Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
in ta dafa ma kanta haka zata tara su,in tazo wankewa tayi ta mita wai bari ya dawo ya nemo mata yar aiki,ita ba za ta iya yin wahala ba.watarana ta mishi waya wai ita fa tana son zuwa saloon ba ta da kudi,sai ya ce ta amsa gurin ikilima.A haukanta sai ta za ci kila mai kudin shi ne a gurinta,don haka da taje wai ikilima ta bata dubu daya in ji beby.Ikilima tayi shiru,don daga ita sai dari takwas,sai ta tuna da kudin musa,ta shiga ciki can karshen dakin ta kira shi,suka gaisa ta ce,musa zan iya aron kudinka?ya ce, eee.ki dauka ba yanzu zanyi amfani da su ba.ta ciro dubun tabata.Ashura ta amshe cike da isa,ta tafi tana cewa,lalle wannan dan raini wayon wato matarshi ya ba wa ajiyar kudi ya ce min ba shi da su?Tun daga ranan kullum tace dari biyar,ban dari biyu.ikilima bata taba cewa babu ba, zata dauka cikin kudin musa ta bata sai de tana rubutawa da lokaci da rana,da kuma nawa ta amsa.Hudu saura ya kira ikilima wai ya fasa zuwa,ta ce, too tasan zolayarshi ce da ya saba yi.Ashura kuwa da ya ce haka sai a ja tsaki ta ce,ina kaga dama ka daka dawowa ta kashe wayar ta mike ta shiga kichin inda ikilima ke ta hada hadar kammala komai kafin ya shigo,don tunda ta ji ya ce haka ya kusa shigowa garin kenan. Ashura na mitar kada ka dawo din mana,ni dai kayana na sani wallahi wanda aka kwasar mini da akwatina in ko ba a kawo mini ba za,ayi rigima.ta dau kofo tayi gidan sakina.Ikilima ta ce a ranta,yau za ta ba shi kayansa,don haka taki amfani da su.ta gama komai tayi wanka ita da yaranta ta wadata gida da turaren kamshi.hudu da kwata ya shigo suna daki ya kwankwasa ta ce khalil abbanku.da gudu suka tafi ta dauki ummita ya daga khalil ya hada su ya rungume suna dariya.Ta zare jikinta ta ce,sannu da zuwa.ya mika mata jaka ta ce, ba nan ne masaukinka ka ba, ka manta ne? ya nufi dakin ashura,khalil ya bishi.kofar ya ji a kulle,ya ce ina take?ikilima ta ce, yanzu ta shiga makota kira wayarta.nan take ya daure fuska ya ciro waya ya kira ta ke ina ki ka je na dawo ba kya nan?ta ce,too ba ka ce ka fasa ba?tsaki yaja ya kashe wayar,ikilima ta koma cikin dakinta .Ahura ta shigo ta bude daki suka shiga ciki.Ya ajiye jakarshi ya zauna,itama ta zauna kusa dashi tare da cewa,kasha hanya shi ne ka ce ka fasa?ya ce, Ashura don na ce na fasa shi ne ki ka tafi yawo,ina ki ka je?ta ce nan makota na shiga gidan sakina.Ya soma cire takalminsa,ta faki idonsa ta harari khalil da sauri yayi waje,mahmood yana ta cewa zo mana babana,tuni ya kai dakin mamanshi,ita ko sai ce ruwan khalil ya kasa sabawa da ni.ya dubi ta baki ja shi a jiki ba ne ko?yaron nan da saurin sabo.ta ce um,ta canza zancen ban gabka da kayana ba.ya dube ta.ko ruwa baki bani ba kina min zancen kaya?ta tashi ta nufi kichin ta dauko pure water leda daya ta zo ta miko mishi.takaici ya cika shi,ya mike bayan ya cire takalmin ya fita zuwa dakin ikilima yayi sallama,suka amsa tana zaune lana koya musu alifun. Ya zauna kan kujera,yunwa nake ji ita waccan ko ruwa don wulakanci bata bani ba ta soma tambayana kayanta?ikilima bata tanka ba, ta nufikichin.ta shirya masa komai gabansa nan ya manta da bacin rai ya shiga diban girki.suna hira.ya koshi dam,sauran wanka za,ayi mini taimako ne.ta ce,ai dakin amarya ka ke,ka je ta maka.ya yi dan tsaki taje bayan durowarta ta janyoakwati daya aka dinka leshin sai shadda wadda aka yi wa aiki ba a hada ba,ta dire gabanshi.ga kayanta ka bata,dama ni ba zan saka ba.ya hade rai ba na ce ki dauka ba,yaushe kika fara gardama ? ta zauna kusa dashe,ban isa na maka gardama ba baban khalil,don Allah kabata kayanta nina ci girma.Ashura ta turo kofa bako sallama,ta dube su amma de ba,a mini sati daya na da musulunci ya ba ni bako?aka zo akayi shiru a cikin daki,ke kina nuna Allah a fili daman ranki ba haka bane?Zai yi magana ikilima tasa tafin hannu ta rufe mashi baki,don ta lura ba alkhari zai fada ba.Ashura ta hango akwatinta,ta shigo da sauri.haba ashe ga inda aka kawo mini kayana,lallema mahamood kun cika isassu kai da matarka,baki dama ku ka had?ta ja kayanta tana cewa,Allah yakama ku.ikilima ta hana shi magana,sai kallonta suke yi har ta fita.ikilima ta ce,shi kenan daman nafi son ta dauki abinta. Ya ce, ita ta siya to?ta ce, da sunnanta amma ka siya.ta ce gaba ta fika gaskiya, sannan don Allah koda kaje dakinta kada ka tado da zancen pls,to wai ke so ki ke in zuba mata ido? Dubi fa yanda ta yi mana ,ita ce ya dace ta bani abinci amma bata yi hakan ba,nazo nan kuma ta biyo ni da rashin kunya.Ikilima ta ce, to kayi hakuri,in dai na isa in baka shawara in kaje dakin ta kada ka tada komai kuma laifinka ne ya zaka ce ka fasa zuwa ita kuma bata son tsokanarmu ka ke yi ba,nasan da zata shirya maka wani abu. ya ce, ba wani, kina kare ta ne kawai.wannan ya nuna min bata damu da ni ba, ke bana manta ranar farko haka nace miki na fasa zuwa san da na zo na samu komai is ready.ikilima ta ce, too mubar zancen kaima don Allah ya wuce.ya ce, shi kenan,yanzu bari naje nayi wanka da bayan isha,i sai na zo amin lissafin bashinna in biya shi ko? ta ce, too. ya ce,Allah ya miki albarka.ta ce amin.Da ya shigo dakin ashura ta baje kayan kan gado ya ce,ina son yin wanka ta ce,to ka shiga mana.ya ce, ba za,a taimaka a min ba?ta ce,, me yasa ba ayo maka a can inda aka baka abinci ba?ya ce,na ce amin an ki ne.Haushi ya kama ta shi ne ni ga marainiyar wayonku kaje ka kwanta da ita ni kuma na zo na wanke maka kazantar ko? To wallahi bazan yi ba.yayi murmushi,shi kenan.ni bari naje na wanke da kaina.ta taso da gudu ba a bayi naba.ya shiga tabishi ya kunna ruwa yana tarawa cikin baho wanka ta tsaya tana cewa,mallam zo ka fita. Ya jayo ta ya tura cikin baho shima ya shiga,nan ya mantar da ita komai.tana shafa,i da wuturi ya shigo,ya zauna ta idar tana mishi sannu cikin fara,a,ya ce a fada min bashina, ta mika mishi littafin da ta rubuta,ta ce dubu biyar da dari uku ashura ta karba,ya ce me ta yi da su?saloon tace zata nace ki bata dari biyar ta ce sai dubu na ce ta karba.Ikilima ta ce, too ni dai gashi nan.ya mike mai kikayi da dubu biya,in ji wa?ya ce, gurin ikilima. tace, bai kai ba,sau nawa ni na amshi kudi?too in ma na amsa meye dubu biyar a tunanina nafi karfin dubu dari ma a gurinka bare dubu biyar.bana harkar talauci wallahi,ai kasan gidanmu.Ya ce, to ban ce miki kuma ni mai kudi ba ne koo?kin kuma san gurin aiki na bare kice na miki karya,don haka bana son irin wannan,shi yasa kake bata ajiyar kudinka wato ni in ka bani zan kashe ko?Ya ce, ehh. ya fita. ikilima ta ce haba baban khalil,mainene zaka bita kuma har daki? baice komai ba ya dubi takardan ya ce,to ni kuma da zan tafi na amshi dubu uku,ke kuma nawa kika kashe?ta ce, wannan dai zaka bada,wanda ta amsa,wanda na kashe ko na mota bar su kawai nawa ne. bai ce kala ba, ya saka hannu aljihun ya ciro yan dari bibbiyudauri daya ya ajiye a gabanta.ki cire dubu biyar dinta kema ki cire adadin da ta dauka,sannan sauran ki cire wanda na ranta da wanda ki ka kashe. Tayi tayi ya bar shi ya ki, daga karshe ma ya tashi ya fita ma tare da cewa sai da safe,haka yaye kwana biyun shi ba wani jin dadi,tun kafun aje ko ina ya soma gane kuren shi na son mace mai tsananin wayewa.da za ya koma ya ba su dubu bibbiyu tunda komai yara da kudin mota ikilima kuma dubu uku.nan fa ta ce bata yarda ba ya zai bata dubu biyar ita dubu biyu?haka ya tafi da damuwa.Nafisa tana tsifar kai ikilima tayi sallama ,hama tana zaune tana dinkin hula,haula tana bakaican masara,duk suka amsa itama ta sauke ummita ta zauna.nafisa ta ce, uwargida sai yau?ikilima ta ce,ina fushi da yen gidan nan baba hama,ba wanda ya zo bikin mijina har ke anti nafisa.hama ta ce mai zai kawo mu cikin yara? ikilima ta kalli nafisa kuma mamarki tayi tayi ta ce ita ba zata ba.ikilima ta kalli nafida,to saboda mai?nafisa ta ce,haka nan.ke ba ki ma da hankali,in ni ce mahamood ya isa yayi aure? Ikilima ta ce, to ai lokaci ne,ba isa ba ce.haula ta ce,kuna de zaman lafiya ko?naga duk kinyi kashin wuya,ko har an soma gasa ki ne?ta ce lafiya muke,ai ya samo yariyar kirki.nafisa ta ce, kada dai kiyi saurin yabon dan kuturu,sai ya girma da yatsu. kilima ta ce, mu dai muna lafiya,kuma baban khalil yana da adalci sosai.nafisa ta tabe baki tana cewa,kar dai ki cika baki,hama ta ce to ai alamar karfi tana ga mai kiba.mahamood yasan abinda yake yi.haula ta ce Allah yasa kada ya chanza yanzu.ikilima ta ce amin.nafisa kuwa shiru tayi,don bata son a cika tadin mahmood,yanzu a fama mata ciwon sonshi.Ta dan jima sannan ta yi musu ihsani ta tafi,nafisa ta rakata ta hau machin suka rabu tana yi ma nafisa mitar to ta zo taga gidanta,ta ce zata zo.wannan satin ma dai haka ya yi shi ya kuma tafida damuwa,yana lura da irin abunda ashura ke yiwa yayanshi,yana lura da cewa ikilima ke komai na gidan,hatta abinci.ita da ya mata magana kai tsaye ta ce,ba zata iya ba sai dai ya dauko mai aiki tunda yaga gidansu,kuma yasan bata gaji wahala ba.shi kuma ya ce ba zai dauko ba.tun kafun ya tafi yake ma ikilima in ya dawo gurinta zai sauka,ita kuma ta ce a a sauran kwana daya ya gama yiwa amarya satinta,sannan ma ita ai ta kara mishi kwanakin.ya ce shi fa baya so.too ranan alhamis ma kiranta ya yi da dare ya ce gobe ina hanya ina son tarba sosai fa.ta ce,too ka gaya mata ko sako nein fada mata?ya ce wai wa?ta ce amarya.ya ce ke ni fa na gaji gaskiya ki tambaye malamanku ban amince da wannan fatawar ba, ace bana gari sai sati zuwa sati biyu nake zuwa amma ko yaushe dakin amarya zan sauka har sai nayi kwana bakwai?vels BOOK MABUDIN WAHALA 3**9 Ta ce, ehh,haka ne kaima ka tambaya.to wai kai menene matsalar kai da ke da sabon inbox? yaja tsaki mata da yawa suna zaton kwanciya da su ne kawai abin da muke bukata?ikilima ta ce,to da mai kuke bukata bayan wannan?ya ce,irin kulawar da kike bani.sai da kulawa sannan sha,awa take zuwa.too yanzu kai menene damuwar ka?ta tambaye shi?bana samu kulawa gurin ashura ,sai ta kwanciya.ta ce,too zan baka sauran kulawar,ka ci gaba da kwana da ita har zuwa lokacin da zaka ji a ranka cewa ikilima ta bani gudumawa.ya ce, na gode.kafin ya iso tayi duk shirin da ya dace ta gyara gida.ta samu ashuracikin dakinta,zaune take tsakiyar gadonta wanda ke hargitse da kayan da ta cire,da kuma kayan shafa kuma ta ce gurinki na zo.ashura na ci gaba da yin 2go dinta ta na cewa ina jinki.ikilima ta ce,shawara zan baki akanmaigidanmu,kin san shi namiji kullum tamkar yaro yake,dan son kula ne.Ta hada rai tare da daga mata hannu,shi ne ya ce miki bana kula dashi?ikilima ta ce, a a nasan kina yi,nufina ki kara.ina son ne na fada miki abubuwan da yake so da wandada ba ya so,don ki kiyaye.Ta aje wayar hanunnuta,malama ban son salo kece za ki gaya mini abinda yake so ko shi ne zai fada min?ikilima ta ce,da za ki daure ki saurareni da kin kar..........ashura ta katse ta don Allah fita malama,bazan saurare kiba.kada kiga kina da yara ki raina ni,ba kin girmai ni bane nima da ace ban tsaya karatu ba da nayi uku ma ba biyu ba.sannan kiyi kadan ki hada kanki dani a wayewa.ikilima ta ce,kada kiyi girman kai,yana daya daga cikin tushen zunubi ki saurareni.tsaki ashura ta ja.ke na ce ki fita ,bana son shisshigi don Allah.ikilima tace shike nan tafita. Ta ciji yatsa,lalle wannan na lura so take ta raina min wayo,itace ma zata koya mini zama da miji?jahila irin ta,a gurin wadda ko secondery bata gama ba. ita kuwa ikilima ta zauna a dakinta tana jin zafin yanda ashura ta ki sauraronta.lokacin da ya iso ya samu ashura zaune inda ikilima ta barta tana aikin 2gota ajiye wayae tana mishi sannu ,ya dubi koina na dakin a hargitse.ya ajiye jakarshi ya fita.Dakin ikilima ya shiga,suka mishi oyoyo ita da yara.ya shiga wanka,kafin ya fiti ta tanadar mishi komai da tasan zaya yi amfani dashi.ta taimaka mishi gurin shafa mai da kaya,sannan ta shirya mishi abinci suna ci suna hira.farin ciki a ranshi kamar me,sai da suka gama ya ce,madam albishirinki?ta ce, goro.ya ce,bana son goro,sai dai in za ki min iri jus din shinkafa da kika min wacan satin.ta ce zan maka.ya ce,an maido ni abuja wannan satin.tace kai amma nayi murna.ya ciri kudi daga aljihunshi kayan dakinki da kayan sawan wanne zan fara sai miki?kin san alkawari ne bashi ne a kaina.ta ce, a a ni dai ka bari su nan gaba ya ce, a a yanzu zan biya.ta ce,tooduk wanda kafara don ta sanshiin zata shekara rokonshi ba zai yarda ba,don ta ce ya abr shi ba zai bashi ba.ya ce,shi kenan,gobe za muje kasuwa.ta ce Allah ya kai mu.da ya koma dakin amarya ta hada rai har da kuka.ya ce ba kya iya kula da ni dole naje in da za,a kula dani.ta ce,tunda nazo gidan nan ka taba nemana naki? Ya ce, ba a nan matsalar take ba.kada ki dauki damuwata kawai na kwanta da ke ne a a ,wannan ya yakan fita kaina amma ba kulawa.ki dubi yanda ikilima ke tatalina,ko ta fanni abinci ita ke min wanka, ke ni fa ban san yanda ake cie takalmi ba sai da na fara zuwa kaduna.Amma ke ko yaushe kina nade a gado,ko kina makota.ta ce,daman ina so in fada maka, ka samo min yar aiki wahala bazan iya duk wannan ba.yaya ma batun aiki na?ya ce,yana nan,hajjiya kuma ta mini magana.Akwa fin bankaina ga kila litinin su neme ki.amma gaskiya ki chanza hali.Ta ce,too da suka zo kwanciya,ya ce, ta gyara shimfidar gadon sai ta ce a a suje dakin shi tunda ta zo gidan ba su taba kwana ciki ba.ya ce, a a sai randa ya zuba kayan shi tukunna nata kwashe wa za,ayi.ta kuma jin haushi.Washegar i kuwa suka gardama da ikilima, ya ce ba ya son karin tun da yayi satin shi kenan,ita kuma ta ce a a,har yayi fushi ya fita kofar gidan.ta ciro wayarta ta yi ta kiran shi yana kofar gida amma ya ki daga wayar,tunda ya lura ita ce.Ta rubuta mishi text tana bashi hakuri,sannan ya dawo.ta tsuguna gabanshi tana cewa,ya yafe mata bata yi ba ne don ta bata mishi rai,ya ce ya sani.kuma shi ya yafe mata tun kafun ta roke shi.can nisan dare tana bacci shi kuma tunani yake,ikilima ce yake gamsuwa da ita,ashura kam tun da yake kwanciya da ita kara mishi kwadayi take,ko zai kwanta sau uku da ita cikin dare baya jin nutsuwa,ko haka mata suke?kasa daurewa yayi.Da safe suna kari ya chanza maganar shi zuwa turanci don kada khalil su ji,ya ce wai mata daban daban ne?Ikilima ta ce mai yafaru? ya ce,baya gajiya da ashura,don bai samun nutsuwa ita kuma yau ya samu nutsuwa da ita.amma bai yawan kwadayinta. Da sauri ta rufe mishi baki,ta ce,ba kyua ga baban khalil,ba kyua ka tona sirrin matarka.ya ce, too ai ba wani gurin naje na fada ba,kema don naga mun zama jini da hanta ne.ta ce, duk da haka ba kyua.shi yasa ake cewa ku ke hada gidanku a yi ta rigima.nata kowacce da kalarta,sirrinka ne ka bar ma cikinka.ya ce, shi kenan.sun je kasuwa ya darzo mata atamfofi da lesuka da shadda,har da yara,ya ce, sauran gyaran daki.An maido shi abuja,matsala daya ikilima ke fuskanta yanzu,ya fi son kwanciya da ashura kuma wani lokacin yana nuna mata hakan karara.Da farko har zata dau fushi sai kuma taga ya dace ta nemi shawara.Tuni har ashura ta samu aiki kuma tasa shi ya samo musu mai aiki don itama yanzu bata zama.haka nan yana jin maganarta,jininsu ya hadu da luba,luba na kawo mata shawara,don haka itama sai ta nemi luba shawara.Don yanzu sai yazo dakinta ya bar dakinta bai nuna sha,awarta ba.luba ta ce,duk yanda akaye tana amfani da kayan mata.ikilima ta ce,mai ke nan?nan fa luba ta rike baki tana mamaki dama akwa matan da basu san gyaran jiki ba? Ikilima ta ce, gani.luba tace, tafdi!to ke ko lokacin bikinki ba a miki ba ne?ta ce,wallahi ni bikina da ba shiri?koda shirin ma wa zai mini? nasan ana fada.Da an ci gaba ma wata rana sai ya nemi ki bar gidan.luba ta ce zo muje ki gani. Ta bude wata durowa ta soma fito da rabobo tana mata bayaninsu.ikilima ta ce ba sa cutarwa?kin san da addinmu bai yarda mu sha abin da zai cutar damu ba.Luba tace ni nake hada kaya na da kaina,duk abubuwan mu ne fa su aya su dabino,su cukui su ayu,furen zogale da sauransu.Ta kuma janta gaban wani fridge duk kayan itatuwa ne dangin kankana,lemon zaki,rake,da sauransu.ta ce amma zo mu fara tanan.suka shiga bed room ta janyo galan ta ciko ta tsumi,sha wannan.ta amsa ta shanye.ta ce, ke luba,na tuna da dandanon abin nan,mamanshi ta taba bani lokacin da muka je ina amarya.luba tayi dariya ta ce shanye duka.ko yaushe zaki dinga zuwa kina sha kafin ya dawo.ta ce,wannan satin guri ashura yake ma.luba tace,za mu samu damar yin aikinmu da kyua kenan.cikin satin ikilina ta nace ma gidan luba,har ta shida mata luba kayan da ya siyo mata.Luba ta ce,mijinki na kula wayayye ne,yana son gayu shi ne dalilin shi na auro wannan kodaddiyar,ki kawo na ba telana ya fito mini da ke sannan dole na hada miki sabulun don gyaran jiki kuma mu shiga kasuwa a siyo mai.ikilima ta ce,ba na son bilicin fa.luba ta ce to nu dubi fatata,nima bilincin din nake yi?gyaran fata kawai,ke har fa kananna kaya zamu siyo.ikilima ta ce kai luba,sai na tambayo malamai na sun tabbatar min da cewa ba haramun.Ta ko tambaye malam kabir ya tabbatar mata cewa shi ne ma tsari,tayiduk kwalliyar da take sodon ta birge mijinta,ta canza hallitarta daga baka zuwa fara,shi ne aibu.amma don ta shafa wanda zata yi laushi ko tayi kyua ba matsala.Ta ce, to kaya fa?mallam ya ce duk nau,i kayan da kike so ko mijinki ke so kya iya sawa,in dai gidanku ku kadai ne.Nan fa ikilima ta kwaso dinkunanta ta kawo ma luba.waya tayi aka kawo mata mai dinki har gida don su zabi wanda zai dace da ikilima,duk da ba gurin ikilima yake ba sai da ya kasa daure kyan da tayi.Ranar ta saka daya daga cikin lasunan da ya siyo mata,an dinka shi riga da siket tamkar a jikinta aka dinka su.ya ce,kanwata kin yi kyua,ke ce kuwa? Kodai ummita ta samu kanine?tace a'a bana sallah ma ni yanzun,yace waya miki dinkin nan gaskiya kinyi kyau,tace to na gode,telan luba ne yace gara da bai miki riga da zani ba. Kafin wani satin ta kara tsumuwa tare da gogewa da darussan da luba ke koya mata ga girki iri-iri ita kam bata ce da luba kome sai godiya. Ranar da xai dawo bayan kitso har da lalle luba tasa a xuba mata sai kace amarya tayi masa girki da kalolin jiice ta gyara gidan ta wadata shi da kamshi. Lokacin da ta tabbatar ya kusa isowa ta shirya cikin wani riga da wando yan kanti da lubar ta amshi kudi ta siyo mata su kala kala dama musa yaxo ya tafi da khalil,ta kwanta kan kujera tana kallon tashar ikra'a ya turo kofa.... Sai ta samu kanta da jin kunyar mikewa dan bata saba ba. Shi kuwa sakin jaka yayi yana kallonta,yace come on taso kizo na ganki kanwata ce kuwa?ta mike yace wow dama haka kike shine kike boye min hakkina?ta rufe face. Rigar da wandon sun bi jikinta dam sun fitar da surarta ya mannata jikin shi yana shakar kamshinta,ta zame tare da cewa ina zuwa. Ya zauna idanunshi dai suna kanta ta zura hijabi yace ya haka kuma?tace kicin zanje ina zuwa ta shirya kome a gabanshi yace don Allah cire hijabin nan. Ta cire yace ina kika sai kayan nan?tace gidan luba,yace da wasu kalolon in sai miki dan duk lokacin da zanzo su nake bukata ki saka min. Tace sai dai ka sai mana mu 2 yace keda wa?tace da amarya. Yace ai kece amaryar dubi lallen nan naki duk gidan luban kika yi shi?tace eh,yace kai kin dace da makociya Allah yayi mata sakayya ta alkhairi,nayi murna da abotar ku,tayi dariya. Kafin ya dawo sallah tayi sabon wanka da sabon ado na kayan bacci ,masu shegen kyau kalar jan ra'ayi yace kai yau dai kanwata ba sauki duk kin rudani. Ya dauki Ummita dake bacci kan gadon ya gyara mata kwanciya kan kujera tare da cewa gobe kayankii xanje in siyo wadannan a kai su dakin yara su fara kwana can. Tace ya ka dauke min yarinya?yace sakona na yau bashi da sauki bata kara magana ba. Lallai shi da ita duk sunga canji. Ya rasa inda zai sata yace tasha wani abu ne? tace a'a menene?yace akan kome yaga canji tace ita dama haka takenuna misi tayi shine dai ya shiga rudu. Har da safe yaki barinta sukuni,tana kicin shima yana manne da ita,ranar ya hana ta xuwa islamiyya wai shi dai ta zauna gida yayi ta kallonta. Tace baban khalil nice fa,baka sanni bane?yace iklima kin canja inda haka kike yi min baxanji sha'awar kara aure ba. Tace a'a dole kayi auren so donni auran mu kusan na dole ne xance ko na biyayya don haka dama ni ina sa ran xaka iya yin aure duk lokacin da kaga wadda kake so. Tana xaune gaban madubi take maganar shi kuma yana bakin gado,zuru yayi yana kallon ta ya hade fuska, iklima don Allah fada min me xanyi ki yarda ina sonki?wlh ina sonki sai daga baya na gane ke nake so ba Nfsa ba. Ita Nfsa sona kawai take ni ina sonki don ko lokacin kullum dake nake bata misali ince ta dinga koyi dake. Iklima tace ba ita ba, Ashura ba sonta kake ba? Yace sonta nike tace to nufina kenan so daya tak yake,yace to ke nake mashi tayi dan murmushi ban yarda nasan dai kana daraja ni. Yace wlh sonki nake kece ma nanaga tamkar ba kya sona. Ta dube shi me yasa kace haka? Yace dubi fa aure nayi amma ko a jikinki tace ka jika to don ina sonka xakayi aure sai nayi ta hauka ko me?abbinda na sani ina sonka so na hakika kuma ina tayaka son abinda kake so matsawar bai kauce shari'a ba. Yace nima ina sonki ta marairaice ina son kullum da safe kace kana sona ya iso gurinta tare da dago kanta in na miki hakan zaki gamsu ina sonki?ta lumshe ido sannan ta daga kai alamun eh. Yace to xan fara daga yanzun,iklima ta ware idanunta manya tana kallon shi cikin idon shi,ina sonki ya subaci kuncinta sannan ya rungume ta. Shi da musa suka shiga kasuwa ya xabo mata gado da kujeru ya siyo tafkeken TV ya saka musu a babban falo. Nan fa ashura tace sam bata yarda ba an cuce ta,ya xa ace ya canza mata kome?yace alkawari ya cika amma sam taki yarda har ya tafi suna tsiya. Haka suka cigaba da zama iklima tana koyan abubuwa a gurin luba,dabarun jan ra'ayin miji cikin sa'a ko yaushe ya dan samu dama xai kirata a waya yana fada mata I Love You,in ko yazo a ranar girkinta yana nuna mata so tamkar ya cinyeta. Ita kuwa duk abinda ta san xaya birgeshi yanzun shi ne aikinta haka kuma kara2nsu ya dau xafi dole ta bar koyarwa dan yanxu lamura sun mata yawa.K MABUDIN WAHALA 3**10 Cikin haka Ashura ta samu ciki nan fa suka soma tsiya tace sai ta cire yace bai yarda ba. Tsiya tayi tsiya har sai da ya 2ra ta gdansu hajiyanta ta goyi bayanta da cewa ciki xai hanata aikinta kuma yasan aikin yanda yake don haka dole su cire ciki shi dai yace bai yarda ba. Kawayenta suka kara xuga ta da cewa kada ta yarda ta haihu yanxun taje ta tsufa a banxa ta bari ta ci xamaninta,taje ta cire cikin yace xai sake ta iklima tayi ta rokon shi a karshe taje ta hada shi da su Hajiya Uwa, Baban shi naji yace kul ya fara 2nda wayayya yake so gata nan,dole ya maido da ita suka cigaba da xama haka. *** Nafisa gurin shan magani suka hadu da wani Mustapha irin samarin nan masu leke leke yaje ya jangwalo ciwon suka daidaita kansu nan ya 2ro mahaifanshi aka sa lokaci. Likitoci sun basu shawarwarin da suka dace har xuwa lokacin da xasu haihu kuma sunce xasu iya samun yara marasa ciwon in dai sunbi dokokin,mustapha iyayan shi sunji dadi. Baban shi dan kasuwa ne a babbar kasuwar Minna shi ma nan yake taba yan harkokin shi mahaifin ya basu gida dan madaidaici aka gyara shi in anyi biki su xauna. Mahmood yayi murna lokacin da iklima ta sanar dashi yace Allah yasa ina gari xa'ayi bikin domin bankin mu sun 2ra ni lagos tare da karin girma. Lallai mahmood likafa tayi gaba don kuwa 2n da ya koma lagos suka warke sai dai baya xuwa kowanne sati duk lokacin da ya ya samu dama xaixo in kwana2 ne kowa dai dai in kwana daya ne kuma sai ya kwana gurin daya yace in ya dawo xai sauka gurin daya. Yaana son tafiya da iklima kara2nta Ashura kuma aiki,da kaga mahmud xaka san lallai ya samu sukuni. Yayi yar kiba da dan tunbi fatar nan shar ta goge ya sai mota ya sa Musa ya koya ma Iklima saboda khalil ya shiga makaranta ga makarantar ta. Nan ma Ashura ta tada balli itama yace ya koya mata kafin wani lokaci sun iya. Amma dan gudun rigima ya dauki driver yace ya dinga kaisu. Anyi bikin su Nfsa mahmood baya gari amma ya 2ro da kudi masu dama iklima ta sai mata kayan daki kuma duk zirga zirgar da akayi iklima ce ke dawaiyniya da motarsu. Hakan ya kona ran Ashura take ganin kamar gadara iklima keyi da mota. Ita ko ganin sati da lahdi ne Ashura bata da aiki shi yasa bata dawo da motar gida ba,take barin ta gidan Mahaifin shi,an tashi biki lafiya. Iklima tana kwance a dakin shi dan 2ni yasa Ashura ta kwashe kayanta tasa a dakin yara maxa dake kusa da dakinta sai tayi fushi ta saida su ya shirya dakin sosai tare da xuba kayan alatu. Haka babban falon suda

Chapter 19 of 20