Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
Yace eh nafiu ya sayo min kije ki ci abinci ki samo takardada biro kixo ki rubuta min wasika xan aika gida. Ta mike ta nufi ciki bayan ta kammala ta fito da pen da takarda yace ta rubuta ma yanuwansa yana nemansu kada su bari sai ranar daurin aure. Bayan ta gama ta karanta mishi yace yayi sai tace baba lafiya kake son ganin su?yace saboda maganar yaruwarki ne suna son kunyata ni ne a idon duniya. Iklima ta dube shi cikin tausayi tace baba har yanxu basu amince ba?yace baxasu amince ba domin sunga mai kudi. Iklima ta kalli gurin dakin su kada haule ta jiyo ta tace baba kudi fa lodi haka xaka ga ya bata ina ganin ka daura mata auren kafin ranar,yace ina ganin haka xa ayi shi yasa ma nake so suxo tace in kayi hakan xaya fi dole ta rabu da kowa. Yace jeki kai min ruwa in dan watsa ko xan ji karfi in fita gurin malam haladu shi ne xashi gida gobe,iklima tace to ta mike ta nufi kai masa ruwan Alhaji jamilu ya kira layin nfsa ya shaida mata yanda sukayi da mahaifinta yace yana gdan saukar baki na nishadi ta same shi. Cikin sauri tay wanka ta shirya dole ne yau ta saka hijab 2nda babanta yana gida sannan tace haule ki masa karyar kin aike ni ne in ya tambaya,haka kuwa akayi tana fitowa yace ina zata?haule tayi caraf tace gdan hajiya baba na aiketa ta dubo min 2kwanen da na kai ajiya bai ce kome ba ta wuce. Tana xuwa masu lura da lafiyarshi suka mata jagora xuwa ciki wajensa ta same shi ya bude jakar kudin nan yana ba ma wasu samari su2 kowanne dauri 2 sukay godiya suka fita ta kauce suka wuce tare da ce mata sannu hajiya,kanta ya kara girma ita ga matar oga tace mussu yawwa ta wuce ciki. Bakin gado ta xauna kusa dashi tace wadannan yaran fa da suka fita?yace wiyarin suka min a wani gida da na siya wanda shine xan bama mahaifinki yayi taurin kai ban taba ganin matsiyacin mu2m irin mahaifinki ba. Ta daure fuska amma batace kome ba,yaci gaba banda matsiyaci duk kudin da nace xan bashi amma yaki yarda kai wannan mu2m baida rabo sa'a daya yaci ina sonki da na bar mishi ke ya jika yasha. Amma 2nda ina sonki yanxun ma na kira kine in baki xabin abu daya cikin 3 domin babu ba2n in rabu dake don yanxu ko kin fasa ni baxan fasa ba tace bare ma ba xancan fasawa in auri wa? Yayi murmushi yace na farko ko a kashe yaron da mahaifin naki yake son ya baki ta xaro idanu tace Mahmud?yace eh saboda in mahaifinki bai ga yaron ba dole ya hakura ya daura dani. Na2 ko in tsare mahaifin naki har abada ko labarin shi ba xa aji ba mu kuma muy auranmu. Na 3 kuma mafi sauki shine kiyi karar mahaifinki a ko2 can Abja alkalin a hannunmu yake sai yanda muka ce dashi in a lokacin mukeso xa a daura mana aure in yaso daga baya xaki iya xuea ki sasanta da mahaifinki musamman in yaga kin sakar mishi kudi. Tayi tagumi tana naxari daga bisani tace ko xaka daga min kafa in sanar da mamana in yaso duk yanda muka yanke in kiraka? Yace ba matsala xuwa gobe ne don gobe xan koma tace shikenan ni xan tafi ya kira daya daga cikin yaransa yace ya kaita gida.s BOOK MABUDIN WAHALA 1***8 Daga baya ita ce ta samo gurbin kara2n da kanta ta hanyar kawarta da ta hada ta da wani lecturer wanda sai da ya gama lalacewar sa da ita shi kuma mahmud yana ta barin kudi. Kai wanda yayi nisa baya jin kira mahmud ya kasa gane wacece nafisa,tana dai xuwa makarantar ne don kawai ace mata yar poly,shigarta gurin ta kara zama wayayyiya a ganinta sai dai cikin kwanakin ta soma kasa gane kanta sai amai da kasala,mahmud yazo suje asibiti amma sai haule tace ai shawara ce ba sai anje asibiti ba xata dafa mata huntu,ya dai jibgo lemo da ayaba kullum kuma zai zo sau 3 a rana. Nfsa ta damu kwarai a zubar da cikin da likita yace 3 months 2naninta in mahmud ya sani shikenan sun rabu har abada don koyaushe burinshi randa zai bude littafinta ba,bai sani ba 2ni wasu sun bude har sun karanta ba. Haule tace wa iklima in taji zancan a wani guri sai ta kashe iklimar 2nda ba a kanta aka fara ba kuma dama Allah ne ya kaddara mata haka tsautsayi ne don wannan ba halin nafisar bane,iklima tace mama ki daina cewa Allah ya kaddara ma ya nafisa domin shi ba azzalumin sarki bane sai wanda ya zalunci kansa inda fyade akayi mata sai ace ba laifinta bane, haulke tace ke dai kika sani mu gobe ma war yanzun mun fidda abin banza mun huta. Wa iyazubillah inji iklima mama kada kuyi haka laifin zai zama 2,yaya zaku ce da Akkah ranar gobe kiyama?me zaku ce da ran da kuka kashe in ya tambayeku dalilin kashe shi a ranar sakamako? Haule ta jefe ta da murfin kwano yi min shiru shegiya ai ke nan gaba ma kila kice mu kafirai ne ba wanda ya isa yayi wani motsi yanzun kya ce ba haka musulunci yace ba,kada ki manta mune muka haifeki laifi wanene baya yinsa illa muy istigfari, iklima bata daddara ba ta sake cewa ni nafi son kuji tsoron Allah fiye da mu2m,ina so mu shiga gidan tsira tare daku. Nafisa da ke kwance tana ji da ganin abinda ke faruwa tace kyaleta haule,so take inji kunyar duniya kuma bazan ji ba,iklima tace kema kina cikin matanan da suke cewa da kunyar duniyya gara ta ta lahira,kun san kunyar lahira kuwa? Haule tace tashi ki fita daga nan! Iklima ta mike cikin takaici tasan ba mahmud bane abokin lalacewar nafisa shi ya shanya baki zai auri budurwa. Sunyi nasarar kwakwale cikin duk da tasha wahala tazo taci gaba da jinya har ta warke sarai tamkar batayi jinya ba,sannan aka dora daga inda aka tsaya, Allah ka shirye mu. Iklima yau ce ranar tafiya gasarsu wannan lokaci har sabon dinki baban su yayi mata da hijabi da takalmi. Goma daidai aka soma gabatar da gasar,lokacin da aka zo kanta taje cike da kwarin gwiwa don malam yunus in yazo zance girinta bitar kara2 sukeyi yana mata yan gyare gyare,cikin ikon Allah wannan karon ma iklima usman tana kokarin zuwa ta daya,ga zazzakar muryarta in tana kara2 gurin tsit yakeyi tamkar kada ta daina,suka rage ita da wani yusuf Adam dan kano state a karshe tazo 1st shi kuma 2nd,iklima si ta samu kanta da yin kuka da kawayenta lokacin da al'umma suka shiga daukanta hoto yan jarida suka baibayeta yan agaji suka shiga bata kariya ta musamman,mahaifinta ma sai da yai kuka don dadi nan take aka shiga raba kyautuka ga dalibai da sukai nasara. Iklima ta daya an saka mata alkyabba kyauta daga sarkin garin,gwamnan jihar ya bata kujeran makka ga tsabar kudi 300K a sai mata kayan daki in ta tashi aure banda littatafai na addini ga kuma kyautuka daga wasu mutane daban. Kafin kace kobo gidajan radio sun shiga labarta yanda abin ya kasance talbijin kuwa nunawa sukeyi,nan makota suka ta shiga yiwa haule murna daga nan aka wuce da iklima islamiyyar su tare da sauran daliban. An sake tabbatar mata da cewa ita xata wakilci kasar nan don yin na duniya,an sanar da haule harda rungume iklima sai murna take yi tasu ta samu. Nfsa ma sai murna sunji ba2n makka tace haule ya kamata kice ta baki kujerar makkan, haule tace ai dama in ta kuma cin wata gasar taje,iklima dai tana jin su bata ce komai ba. Koda makaranta suka bata duk abubuwan da ta samu,yunus ne ya bata shawara ta dan ba makaranta wani abu, 100K ta bada sannan sauran komai ta mallaka wa mahaifinta shi kuma yace ta ciri wani abu ta bari a hannunta sai zannuwan da ta samu daga wasu yan kasuwa ta bawa su haule da nfsa itama ta dauka duk haule bata damu ba don iklima bata bata kudi ba don koyaushe burinta naga kujerar makkan nan. Sai dai bata san lokacin da aka bukaci passport ba 2ni iklima tace mahaifnta yaje yayo ya bada sannan ya dawo ya shaida ma haule nan ta bude faifan bala'i ta shiga zagin iklima. Bayan baban ya fita tace ai dama 2ni nasan ba sona kikeyi ba kin fi son ubanki dani matsiyaciyar yarinya ilminki bai kare ki da kome ba 2nda ko musulunci sai da ya kira uwa sau 3 yace uba. Allah ya jikan nfsa badan ta mu2 ba da ace ita ce ni zata ba,iklima ta lankwasar da kai tace ayya mama baki fahimce ni bane in na sake samu ke zakije malamai na ne suka ban shawara kan cewa in bawa baba 2nda shine shugaban mu a gidan gaba daya kudin kuma ya kara jari 2nda shi ke dauke da nauyin mu in Allah yaso ma sai ki ga dalilin haka wata rana ya kaiki...ta katse ta da ke da Allah rufe min baki ai su malaman naku dama nasan munafukai ne bare wannan yunus yake ko wane?da ganin shi kaga mako ya dafo dan wando yana sunne kai to aniyar ku ta biku munafukai kuma ko kin samu din bana so nafisa ta kaini. Lokacin da nafisar ta dawo haule ke labarta mata abinda ya faru,nfsa tace kwantar da hankalinki haule Hajji da umra sai kin gaji da zuwa haule tace ai ko da bakya nan ma na fada shi yasa ko yaushe nake saka miki albarka kuma tana binki. Cikin kwanakin iklima tana fuskantar cin zarafi daga yaruwarta da mahaifiyarta hakuri ta dinga yi dasu har suka gaji suka dan raga mata. *** Nfisa ta shiga makarantarsu rungume da litatafai jikinta sanye da wani yadi mai ruwan kasa takalmanta masu tsananin tsini ne iri daya ne da jakar tana tafe cikin taku na isa da kasaita da dama suna yi mata kallon yar wani kusa ne a gwamnati yayin da wasu ita ce da kanta tace musu uban ta minista ne wasu kuma tace musu jakadan nigeria ne a england babu wanda bai gaskata ta ba saboda la'akari da irin tsinannun motocin da ake kawota cikinsu,nfsa bata da wani takaimaiman fannin da take karantawa don bata shiga aji kuma koda ta shiga sai dai tayi ta zare idanu in anyi dariya itama tayi domin in za a shekara ana 2ranci bata san me ake cewa ba,itama 2rancin nata irin dan na tsintan nan ne amma ko kai waye baza ka gane ba,ta isa gurin kawayanta nan suka shiga koda shigar tata tare kuma da yi mata tafi ita kuwa ta shiga yi musu juyi kamar me yin paret, abokansu maza sukace ta shiga gasa da za ayi ta sarauniyar kyau anan makarantar tace haba?sukace Allah matan ma suka shiga zugata,guda daya ce mai suna jamila tace nafsa kada ki shiga sai kace ba yar musulma ba? Nfsa tace dakata min malama! ban kasa da ke ba ni nan da kika ganni ko gida ba a matsa min ba kuma ni zan iya saida rai in nemo suna,jamila tace zadai ki saida mu2mci ki nemo suna to Allah ya ganar dake,tace jamila sunanki kowa?don Allah dan maida min hankalinki kinji ko?duk gurin suka fashe da dariya jamila ta mike ta kama kanta. Zuwa yanzun ko a gaban mahmud nafsa tana yin waya da samarinta kuma in yaxo ya kan same ta da wasu ko in yana tare da ita wani yazo. Sun yi fada sun shirya yafu a kirga don ya lura baxa ta canza ba ko da kuma yaki zuwa zata bishi ta lallaso shi. Irin san da ya ke mata har haushin kansa yake ji kafatanin kannansa basu kaunar ta basa dokin auran yayan nasu,iyayansa kuwa adduar zabin alkhairi suke masa don kowa yasan yarinyar ba mai natsuwa bace,shine kadai so ya makantar,lokaci na tahowa ango ne kawai ke hidimarsa dan buga bugarsa in yayi ya sai kayan lefe don mahmud yanxu har aikin gini in ya samu yana zuwa tunda shagon ba kayan kirki. Satin da zai kama nafsa suna da bikin safina ita da mama zee sune manyan kawayan don haka suke ganawa da abokan ango wadanda ke ta yi musu barin kudi tamkar basa so,jikin nfsa har tsuma yake yi saboda irin kudin da ake musu bari ga dinner na garari,nan cikin abokan mama zee ta samu nata angon da dama sun kai hari ga nfsa taki amincewa duk don son mahmud in da soyayya kawai xa ayi xata yarda to duk ba2n aure suke mata. Bayan wata1 da yin auran safina suka sha na mama zee nan ma sunga barin kudi fiye ma da na safina abinda ya dada firgita nafisa jibgegiyar motar da safina ta shigo mallakinta ga wani kyau da tayi suka gama bikin mama zee nfsa tana nazari. Wata rana taje gdan safina ta same ta tana ba yan aikinta umarni kicin dinta ga girki nan kala kala wai mijinta zaiyi baki, suka shige uwar dakin safina suka fada kan gado nafsa tace kin ganki kuwa hajiyan Allah? duniya tana kai muku. Safina tace kece kikaso gashi cikin satin nan zamu tafi subai shakatawa ni da mama zee don mazan mu suna da meeting zasu tafi france kin san abokai ne kuma aikin su daya,nfsa tace kai kawata ina ganin xan yada ba2n so din nan nima in shigo sosai safna tace xama ki dao hanya in kin ki to kije kiyi auran so inyaso in mun cire kaya mun baki ki saka. Nfsa tace xanyi 2nani,yini tayi zugur gidan da zata tafi kayan shafa na iyayan kudi har da turmin holland ta bata yayin da Alhaji sani ya dire mata 20K sannan suka sa direban su ya kawo ta gida. Da dare sna cin balangun su ita da haule suna labari iklima kuwa tana gefe tana kallon su tare da sauraron irin labarin da nfsa take baiwa haule na daular da kawayanta ke ciki,haule tace a to kin dai gani kema ki sa kafa ki shure ba2n wannan dan iskan yaron da kika nace ma mu huta,nfsa tace ai ina zaton wannan karon zan jure in share shi baba kawai nake tsoro,haule tace shima share shi ana shiga daula zai manta daina tsoro zan tsaya miki. Iklima tace haba mama bai dace kiyi mana nuni da mu bijire daga umarnin mahaifinmu ba. Haule ta kwabe mata baki da bayan hannu tare da cewa uban wanene ya kasa dake da zakiyi caraf ki kwashe?iklima ta rike bakinta nafsa ta shiga yi mata ruwan bala'i a karshe tsakar gida ta fita ta bar musu dakin. Biki sauran sati2, 2ni abokan ango sun fito da katin daurin aure da na biki,ka2nan sun birge mahmud don haka ya kosa dare yayi don yaje ya shaida mata cewa gobe za a kawo lefe sannan ya bata katin da ya isa gidan bata nan wai suna bikin wata yar ajnsu inji nafiu,zuwan shi uku iklima ta fito suka gaisa tace mishi suna biki ne xasu kai amaryar Abuja sun ma tafi can xasu kwana,yayi shuru gashi bashi da waya bare ya kirata ya dubi iklima yace to shikenan sai da safe. Cikin dakin shi ya zuba ma ka2nan idanu haka kawai yake jin gabanshi yana faduwa a duk lokacin da ya kalli ka2nan sai yaga kamar auran ba zaya yiwu ba in ya 2no hali irin na nfsa da mahaifiyar ta game da son abin duniya. Yanzun haka da karma karma da taimakon dangi ya hada akwati babba daya da kit ya san rainawa zasuyi to amma yana dogara ga Allah da kuma son da take mishi, fatanshi dai ayi lafiya a gama domin yanzun wani sonta ne mai tsanani yake kara shigarsa. Nfsa suna bikin fati wata kawarsu ce itama dai irin nafsa ce wato yan cika poly ko yan garari cikin makaranta wai su a dole dalibai. Nafisa ce babbar kawa cikin kawaye. Fati ta auri wani kusa ne a gwamnati dattijo ne mai shekaru kusan hamsin haka nan abokananshi kuma 2nda aka soma biki abokanan suke ta kai hari gurinta sai dai hankalinta yafi tafiya kan Alhaji jamilu dukku na farko ta kula ya dan fisu kuruciya ga kyau tamkar ba mu2m ba sannan uwa uba ya lillinka su kudi 2nda aka soma bikin yake canjin mota in yaxo da wannan yanxun anjima da wata xa ka ganshi, sam shi bai damu da yanmata ba nafsa ce take yawan shige masa. Yau da ya kasance ranar dinner kwalliya sosai ta xauna gaban madubin amarya tana yi,burinta Alhaji dukku ya taya,wani yadi ta saka ja mai adon kyallin ruwan gwal,riga ce da skirt sun matse ta iyaka matsewa da kyar take sauke numfashi,takalminta mai tsini ne sai jakarta pos, gashinta da ya kone da mai ya sauka gadon bayanta,rabin kirji da bayanta a bude, net aka nada mata gwagwaro ta dora shi bisa kanta duk kawayen sun ga kyan tsarin adon ta tare da jinjina wa telanta. Lokacin da suka isa gurin dinner guri yayi guri makada sun cika gurin da sautin zamani,nfsa shedaniya jikinta har nari yakeyi saboda jin sauti ko gurin zama bata nema ba ta nufi gurin kidan cikin tafiyarta mai jan hankalin mazaje ta shiga yin wata irin rawa,juya jikinta takeyi tamkar babu kashi ita kadai ce ke rawar don haka ta zamar wa mazan gurin tamkar T.V ko kuma a club nan kuwa alhazawan birni suka shiga yi mata ruwan nera. Alhaji jamilu shine karshen likin inda yayi ta yiwa nafsa liki da dala hakan ya dada firgita ta yayin da mai wakar ya cigaba da yi mata waka. Mai abin magana ne ya sanar da makadin cewa su tsagaita za a soma gudanar da dinner. Alhaji jamilu ya amince nafisa tayi daidai da tsarin sa, don haka baiyi kasa a gwiwa ba yace da bodyguards dinsa su tanadar ma yarinyar abun zama sannan su kawo masa ita. Sun sha mamaki don maigidan nasu mata basu ishe shi kallo ba, nfsa tana zaune taji an dafa mata kafada ta waiga yace xo muje,tayi mishi wani kallon kai gaja yace maigidan mu ne ke son ganinki tace wa kenan? ya nuna mata shi. Zaraf ta mike tare da cema sauran kawayan nayi kasuwa cikin irin salon takunta na musamman ta isa gabanshi ya dubi kujerar da ke gabanta tare da cewa kya iya zama. Ta zauna tare da kafe shi da idanunta gwarza gwarza da take jan hankalin maza har ma da mata yace sunana Alhaji jamilu ina zaune nan Abj,malamar fa?nafisat usman ina zaune a minna. Ya jinjina kai haka yayi kyau ke daliba ce?tace eh ina kara2 a poly yace good me kike karantawa ne?tace uhm tana dan sosa keya accounting nake karantawa. Ya zuba mata idanu kin shirya aure?donni daga nazo fa aure za ayi,cikin tsananin doki tace ai kada kaji komai nima dama kai nake jira kuma gaka kazo,yayi dan murmushi. Ya salam!tace cikin ranta saboda kyan da da ya kara,namiji har da dimple. Yace to ya xaayi in san gidanku a minna?tace me sauki ne in zan tafi sai muje tare yace a'a zan hada ki da yaro daya cikin yarana ya kaiki tace duk ba damuwa. Tayi shiru xuciyarta cikin takaicin kasancewarsu talakawa ko dai ta kaisu wani gida ne? To wane gida dangi ma babu mai silalai kowa fdakara'u,2naninta ya katse lokacin da wayarshi ta shiga ringing ta kai duba kan teburin wayoyi ne wadanda ko cikin mafarki bata taba ganin irinsu ba. Kai ranar saboda tsabar rudewa duk kwadayinta da nama kasa ci tayi don murna ruwa ta iya sha kadai. Daya saura suka tashi shi ne ya saka daya daga cikin yaranshi ya kai ta gida yayinda masu tsaranshi suka rufa masa baya sai kace shine shugaban kasa. Kawayanta kam sai murna suke mata a gidan amarya tayi babban kamu, da zata gida kuwa suna sallama cikin motarsa akwati ya bude mata makil da kudi yace ta dibi son ranta,yan dubu dubu ne sabbi fil tayi ta wurga idanu yace kada kiji komai ki diba yanda zaya isheki. Sai da tayi ma jakarta dam,sannan ya hada ta da wanda zaya kai ta har gida ta dibi sauran kudin suka nufi gida cikin murna. Shi kam Alhaji jamilu 2n da yaga yanda ta dibi kudi yan dubu dauri 9 yasan cewa lallai wannan yar hannu ce,shi dama yafi son mace da zata saki jiki taci kudin shi son ranta ba wadda zata tsaya nuku nuku ba. Bayan yayi waya da direban cewa sun sauka lafiya,yace ta dubi hanyarsa jibi, tace ton gara kam yazo don akwai wata yar matsala... Lokacin da ta shiga gida haule bata nan don haka ta shiga dakin su,iklima ce ke rubutun ta na hadda tayi mata sannu da dawowa nafsa cikin fara'a ta amsa tare da cewa ina haule? Iklima tace ta tafi gdansu na saman layi. Nfsa ta zauna kan shimfidarta jiki na bari ta ciro jakarta daga kafada ta zuge zif ta ciro kudadan ta zubesu gabanta. Iklima tana kallo ta fiddo dukkan idanunta tare da cewa Ya nfsa wannan kudin fa?ckin dariya tace Alhaji jamilu kenan sona yake jakar kudi ya bude min na diba kadan na dauka dubu dari 9 da na kara dauri 1 miliyan kenan.iklima ckin tsoro tace miliyan?ke yaya nfsa kin san in da ya samo kudinnan ya baki su har haka?tace ke rufa min baki da Allah,iklima ta mike ta fita tana cewa ki dai yi a hankali. Lokacin da haule ta dawo har da rawa da taga kudi suka shiga shawarar yanda za ayi dau, haule tace mu sai kayan abinci da nama da kaji mu sayo freezer nfsa tace kuma muyi dinkuna da zai yiwu ma mu gyara gidannan don kada yazo yaga yanda gidan namu yake. Haule tace baza mu gyara gidan haya ba bar shi haka muci kudin mu ai ke yake so ba gidan ba. Nfsa tace haka na mu sayi gwal mu sa ma kunnuwan mu,haule tace mu bari sai da dare maje kasuwar. A ranar da dare mahmud yazo gurin nfsa suna zaune suna lissafin abinda xasu sayo ko magrib basuyi ba bare ishai,nafiu yazo kiranta taja tsaki ni wallahi har na mance dashi ashe kudi yana shafe soyayya?yanzun kam sai dai ayi rigima amma baxan auri mahmud ba haule ta sheke da dariya sannan tace in na zai ce a biyashi hidimar da ya miki ne nasan Alhaji jamilu tsaf zai biya shi tace da nfiu ce masa ina zuwa zanzo muyi ta ta kare. Mahmud yana zaune a kan dan dakalin da suke hira,can gefe kuma iklima ce da yunus dinta suna hira irin ta masoyan da ke da ilmi. Nfsa ta fito babu ko dan gyale dankwalinta ne ta rufa da shi ta tsaya a gabanshi kerere yaxo da nufin nuna masa jin haushinsa ta tafi biki bai sani ba,don haka shima sai ya shareta. Tace malam in baka da magana in koma yace amma ai kya yi sallama da kikaxo ko?cikin isgili tace ya ma akeyi?ban iya ba ya mike tsaye wannan kuma Allah kikeyi wa isgili. Ya ciro ka2nan gasu kuma gobe za a kawo lefe,2n shekaranjiya suke son xuwa amma kin tafi biki saboda kin isa da kanki ko in sani,tace kai dakata! ta daga mishi hannu wannan katin menene?yace saura kwana 12 sannan kice katin menene?ta shiga tafa hannu tare da dariyar renin wayau tace mahmud kenan don Allah ka sanar da yan gidanku su huta ba sai sun kawo ba,don kada su sha wahalar xuwa su dauka,ka sni baxan auri talaka irinka ba,sai yaushe xan samu babban gida da babbar mota?kwashe ka2nanka Allah ya hada kowa da daidai dashi. Kafafunshi suka shiga karkarwa dole ya xauna,muryarshi na rawa yace kada kiyi min haka nfsa baki min adalci ba. Ckin daga murya tace ban san adalci ba yaya ma ake yinsa?aure ne dai na fasa. Iklima da suke jin duk me eke fadi tace ya nfsa lafiya kike daga murya haka? sam matakin da kike shirin dauka hakika bakiyi masa adalci ba,nfsa ta kai mata mari ikli ta kauce nfsan tacigaba da cewa nace bazan aureshi ba don ubanki ke ki aureshi mana kin san ni waye ai talaka ba abokin tafyata bane. Muryar baban su ta jiyo yana cewa sannu yar karuna ya iso ya haska su da tocila don ganin wa take caba ma magana irin haka?ya sha mamakin ganin mahmud,dama kaine take cewa baza ta aura ba? Mahmud kanshi kasa yace nine baba. Malam usman ya jinjina kai sannan yace ina fata ka raba katin gayyatar daurin aure?mahmud yace kwarai muna kan rabawa,yace to kada ka fasa kaji ko?tashi kaje Allah ya maka albarka a kuma cigaba da shirye2. Cikin kwarin gwiwa mahmud ya tashi yayi sallama da yunus da ke can gefe yana kallon duk diramar da akeyi ganin haka nfsa ta nufi gda tana kuka tare da cewa nifa baban mu bana sonshi fa yace nima gidan xan shigo in na karaso kya shaida min,ya dubi iklima kema sallami bakon naki kizo ki shiga gida kuma haka nan,tace to,da sauri taje tace masa malam sai da safe shima ya mike don yaji abinda babanta yace tare da cewa mu kwana lafiya. Malam ya shga gdan daidai nan nfsa tana cewa maman mu ni dai wlh ba xan auri mahmud ba kinji babanmu wai su cigaba da shiri wlh ni kam xan shiga uwa duniya...jin haka yasa malam usman waige waigen madoki idanunshi suka sauka kan faskare ya isa gurin ya dauka ya nufi dakin,saukar duka taji a gadon bayanta ihu ta saki tare da hayewa gado,ya bita yana cigaba da kirba mata,haule itama cikin ihu ta rike shi tana fadin malam! malam! yayi wurgi da ita ta tashi tana cewa jama'a ku kawo dauki malam kada ka kashe ta fa,iklima itama sai kuka takeyi tana cewa baba kayi hakuri,sai da yaga ta daina ihu don wuya lokaci guda kuma ta daina motsi ya yarda itacen.kinyi kadan kice xaki maida ni karamin mu2m shekera da shekaru yaron yana yin wahala a kanki iyayansu sun zo na basu ke da yardarki da amincewarki yanzun sai da aski yaxo gaban goshi sannan xaki ce baki son shi? yana huci ya nuna haule wadda ke rabe gefe tana kuka yace ki maida hankalimki dani don nasan ke ce mai hure mata kunne,ya fita. Ta nufi gurin nfsa wadda numfashinta ke fita sama sama ta dago ta jini na xuba daga kumatunta iklima ta taimaka mata suka nufi kyemis inda ta anshi magunguna da allura tare kuma da gyaramata gurin ciwo suka kuma tarairayota suka dawo da ita gida. Har gari ya waye kuka take kuma bakinta bai mu2 ba,rantsuwa take tana karawa kan cewa ba xata auri wanda bata so ba,iklima kuwa cewa take ya nfsa don Allah ki bar wannan xancan kin san baba ba xaya canxa ba gashi kin ja ya dake ki irin haka. Nfsa tace kada ki dame ni,ai ke ma munafuka ce. Cikin kwana 2 ta ware sai plasta da ke kuma2nta.vels BOOK MABUDIN WAHALA 1**9 Musa kanin mahmud yana fitowa daga dakin mahmud malam usman yayi masa sallama,ya mika masa hanu suka gaisa yace

Chapter 6 of 20