Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
Tana kudundune kan gado sam bata son su hada ido sbd wata matsananciyar kunya, ga surutn daya dinga yi tana tuno su. Yaxo ya xauna bakin gado "tashi kije kiyi wanka kanwata" ta tashi tana nade jiknta da zanin gadon, sai dai kanta na duke data mike kuwa hannu tasa ta kare fuskarta dashi. Shi kam daria yayi mata ynda ta cukwi-cukwiye jiknta da zanin gado. Tana zaune cikin baho tana tuna abubuwn da suka faru, ynxun nan. Shikenan ynxu ta xama mace sosai, haka nan batayi bakinciki ko jin haushn abnda mahmud din yai mata ba, sai ma take ganin ynxun zaifi bata daraja da kulawa. Ta leko ta gefen kofa ta hange shi kwnce rigingine kan gado, idanunshi suna kallon silin, yana sanye da boxer. Tunani yakeyi na abinda ya faru ynxunnan, kai gskia auren sunna yayi, ya kamata duk musulmi ya gode ma Allah, ynxu da zina ne memakon farinciki sai bakinciki da dinbin zunubi. Sannan dk wnda ya aikata zina boyewa yake kar a ganshi, in km ciki abokiar zinar ta samu shikenan ta shiga gararin ryw, danginta su ki ta shi kanshi saurayin yace banashi bane danginshi ma suce anyiwa dansu sharri. Dan ma in an haifa kila a yar, inya girma yaji cewa shi dan tsintuwa ne bakinciki yasa shi gararin ryw, in ma ta rike shi inya girma wataran dole yace ina dangin babana? In bata nuna mishi ba ya tsaneta. Kai akwai wanda ya shake uwarsa kan cewa sai ta nuna mishi ko hoton babansa ne. Muryarta ce ta katse shi da cewa "dan miko min zanina yaya. Firgigit! Ya kalli gurin bayin, yace me kikace kanwata? Tace zani zaka bani cikin shagwaba tai maganar, ya kwaikayi muryarta tare da cewa to yar kanwata, amaryata" ya dauki zani akan akwatinta ya mika mata, ya dora mata kan hannunta sannan ya sumbaci hannun. Da sauri taja hannun ciki tare da cewa "yaya bana so" yace sako ne shima wannan din na baki kanwata" ta daura zani ta fita ta rufa da tawul dinsu na wanka, zanin gadon ta saka cikin robar wanki, idonta rufe da tawul din ta fito. Yana tayi mata daria game da tsokanarta cewa bari ruwan saman ya tsaya inje in fada ma baba in ce...." ta katse shi da sauri "kace me? Tare da cire tawul din dg fuskarta. Yace "yee! Naga fuskarta me cewa yaya kayi hkri zan tsaya" ta sake rufe fuskarta dn ta gane wayo ya mata, zolayarta ma yakeyi. Daya fito ya samu ta saka kaya ta dan saci kalln shi tana dan murmushi yace kanwata amarya bari inxo in hada mana tea dole yau na nemo miki kazarki dakika ki ci ranar daren amarci. "tagumi tayi tana mamakin shi sam bata yi zaton yn mgn ba da lkcn da yake zuwa gurin anty nafisa, kai ko ynxun da akayi musu aure bata zaci cewa yana daria ba. Shine ya hada musu tea tace ita b ynxu ba, ya dinga tarairayarta hatta da gyaran daki shine yayi ranar ta dinga mamaki dama maxa abnda suka fi so kenan ko me? Sai kusan biyu ruwa ya tsagaita, dama shine ya musu limanci sukayi sallar azahar. Da ze fita yace kanwata kada kiyi girkin komai ki huta kiyi bcci zanje shago. Me zaki ci in shigo miki dashi? Ta dube shi "ka dawo lfy yaya ni bana son komai. Ya matso ya dago kanta ya sumbaci goshinta, idanunta a lumshe sannan ya fita cikin farinciki da annashuwa, wnda ada yafi xaton samun hk dg nafisa. Allah knan me juya lamarinshi ynda yaso, ita kuwa cak ta mike ta kwnta kan gado tare da rungume pillow. Yanayin yai mata dadi, Allah yasa su dore cikin farin ciki tare da duk wasu ma'aurata musulmai. Nafisa wadda ke ta kai-kawo cikin dakinta, zuwa yau ta soma tunanin ko kudi zasuyi maganin komai to bazasu iya yin na so ba, ga kudin ta soma jukuwa amma sun kasa mantar da ita son mahmud, dama shi wayayyene data jawo shi jikinta ta sakar masa kudi suci gajiyar soyayyarsu. To ko zata gwada xuwa minna ne? Ta sani ma ba son ikilima yakeyi ba, abnda ma ko dama ba shiri suke wani yi ba, km ynda ta san shi miskili km tasan irin abubuwan dayake so tasan matar dayake so ba xai kula ikilima ba dn bata dace dashi ba. Ranar hk ta kwana zullumi ko alhji jamilu zai brta yau sati 3 da biki? Sannan inya brta mahmud ze yrda km ze amince suyi soyayyarsu cikin jin dadi? Wata xuciar tace da kamr wuya. Ta kira shi yau kwananshi 4 wai suna south africa, tace tana son xuwa minna ne ta duba mamanta, in ze bari. Sai da yayi yar daria sannan yace "nafisa kin kasa fahimtata, ni mu2m ne wnda yasan yancin dan adam, kada ki damu dk inda zaki kije inda kike so a lkcin da kikeso, kiyi abnda kike so, kici abnda ranki yaso, ba matsi. In ina son mgn dake xan kiraki ba sai kirani ba. Ynxu xaki iya jan motar ko da direba zaki? Tace xan gwada xuwa in gani ko xan gane? Yace tukin nake tunani, kada ki gaji. Tace xan iya. Yace shikenan, xan sa a tura miki kudi sai ki musu tsaraba. Tace "to na gode. Yace ki rufe tsakanin mu kada ki yrda kiba wata kawa ko mahaifiyarki lbrin cewar ni ba namiji bane. Tace kada ka damu ba me ji. Yace "Good, zakiji alart in kudin sun shigo, sai na dawo. Tace, to. Bata samu wata matsala ba dg abuja xuwa minna sbd motocin gaske ne. A gjy ta isa gidan mamansu. Ta samesu suna ta hira da shewa ita da kawayenta, nan fa suka shiga murna ga hajia nafisa ga hajia nafisa, sai cewa suke dubi ynda tayi bul-bul, jiki lumi sai dai tayi rama. Hajia baba tace kun san maxannan ba dama, a sa samu yarinya bare wannan yar kare ta diddirki kayan mata ba dole ne ya makale mata ba? Kin ko san wannan harkar tana sa rama. Sauran suka ce, haka ne. Waya sani ma ko ynxun da ciki? Nafisa dai sai dan yake takeyi. Haule tace anya da cikin nan kuwa? Wata tace kin san yayan zamani ba kowane yake son ciki da wuri ba. Ita dai jaka ta balle ta shiga rabar musu da kudi. Can gurin karfe 1 tace bari taje gdan kawayenta dk da ba yau xata koma ba. Gidan safina ta soma xuwa, suka rungume juna da murna. Nafisa tace ina ta xuba idon ganinki shiru? Safina tace ke dai xauna in kawo miki abin sha, sannan musha lbri. Suna cin dambun nama da hollandia suna ta lbri. Nafisa tace kawata alhji sanin ya gane kurensa ne ynxun ko? Safina ta dafa nafisa tare da cewa wannan dan iskan mutumin ne ze daina halinsa? Nafi tace hkri kike yi kenan kiyi xaman kudinshi? Tace kudi fa kika ce? Ta yatsina mouth, ai karamin me kudi ne wannan ba irin naki ba, dama kudin nasa dk a wajene. Tnda ya bani na amarci ya daina. Mafita na samo ma kaina, mama zee ma ynxun da hk ta amshi shawarata asirinmu a rufe . Nafisa tace to nima ku fadan shawarar ko zata amfane ni? Safina tace, ke ni kin wuce nan, mu dan mu samu kudi muke yi, ke ko kina da kudi. Nafisa tace fada min. Safina tace alhazai muke bi. Nafisa tace a'uxubillah! Safina da auranku fa! Safina tace da auren fa! Mata dubu nawa ne masu auren suke km bin mazan? Kudi ba karya bane, ke kin samu ne shi yasa. Nafisa tacn to maxanku sun sani? Safina ta ce dube ki da wani sabo, ya za'ayi mu bari su sani? Iyaka da sun fita mu ma mu fice. Wancan satin har abujanku, ya min karya yai tfy aka ce min yana nan wani hotel da karuwai, ni km wani dan majalisa ya daukeni mukayi abuja, dubu dari ya bani gobe ma ze dau mama zee". Nafisa tace wnda ya daukeki din ne km ze dau mama zee? Tace eh, ina ruwana mijinane? Wata kwngila ce ya bni kawata, wai in samo mishi matan aure 40, dk guda daya ze bata dari, ni km yan dubu hamsin. Nafi tace meyasa yake son matan aure km har adadin arba'in? Safina tace, Oho mishi, kila wani asirin ne dn najh yace in ya gama da arba'in din xan samo masa kananan yara yan sha daya. Nafi tace "Innalillahi! Don Allah kada ki cuci yara. Safina tace ke ni fa kudi!! Ba karya a cikin kudi. Shegia kema ai kudin kika gani. Nafisa tace "um ni naga kudi! Amma zuwa ynxun sun soma fita kaina, dk da bn jike sharkaf ba. Ta tsura ma safina ido, ta ce wlhy kawata ina cikin wani hali, son mahmud tamkar ynxun na soma kllm cikin tsananin begensa nake kwana. Safina tace "gashi ya auri kanwarki, ya knan? Nafi idanunta suka soma kawo hawaye, cikin shesshekar kukan take cewa, ko yaushe tunanina kenan, km dalilin zuwana minna kenan ynxun. Safina tace don Allah ki haka rami ki binne son mahmud, ga mijinki me kudi, mai kyau dashi, me mahmud zaya miki wnda alhji jamilu be miki ba? Nafi tace akwai, safina mijina ba namiji bane, ina nufin baya iya komai dani. Ya aureni ne kawai dn ya kare kansa daga suru2n yan siyasa. Safina ta saki baki tana kallon nafisa sannan ta girgiza kai tare da cewa "tirkashi! Gaki da rashin hkri ina nufin kina cikin mata masu sha'awa. Nafisa tace ashe kin gano kawata, kina ganin rayuwa zata yiwu a haka? Safina tace ina fa! To ke ki kaso auren mana? Nafisa tace yace sai na xube masa kudinsa, ina xan samo su? Ni da xuwa nayi mu jone da mahmud ba tare da ikilima ta gane ba, kin san fa shi bagidaje ne. Safina tace "shegia nace muna bin alhazan zakiyi min salo, kice kema irin harkarmu ce ta kawo ki? Nafisa tace da bambanci, nifa matsala gareni. Safina tace kawata bb wata kwaskwarima da xakiyi, zunubin mu 1, bambancin kina bada kudi ne dn aikata laifin mu km mu ake ba. Nafi tayi shiru, can tace "zunubin ne in na tuna sai naji gara in hkra. Safina tace kin yi lkcn da kina gida, dn hk gara ki cashe kawata, a laifukan dunia me kika yi ma? In yaso daga baya se ki tuba, ke da kike da kudi ma sai ki ta yin alkhairi dn ki fanshe laifinki. WA'IYAZU BILLAH! Safina da nafisa kuna nufin zakuyiwa Allah wayo ne? Hakika matan aure da dama suna cikn wannan halakar. Nafisa tace haka zanyi km kin san Allah safina, zo kije abuja ki soma ganin masifu iri-iri, mata da dama suna cikin irin wanan harkar. Ga masu madigo, ga masu ludu, safina tace to nima kwanaki wani dubu dari biyu ya bani wai in samo masa namiji dan shekara 14 naki, nafi tace na shiga 3! Mutane na tsoron kwncyr kabari kuwa? Safina tace mu br xancen tnda kin soma kiran kabari, mu ma masu lefi ne ynxu dai tashi muje gurin mahmud masoyinki, tn kafin jikinki yai sanyi kice kin fasa, gashi za'ayi gwarzon namiji shine ma ze iya da fitinarki. Ita ke jan motar har suka shigo layin, safina ta dubeta gidanshi zamu? Nafi ta sakar mata harara. Ba can zamu ba, me zanje nayi? Kin san Allah safina, dk da nasan ba sonta yake ba gani nake da mun hadu da ita shake wuyanta zanyi sai ta mutu. Safina tace ina ruwanki da ita, nasan dai ba kulata ze yi ba tnda ance ranar bikin ma fuskrshi dk a daure. Lkcn da suka tsaya a kofar shagonshi sam be lura bama, shi yana ta harkoki da abokan ciniki masu siyan siga, madara da sauransu Cikin takun kasaita suka nufo shagon, kmr ance dago sukayi ido 4 da nafisa tana sanye da riga da skirt na wani tsadaddan material tmkr kayan su fasa jikinta don matsewa. Dan siririn gyale ta yafa a kafadarta. Tai kyau jikinta luwai-luwai, hutu ya soma ratsawa. Nan take mahmud ya daure fuska dama gashi gwanin dakewa, sannan ya kauda kai tare da cgb da harkar gabanshi. Nafisa suka kalli juna, safina tace salamu alaikum" be tanka musu ba. Nafi tace mahmud gurinka mukazo, har sallama gashi munyi maka amma kayi mana bnxa. Ya dube su rai bace yace "A'uzu billahi minassh shaidanin rajim. Me kuke nema anan? Nafi tace ynxu mahmud sbd mu kake ta'awizi kmr kaga shedanu? Yace kunfi shaidan shedanci da shu'umanci, dole in nemi tsari daga sharrinku. Miyan bakin nafi ya kafe, tai ajjiyar zucia sannan cikin in...ina tace kayi hkri na sani nayi maka lefi, ina fatan komai ya wuce. Be tnka ba, tace don girman Allah in ci albrkacin soyayyarmu. Ya sake dubanta cikin harara yace sai dai don Allah da kika ce da kuma albrkacin ikilma bare bn ma shirya yafe miki ba sai ranar da mahaifinki ya yafe miki. Kiyi gaggawan barin na gurin. Ta soma hawaye, ni kake kora? Yace na kore, ki br nan na tsaneki. Safina zatai magana yace ban son jin komai, ku br nan kawai. Safina taja nafisa tana kuka rurus suka shiga mota. Safina tana bata baki tare da cewa tuka muzo gidana mu canza shawara ta ina xamu bullo mishi ***Shi kuwa takaicinsa daya ta zo ta tada mishi da gyanbon sonta,alhali shi ko iklima ta mutu ne ba zai aure ta ba. Ranshi yana zafi ya rufe kofar shagon duk da cewa ga 'yan siyayya nan tsaitsaye ya nufi gida suna kallonshi.iklima tana cikin nika kayan miya zata dora abinci ya shigo,ta dube shi tare da cewa "sannu da zuwa" umhum kawai yace ya nufi ciki ta bishi da kallo don hakan bata taba faruwa a tsakaninsu. Ta mike tare da ajiye injin nikan ta bishi.yayi rigingine kan gado,kafafunshi suna kasa ya dora pillow kan fuskarshi.tasa hannu zata zare pillow'n tare da cewa yayan...tsawa ya daka mata."Ke da Allah can kada ki dame ni" taja baya da sauri tare da razana. Ta daure ta sake cewa kayi hakuri dama ina son in ce baka da lafiya ne? Yace asibiti ne ni? Ta zaro ido tana kallonshi sai ta fita jiki babu kwari idanu suna kawo hawaye. Taci gaba da aikinta.Maman Ummi matar gidansu tazo tace "amarya ga wukarki" tayi saurin kakaro fara'a tace "to maman ummi,ta amsa tana share hawaye tare da cewa "albasar nan tana da zafi" maman ummi tace nima yanzun na gama fama da tawa. Ta gama dora komai amma ta kasa shiga dakin don tsoro. Kusan minti talatin sannan ya shiga bayi ya sakar ma kanshi shawa.Yana tsaye kusan 4mins ruwa na sauka a jikinshi sannan yasa sabulu sama- sama ya fito ya canza kaya,zata shigo daki zai fito da sauri ta koma gefe tare da firgita tamkar ta ga abin tsoro har tana bigewa. Bai ko kalli inda take ba ya fita.ta sauke ajiyar zuciya sannan ta shiga ciki ta zauna a falo tare da cewa "Ya salam,me yake shirin faruwa dani ne?Allah kada kasa shaidan yaci galaba tsakaninmu. . Shi kuwa yana fita gidansu suleiman ya nufa,ya ko same su har da mukhtar. Suna ganinshi suka ce "angon nan yaya ne yau?" Bai tanka su ba,sai da ya zauna sannan yace hum Allah ya isa tsakanina da nafisa. Suka hada baki gurin cewa,"wace Nafisa?" Yace,in nace muku Nafisa kun san wadda nake nufi. Nan ya zayyane musu duk yanda suka yi,ya kara da cewa,shi yasa naji iklima ma haishi take bani. Mukhtar yace, ita wannan 'yar aljannar ina ruwanta? Mahmud yaja tsaki tare da cewa,Gaskiya mata ba su da kunya,ba su santa ba ma. In ba haka ba dubi cin amana gami da cin zarafin da ta min,amma har ta iya zuwa inda nake. A tunanina nan gaba sai ta shekara goma bata iya hada ido dani ba. Suleiman yace,to kunya gare ta ne? Kai dai ghara daka yi mata haka.Amma matarka kada kasa ta cikin matsala. Mukhtar yace,gashi har kayi kyau,zamanku ne ya sani sha'awar yin aure,Suleiman yace ko ni wallahi. Nan suka yi ta ba shi shawara har zuciyarshi ta sauka,ya kuma bayyana musu abinda yayi mata tare da cewa yasan yanzun tana can cikin damuwa. Suka ce "don Allah yaje ya kwantar mata da hankali. Yace,su zo suje tare su ci abinci. Nan suka nufi gidan lokacin ta gama abincin amma ta kasa ci taje toilet ta watsa wanka ta fito. Gama sa kayanta kenan suka yi sallama. Cikin sanyin murya ta amsa,duk suka zauna falo har da shi. Ta fito cikin tsoro daga ka ganta kasan a firgice take,fuskarshi ta soma kallo har yanzun tana daure da sauri ta kauda kai tare da gaida su mukhtar. Mahmud yace "ki ka ...." Maganarshi ta katse yanda yaga tayi wata razana har ma abin ya bashi dariya.Amma sai ya dake. Ita kuma maganar ce ta ji ta a sama dama wanda ke a tsorace haka ne. Ya dube ta abinci nace da sauri tayi kicin.Suleiman yace,kai dai mugu ne,duk yanda akayi dukan yarinyar nan kayi. Mukhtar yace,tunda muka shigo duk a gigice nake ganinta. Yace,dukan lafiya?wlh ko zagi. Ta shirya musu abinci da komai ta koma daki ta cire hijabin ta hau gado har suka gama suka fice,tazo ta gyara komai. Da dare dama baya dawowa da wuri,sai gurin sha daya ko sha biyu yake rufe shago. Tana kwance tamkar mara lafiya ta kasa bacci shigowarsa sai ta lumshe ido tamkar mai bacci,tasan har yanzun da matsala tunda bai aiko an karba mishi abinci ba.ya tsaya kanta yana kallonta,tausay inta yaji ya san baccin cikin damuwa tayi shi. Ya zauna bakin gadon yana shafa kumatunta gami da kiran sunanta a hankali,"ikeelee kanwata! Ta bude idonta a hankali ta zuba su cikin nasa. Yace,sry na tashe ki daga bacci. Ya kara yin kasa da fuska har suna jin numfashin juna. Ban baki sako ba kika yi bacci bayan kinsan ba zan iya aje shi har sai gobe ba ko? Ta tashi zaune tana murtsuke idanunta. Baccin damuwa nayi Yayana,baka aiki an daukar maka abinci ba.yace,koshi nayi.Ta sunkuyar da kai,don Allah ka yafe min laifin da nayi maka dazu. Ya mannata jikinshi ta baya,baki min komai ba,can ne a shago aka bata min rai. Ta sauke ajiyar zuciya,sannan tace kayi hakuri,Allah yana tare da masu hakuri,sannan manzon rahama yace mu daina yawan fushi,damuwarka ta sani cikin wani hali,don ko abinci duk yau na kasa ci. Ya dada manne ta "yi hakuri kanwata tashi ga namanki da yoghurt ki ci. Tare suka ci naman suka sha yoghurt suka koshi,yace muyi wanka saboda zufa sai ki amshi sakon ko? Tace to tare suka shiga bayin hakan lokacin da yake bata sakon sai tana mamakin a duk lokutan da zai bata sako shi baya gajiya ne? Don sakon nashi kan dauki lokaci. Sai dai tana jurewa tare da daukar wa kanta alkawarin ci gaba da jure amsar nauyayyan sakonninshi. Nafisa kam dakyar tayi shiru a gidan safina kuka take rurus wai ita mahmud zaya ce ta ci albarkacin iklima.Safina tace,don ki ji haushi ne yace haka,ni a nawa ganin ki nutsu ki sakar mishi 'ya'yan banki tsaf zamu shawo kanshi.Ai dama ba farat daga zuwa zamu ci galabar shi ba,sai kace bai san ciwon kanshi ba,abin da kika mishi fa ba duk bane zai jure. In wani ne ma dukanki zaya yi. Da kyar ta sha kanta suka ci gaba da shirya yanda zasu sha kansa da kudi amma sai ta sake zuwa. 2 days ta tafi cikin damuwa.Sam bata leka mahaifinta ba,bata san ma sun tashi ba. Washegarin dawowarta gidan anty hajara ta nufa,suna kwance kan gadon antyn suna hira tace tana son tayi dinkuna don Allah anty hajara ta hadata da telanta. Tace zan ko hada ku ga yaron ya iya dinki.bari in kira shi ince yazo gobe sai in sa driver ya kawo shi, nafisa tace to washe gari driver'n mai suna bashari yazo aka kawo shi ta bashi dinkuna tare da kudin da ya sara mata babu ko ragi. Wata biyu kenan da auran su ikilima koyaushe tana son yi ma mahmud batun komawa skul amma tana shakka,don ba wai anyi yarjejeniya bane.yanzun dai da ta lura yana cikin nishadi suna karin safe sai ta dube shi tace"Yayana tunda na shigo gidannan ban taba fita ko nan da can ba" Ya dube ta ina kike son zuwa? Tace gurin babana,ban san matarsa ba sai mamanmu in je? Sannan ina son inje skul.ta dubi fuskarshi don taga ya ya ya amshi batunta.Sai taga ya sha kunu. Gabanta ya fadi tace "Yi hakuri in ranka ya baci" Yace wace skul? Boko ko islamiyya? Tace duka wai da,yace to sai nayi tunani,gida kuwa ki bari zamu fita tare gobe ki shiga gidanmu kije gurin mahaifiyarki ki fito sannan gidan babanku dan can zaki yini,zan zo mu dawo. Tace,nagode yaya. Bai ce komai ba yaci gaba da karinsa. Hakan ce kuwa ta faru,washegari suka shirya ta ciro safa da niqab yace,wai ke duk uwar ranar nan da ake yi sai kin rufe fuska? Ta dube shi "ba zan iya fita haka ba" Ya taba baki tare da cewa manzon Allah dai yace imani yana zuciya" ta dube shi ranta ya dan sosu ta jima da lura da shi baya son irin shigar da take yi tace"amma yaya hijabi cikar kamala ce da mutunci,ya kamata ka lura da bambancin da ke tsakanin mace mai sanye da hijabi da kuma mara shi. Yace ni ki min sauri ba dogon tarihi na tambaye ki ba. Tace Allah ya baka hakuri. Suka fita tace da matan gidan sai mun dawo suka ce to. Da ta fita kuma sai suka dasa zancanta kun san mta. Maman ummi tace,Aisha kin Allah,amaryar gidannan suna bani mamaki,ita da mijinta.Aisha tace na me? Maman ummi tace, na jaraba,koyaushe da ya shigo sai kiga an karo kofa.Aisha tace,ashe kin lura,ni haushin da take bani cikin gida da hijabi sai kace mazan mu suna da lokacin kallonta ne.mu kuma me zamu kalla a jikinta wanda ba mu dashi? Maman ummi tace shi na gani. Ita a dole mai ilimi,shi fa mijin ma da take wannan rawar kafa ba fa sonta yake ba.Aisha ta tare ta da cewa,to waye a ung nan bai san cewa Yarta yake so ba,taga kudi ta ki shi shine uban ya lika mata mishi kanwar. Suka kwashe da dariya.Aisha tace,kina nan wata rana zai gara mata,sai an gama amrci da abu ya hada zai ce abinda ba sonki nake ba. Ikon Allah! Ko ina ruwansu maman ummi? Wannan shine ana kayan zunubinka kai kana kayan na wani, dama mata muyi harkar gabanmu dn kowa tashi ta fisshe shi. Zaman gulma ba abinyi bane. Allah ka shiryemu mu daina Amin. Gidnsu mahmud suka soma shiga sannan suka wuce gidan maman tasu don bata san gidan ba. Yaja tunga daga can nesa yace "minti talatin" ta dube shi "kai bazaka shiga ba? Yace kema dole ce tasa, don dai uwarki ce km baxan rabaku ba, ki wuce kina cin tym dinki ne. Bata ce komai ba tai gaba. Yau ne ranar farko data soma zuwa gidan, ta tura gate din gidan ta shiga, flat me kyau, ta kwankwasa kofar can aka bude ta daga nikabinta, haule ta tabe baki ta koma ciki. Ikilima tabi ta falon yaji kayan alatu gwanin sha'awa ga sanyin a.c. Mamansu fa tayi kiba jiki shar dole ta guji babansu. Ta zauna kan kujera itama ikilima ta xauna tare da cewa mama ina kwana? Tace lfy. Ta cgb da cewa ai na zaci kin cnxa sbwr uwa ne ke da nafi'u, ku ne baku taba xuwa gidannan ba sbd bakinciki. To ynxu meya kawo ki? Tace naxo gaisheki ne dama haule tace dama kin rike gaisuwarki, dk abinda kuke ciki lbri na xuwa min daya byn daya. Ance ubnki yai ma mahmud huce haushi da ke. Km kinje gasa kin samu kudi kin sai ma ubnki gida. To ni da baki bani sile ba duban ni ki gani mena rasa na jin dadi? Nasan duk kyau da girman gida dakika saima uban naki bnyi zaton yakai wannan ba. Ikilima tace ni dai mama don Allah kiyi hkri, auren mahmud nayi ne dn na daidaita ku da mahaifina, ba wai dn baba ya huce haushi ba, gda kuwa danku na siya. Tayi shiru jin maman bata ce komai ba, ta cgb da cewa don Allah kiyi hkri ki koma gurin baban mu.ls BOOK MABUDIN WAHALA 1***3 Da safe bayan ya gaida matan babansa yayi sallama kofar dakin mahaifin nasa,Alhaji Ibrahim kwantagora ya amsa,mahmud ya shga ya xauna ckin grmamawa yake gaida baban nasa shima cikin farin ciki ya amsa. Mahmud yace Alhaji mahaifin nafsa ne yace in sanar da kai ake sai dai ni kamar yanda na gaya maka a dan tsahirta min saboda yanayin harkokin kasuwar ta tsaya 2kunna. Alhji Ibrahim yace banda abinka mahmuda ni bance kayi kome ba a hidimar auranka nine xanyi maka kome,yace ni nafi soxuwa gaba ne kadan. Alhaji Ibrahm yace to shkenan ban san nufinka da haka ba amma xan sanar da Alhj mustapha(kanin shi kenan) in sunje sai a ce a jiramu,yace to nagode. Koda su Alhaj mustpha sukaje gdan malam usman sun bada kudn gaisuwa kuma ya yanka musu sadaki 5K sunce a sauraresu in sun kawo sadaki asa rana. Sun roki alfarmar suna so yarinyar ta karasa kara2 malam usman yace amma shi yaron yasan da wannan magana?suka ce shine ma yace su nema masa alfarma,malam usman yace ba komei shekara biyu ai kamar yau ne gurin ubangiji sukace hakane kam. Sai dai shi malam usman da yake yasan halin yarsa ko shakka bayayi yasan ita ce ta matsa mishi. Lokacin da ya shga gda ya kira haule sai da ta xauna sannan yace iyayen wannan yaro mahmud suka xo ta daure fuska shi kam ba tare da ya kalle ta ba ya cigaba da cewa ga kudin gaisuwar su nan kuma xasu kawo sadaki sai dai sun roki a bari ta karasa kara2 duk da nasan ita tace dashi hakan. Haule tace to malam nawa kace sadakin?yace dubu 10 da sauri ta dube shi tamkar ya watsa maya wuta dubu 10 malam sai kace wata kaxa? Yace mu albarka da alkhairin aure muke nema ba tsawwala sadaki ba,sannan ki min shiru haka naga dama. Ta mike ta fita ba tare da tace kala ba. Lokacin da yar tata ta dao sai ta shaida mata cewa ga hukuncin da babanta ya yanke. Nfsa tace sunyi ta banxa don ba dai dani ba to ko kudin gaisuwar safina dubu 50 ne bare ni in ba a kawo min 100 ba ai sai dai nima a bani 50 din,amma dubu 5 sai kace dan tsako. Haule tace ashe kin fara hankali yanxu kyale shi 2nda ance sai kin gama makaranta ki karta mishi rashin M har yayi xuciya ya daina xuwa sannan kiyi ta dora mishi nauyin abinda bashi dashi duk abinda kika sanyafi karfin shi shi xakice ya sai miki. Nfsa tace ki bar shi sai mun karya shagon kema ki dinga aikawa kina amso sabulu da omo haule tayi dariya tace xan ko dinga aikawa. Hakan ce ta kasance,tashin farko ta sake bijiro masa da ba2n waya jiki na bari ya siyo mata har da

Chapter 2 of 20