Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
dan tsaya mshi a rai . Lokacin data rako shi ya rike hannunta.宄歵a sai munyi waya: Abban Khalil don Allah ka kauda anka daga haramun顏� Ya kale tad a son jin dalilinta na cewa haka Tace tunatarwa ce kawae. Kana da yara mace da namiji kai ne zaka tsare musu mutuncin ta hanyar tsare naka Ya fuskance ta yace in nasi in fahimceki kina nufin zuciyarki ta soma raya miki ina neman mata ? Auzubillah! Kullum zuciyata tana kyauatata zato a kanka tunatarwa ce Ya girgiza kai. Maganar tad an tsaa mishi a rai. It kuwa tunda yatafi tana cikin damuwa, koda sunye waya bata taba nuna mishe Ba, haka yanzu ta koma adu,a ko matar banza ce ya hadu da ita Allah yarabasu. Sannana ta Kara Zage damtse gurin ye mishe duk wani abu da zai Sa she cikin farin cikin Tare da kare mutuncin she. She kuwa zuwa yanzu Yagama shagala da son ashura, burinshi kawai ya aure,Yana son mace yar gayu, sai dai Yana ganin iyayenshe bazasu yarda Ba, sannan Yana tsoron ikilima ta sani, don yasan tana tana da zafin kishi. Sai dai fa shi zai shanye komai in dai zaye samu ashura. Nafisa dai suna nan suna Shan magani labarin mutuwan mama zee da safina ta samai ta, tsakaninsu kwana daya. Nafisa Taye kuka tareda nadama. In tana tuna kanta, shekaru biyu baya tana shan mamaki, bata San yau zata zo mata a haka Ba, koda yaushe tana gane illar son zuciyarta da taye, ta dinga gantali zina don kawai ta samu abun duniya. To yau gashe shekara biyu jal da yan watanni ba kudi Ba mutunci, ba kuma lafia, ciwon da kowa ke gudun ka sai dolenka, Wanda kuma take mutukar so ya zama ba Rabonta ba, mutane na kyamarta ko Islamiya taje sai ayi ta matsawa daga kusa da ita. Mahmood yana zaune gaban mahaifinshe a wani hutu dayazo,so yake ya gabatar da batun Asurah,amma mahaifin nashe sai ya tareshe da batun gini,kan cewa yaye kokari ya karasa sai yace too, ai kwanan nan zaya gama. sannan ya ce,daman kan batun wata yarinya ne da yake so, shene iyayenta sukace ya turo manyanshe.ya tsura mashe idanu,sannan yace Aure ? Aure yanzu ?baka samu ka kammala gininka.yace Alhaji zancen nakeson a gama komai in an tsaida rana saina karasa ginin kafun bikin,Alhaji yace, madalla, to a ina kasamu matar?Can kaduna ne gidan da nake, kanwar aboki na ce. shekenan amma baka ganin kaye gaggawar sake aure? Mohmood ya sunkuyar da kai tareda cewa, Allah zaya rufa asiri Alhaji.yace shekenan zan samu su alhaji mustapha sai mu ji lokacin da za a tafi din.Duk wananna shirin ikilima bata da labari,haka nan mahafiyarshe dasu hajiya uwa sun bashe shawara yace shede su tayashe da adu,a.Matar muktar itace ta soma tsegumtawa ikilima batun auren mohmood, har an saka rana ikilima taye murmushe yake tare da cewa,ai ta sani.matar muktar tace she a gidanmu yace baki sani ba,don Allah karna fada miki.ikilima tace wasa yake miki nasani.bayan tafiyarta ikilima ta zame ta kwanta.tambayar kanta take wani irin mugun hali ne da ita wanda har mijinta mijinta zai boye mata batun aurenshe?Don ita a hagenta nesanta mugun hali ke sa miji ya boye wa matarsa don gudun fitina. Ta shiga daki taye ta kuka sosai don tana kishen mijinta,amma hakan bazai sata bijirewa Allah ba,tasan kisheya babu dadi amma Allah yace a yi.farko ma da biyu ya soma,sannan yace uku,ko hudu.sai inkana tsoron baza kaye adalci ba ne aka ce kaye daya.Da an doge da biyun da duk wanda zai ye aure biyun zaya yi,matsalarta boye matan da yayi,tunda ba ya so ta sani ita ko tasha alwashin ba za taba yi mishi zancen ba. Ashura dai tana rabonta,don ko kayan Akwati tare suke zuwa su siya.musa ne da yaje kwantagora ya shaidawa mahaifiyarsu,nan ko ta fusata,dama shima musa ba son auren yake ba. Ta ce kira mini shi ,ya kira shi ta ce, too duk da ban isa shawara ba don za ka yi aure in ka gama ina neman ka, don ban amince da batun aurenka ba. Duk yaushe ka soma samun kudin da har zaka sakawa matarka da kishiya? ka manta wuyar da yariyar nan tasha kanka.ko dadin kudin ba ta soma ji ba zaka debo wadda kila ma kudin ta gani zata aure ka.shi dai shiru yayi tamkar ruwa ya cinye shi, ta ce don haka ina nemaika. koda yake nasan ban isa ba,ta mikawa musa wayar ya kashe.ranan juma,a daga kaduna kai tsaye kontogora ya wuce,da kyar ta amsa sallamar shi don tasan muhimmancin sallama.tsuke fuska taye yanda bai taba ganiba daure fuska irin haka ba.jikinshi babu karfi ya shiga,cigaba taye da aikinta ta share shi,saida ta gama komai ta shigo.yana zaune ya zabga tagumi ta zauna tana ninke kaya ba tare da ko ta kalle she ba.ina wuni hajjiya da kaushin murya ta ce,kaga alama ai tunda aiki kaga ina yi ba a kwance ka ganni ba,kaga lafia kenan.wallahi bana ki sheda miki ba ne,daman zan zoo.....ta ce rufa mini baki,baka maida ni bakin komai ba har a sa maka rana ban sani ba?don bani da abunda zan baka ko kai kayi kudi!ya zuba gwawoyinshi a kasa yana cewa,don Allah ki yafe ni naye laifi,amma ba don baki da shi bane,ni wallahi aure kwai nake son karawa.saboda matarka tana maka mai?ta katse shi.ya dube ta wallahi ikilima tana min duk wata biyayya,in ma nace bata min sai Allah ya kama ni,ni de ina son ashura ne.don Allah hajjiya ki sa min albarka cikin auren nan.Bazan saba naji ance baka son ikilima ta sani,adalci kenan? cikin in ina yace a a a ta sani,ai ita ce ma ta karfafa min gwiwa fa.ka ji karya.yana ta share zufa hajjiya taye shiru, can ta ce yarinyar kirki.to shi kenan, ai zan zi minna din.nan dai ya kwana da safe ya zuba mata kudi ya nufi minna.ikilima tana kwance ba lafiya,tunda matar muktar tazo mata da labari auren mijinta karfin hali kawai take yi,su maman ummi sun samu labari,sai dariya suke suna Allah kara,tun suna habaicin cewa ai daman duk shegiyar da ta rike namiji uba zata mutu marainiya,har dai suka samaita har daki suka ce wai an ce baban khalil zai kara aure?Ta ce ehh Aisha tace,kizo in kai ki gurin aminyata ta kai ki gurin bokanta ta tarwatsa abun.maman ummi tace ce ,ke ko nan gurin malam na ketare aka kai ki tuni zai wargaza lamarin. Ta ce A'uzubillahi! A wargaza sunnar manzo (saw)? bana cikin wannan layin, ban ce bana kishi ba amma ba ni da abin yi sai adu,a Allah yasa abokiyar zaman arziki ce Allah yasa mu zauna lafiya.aure inkun yi tunani sunna ce, Allah da kan shi da biyu ya ce su fara, don haka kuma mijina fatan alkhairi nake mishi don na rike shi uwa uba.jiki ba karfi suka fita suna taba baki, Aisha ta ce, don Allah kyale ta,karfin hali ne gashi nan duk ta rame? maman ummi ta ce,in ya sake ba sai kuma muga ta kaudi ba,ai dama su maza haka suke, daga sunyi kudi sai sake aure,sai kuma saki.muna nan zai sake ta.su khalil da ummita suna gidan su mahmmod,ranar ma nazira ce tayi mata aiki ya shigo da sallama,bacci ya soma daukanta.ya nufi bed room, nan ya same ta kwance ya sabule jakarsa ya aje ya tsura mata idanu,ya tsorata da ramanta. ya kai hannu ya shafi kasuuwan wuyanta,sun fito rada rada firgigit!ta farka ganin shi ta kirkiro fara,a ko na yake.ta yunkura zata tashi ya zauna da sauri tareda rungumota ta zuwa jikinshi dunib jikinta ne ya firgita shi,ya ce ikilima tun yaushe ba ki da lafiya? tashi muje asibiti.ta ce zazzabi ne kawai ,bari na kawo maka ruwa.mai zaka ci na dafa maka?ya tsura mata idanu,sannan ya kwantar da ita ya canza kayan shi da sauri ya dauki key din mashinsa tare da zura mata hijabi.tashi muje.ba don taso ba, dole ta mike suka nufi asibiti. duk gwaje gwajen da likita yayi hawan jini kawai yagani,shima ba ta'azzara ba ne, ya dai ba su shawarar su kiyaye duk wani abu da zaya sa jininta din ya kara sama.Hankali mahmood ya tashi sosai, koda suka dawo gida yasa ta shi lallai ta fada mishi damuwarta, ta ce ba komai.ya tsargu, ko dai ta samu labarin auren shi ne? ya ce, ikilima ko an zo miki da labarin game da ni? Ta dube shi "na me?" Yace a'a am...na zata dai ko ni ne na bata miki? Tace ko daya, me za kaimin? Yace to kila yaran da kike koyarwa ne hayaniya shi yasa nace ki daina koyarwa kiji da karatunki. Ta dube shi kayi hakuri, inason karatuna da koyarwa. Yayi shiru kawai yana tunani, in kuma taji batun auran shi sai yaya kenan? Kila jininta ya kara sama. Kafin washegari tana ta samun sauki, yana kula da ita, hatta wanka shine ke mata. Maimakon ta tafi lahadi da yamma yadda ya saba, sai washegari litinin yayi asubanci, a cikin mota kafin ya sauka ma ya kira ta yafi sau goma. Ko ashura bai saurare ta ba a wannan zuwan kamar yadda suke hira cikin internet in yazo gida. Bai samu sukuni ba har sai da ya samu tabbaci daga kannan shi cewa taji sauki, don shi ko tace da sauki sai yaga kamar fadi ne kawai dan kada ya damu. Duk lokacin shan maganinta zaya kiraa yace mata tasha yana jiranta har ya kan ce ta kara wayar yaji shan ruwanta, sai ta tsokane shi tace amma gara ni ba sai an jika a cokali ba, yace eh naji sha dai ina jinki. Ranar wata asabar sai ga mahaifiyar mahmud tamkar an jeho ta. Taci sa'a yana gari. Tunda nazira tazo ta shaida masa zuwan hajiya gaban mahmud ke faduwa, yana keta zufa. Yasan yau ba makawa ikilima zata san abnda yake boye mata, ta gama abinci kenan zata aika mata sai ga ta, tayi sallama shima yana wanka yana sauri ya fita don kada tazo ta same shi. Suka gaisa da ikilma tace "dama yanzu zanyi shirn makaranta ne in zo mu gaisa". Ta gabatar mata da abinci. Hajiya tace a'a a kai min can tunda kika ganni gidanku kinsan ba zuwan kowa nayi ba naku ne, ina shi wannan yaron? Tace yana wanka. Ya fito jiki ba karfi, ko turare bai sa ba ya zauna yana gaishe ta cikin yake da fargaba. Duk suna zaune ne a kan carpet, tace ikilima kwanaki musa yaje min da batun auran mijinki, har yake cemin shi mijin naki yace baya so kisani, shi kuma da yazo yace min kece kika karfafa mishi gwiwar yin auren, haka ne? Ta dan dakata yayin da take bin ikilma da kallo da idanunta, alamar tana son fahimtar wani abu a tare da ikilimar. Kafin ikilima ta bata amsa, sai kuma taci gaba. Don ni ban kama zancen shi ba, shiyasa nace sai nazo naji daidai lokacin yana garin, ba ruwana da munafurcin maza.vels BOOK MABUDIN WAHALA 3**7 Ikilima ta kalle shi duk yayi zufa, yasan hajiya na jin cewa ikilima bata sani ba, batun auran ya rushe, gara ma ya fada da kanshi kafin tayi magana. Yayi saurin cewa gaskiyar magana.... Hajiyar ta katse shi 'ban tambayeka ba, ke 'yar nan fada min gaskiya, kin sani? Ikilima ta danne bakin cikin da ya taso mata tace na sani, ni ce ma na karfafa mishi kamar yadda ya shaida miki. Cikin mamaki ya tsura mata ido, tana kallon shi sai yayi maza ya sunkuyar da kai, kunyarta mai tsanani yaji. Hajiya wadda ta kasa magana don jin wai ikilima ita ce ta daure wa mijinta gindi yayi aure, ta nisa sannan tace. Yau ne na yarda 'yan nan baki da kan gado, hankalinki daya zaki ce mijinki yayi aure? Kin san kishiya kuwa? Kin san halin maza kuwa? Ban da rashin hankalinki in shi ya manta wuyar da kuka sha ke ai bai dace ki manta ba. Yaushe ne ma kuka samu rufin asirin? To ki sani ita kishiya cikin dayan biyu ne take zuwa, ko ta kore ki ko ta mulke ki. Shi ko in bai juya miki baya ba to saki ne zai biyo baya. Ta dubi mahmud nasan sakinta zakayi wata rana. Duk suka kalle ta yace saki? Haba mama. Ikilima zufa ya rufe ta, dama daurewa tayi ta sake cijewa tace mama kiyi mana addua, nasan ba zaya min haka ba. Tace Allah yasa. Bari in tashi, na lura kece kika bashi fuskar yain auren. Ikilima tace ki sa mana albarka mama, bakinki yana da fa'ida ga auran. Ina nufin albarkar ki. Tace um Allah yasa alheri. Ta dube shi kai sunkuye sai kace munafuki. Tace wane shirye shirye kake nagam ginin? Yace ai mama har an rufe, tiles ake sawa sai painti. Ta taba baki ta dube shi. Yaushe ne auren? Ya dubi ikilima suna hada ido ya sunkuyar da kai "kwana arbain da daya ya rage. Tace to a nan kake aje lefen? Yace yana gurinta, in mun siyo sai ta aje saboda nisa nace ba sai anje kaiwa ba an huta. Ikilima ta danne wani abu da ya taso mata tare da maida hawayen idanunta. Hajiya tace tabdi! Auren bariki zakuyi? To ba da ni ba, ka amso kayan ka kawo daga nan za'a kaisu , ina ka taba jin ance amarya ta tara kayan lefenta? Kai ka raina danginka ko? Yace a'a zan karbo. Tace ita ma ikilima duk abnda kayi ma waccan shi zaka mata, butulu. Har ka manta wahalar da tayi dai? Ikilma tace don Allah mama kiyi hakuri, ni yaji da amaryar da kuma gininshi. Mama kisa albarka. Hajiya tace bai isa ba yace ba zai miki komai ba. Da sauri yace duk abin da take so zan mata ai. Tsaki hajiya taja tare da mikewa. Ikilima ta kallo agogonta, nima lokacin makaranta yayi, ta mike tace mama bari na dauko miki abincin mu wuce tare. Yace hajiya sai na shigo. Bata amsa ba ikilima ta sabi jakarta ta dauko kwandon abincin hajiya, ta dube shi tsananin kunya tasa shi sunkuyar da kai, ikilima tayi murmushi tare da cewa sai na dawo. Duk abn duniya ya damu ikilima, tana zaune cikin aji. Duk wanda yaji batun auran sai yace ta tashi tsaye, to tayi me? Menene tashi tsaye? Hatta maman shi sai da tace ki nemi tsarin jikinki, 'yar bariki ce. Tsaf sai ta raba ki da mijinki. Haka mamanta tace ke sarkin gaddama, to yanzu sai ki dage ki nemi mallaka. Ki mallake shi in ba haka ba wata tazo ta koreki. Nafisa kuma kuka tayi ta yi, wanda ikilima ba zatace ga dalilin kukan ba, sai dai ita tana yi ne saboda rashin masoyi da tayi. Tasan har duniya ta nade baza ta daina son shi ba. Su haj uwa ma duk ce mata sukayi ya tashi tsaye. To wane tsaye zata yi da ya wuce adduoin da take yi? Sam tayi nisa cikin tunani bata san me akeyi a ajo ba, bata san an tashi ba sai dai juwairiyya usaini ta buga tebur sannan tayi firgigit. Juwairiyaa tace tunanin me kikeyi haka? Hawayen da take makewa suka saukar mata, juwairiya ta zauna me yafaru? Ikilima tace um, bansan me mutane suke nufi da cewa in tashi tsaye ba, kowa tsorata ni yake da cewa matar da mijina zaya auro zata zo ne don ta kore ni, ban samu mutum daya da ya ban shawarar kwantar da hankalina ba. Juwairiyya dama duk wadda mijinta zaiyi aure sai ta tashi tsaye? Kafin ta amsa malamin su ya shigo kwasar littatafansa, sai yagan su. Lafiya ikilima kike kuka? Juwaoriya tace malam tana da matsala ne. Meke faruwa da ita? Malam ya tambaya da saurin shi. Nan ikilima ta shaida mishi cewa mijinta ne zaya kara aure bai fada mata ba, sannan kowa yana bata shawarar ta tashi tsaye, ma'ana ta shiga malamai. A'uzubillah. Inji malam kabir. Ya kausasa murya, koda wasa kada ki kuskura ki dauki wannan muguwar shawarar, ba kya yin adduoi ne na tsari? Tace inayi, yace ki tsaya akansu, su kadai sun isar miki. Azkar din safe da yamma. Wallahi ba mutum ba ko aljan sai ya barki, kuma duk abinda kika ga ya same ki sai kaddara daga Allah. Ya gyara tsayuwa. Abin da mata ku ke kasa fahimta, kishiya ba abokiyar gaba bace, 'yar uwa ce. Sunna ne mu aje ku ku hudu, duk matar da take yakin bata son kishiya fada take da Allah da yace a yi, don haka ki nutsu kiyi wa mijinki addua, kada ki zama cikin matan da ke cewa namiji ba dan goyo ba, namiji kaza namiji kaza. Da zaki bukaci jin dalilin zagin namiji, zakiji duk kan batun kishiya ne, don haka ki nutsu. Ikilima tace to malam, nagode. Yace ki dinga tashi cikin dare, misalin ukun dare ko biyu daidai lokacin ubangiji yake cewa ina mai bukata ya roke ni, ni kuma in biya mishi? Kiyi nafila ki gaya wa Allah damuwarki. Amma bakije gurin wani makaryaci ba ya amshe miki kudi ya rabaki da imaninki, kuma wasu malaman har zina suke yi da matan mutane. Tir! Da irin wadannan mutane. Ikilima tace to malam in sha Allahu zan kiyaye. Tace malam babu wata addua da mutum za yayi yayin da kishiya tazo masa? Yayi murmushi yace ikilima shi kishi halitta ce da dan adam ba ko dabba yana da ita musamman ku mata. Ki dai rike zikirin Allah cikin zuciyarki yana wanke damuwa ko yaushe. Ki dinga la'ilaha illah ko subhanallah, walhamdulillah, wallahu akbar. Ko istigfari. Ki ringa yinsu kala kala. Kin iya malama ikilima zaki samu nutsuwa kuma Allah zai sa miki sanyi cikin zuciyarki. Ta mike to malam, zan rike duk na iya su. Adduoin tsari fa? Yace nasan kina ayatul kursiyu, falaki, nasi da kulhuwallahi uku uku. Asubahi, azahar, la'asr magriba da isha'I dai dai? Tace inayi. Yace ba abn da zai same ki, ki tsare adduoin bacci nasan duk kinayi ko? Tace eh, yace Allah yaja mana gaba. Ta gidansu ta biya, tayi dace samun mahaifinta inda yace dama yana so yazo gurinta, domin duk yaji batun da mata sukeyi a gida na game da auran mahmud. Yace da ita. Ikilima na sanki na san halinki, don Allah bana son ki canza don za'ayi miki kishiya. Ki zama mai biyayya da son abn da mijinki ke so. Kiyi zama na tsakani da Allah da abokiyar zamanki, kinji ko? Tace to baba in sha Allahu zan zama abin kwatance a gurin sauran mata, zan bar misali. Yace Allah yayi maki albarka ke da 'ya'yanki. Tace amin baba na gode. Tana shiga gida dakinta a rufe, mahmud ya fita. Tasa hannu ta ciro key din a gurin da suke ajiyewa ta bude kofa ta shiga. Tun lokacin da malamin yayi mata nasihar take zikiri cikin ranta, don haka sai taji rayuwarta fes. Nazira da ta kawo su khalil itace ta tafi da abincin hajiya na dare. Mahmud kuwa har taran dare ya kasa shigowa gidan. Suna fita shima cikin sanyin jiki ya bar gidan, gidan su sulaiman yaje yana neman shawarar shi game da abinda zaya fada ma ikilima inta dawo. Bayan ya sanar dashi duk abubuwan da suka faru, sulaiman yace Allah ya kara maka, sai da na ce kasanar da ita tuni ka ki, to gashi yanzun ta sani lokacin da baka shirya ta sanin ba, ta kuma rufa maka asiri, don haka sai kaje ka bata hakuri. Suleiman ba zan iya kallontaba, ina jin nauyi. Don Allah muje ka raka ni. Tab! Wallahi ba zan je ba, kawai ta zo tana Jin haushen na a banza? Mukhtar ma nan ya same su, amma shims cewa yaye bazai je ba. Lokacin da ya shigo ikilima tana wanka,falo ya sauna cikin fargaba tare da tunani in ta fito Kilauea ta balla Mishi harara ko ta ja mishi tsaki,wata zuciya tace in ma haka taye maka da sauki,kila da hauka da zai tare da ce maka munafuki maci amana. Haka dai yaye ta tufka yana warwarewa har baije fitowarta ba.ta shirya cikin Kayan barci tasa turare,bata san ya shigo ba ta dubi ago go tara ta gota,don haka sai ta ce Bari ta shirya masa abinci kafin taye shafa"i da wutiri kada ya shigo taye bacci ko tana sallah.taja ta tsaya saboda ganinshi Zaune ya rafka tagumi.a hankali ta ce sannu da zuwa,firgigit yayi sannan ya ce yauwa,um hum.duk ya rude.tayi guntun murmushi,sannan ta nufi kichin ta dauko mishi abinci ta shirya mishi ko ya kasa kallonta,ta zauna ta cewa tuwo" na maka, na San ka da son tuwo.ya ce, "EH, ai gara tuwon ne." ya soma ci duk da ba ya Jin yauwa saboda damuwa. Ganin yana duk ya kasa sukuni sai ta nufi ciki ta fara sallah.yau dakin tamkar bakon shi,ya kasa shiga. Can dai ya yanke Shawara yasame ta ya bata hakuri ya huts da Jin nauyin nan dake damunsa.yasan kuma Zara hakuri don tana da matukar hakuri.lokacin da ya shiga ta soma barci,don haka ya kwanta amma ba don bacci ba.ya shiga tun daga ranar da ya kwanta ciwon bakin ciki da nafisa ta dasa mishi zuwa lokacin da mahaifinta ya ba shi kanwarta ikilima. Ya dubi yaran su guda biyu mace da namiji,ya sauke ajiyar zuciya.sannan ya soma tunani a tsawon zaman nan ko zaa tuna mai ikilima ta Fada mishi na bacin rai? Yayi ya yi amma ya kasa tunawa,Kirkinta ya shafe..ina ma ta taba mishi ya shiga tuno halayanta na kware.ya tuno lokacinda itace ke ci yarda su da dan albashinta, ya yi ta tuna abubuwan daki daki har zuwa yau da ta kare shi gaban mahaifiyarshi.ya juya ya zuba mata idanu, ya sani ya yi Dacen mata,Allah yasa ya fita hakkinta.baya ga son da yake wa ashura da tuni ya shafe babinta,abin nufi ya fasa.uku saura ta fara,lokacin ya soma bacci amma motsinta ya farkar dashi,sai dai ya yi shiru ta dauro alwala ta shiga nafilfili, sai jikinshi ya sake mutuwa yaga tamkar bai mata adalci ba ne take Kai karar shi gurin Allah. Don haka da safe ma kasa mata zence ya yi.iia zugum da ya yi yana tuna lokacin da ta dawo alwala a jiyan da dare ta shafe mishi jikinshi tsaf.tana cewa " nasan baban khalil sakaci da wuya in ya yi adu,a. Sam bata Canza mishi ba, yanda ta saba kaf kayan kunya har ya tafi..lokacin da ya dira garin kaduna yafita wanka yaye shirrin bacci, abubakar na rokon shi don Allah yasa kaya manya suje malali gurin budurwanshi.ya ce, na gaji ka Gaida ta, kasan gajiyan tafiya..abubakar ya ce,ka cika raki,in Kai ke jan motan sai yaya? Ashura ta shigo da tire abinci a gaban mahmoud,fuskarta a daure ta koma gefe ta zauna.abubakar ya fesa turare ya jefa kan katifa tare da cewa" ni na wuce. Ya ce, " to in kayi dare zamu rufe gidanmu ne," abubakar yayi dariya tare da cewa, sai na hauro katanga." ya maido duban shi ga ashura.ranki ya dade ina yini? Ta sake Cuno baki ya ce " to nayi laifi kenan? Tayi fari da matsakaitan idanunta tare da cewa, " au, ba ka ma sani ba kenan? Na lura in ka tafi garin ku share ni ka ke yi, Kuma da ai ba haka kake min ba,ko dan chatting Bama yi yanzu. Jiya fa har kashe waya kayi.yace, to nutsu in Fada miki uzirina,haba my love, ta ce, na ji." ya ce kin ga kwana Bihar fa mukeyi kullum muna hira,amma ita kanwarta kwana biyu jal yana da kyua mu lura da hakkinta? Ta tabe baki, ni wannan ba matsala bace." na Kai ma tella dinki anko har da nasu hajjiyaduka yaye mini lissafi dubu sha biyar.sannan zaka bani kudin gyaran jiki dubu sittin.ya zuba mata Ido tare da cewa,dubu sittin ashura? Gaskiya bani da halin ba ki su,kin fa San gurin aikinka.so ki ke na shiga diban kudin Jama,a. Ta daure fuska," to ya za,aye yanzu? Ya ce, kin San na ce miki da dan karashen aiki a gidan da zamu zauna.kanwata ban sai mata komai ba,lafe ba a gama hadawa ba,duk fa ni kadai ne.ki lura da wannan." ta ce," kana nufin na hakura da gyara jikin,don Kai fa zanyi?ya ce, wai wani Irin gyara bane? Ta ce, gyaran fata ne zuwa lalle da za a zana min." ya ce, " too zan bada rabi dubu talatin,kince na dinki dubu sha biyar, anko har guda nawa ne? Uku ne, sai na hajjiyata da kawayenta su biyu. Too naji, zan bada arbain da biyar ke nan ko? Ta ce, um, too yaushe za,a karasa kayan lefan? Ya ce, " kafin na tafi gida sati na sama da su zan tafi sai su kawo." ta ware idanu shi " da su" ya ce," eh," amma ai da ba haka muka yi ba da Kai ba,ya za,a Kai mini kaya can? " ya ce, na Canza ne,dole na Kai sai dangina su kawo,zai fi daraja koo? Kema zaki fi kima a idon dangina.ta ce" to gaskiya ba za,a Kai min kaya Kauye ba suje su kwashe. " ya daure fuska " garin namu ne Kauye? Ya kauda Kai " ki zauna da shirrin zan tafida su Koda garin mu daji ne.fuu ta fice tana kara kumbura fuska,ya Fada kan katifa a baya tare da lumshe ido.ya ciza dan yatsan shi na tsakiya, wannan lokacin ne yasan matsalar aure daya so nafisa wanda son ya rikide ya koma na ikilima,ko zanin dubu uku babu.shaddar cikin ce kurum ta dubu biyu da dari biyar. In zai tuna atamfofin da suka siyo kawai kowace daya dubu ashirin da biyu ce guda biyar,ga lesuka da shadda duk masu tsada gaske,kudin shi na wannan shekaran kan ashura suka kare.yaja tsaki gashe bata San darajan shi ba,kuma yana ganin da kyar in Zata yi biyayya. Ta wani bangare sai yake ga kamar ya cutar da ikilima don bashi da karfi sai musu iri daya,komai ya dauko wayar shi ya dubi lokaci sha daya yasan tayi barci,ya rubuta: NA SANI NA MIKI LAIFI, DON ALLAH KI YAFE NI INA JIN NAUYENKI.Ya tura mata, sannan ya kwanta yana karanta addu,a wanda in gida ne ita ke shafa masa.da safe taga sakon shi,murmushi taye.koda wasa ba zata nuna mishi taga sakon ba,bare yaga amsa.ya ko sa ran ganin amsar sai dai shiru ta bashi labari.saboda ya samu a karasa gidan duk sati yake zuwa.wannan lokacin ko da ya zo da kayan lefen gidansu yakai duk zuwa in sun siyo sai ya zo da shi ya gama gidan amma bai samu halin canza ma ikilima komai ba.yanzu ma da ta zama surukarshi,har sakonnin shi sub dame shi amma baya iya tunkararta,ita kuma sai take ga dan zaya yi aure ne ya chanza mata,ya daina kawo sakon tunda gashi zaya yi sabon inbox.sauran sati daya biki, hajiyar shi tazo da kannanshi taga lefen amarya,amma bata ga kayan uwargida ba,don haka ta kira shi a gaban babanshi ta ce,ina na ikilima?ya ce, wallahi zai sai mata ko bayan biki ne,wallahi kudin shi duk sun kare kayan dakin zai chanza mata.hajjiya ta ce, ina, wannan ma labari ne.ta tura musa ya kira mata ikilima,ta ce darji wandanda ki ke so.su hajji uwa msukace ta diba.ta dube shi ya sunkuyar da kai ta ce, ba lefen amarya ba ne? hajji uwa ta ce, ki dauka ya za,ayi ace ke ba a miki ba?dubi

Chapter 17 of 20