,sai dai yana samun sauki ya dora daga inda ya tsaya. Tir Allah ka shiryemu amin. Ita kuwa Nafisa ko a jikinta,yawo kasashe shine a gabanta. Anty hajara ta sake sata a wata hanyar madigo, inda suke diban kazantar da suke fitarwa suna kai ma bokan yana hada musu sihiri don bunkasa kasuwancinsu. Tsafi gskiyar me shi, suna ganin cgb sai inda dk bokayen suka fado shine har yau ta kasa samun wnda ya shawo mata kan mahmud, dk bokan da taje tasa aiki sakamakon yana zama in aikin yaje sai ya dawo. Musamman ta yanke shawarar samun shi gaba da gaba kmr ynda cocein din data sha ya gaya mata. Ta tsaya da mota kofar gidansu ikilima ta shiga sai dai kash! Dakin na kulle ta koma gidan su, sa wa tayi aka bi mata diddigin inda zata ga mahmud, ta hanyar safina. Anxo mata da lbrin majalisar su da suke hira da dare. Gidansu ta koma gurin haule ta kwnta. Kamar ynda aka shaida mata cewa byn isha'i hakan tayi lkcn su 3 ne a gurin shi da muktar da wani babayo, yawanci nan suke daukar karatunsu gurin malam ya'u. Basu cika hirar bnxa ba a majalhsar tasu. Ta aiko wani yaro ya kira shi koda yaron ya nuna mishi motar be kawo ta ba a zatonshi namiji ne cikin motar, yace to wanene wancan km? Muktar yace kaje ka gani mana dg ganin motar can kasan samu ke kiranka. Ya nufi motar yana zancen zuciya. Kofar gaba ta bude, daidai da lkcin da wutar motar ta dallaro, nafisa ce cikin wando da riga na wando da riga na wani jan uban sun yadi. Zai juya sai yaga wasu samari 2 a bayanshi ta gefe dayan ya dora mishi bindiga a kugu, ynda ba kowa zai gane ba. Ko da ranane bare dare. Suka ce shiga kawai muje, yace bari in sallami abokina suka ce a'a ba jimawa zakayi ba. Wani shahararren hotel ta nufa dasu yana tsakiyar mutanen nan. Suka fito suka jera su 3 tana gaba suna binta har suka iso kofar wani daki ta ciro key cikin jakarta ta bude suka shiga. Ta dubi mazan sannan ta ciro kudi cikin jakarta ku jira mu can wajen shakatawa, ko a falon karbar baki. Ta maida kofar ta kulle ga mamakinsa sai yaga taje ta windo ta jefa dan mukullin. Da sauri ya isa bakin windo ya leka can kasa ne cikin swimming pool ya zunduma, ya juyo ga mamakinsa ta soma cire tufafinta. Ya daure fuska addu'a na cikin zcyrsa. Da in ina yayi magana me me ki.....ke so dani da kika kawo ni nan? Tace shine xan gwada maka ynxu. Pant ne kawai ya rage a jikinta tai juyi dubeni kasan ina da kyau ko? Bai bata amsa ba ta cgb nasan kana so na, ta dafa kafadarshi. Mahmud wlhy-wlhy dk abinda nake so nan dunia ina samunshi, kaine kawai na gagara samu, na kashe kudi, na zubar da hawaye don kai kadai to na gaji dole ne ka amince min mu dinga hulda tnda bazaka rabu da kanwata ba. Ya zame hannuta daga kafadarshi. Allah ya tsareni, ya nuna ta da yatsa ki bude min kofa in tafi ke kanki kin san kin yaudari kanki, bn amince dake ba lkcn kina budurwa sai ynxu? Shedaniya in dai nine kin rasa ni har abada sai dai hawayenki su kare. Ya sake zuba mata harara tare da cewa baki da wani kyau dama kyan naki a fuska ne? Wlhy matata tafi ki komai na dirin jiki, ni bana sonki ma ynxun kwata-kwata, na kara tsanarki. Ya kaita bango dn hk ta zabga mishi mari, tace karyane kana sona km nafi ikilima kyau. Shima ya yarfa mata mari gefe 2. Ga mamakinsa sai yaga ta shafa kumatun da tafin hannunta ta sumbaci hannun. Ko duk jikina zaka zane czan damu ba ni dai burina jikina ya taba naka. Ta kawo mishi runguma ya kauce ya nufi kofa yana jijjigawa tace kada ka karya musu kofa gabanka na yarda mukulli. Ta ko taso gabanshi zan so kawai ka yarda ta zuge jakarta ta zazzage masa kudin ciki yan dubu dubu ne dauri dari. Zan baka kudi km zan samo maka aiki, in ka amince zan fidda ka dg kunci da wahalar rayuwa, zaka shana in fita da kai kasashen dunia dn ka kece raini, zan zamar da kai abin kwatance cikin abokanka da family dinka. Ke! Ya daka mata tsawa, kinyi kadan ki aikata dk wannan, wahala da hutu, arziki da talauci dk na Allah ne. Shi ne kadai zai maidani abin kwatance, in yaso in be so ba km ya brni cikin wahala. Amma hakan ba zai sa inyi ynda kike so ba. Tace to zaka san ynda zaka kare kanka dg gurin yan sanda in suka sameka anan dakin, nace dasu fyade zaka mun. Zufa ta soma keto mishi yace ba kece ta farko da tai wannan sharrin ga namiji ba, sai dai yi min sharrin ze fi min sauki fiye da aikata abinda kike so. Inyaso ni km Allah ya saka min ranar gobe kiyama. Ta sake yo kansa da nufin runguma ya hankadeta tn karfinshi ta zube ta shiga kuka ta soma rokonshi da girman Allah wai ko sau 1 ne ita tana tasan shi wanene a rayuwarta. Yace wlhy sai dai ki mutu. Ta mike ta nufi jakarta ta zage zif din bayan ta ciro wata kwalba, be taba yarda mata nashan fakalin ba sai ranar, ta nufi water filter ta matso ruwan sanyi ta bude kwalbr ta juye ta kafa kai ta shanye. Tace ni da kai zamu kwana anan. Nan ta shiga surutai wadanda bazasu fadu ba daga baya ta zube kan gado jim kadan sai bcci. Tun lkcn da bcci yai gaba da ita yake neman yanda zeyi ya fita. Daga bisani ya dannan waya yai magana da masu kawo abinci cewa su kawo chips, lkcin da sukazo budewa ya leka ta window yake shaida mishi cewa sistr dinshi tayi bcci km key din na hannunta, tasha maganine don Allah ko za a samu wani? Yace sai dai gurin manyansu. Yace don Allah yaje gurin masu kula da dakunan ya shaida musu. Sai da suka zo har bakin gurin suka mishi tmbyoyi sannan suka bude suka shigo dakin sukayi dube-dube sai suka fita. Dama ya kalli agogo daya saura, sun fi minti 30 da tfy sannan ya sauka ta dayan gefen da nisa tsakani da unguwarsu gashi bashi da sisi, a kafa ya dau hanya. Hnkln ikilima ya tashi matuka, rashin ganin baban khalil ita har ta soma bcci ta farka bata ganshi ba. Ta dubi agogo sha 2, rabonshi da kaiwa 12 tn suna husuma dashi. Nan idonta ya gyara har dayan dare, biyu saura sai gashi hajaran-majaran, dama shine ke rufe gida. Ta kalleshi cikin dmw tace daga ina yayana? Ya sauke ajiyar zucia munje ganin wani aiki ne motar ta lalace gashi unguwar da nisa muka tako a kafa. Tace sannu, zo ka kwnta dk na damu hnklina ya tashi na rasa ina zan saka kaina. Shi kuwa shiru yayi cikin zuciar shi yana fadin "Astagfirullah, sbd karyar da yai. Sam be runtsa ba yana mamakin dama mata sun lalace haka? Musamman matan aure, shin bazasu ji tsoron Allah ba? Mace da mijinki amma kina bin wani don son zuciarki? Ki dau cikin wani ki kai gidan mijinki. Basa tuna mutuwa, basa tuna kabari ba ruwansu da tashin kiyama bare su tuna wuta. Rywr dunia kalilan ce, ayi ta aikata zunubi. Ana cin buri kwana suna karewa, lallai kada mu biyewa zuciarmu don dk wnda ya bita karshensa nadama. Allah ka tsaremu da aikata aikin dana sani. Dk lkcin da ikilima ta farka sai ta ganshi ido 2, dn haka itama sama-sama tai bcci. Da safe bcci ya dauke su byn sunyi sallah. Sama-sama suke jin ana kwankwasa kofa, ta tashi ta bude. Baban ummi ne tsaye yace ina maigidanki tace gashi can yana bacci. Yace ana sallama dashi. Taxo ta tashe shi. Singlet ce da dogon wando a jhkinshi ya fito. Nan take ya kara wartsakewa ganin yan sanda. Suka dube shi. Kaine mahmud? Yace eh nine suka ce bismillah muje sashinmu zaka amsa wasu yan tambyoyi. A hnkli yace inna lillahi wa inna ilaihir rajiun. To bari in dauko riga. Suka ce a'a. Sai ga baban ummi. Ya dubeshi don Allah yi min taimako da rigata sannan ka fada ma matata. Ikilima ta miko rigar tare da cewa lfy dai ko? Yace ina fa lfy, yan sanda ne. Ta dafa kirji yan sanda? Ta suri hijabi ta fita, daidai yasa rigar muryarta na rawa ta dubi yansandan malam lfy, meya muku? Dayan yace ya sani inya dawo zai miki bayani. Mutane har sun fara taruwa suka shiga mota suka tafi dashi. Da kuka ta nufi gidansu, a waje taci karo da musa yace antyna lfy? Tace yansanda ne suka kama baban khalil, yace meya faru? Tace nima bn sani ba. Yace to koma gida bari in sanar dasu. A daki sai kai da kawo take yi ta rasa wane tunani zata yi, ta xauna tana so ta tuna wani lefi mijinta yayi? Su maman ummi suka shigo suna bata hkri tare da cewa ko meye ze zo da sauki. Sai da suka fita suka kebe suna cewa kila ma sata yayi don jia sai cikin dare ya dawo. Na fito fistari na ganshi. Inji aisha. Maman ummi tace zai yiwu kin san wasu in basu dashi basa hakuri, sai a shiga dan hali. Aisha tace kai, amma anyi wayon banza, za a gina jiki da haramun. Ikilima dai ta kosa taji meya faru, ta sake zarar hijabi ta fita suna cewa ina zaki? Tace a'a gidan su zanje. Tana fita suka sheke da daria wai wahala ta ganta. Tana isa gidan ta samesu cirko-cirko, nan suka shiga tmbyrta ynda abin ya faru. Ta shaida musu cewa ita dai jia byn yaci abinci ya fita be dawo ba sai wajen biyun dare. Km tnda ya dawo be runtsa ba sai byn ya dawo masallaci. Mahaifin nashi wnda ya shirya don tfy ofis din yansandan shi dasu musa yace baki tmbyeshi inda yaje ba? Tace yace min sunje ganin wani aiki ne mota ta lalace km dama be fita da kudi ba, a kasa ya dawo. Zasu tafi tace zata bisu yace a'a ki zauna ynxun zamu d awo ba musan wane ofishin ne ba sai mun bincika tukun. MABUDIN WAHALA 2**9 Lkcn da mahmud suka isa gurin yan sandan, nan suka soma mishi tambayoyi akan matar dayai niyyar yiwa fyade jia burinshi be cika ba ya dibar mata kudi ya gudu byn ya shaka mata abin maye. Ya jinjina kai lkcin daya ga mijin kullin da nafisar tai mishi. Yace yallabai ba hk bane, ina zaune da abokaina tazo ta daukeni, sannan ita ce ta rokeni inyi zina da ita naki sannan bn shaka mata komai ba fakalin tasha, km bn daukar mata ko sisi ba a kafa ma naje gida tn daga Togo guest inn har unguwarmu. Wani ya falla mishi mari uban wanene ze ga wannan matar yaki? Kafin su alhji ibrahim su iso yan sandan sunyi masa ligis dk sunji mishi ciwo. Da alhaji ya iso kuwa yan'sandan sunce yabi wata matane har togo guest inn yayi mata fyade sannan ya diba mata kudi. Sunce tabbas hakan ya faru dan ya rupe kofar ya jefar da dan makullin ta baya, sai da ya gama abinda zaiyi sannan ya sa akawo mishi chips daman don a bude ne ya sulale ya gudu. Alhaji ibrahim yace to ya ya aka gane cewa shine? Ai tasan shi ya taba nemanta tana budurwa kuma shima ya amsa laifukan yace yayi. Alhaji yace innalillahi.... Ya amas? Suka ce ya amsa, ya mike ranshi bace tunda ya aikata shi ya sani da iyalinshi da komai dan fitinar tsiya. Musa yace alhaji hakuri zakayi tunda bai taba aikata hakan ba ayi maganar belinsa. Alhaji bai ko saurare su ba ya tabi. Musa ya dubi yan'sandan yana cewa zamu iya samun belinsa? Sukace a'a, kotu zamu mikashi gobe, musa yace to zan iya ganinsa? Har sunce a'a wani ya ce ku kira masa shi ya ganshi. Musa idanuwanshi suka ciko da hawaye, lokacin dayaga yanda suka maida mahmud da duka, yace yaya me yaja maka wannan danyan aiki? Dubi yanda sukayi maka kankanci? Mahmud yace kasan wayeni musa, in zanyi ka sani in ma bazanyi ba duk zaka shaida kai dai mu barma Allah. Mura yace hakane amma sunce ka amsa laifin? Ya girgiza kai ko kusa ban amsa ba don ban aikataba, sune kawai suka kagamin suka kuma amsa min. Ni saida Allah ya sakamin. Musa ya jinjina kai, wai wace mata ce? Mahmud ya yi shiru sannan yace bansanta ba. Shi kanshi bai san dalilin da yasa baice nafisa ba kila don kada haushin nafisan ya shifi ikilima ne. Yan sandan suka tasa keyersa don mai dashi ciki, ya daga murya ka kwantar ma da ikilima hankali, da son samu nema kada ka gaya mata musa ya ce to. Sai dai kash!! Kafin musa ya iso alhaji ya ba su lbrn laifin da mahmud ya aikata, alhaji ya ce kuma zan iya yarda tunda matar sa tace cikin dare ya dawo jiya shine zai yi karya wai anje nuna musu aiki, wane aikine za'a nuna da dare? Don haka ni ba ruwana, ya karata can ba kanshi zan kare ba tunda bashi kadai na haifa ba. Shine babba amma kullum matsala, iklima ta kasa motsi tana sauraron kowa saidai ita zuciyarta taki amincewa da batun, kaman yadda yan gdan suka kama. Suna cewa bai kyauta ba. Musa yanufi gurinta zo muje gdanku. Ta bishi suka fita. Su hajiya uwa sukace sai hakuri kaddara ce. Lokacin da suka shiga gdansu makota sun shigo su maman ummi suna basu lbrin. Suna shigowa makwabta suka yi mata jaje ta amsa tare da shigewa. Musa nifa banyarda ba, yace yauwa wlh dama shima ke yakeji, tace haba nasan wanene mijina, nasan sharri ne yanxun za'a bada belinsa ne? Yace a'a sunce sai gobe zasu kashi kotu ta soma kuka yanxu cikin bainar jama'a za'a tona masa asiri. Musa yace kada ki damu Allah ya tare da ku, ki ci gaba da addu'a matan gdan kuma kada ki nuna musu ko mai. Tace to goben kowanne hukunci za'a yanke masa? Yace sai dai goben tunda matar tace baiyi nasarar yi mata fyaden ba sai dai kudin da tace ya di ba ikilima tace nawa ne? Wai dubu ishirin tace to zani gdan wancen dillaliyar tazo ta sai kujeruna yace ni kuma ina ganin kamar gurin mamar mu, tace a'a hankalinta zai tashi barta. Dillaliyar tasai kujeru dubu sha daya, tace ga gadon. Ladi tace sabbi zakiyi ne yarinya? Tace eh gadon ta tarkacensa ta siya dubu sha biyar, nan ta amshi kudin cikin dare kuwa aka fita da kayan, ta'aje katifar ta a kasa kwana tayi tana kai kukanta gurin Allah, kan cewa ya biya mata bukatarta wato ya sakawa mijinta.els BOOK MABUDIN WAHALA 3**1 Tana cikin sama khalil kaya musa ya shigo, ya dubi dakin ina kujerun? Tace na saidasu, yanxu ni ga dubu 25 a hanuna da shida ne zan aje dubu 1 a gurina. Yace to nima wasu shaddodine da baba yace a kaima su kamalu dinki soboda zuwan sallah na saida dubu 3 tunda kin san ni din dan makanta ne ba kudine da ni ba. Sannan abokansa sun hada kusan dubu goma sha biyer. Shima fa baba ya damu yana ganin kamar gaskene shiyasa ya share zance. Amma yanda yake son yaya mahmud ai ba ma zan yarda a ce bai damuba. Kana ko yi addua? Ta tambayeshi, inayi mana addu'a kuwa yinta ya zama dole, koda kuwa mu2m baicika matsala ba. Suka fita ya sao mashin suka tafi, can abokanshi suka samesu. Bayan alkali yazo shari'a 2 akayi kafin nasu, nafisa bata zo ba sai lauyanta. Alkali ya saurari bayani daga kowane bangare bisa shedun da yasan dake dasu. Musamman yan togo guest inn da suka bada shedar. Alkali ya yenke masa hukuncin tara dubu ashirin kudin daya diba kuma zaya biya. Tunda aka fito dashi ikilima ke faman kuka saboda cikin kwana daya dubi yadda ya koma ga jikinsa duk jini. Ta mika ma musa ya basu nan suka hada dubu arba'in suka bama alkali. Sulaiman ne yakai kudin koto ta sake shi. Jama'a sukayita masa murna, wasu kuma suna cewa Allah ya shiryeshi ya kiyayi gaba. Ikilima tana zuwa ta daura ruwa dan sunriga mahmud dawowa. Lokacin da ya shigo dakin tare da abokanshi, sai ya shiga waige waige, tamkar zaure ya fada a ranshi, ta shimfida musu taburma sun dan kara jajanta mishi nan sulaiman yace ikilima ga sauran kudin, dama mu mun hada dubu 12 ke da musa kun hada 35 yanxu ga 7. To mungodai. Allah ya bar kauna ku bashi, inji ikilima suka mika mishi ya amsa yana godiya tare da addu'a. Matan gdan suka shigo suna gaisheshi. Bayan fitar su ita ce tayi masa wanka tare da gasa masa jiki,tanayi tana kuda dama taba musa ya siyo mata manzafi tunda suka dawo, ta shafe mishi jiki sannan ya sha tea da panadol ya kwanta. Ko lokacin da su hajiya uwa suka zo yayi bacci, lbr malam usman yaji yazo dan ita batayi niyar sanar da mahaifinta ba, yazo shima ya same shi yana bacci yace kada ta tasheshi Allah ya kyauta gaba, tace amin yace ni da'akace mahmud yaje sata har yayiwa matar fyade banyarda ba. Tace ai abin yarda ma daban yake baba. Sharri ne dai kuma zaya koma ga maishi. Kiyi ta hakur,gaskiya zata fito inji baba. To

Chapter 13 of 20