Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
kuma gefen hajiyar shi da gefen baki. Ashura saboda xuciya da tayi tace baxat taba xuwadakin shi ba sai dai shi in ya matsu yaxo nata dakin, ako haka suke. Iklima duk jinta take ba daidai ba,2n ana bikin Nfsa karfin hali kawai takeyyi ko bata je asibiti ba tasan cewa ciki ne da ita taji bata marmarin komai sai taliyar murji ta fulawa ta mike ta nufi kitchen tana 2nanin ina xata samu? Hijabi ta xura ta nufi gidan Luba Suna gaisawa tace luba ina xan sau taliyar murji?luba tace bari a kira A'i me aikina kila ta sani,dan taliya muka samu kenan?tace wlh ina xaton ciki ne dani luba. Luba tace ai ummita ta sha miya,iklima tace haka babanta yace ranan wai shi fa kada na yarda nasha wani magani,ashura ma da take sha ya fada mata ta daina ba da yawunsa ba tace ita bata shirya haihuwa ba yace ita ta sani shi 2nda yana da yaran shi. Luba tace saki jiki ki haihu kawata lokacin da kike sunbulo ma mijinki yara lokacin yake kara sonki iklima tace hakane. A'i ta dawo daga siyan taliya iklima ta shiga gida. Tana cikin dafa taliya khalil na kofar kicin yana shan dudu Ashura tazo shiga kitchen tace kai tashi a hanya dan iskan yaro kuna ganin mutane matsiyatan yara baxa ku matsa ba. Iklima abin ya soki ranta tace haba Ashura ki daina zagin yara na yan iska gara in sun miki laifi ne ki dake su bana son zagi bana yi bana so yarana su tashi dayi. Ashura tace na xaga koke sai in xaga bare su,su din banza?gidan miji na ne,ran iklima ya baci sosai bata saba da fada ba tace to ai suma gidan uban su ne ko? Ashura tace gidan uban manya dama uban ya damu dasu ne to uwarsu ma cuso ta akayi mun san komai yarki ya nema taga kudi ta guje shi aka manna mishi ke ba sonki yake ba,ita kuma ta kwashi kanjamau. Iklima ta tsura mata ido sannan tayi karfin halin cewa wa ya fada miki? Ashura tace wa kika sam xai fada min?don haka bar ni na sake soyayya tasa aka auro ni kuma da xaran na shirya haihuwa xan soma zubulbulo yayan soyayya. Iklima ta lumshe ido in ma shi ya fada miki xai dawo ya same ni,ashura tace shi ne ya fada min kuwa don haka ki san matsayin ki bar gani ina raga miki. Daki iklima ta shige tare da kama yaronta tayi shiru akan gado. Tabbas Mahmood shine ya fada wa matarsa sirrinsu domin babu wanda ta sani a garin da xai bata labari,a saninta sakina makociyarsu itace kawar ashura kadai kuma bata xaton tasan labarin 2nda ba unguwar suke ba,ta gama duk 2naninta ta gano cewa in ba mahmood ba ba wanda xai fada mata. Ranta yayi ma2kar baci kenan ita da mahmood ba sirri?ta xata sirrin shi nata ne haka nata nashi ne ashe ba haka abin yake ba?ranar dai kasa cin taliyar tayi yini tana daki. Ashura kuwa an sami abinyi shiga goma fita habaici,waka,wai matar cushe bata daraja. Iklima tayi kuka har ta gaji da dare luba ta shigo ta ganta kwance tace jikinne har yanxun?iklima tace wlh amma dole xan gyagije gobe Asabar ina da jarabawa a makaranta. Luba tace kuma yayan naki baya kusa bare kiyi shagwaba,sukay ta hira luba ta tafi bata fad ma luba komai ba domin sirrin gidanta ne. Washegari tayi shirin islamiya ta fita ko duban inda motar take batayi ba ta nufi taxi,su khalil suna gidan luba. 2n jiya kome na mahmud yasure mata hatta wayarta ta kashe don bata ko son jon muryarshi ya kira ya kira yayi text shiru ya tambayi Ashura iklima fa? Tace ita tana daki bata san ko tana nan ba yace ta duba ta tace ta kunna waya,ko motsawa batayi ba da ya sake kira sai tace ta fita 2ni gurin magrib ya sake kira Ashura tace bafa ta dawo ba don sharri,kawai ya cika da mamakin ina taje?washegari ma duk bata a ntwk ya damu sosai. Ta dawo islamiyya ta shiga kitchen tana kokarin dora girki sai ga A'i mai aikin luba da uwar kula cike da 2won shinkafa miyar ogun,iklima tace kai jice da luba Allah ya biyata sai nazo, Ashura na jinsu ta hau wakar habaici wai kwadayi mabudin wahala ga roko an bani dai. Iklima dai tayi daki cikin ranta tace bada ke xanyi ba da wanda ya daure miki gindi xanyi bari yaxo garin. Uku saura suka bar office da yake yanxu ya xama babba har sati yana office daga office jirgi kawai ya hau xuwa airport sai dai ya kira wayar direbansu mabde yace yaxo ya dauke shi,iklima na kwance tana sauraron kaset din wa'azi na Sheikh Aminu Daurawa (siffar mace ta gari) ya shigo da sallama banda sanin muhimmancin sallama da baxata amsa ba sai dai a ciki ta amsa,sannan ko motsi batayi ba bare ta dube shi ya iso gabanta ya sabule jakar daga kafadar shi iklima ta dube shi irin duban da bata taba mishi ba shi kanshi yaga kallon tsana ganin idonshi yace lafiya?tace kalau cikin muryar rashin ladabi,al'ajabi ya cika shi. Ya sauke ajiyar heart ya kika kashe wayar ki 2n jiya ina ta nema?tace bana son damu ne na kashe,yace tashi wai meke faruwane?yau ban gane miki ba kinxo da bakin dabi'u,taja ajiyar heart lokacin da ta soma 2no xantukan ashura tayi mata gori dasu sai kuka,duk ya rude xai taba ta ta tashi xaune tare da cewa kada ka taba ni ta sauka daga kan gadon binta yake da ido cikin mamaki tace Mahmood! Ya xaro eyes bai taba jin sunan a bakinta ba taci gaba cikin kuka dama jiranka nake yi kaxo ka sallame ni in tafi gida,bai san lokacin da ya iso ya daga hannu ya wanka mata mari ba sannan yace anki a sallame ki kin san me kike fadi?ta dafe kunci tare da fashewa da sabon kuka ni ka mara?ni ka daka?ta janyo hijabinta daga kan kofa xan tafi gidan makwadaita. Yace iklima in kin fita kofar gida Allah ya isa ban yafe ba ta tsaya cak sai ta fashe da sabon kuka tana cewa ka cuci xuciyar da bata taba 2nanin cutar ka ba,kaci amana ka kuma tona sirrina don ka birge abin sonka ta dube shi ni yanxun kimarka ta ragu a idona. Yaxo ya tsugunna kusa da ita ki fada min lefina kin tsorata ni,yaya kike gani xanyi wata rayuwa mai dadi in baki?haba iklima me yasa xaki yanke min hukunci da xai xamar min tamkar na kisa?wannan ba halin ki bane ina kika samo bakon hali? Wlh iklima keme hakuri ce ke me biyayya ce,keme adalci ce kuma kece rufin asiri na ta dube shi gefen da ya mare ta idon gefen har ya kumbura amma kai me yasa baxaka rufe nawa sirrin ba?mahmood na sani baka sona kuma banga lefin xuciyarka ba don bata soni ba 2nda mahaifina yayi maka tayina ya 2ra maka ni da ka sani baka karba ba,tausanta ya cika xuciyar shi dole akwai wani abu yaxo ya kamata ya rungume tsam,fada min me aka ce miki nayi?tace ka fada wa matarka cewa baka sona da yarana dama auren dole akay maka dani yayata kake so ita mai kwadayi tabi mai kudi gashi nan ta dibo kanjamau....ta fashe da sabon kuka yayi shiru ya rasa bakin magana don al'ajabi,ya sake ta ya fita. Ashura dake labe ta jiyo takunsa ta ruga ta shige kicin ya duba dakinta yana kia Ashura! Ashura!! Ta amsa daga kicin yace zo nan,tana fitowa ta biyoshi iklima na zaune kasa suka shigo ya tsugunna kusa da ita,tashi ki xauna kan kujera ya kamata ta tashi,yace Ashura me kika ce mata? Tace na me? Yace kada ki kawo min raini. Ya dubi iklima me tace miki?iklima ta harare shi abinda ka fada mata,tace kace dole ka aure ni shi ne nekeso ka sallameni,kace iyayena kwadayayyu ne,yayata kaso ta auri maikudi tana da kanjamau duk ina ta san wannan in ba kai ka fda mata ba?ya fusata to ke Ashura ina kikaji wannan xancen?tace ina kuwa xanji?kai ka fada min kace dole kake xaune da ita har yaranta kace kyamar gidan su kakeji saboda kanjamau. Bai san lokacin da ya daga hannu ya wanka ma Ashura mari ba.yar sharri a ina na fada miki?ta dafe kuma2 shine ka mare ni dan ban fadi sauran ba?ta nufi kofar fita kace iyayanta talakawa matsiyata,kai kake ma Babanta dinki kuma kai kayi ma yarta kayan daki.... Ya nufo ta da sauri ta fita,kan ikilima ya sara ta ji zuciyanta na tashi.ta shiga bayi da gudu tana sheka amai.ya biyu ta yana tsaye yana mamakin sharri irin na ashura,ta gama amai ta yunkura zata mike jiri ya debe ta da gudu ya shiga ya dago ta can zuwa kan gado,ta ce ikilima don Allah kiyi hakuri,wallahi ta fada ne don kawai ta hada mu.ikilima tayi ajiyar zuciya,mahamood so nasa mutum yayi abinda yafi haka,kana sonta zaka iya fada mata.maza nawa ne suke zagi matansu suka tozarta matansu a gurin budurwa ma ba mata ba?Don ka fada mata ba wani sabon abu bane.ya ce ikilima ta ce bana so ka musa,don na tabbata duk sharrinta ba za ta kalli idonka ta maka ba,gashi duk abinda ta fada an yi.Gurinwa taji? wa muka sani nan unguwar?ya ce zata fadi in da ta ji.nafi son ki nutsu ki kwantar da hankalinki,dubi yanda ki ka yi.ke jaruma ce na sani kina jure abubuwa,ki jure wannan.Ta yunkura ta tashi zaune,ta soma magana hawaye na bin kumatunta.zan jure duk wani abu da zaka min,zan jure abunda matar zata min.amma ka sani ba zan taba jure abin da zai shafi mutuncin iyayena ba... kuka ya sarke ta,ta ci gaba da magana.Don iyayena koda hannu suke karawa a gaba don talauci ban da kamarsu,kuma zan tsare musu mutuncinsu,in ma tambaya ka?ya ce,Babana ya taba zuwa rokonka wani abu?taja numfashin a a,ta ce zan karba maka.ya rugumai ta,ba ke ba ko ni ba zan bari wani ya ci mutuncin mahaifinki ba. kiyi hakuri zan bi diddigin maganar nan.Ya dace zuwa yanzu kin san abin yi,kin san sharri da za a yi min,ta ce an sha fada min cewa namiji ba shi da tabbas ina musawa,ya ce kici gaba da musawa,kada kuma tabbas miki haka.Nan dai yayi ta lallashinta kin san wanda bai saba yin fushi ba,ina yayi ba kyua.da kyar ya shawo kanta,lokacin magariba ta gota,yayi wanka a dakin yayi sallah,itama tayi sallah ya ce ina yaran nan?ta ce suna gidan luba.ta dauki wayarta ta kunna tana kiran luba,suka gaisa ta ce,a"i ta kawo su khalil,baban su ya dawo.luba ta ce yanzu?ikilima ta ce,ehh,luba ta ce to ya jikin naki?tace da sauki.luba ta ce naji muryanki duk ta shake?ta ce,eh,kaina ne ke ciwo. A"i ta kawo su khalil,sun ci sun koshi har an yi usu wanka,suka ruga suka makale jikin babansu.a"i ta sauke kulolin da ta zo dasu,ta ce ya jiki?ikilima ta ce da sauki,ki ce mata na gode.taje ta dauko plate ta zuba mishi sinasir da miyan kaza,taje ta kawo mishi kunu aya.Ashura na lekenta bata so haka ba,tayi ne don su yi ta gabza fada,ya ce rabona da abinci tun break fast kema kina jin yunwa?ta ce,a a.ya ci ya koshi sannan ya yi isha:i,bai fita ba laptop ya jawo ya shiga harkokin aikin shi har lokacin bacci.ita tuni ma tayi bacci,ya aje komai ya kwanta a bayanta,ya nutsata jikinshi,zafin jikinta ne yasa shi hakura da bukatarshi.da safe kam bayan asubahi kasa jurewa yayi,don satinshi uku rabonshi da gida,don haka duk da bata jin dadin jikinta ta fahimce shi,don haka sai ta saki jiki ta mishi duk abinda yake so.bayan sun karya ya kira musa a waya ya ce yazo zai aiki shi gurin mahammod.ya nufi dakin ashura,rufda da ciki tayi tana ta chatting,ya fizge wayar ya duba da wa take hira,namiji ne suke hirar ya ce wanene wannan?ta ce dama can da abokina ka ganni.ya kashe ya saka wayar cikin aljihunsa ta ce ban wayata.ya ce bazan baki ba,a ina ne nake fada miki zantunkan da ki ka fada ma matata?ta mike tana hura hanci ba kai ka fada mini ba.ya ce a ina ki ka ji?ta ce,zancan duniya yana boyuwa ne?ya ce to me yasa ki ka zabi ki mini sharri ki ka ce ni ne na fada miki?ta dube shi don nasan haka ne zai fi yi maka zafi.ya ce, tashi muje ki karyata kanki,tayi mishi wani kallo.wallahi in mun je gabanta zan fadi wani abin,kuma ba zan canza ba.ya yi shiru yana kallonta,ya fita yayi shiru akan kujera yana tunanin yanda zai mata. kilima ta fita ta zauna kusa dasji lafiya?ya dube ta,ikilima za ki yarda da duk abin da zan fada miki? ta ce fadi naji,ya shaida mata duk yanda suka yi da ashura.ya ce,na baki dama ki je ki tambaye luba kawarki ba mata masu irin wannan makircin?ta kuwa shiga gidan lubata shaida mata komai.Luba ta ce,tabbas akwa matan da sun dama ashura a sharri,dan ke ba kya shiga jama,a sosai shi yasa ba za ki san wadannan abubuwan ba,shawarata ki saurari mijinki kuna da fahimtar juna ke da shi,shi yasa ake son mata da miji su fahimci juna duk matsalar da ta taso muku ba za ku sha wahala ba gurin magance ta.sannan in zai auro mata uku dole su biki a baya,don kin san mijinki fiye da kowaccan su.ki share ki yarda da abinda ya fada miki.ikilima ta ce to ni mamaki na ina ta ji zancen?luba ta ce,ke ki barmakiyinki,duk inda za taje ta lallabo zata je,a yanda ya damu ma za ki san cewa ba shi bane.Ikilima ta ce she kenan,na amince.Ashe tura ta gidan luba da yayi hukunci zai yi,tana shigowa ta soma jiyo ihun ashura sai jibgarta yake,ta fada dakin da gudu ta kama shi ta karfi ta rike yana barta yarinyar nan in koya mata hankali,in za ki yiwa sharri?ki hada ni da matata,ke ban da arzikinta ma da ki ke ci ta hana da tuni ban yarda ke na huta ba?Ikilima ta ce to ya isa ka bari ba kyua dukan mace,Manzon Allah bai taba dukan matan shi ba.ni dai aka yi wa laifi ko?to na yafe.ta dubi ashura kiyi hakuri ashura,da ke cin kuka tana zage zage ta ce ba zan hakura ba,munafuka duk ke ce ki kasa ai ya duke ni kuma wallahi sai na dauki mataki.ya ce,ki dauka.ya ciro waya ya kira yayanta abubakar abikin shi ya sanar da shi komai,abubakar ya ce baka zane yar iska ba?mahamood ya ce,mun kaita ga haka ai yanzu.abubakar ya ce da kyua kuma wallahi tazo gida sai na karya mata kafa,batun waya kuma kada ka barta da ita,in ma zaka ji tawa aikin ma ka ce ta aje tunda kana mata komai.vels BOOK MABUDIN WAHALA 3**11 Mahmud ya ce,tunanina kenan kawai ina duba yanda hajiya zata dauki batunne?abubakar ya ce, kai ke aurenta ko hajjiya?kawai ga abinda ka ke so in zata zauna ta zauna in bai mata ba tsarinka kenan.tazo ta zauna da hajjiya.mahamood ya ce na gode ya fita.Ikilima ta bishi a daki ta nuna mishi bacin ranta na duka ya ce bazai kara ba.da dare ya same ta har lokacin sai kuka take,ya ce bata da waya,kuma karta kuma fita sunan aiki.nan ko ta shiga hada kayanta,ta ce ba dole.da safe yana tafiya itama ta kama hanya.Hajjiya ta daure mata gindi,shi ko share su yayi lokacin da ya ji labarin cikin ikilima yayi murna sosai tamkar wannan ne lokacin na farko,da aka soma yin ciki a gidan shi.Tattalinta yake ita da yaranta,ya canza mata mota ya dauka mata yan aiki itama ta na kula da shi tarea da yin duk wani abu da tasan zai so ko zai birge shi,insuna hutu takan bishi lagos .zuwa yanzu mahamood lamura sun bude,karin girma a kan aikin shi,don haka ya zama bango mai kwari ga danginshe da mahaifanshi.Ashura kuwa sai waya take,ya bata takardarta,da ya yi yunkuri zai bata sai ikilima ta hana ta ce ba zai sake taba,ita dai tafi son yaje yayo bikonta shi kuma ya rantse cewa ba da shi ba.yayanta abubakar da cewa ya yi shima wai ya sake ta,ikilima ta ce sam bata yarda ba.ya ce shi kwnan kuma ba zai bi ta ba randa ta ji cewa zata iya zama da shi ta dawo. Duk da ikilima ta nuna bata son bidi,a wannan haihuwar mahamood ya kekashe ya ce,lokacin abu ayi shi.aka dace lokacin yana hutun karshen shekara,ta sintalo yaronta shima dai yan uwanshi ya biyo,duk suna kama ne sak da mahmood.Wa ya ce da ni ba ni ba sweety kin duba yaron nan da wa yake kama?ikilima ta ce,kana mini wayo baban khalil.ya ce,ki kara himma kin ji kanwata?tun da kin haifo mahmood ki samo min ikilima in fa tayi kama da ke.Ikilima ta ce,bar ni da labari wata haihuwa yanzu ban gama gyagajewa ba.ya ce,na bari.ya yi ma dan shi huduba da mahamood,hidima kuwa tun ranar da suka dawo asibiti aka kada sa dangi ko ta ina sai barkowa suke yi suna kuwa tana bata son taro bata son taro gida sai da ya dinke da jama,a,aka yi ta girke girke.su luba sune masu rabon abubuwa,nafisa kam tunda ta zauna bakin gado ikilima bata iya tashi ba kallon dakin take tana kukan zuci ga kanwarta ikilima ta zama babbar mace hakima.da ka ganta kaga matar manya kamshi dakinta ma dabanne kaya da gwala gwale ba a magana shi ko mahamood yanda yake shiga yana kiran ikilima yana ji da ita shi ne yasa nafisa tunanin cewa kila dama can ba sonta yake ba ikilima yake hari.Abokansa su muktar bai yada su ba,da abokansa na yanzu ta shirya walima an ci an tashi kowa na san barka.washegari nafisa tazo gurin aikin nama,tana gidan yayi wa ikilima albishir da cewa ta shi gudumawar shi da ita da mamanshi za su je umarah,nan da sati hudu har da jaririnsu.duka da ikilima ta taba zuwa lokacin gasar karatun su tayi murna sosai,don tsalle tayi ta rungume shi tana murna. Nafisa ta kara yin dana sani da bata bi son duniya ba, gashi yanzu tayi asarar abib sonta,har abada ta raina zrzikin sa gashi yau Allah ya daukaka shi.dukiyarsa ta halas guminsa ita ko ga ta ba dukiyar ba kuma lafiyar.wai ita taga da kyua ma kenan a kan mama zee tunda ta tuba kuma har gashi tayi aure tana saran samun dan kanta,don tayi bari ma kwanan baya,ita kam ta dau darasi a rayuwa,ta kuma yarda kwadayi mabudin wahala ne.Hajjiya su ashura ba lafiya, ciwon kansa za,ayi mata aiki kusan miliyon biyu,duk su saida komai sun biya mata aikin amma ba a jima da yin aikin ba ta ce ga garinku.Ikilima taji rasuwar lokacin da mahaood yayo mata waya,ya ce zai zo asabar amma kaduna zai wuce,ta ce ya biyo mata su tafi tare.haka kuwa aka yi gidan cike da mutane don ranar ce uku.Ashura taji mamakin ganin yanda ikilima ta koma cikin shekara daya,shima ta ji mamakin shi,daga ganinsu kasan kudi su zauna.duk da tasa hijabi da nikab a kamshinta da yadin hijabin ma zaka gane ta kere sa,a,sun yi gaisuwa da zasu tafi kannen hajjiyar su tayi ta bashi hakuri wai ya maida ashura,ya ce ai shi bai kore ta ba ita ce ta tafi in taga lokacin yayi da zata iya zama da shi to tana iya komawa.Nan dai suka tafi bayan sun sauke musu buhun shinkafa sadaka da dubu hamshin,abubakar yanata godiya.dangi suka yi wa ashura caa kan cewa tayi wa kanta fada ta koma ta ce in fa ina son shi amma yanda ya dauki matar nan sai ka ce uwarshi komai ita.itama komai shi in mutum na son zaman lafiya sai de yabi su dukansu.baba amina kanwar hajjiya ta ce,to ai durkusawa wada ba gajiyawa bane,daga ganinta zata yi hakuti ba zata yi son fitina ba.Ashura ta yi shiru don tasan duk sharrinta ba za ta ce ikilima mafadaciya ba ce. Matar yayanta abubakar ta ce,kiyi koyi da halayanta za ki samu shiga gurinsa.domin komai ki ka gani halin mutum ke ja mada.baba amina ta ce haka ne dama son mace ta zama sirrin mijinta,ta bi mijinta su zama tip da taya,ita da shi yanda duk wadda ta zo sai dai ta biyo ta.Wata kawar hajjiyar ta ce,ko de asiri ne?baba amina ta ce ko daya,ba asiri,hakuri ladabi da biyayya tsaf ta kare sirrin mijinta,kula da hakinshi kula da dukiyashi,tausaya mishi in yana halin damuwa,ki ji cewa damuwarshi taki ce,ba shi shawara mai kyua.kyuata ga daginsa,duk iri wadanna ki ka haro mijinki da su,to shi kuma zai bauta miki tamkar bawa.shi namiji tamkar yao yake.Ashura dai ta dage musu kan cewa sai in ya zo da kan shi ya ce ta koma,suka ce shi kenan ta zauna suka barta. Ikilima taja dalleliyar motarta zuwa gidan su da gidan surakarta don yi musu sallama saboda daran yau za su tashi.ta shiga gida suna da gurinsu maman ummi duk sunji kunya don ba su zo mata barka ba.suka shiga kame kame ta ce ba komai kada su damu,dama sallama ta zo musu za su tafi umra.Nan suka shiga murna tare da cewa,baban khalil ne ya biya miki?ta ce,ehh,yanzu kun yarda cewa akwa maza yan goyo?shawarata ku kama kawunanku kuyi hakuri ku rike Allah ku rike mazajanku da gaskiya da amana Allah zai baku fahimtar juna. Ikilima tana ki tana komai mahood ya ce ta sai ta sako hakorin makkah,don shi yana so ta ko sako,wayooo Allah!sun zama taurari,duk mata kawayenta so suke su koyi halinta don su mallake mazajen su bata tare da boka ko mallam ba.sakina ta doka ma ashura waya cewa sun dawo sai gata cikinsa,a yana gida.ya ko hada rai ko gaisuwarta bai amsa ba.ikilima dai ta sauke ta sauka ta girmamawa,tana kuka tan ba ikilima hakuri tare da neman gafaranta,ta kuma shaida mata cewa dama sharri tayi ma mahamood bai fada mata komai ba,kuma don Allah ta nemar mata gafara a gurin shi.ikilima tasa yan aikin ta suka sharre ma ashura dakinta, tare da gyara shi,ta ce ta zauna ba koma ba. wasa wasa sai mahood ya shiga fushi da ita,kan ta ikiliman wai don me zata sauraro ashura?Hankalin ikilima ya tashi,amma ya ki sauraront,ya ma yi tafiyarshi lagos,ta shirya ta bishi ya ce sam shi fa ashura bata yi hankali ba.ikilima da kyar tasha kanshi ta dawo saboda makaranta ,ta tura ashura.bai san ta turo ta ba sai dai ta kira wayarshi ta ce ya taro ashura,sawa yayi aka zo aka dauke ta,duk da haka ta kusa sati tana rokon shi sannan ya kulata.bayan ya kafa mata sharudda wanda in tayi wasa da su zata bar gidan shi.sharuddan duk kusan saboda ikilima ne,tun daga lokacin ta kare sanin ikilima ta wuce da tunaninta..Zamamsu gwanin sha,awa,ashura ma ta haifi yarta yasa mata sunan hajjiyarta.likafa tayi gaba. yanzu mahamood fita waje kamar nan ya maida ta,ya ci gaba sosai.yayinda ragamar aikinshi ke hanun uwargidan sarautan mata,hajiya ikilima karatu bai hanata yin duk hidimar da ya sakar mata ba.na dagin shi da gidanshi suna godiya da sa albarka.amma shi bai san ma me aka yi musu ba,in ko yazo gari haka zai ta ji makota da yanuwa suna ce mishi sun ga sako sun gode. Wani abun da yafi ba shi mamaki,wani azumi yana gari yaje sallah masallacin layinsu,yaga an kawata masallacin kuma an gina islamiya maza manya ya ce da makocinshi gurin nan ya yi kyua,sai ya ce ai gaskiya ka kashe mishi kudi.ya ce ni?mijin luba ya ce, mai ne mana sai kuma ga yan kwamitin masallaci sun zo suna godiya.ya yi murmushi cikin zuciyashi ya ce,ikilima kenan!shi yasa komai nashi baya iya boye mata duk takardunshi masu muhimmanci suna hanunta tasan duk abin da ya mallaka dan yasan tana da gaskiya.Yanzu su nafisa da dagenta suma a gurinta suke hutawa,bata da rowa bare kyashi.iyayanshi na sonta don ta tsaya gurin kula da shi yan uwana mata kuna koyi da halin ikilima don mallake mazajanku? An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online, Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490 A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu, Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng You can download more hausa novels there Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online It is free we do not charge for uploading novel Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng For feedback and support Facebook : https://facebook.com/taskarnovels Twitter : https://twitter.com/taskarnovels Telegram : https://t.me/taskarnovels

Chapter 20 of 20