Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
tana kuka tace ahmad please try to understand my love for u dagaske nake sonka zan iya mutuwa akanka daga ganin wannan yarinyar irin mayaudaran yan matan nan ne she is just after ur money Fisge hannunsa yayi yana fadin get out of my office Kara matsowa kusa dashi tayi tana fadin ahmad listen I said out !!! Yafada yana daka mata tsawa Dagudu tafita daga office nin tana rera kuka mai ban tawsayi Komawa yayi yazauna kan kujera hade da lushe ido Asma'u ce zaune agaban abba ta sunkuy dakai kasa tana wasa da yan yatsunta Ga inna da Ummi agefe sunkafeta da ido Kanta abba yadafa yace asma'u kinyi shiru kenake sawrare idan kinada Wanda kikeso kifadamun banaso namaki abunda zai takura rayuwarki Carab inna takarbe dafadin yo ina taga Wanda takeso yarinyar dako samari batada Kunyace kawai irin ta asma'u Kafadanta abba yadafa yana fadin a'a nasan halin asma'u akwaita da zurfin ciki kibari kawai muji tabakinta Itadai asma'u tunda abba yacemata jikan grany tayi shiru tana tunanin to wanne kenan amma dai tasan ba abidi bane tunda taji grany tace yanada wacce zai aura Ummi ce takatsemata tunaninta dafadin kinga asma'u keba TV ba kinsa munfakeki da ido idan ba kyaso kifada mu gyara mukeso muyi wa rayuwarki ba takura ba Hannu abba yadaga mata yana fadin a'a Ku sawrara mata mana ina anfanin gaggawa tashi kije har kiyi shawara kinji Zunbur inna tamike tana fadin yo wace shawara kwa zatayi bayan kaji sunce da wuri sukeson ayi komai wai ke asma'u wace irin yarinya ce haka kike so kitsofe ba aure ne gashi allah yamaki gyadan dogo yabaki mijin son kowa shine se kiwani yi shawara Kuka tasa tana fadin Allah jikanka magaji nasan dayana raye da tuni kina dakin mijinki Tashi asma'u tayi takamo hannunta tana fadin a'a inna dan Allah kidaina kuka nayarda zan aureshi amma kidaina fadan haka Rungumeta inna tayi cike da farin ciki tace haba asama'u ko ke fa insha Allah zakiji dadin zaman aure nasan abidi zai kula dake yanda yadace Afirgice asma'u tace 😨ABIDI kuma?? meyasa sai shi 😧ba grany tace yanada wadda zai aura ba Tabe baki inna tayi tace to ai shi aure nufine na Allah Allah yayi ba matarsa bace Sunyi farin ciki sosai aranan bakamar abba dayake ganin burinsa yakusa cika na ganin ya aurar da ya'yan kaninsa ga mazaje nagari Asma'u dai shiru tayi tana tunanin wayar dasukayi da abidi aranan idan har haka yake dazafin kai ya zatayi dashi Kuka sarh take kaman ranta zai fita wannan karon ba idonta kadaiba hatta kanta da fuskarta sun kunbura ikon Allah ne kawai ya kaita gida batako gama yin parking ba tafito daga motar bangaran AK tanufa direct tana isa ta banka kofar tashiga hade da zubewa abakin kofa takara fashewa da kuka AK dake kuance akan gado ya lumshe ido kamar mai bacci Jin anturo kofa yasa yayi saurin dago kai ya kalla Ganin sarah awannanhalin yasa afirgice ya diro daga kan gado har yana hardewa yanufota yana fadin subhanallahi sarah menene meyafaru daga ina kike Rungumeshi tayi tacigaba da kukanta kamar karamar yarinya Duk yarude yarasa yadda zai yi jiyake kamar shima yasa kukan Kanta yafara shafawa cikin sigar lallashi saida ta zagaita kukanta sannan yace menene Cikin dasashshiyar muryanta tace Yaya wai miye laifina miye bana dashi mmeye gareni Wanda ba'aso ajikin mutum hawauenta yashiga share mata yana fadin ba kyada wani aibu kanwata kinada duk wani abunda za'aso mutun saboda shi To meyasa ahmad baya sona !!! Tafada tana rike hannun dayake share mata hawaye dashi Da mamaki yace ban ganeba Kai ta gyada tace eh cewa yayi baya sona kuma bazai aureni saboda yanada wacce yakeso Murmushin gefe AK yayi yakama hannunta yazaunar da ita bakin gado seda ya tsiyaya mata ruwa yabata karba tayi tasha tana mamakin ya akayi bai nuna damuwarsa akan zancan ba Seda yakarbi sauran ruwa ya ijiye sannan yazauna kusa da ita yace Sonawa zan gayamaki idan zaki kuanta kirika yin addu'a amma ba kyaji yanzu gashi kinfara mungun mafarki yakarashe maganar yana kuashewa da dariya Baki da hanci tasaki tana kallonsa ahasale tace wai Yaya kana nufin abunda nafadamaka mafarki Murmushi yayi yace to ai sarah abunne yayi kama da mafarki taya mutumin da kuke soyayya har na saura sati daya aurenku kuma kice wai yace baya sonki yana da wacce kikeso Murmushin dayafi kuka ciwo tayi tanuna masa fuskarta tana fadin Yaya wannan ma mafarkine Dago fuskarta yayi yana kallon shatan yatsun da suka kuanta baro baro akuncinta abunka da faran fata Nan take fuskarsa tacanza dan yatsani yaga abunda yataba lafiyar kanwarsa Cike da mamaki yace sarah tell me what is happening Muryanta na rawa tabashi labarin duk abunda yafaru tsakaninta da ahmad amma taboye zancan marin da tama ahmad In shock yagama sauraren labarin Makullin motanshi yadauka da wayoyinsa yanufi haryanr fita batare da yace kala ba Har yakai kofa yasake dawowa yafizgi hannun sarah yatafi da ita gudu gudu haka yake sakkowa kan stairs sarah dake biyedashi har tana neman faduwa Karo sukaci da aysha zata haura sama shan gabansu tayi tana fadin AK lafiya meyafaru ina zakuje haka Dayan hannunsa yasa yamatsar da ita gefe yawuce baice uffan ba Baki bude tabisu da kallo har suka fita Yana isa mota yabude gidan gaba ya wurgata sannan yazaga yashiga mazaunin driver yatashi motar aguje suka bar gida se company"""""" Ur's ....✍ πŸ‘©β€πŸ’»Maryam Mhd [18/07, 15:03] Hubbey Frd Ameena Kn: πŸ“šπŸ“šπŸ“šπŸ“šπŸ“šπŸ“š πŸ‘¨β€πŸ‘§ _DOMUN KANWATA_ πŸ‘©β€πŸ‘§ Na( Maryam amuhammad jibril) Dasunan Allah mai rahama mai jinkai....✍ 5⃣5⃣ ( sorry jiya nayi nayi mistake nasa Sheraton instead of shoprit) """" haka kuwa akayi da yamma abba yaje yasamu Umma da maganar tayi farin ciki sosai kuma tayi addu'ar Allah yasa alkhairi fatan ta daya Allah sa asma'u ta amince da zancan godiya abba yayi mata yatafi akan idan asma'u tadawo tagayamata yana son ganinta Daren ranan haka sarah tayishi banda kuka ba abunda take idonta ya kunbura yayi ja har wani zazzabin wahala yarufeta se sambatu take ita kadai kamar mahaukaciya gashi taki cin komai kuma taki fadan abunda yake damunta har aysha tagaji da tambayarta tayi tafiyarta yanzu haka ma kuance take akan gado ta lulluba da bargo se kyarman sanyi take hawaye nadiga akan pilonta Aysha ce taturo dakin tashigo dasauri takaraso bakin gadon tana fadin subhanallah sarah jikin ne har yanzu Ko kanta takasa dagawa da kyar ta iya bude idonta takalleta Bargwon aysha tadan yaye tana taba goshinta da yayi raw kamar garwashi Tashi kisha magani tafada tana balle mata magani taimaka mata tayi ta tashi zaune da kyar ta yarda tasha maganin hawaye wani nabin wani Cike da taikaci aysha tace wai ni sarah meyake damun kine kike wannan kuka haka kamar an aikomaki dasakon mutuwa Kawda kai tayi tana share hawayen fuskarta batace komai ba hanyar fita aysha tanufa tana fadin gaskiya zanje nakira AK dole yasan halin da kike ciki tunda ni kinki gayamun Saurin riko hannunta sarah tayi tace a'a base kinkirashi ba zo zan gayamaki Dawowa tayi tazauna tace to ina jinki Labarin wayar dataji ahmad nayi tabata da kuma yanda suka kwashe Cike da mamaki aysha tace amma wallahi ahmad yabani mamaki shiyasa ance kaidai kaga mutum shi yanzu ko kunyar AK bazaiji ba ko yana ganin bazai iya daukan mataki akansa bane to wai ma ita yarinyar yar waye agarinnan Kai sarah takauda hade da tabe baki tace bansanta amma wallahi zan nemota bazan barta ba i will punish her senasa tayi kuka kamar yadda tasa nayi I will make her suffer sannan kuma inkasheta Tashi sarah tayi tanufi bathroom tana boye dariyarta tace yanzudai bari nahada maki ruwa kiyi wanka kyadan ji karfin jikinki inyaso semuyi magana amma gaskiya abunda kika ma ahmad Sam baki kyewta ba Sunkuy dakai sarah tayi tace nasani nima I don't know what come over me nakasa controlling kaina ne amma ko zuwa anjima zanje nabashi hakuri Dadai yafi aysha tafada tana rufo kofan toilet din Hannu sarah takai tadauki wayarta ta kunna photon ahmad ne akan screen din wayar yana sanye dawasu Kayan sport farare da eyepiece akunnensa yana murmushi yayi kyew matuka Rungume wayan tayi akirjinta wasu hawayen nakara gangarowa akan kuncinta cikin muryan kuka tace 😭 don't leave me please ahmad I can't live without u asma'u ce tafito cikin shirinta nafita kusan Umma tazo tzauna tana fadin yanzu Umma bazaki gayamun waye yazo Neman aurena wajan abba bako Murmushi Umma tayi tace a'a inkinje kyaji ai ance waka abakin mai ita tafi dadi fita tayi tana fadin to senadawo Har tayi nisa se kuma tayanke shawaran bari tabiya wajan aikin su ahmad maybe zata sameshi acan Haka kuwa akayi sedai tanazuwa securities din suka hanata shiga wai dole seda izinin Wanda tazo wajansa zasu barta tashiga tayi juyin duniya sunki gashi rana se dukanta take Yahya ne yazo wucewa yahangeta atsaye tarike kugu jitake kamar tahausu da duka Nufo wajan yayi yana fadin wanake gani haka kamar asma'u Murmushin farin ciki tayi tace nice Yaya dama nan kake aikine Eh yafada yana kallon guards din yace lafiya naganki anan Zufar goshinta ta goge tace wallahi wani abu nazo yi shine wa'yannan gumakan suka hanani shiga tafada tana Satan kallon guards din dasuka zaro ido jin ankirasu gumaka😳 Dariya yahaya yayi yana kallon guards din yace let her in she is my sister Sannan yakalli asma'u yace muje ko gaba yayi tana biye dashi atsorace tawuce gaban guards din dan yanda suke kallonta ganin take kamar zasu rufeta da duka Seda ya nuna mata office din ahmad sannan ya juya yana fadin idan kinfito kisameni abakin get zan baki sako ki kaywa zainab Seda tadan jima atsaye kafin ta kuankuasa kofar Daga ciki ahmad yabada izinin Shiga Ahankali ta tura kofar tashiga wani daddaden kanshin turarene yadaki hancinta ga sanyin AC dayaratsata lumshe ido tayi ahankali tayi sallama Dagowa ahmad yayi yana amsa sallamar Mikewa yayi da murmushi afuskarsa yanuna mata kujera yana fadin bismillah zauna mana thank u tafada tan zam akan kujera Murmushi yayi yace asma'u ko damamaki tace ya akayi kaganeni Tashi yayi ya nufi dan karamin frig din dake gefe yadauko goran ruwa da cup sannan yadawo gabanta yatsaya seda yatsiyaya mata ruwan yamika mata sannan Yadawo yazauna yana fadin kuna kama sosai da my flying bird shiyasa naganeki sunan ki kuma abakin khadeeja naji saboda duk rabin firarmu to akanki ne Murmushi tayi takurbi ruwan hannunta sannan ta ijiye cup din tana karema office din kallo ahankali ta furta wannan office ne ko wurin hutawa Murmushi ahmad yayi yace me kika gani Kunyace takamata dan sam batasan maganr tafito fili ba Murmushi tayi tace nice decoration Thank u yafada yana tunanin to mezai kawo asma'u office dinsa yama akayi guards suka barta tashigo Kamar tasan tunaninda yake ta Katse shirun dafadin ahmad nazo baka hakuri ne akan abunda khady tamaka kuanaki duk da nasan maybe kama manta but I can't have peace of mind ahmad ina kaunar khady sosai bana iya jure ganin abunda zai cutar da ita komai kankantarsa sadda kanta tayi kasa taci gaba dafdin nayarda da kai nasan kana sonta tsakani da Allah dan Allah karka cutar da ita I know she is so disturbing sometimes but she have a good heart Idan tamaka laifi ka kwatanta mata zata gane amma dan Allah kar kace zaka rabu da ita Tunda tafara magana ahmad yake binta da ido yana murmushi shi kawai kamarsu da khadeeja take birgeshi Tashi yayi yadawo kujeran kusa da ita yazauna yace aunty!!! Saurin dago kai tayi tace aunty kuma Eh yafada yana danne dariyarsa Idan ma dan wannan ne ki kuantar da hankalinki ni naga deeja inaso kuma aurenta zanyi namaki alkawarin zan kula da ita fiye da yadda zan kula dakaina Idan ma baki yarda ba se in ware maki daki daya agidan dazamu zauna kinga se ayi komai agabanki yakarashe maganar yana kwashewa da dariya Itama dariyar tayi tace a'a ai abun bai kai haka ba nunashi tayi da yatsa cikin sigar wasa tace amma idan ka cutar da ita to ko abangwan duniya kuke se kaganni kuma zan dauki mataki Hannunsa daya yadora saman kansa yana murmushi yace I promise aunty Kauda kai tayi tana murmushi tace Now stop calling me that aunty I don't like it Dariya suka sa suduka kamar wa'yanda suka shekara dasanin juna Daidai nan sarah tazo shiga office din tahangosu suna dariya cak tatsaya tana kallonsu nunfashinta na barazanar dawkewa wasu hawaye masu zafi suna tsere akan kuncinta nan take taji kanta nasarawa Saurin labewa tayi ganin suna fitowa daga office din Muje mana inzaga dake kiga company dinmu ... ahmad yafada yana rufo kofar office dinsa Ido asma'u tazaro hade dafe kirji tace nikuma asuwa?? rufamun asiri Dariya ahmad yayi yace to muje inrakaki mana Kai ta girgiza tace a'a koma kawai kayi aikinka daganan ma nagode Sarah dake labe tana jinsu jitayi kamar tazo tarufe su da duka nan take taji tatsani asma'u Murmushi yayi yajuya yana fadin to nine da godiya ki gaida umma senazo insha Allah Ganin Ahmad ya koma office yasa sarah tayi saurin bin bayan asma'u koda asma'u tafito ta isko yahya yana jiranta abakin get wata sakon takarba sukayi sallama ta tafi Yana juyowa yaga sarah tsaye agabansa taharde hannaye tana hararensa dajajayen idanuwanta Gaidata yayi zai wuce tace kai zonan Dawowa yayi gabanta yatsaya yana fadin gani ma dawre fuska tayi tace wacece waccan da naganku tare Sunkuy dakai yayi yace nasanta sosai madam kanwata ce kuma a unguwa daya muke tsaki tayi tace waye ubanta anan garin Saurin dago kai yayi yakalleta Dakai nake malan ... tafada tana daka mai tsawa Hade fuska yayi yace malamin makaranta ne sunansa malan mahammadu ana kiransa magaji amma yajima da rasuwa Hannu Tamika mashi tace bani wayanka Damamaki yace wayata kuma Daure fuska tayi tace ko ban isa bane Mikamata wayan yayi yana ji kaman ya tattaka ta Fisge wayan tayi ahannunsa tashiga wurin pics tana dubawa cikin Sa'a kuwa tahadu da photon asma'u Wanda sukayi da zainab ranan suna murmushin mugunta tayi lokacinda tayi cropping photon asma'u ta tura awaynta cilla masa wayan tayi tajuya kamar zata tashi sama tanufi office din ahmad Dakarfi ta bige kofan tashiga Saurin dagowa yayi ganin sarah ce yasa yahade fuska yaci gaba da abunda yake bai kara kallon inda take bama Ahasale takarasa ta fizge takardan hannunsa tana fadin yaushe kafara shigo dayan mata office dinka Hannu yadaga mata yace sarah ya isa haka kiyi abunda yakawoki kibarmun office dina Kugu tarike tana fadin ba inda zani seka gayamun wace karuwace tafito daga.... Bata karasa ba yakifeta da wani wawan mari seda kanta yabugu da table dafe kanta tayi tare dasakin wata kara [18/07, 15:03] Hubbey Frd Ameena Kn: πŸ“šπŸ“šπŸ“šπŸ“šπŸ“šπŸ“š πŸ‘¨β€πŸ‘§DOMUN KANWATAπŸ‘©β€πŸ‘§ Na( Maryam Muhammad jibril) Dasunan allah mai rahama mai jinkai.....✍ 6⃣0⃣ Gudu yake banawasa ba sarah duk tagama tsorata dayaninsa Sam batayi tunanin abun zaikai hakaba gaba daya yanayinsa ya canza Yana isa company tun kafin yagama parking yafito daga motar zagayowa yayi tabangarenta yafincikota yana rike da hannunta suka nufi ciki Ma'aikatan wajan suna gaidashi amma ko kallonsu baiyiba binsu sukayi da kallo suna mamakin yaw lafiya AK yashigo awannan halin Office din ahmad yanufa direct yana isa ya banke kofar yashiga Saurin dagowa ahmad yayi dan ganin waye saurin mikewa yayi tsaye yana fadin AK lafiya meyafaru Wurgi da sarah yayi har saida tafado kan ahmad Cike da mamaki ahmad ya maidata gefe daya yanufo AK yana fadin easy AK wai meyake faruwa ne Nima bansani ba kawai ina zaune tazo tasameni da wata banzanr magana wai kafasa aurenta....... baka sonta...... baka menene ...... Shirme dai iriri Sunkuny dakai ahmad yayi yana murza hannunsa Kusa dashi AK yamatso yakama hannunsa yana fadin bawai nazo nan dan nayarda da abunda tafada bane sedan ina so ka karyata abunda tafada agabanta taji I know u can never do this to me ever Shuru ahmad yayi yakasa furta koda kalma daya Cikin muryan kuka sarah tace why are u silent kafadamasa abunda kafadamun mana ai bandauka zakaji kunyar abunda ka aikata ba kafadansa AK yadafa yace friend say something kawai kacemun karyatake I will punish her for hurting u riko hannunsa yayi cikin rawar murya yace AK ...I'm... I am Sorry ...but....she is....she is right what do u mean??? AK yafada yana kafe ahmad da jajayen idanuwansa Nasan ban kyewta ba danayi karyan cewa inason sarah tunda farko amma alokacin bansan mezance ba saboda abun yazomun abazata kuma bazan iya cewa banasonta abainan jama'a that will make u feel bad Shiyasa kawai na amsa mata but I am really sorry Ja dabaya AK yayi yazauna akan kujera tare dasauke wata nannayar ajiyar zuciya yana shafa kansa Sannan yadago yakalli ahmad yace Fine Naji wannan amma dagaske bazaka aureta ba shi kuma akan wane dalili Matsowa kusa dashi ahmad yayi yana fadin AK ni inawa sarah kallon kanwata ne bantaba jin wani Abu dayashafi soyayya atare da ita ba ada nayi niyyar zan aureta ahakan amma daga baya nafara son wata yarinya kuma aurenta zanyi Inada tabbacin idan na auri sarah bazan iya yin adalci atsakaninsuba saboda bazan iya controlling feelings dina akan wacce nakeso ba to akan wane dalili zan aureta Karan bude kofa sukaji koda suka juya sarah suka ga tafita daga office din ko ba'afada sunsan kuka take Tunda yafara magana AK kebinsa da wani irin kallon danakasa fassara manufarsa cikin sanyin murya yace Ahmad kabani mamaki senake ganin kamar ba ahmad dina bane wannan Yaushe kafara boyemun sirrinka yaushe kafara soyayya meyasa zakama kanwata danafiso fiye dakomai karyan cewa kana sonta seda nagama sakankacewa zaka aureta shine zaka zomun da wannan maganar nayarda dakai fiye dayadda nayarda dakaina amma meyasa zaka yaudareni Riko hannunsa ahmad yayi cikin rawar murya yace AK dan Allah kafahimceni nima bansan ya akayi nafara sonta ba bansan miye soba se akanta ni kaina ina mamakin yawshe nayi zurfi asonta dahar nakejin bazan iya rayuwa batare da ita ba Turesa AK yayi dakarfi harsaida yafadi kasa cikin kakkawsar murya yamike tsaye yana fadin Ba abunda zaka gayamun ahmad koma wacece inada tabbacin baka jima da haduwa da ita ba Yaushe har kayi nisa asonta miye ma so ahmad akan sone zaka cutarmun da kanwata har zaka iya dawkan hannu kamareta kafi kowa sanin irin son datake maka baka tunanin halin dazata shiga idan tarasaka kuma ita wacce kakeso din kanada tabbacin cewa tana sonka ?? Tashi ahmad yana kakkabe rigarsa yazo gaban AK yatsaya yana fadin wai yanaga ka dauki abun dazafi ne AK Nasan nayi laifi ban kyewta ba amma tunda wuri nayi kokarin sanar dakai sedai Sam kaki kasaurareni Yes dagaske banjima da haduwa da ita ba amma shi so lokaci guda yake faruwa kuma bandamu yasoni ko kar tasoni ba Abu daya nasani shine ni ina sonta kuma mutuwa ce kawai zata hanani aurenta zancan halin dasarah zata shiga kuma ai bani kadai bane namijin dayarage aduniya ba zata iya samun Wanda zata so yasota har yasa tamanta dani amma ni bazan iya aurenta ba saboda bazan iya yimata adalci ba ni kuma bana fatan na cutar da wacce kakeso fiye da kowa aduniya cikin murya mai kaman rada AK yace kenan yanzu kana nufin .....ba zaka ....auri kanwata ba kenan Sunkuy dakai ahmad yayi cikin sanyin murya yace I am sorry friend but I can't Jadabaya AK yafarayi yana fadin sorry !!! Sorry!!! ur sorry means noting to me since u broke my trust bantaba tunanin zaka ki jinina ba ahmad bantaba tunanin zaka So kanka a abotar mu ba Daidai nan yafice daga office din yana rufo kofar dakarfin gaske Zaunawa ahmad yayi yajiginar dakansa hade da lumshe ido yana murza goshinsa da yafara daukan zafi Ahankali yake fadin Meyasa bazaka fahimceni ba AK khadeeja nakeso ita kadai zan iya aura nazauna da ita na kula da ita kamar yadda nama yayarta alkawari bazan iya auren kanwarka ba bazan iya zama da mace biyu ba sarah bata dace dani ba kace naso kaina dan naki auren kanwarka nikuma idan kahanani auren wacce nakeso saboda kanwarka ni kaso kenan kome!!!! AK yana isa gida bangaren sarah yanufa kafin yakarasa aysha tazo ta tareshi tana fadin AK sarah A firgice yarike hannunta yana fadin meyafaru da sarah ?? Ban saniba tundazu tashigo tana kuka kuma tarufe kofar dakinta taki tabude Dagudu yakarasa kofar dakin yafara knocking sedai shiru ko motsinta bayaji duk yarude se buga kofar yake kamar zai ballata yana magiyar tabude amma taki Cike da damuwa yace sarah open the door please come down OK? I am here everything will be fine I promise Cike da mamaki aysha tace wai meyake damunta ne Ko kallonta baiyiba bare tasa ran zai amsa mata bashiri yakira dai daga cikin ma'aikatan gidan yataimaka mashi suka balla kofar Kuance suka sameta atsakar dakin Sam ba alamun nunfashi atattare da ita dagudu yakarasa wurinta yajanyota jikinsa yana kiran sunanta amma shiru yaron gidan mai suna Nura shine yayi dabaran kiran family doctor dinsu awaya aysha banda kuka ba abunda take Hannunsa yakai daidan saitin zuciyarta amma baiji alamun tana bugawa ba nan take jikinsa yafara rawa jijjigata yake dakarfin gaske kamar zai karyata yana fadin a'a a'a sarah please don't leave me keda grany kunake gani naji dadi arayuwata idan kika tafi yazanyi for god sake say something gefen fuskarta yafara bubbugawa cikin rawar murya yake fadin kitashi namiki alkawarin zan taimaka maki kinji zansa ahmad ya aureki I promise I will make u proud kinsan duk abunda kike so ina maki please wake up ganin ba alaman zata tashine yasa yafashe dakuka ya rungumeta tsam ajikinsa yana surutai kala kala Ahaka doctor din ya iskosu dasauri AK yamike daga zaunen dayake akasa yanufi doctor yana fadin doctor please help my sister Bring her to bed ...doctor din yafada yana ijiye briefcase din dake hannunsa Cak yadauketa yadawrata kan gado doctor yamatso yafara dubata yana fadin idan badamuwa kudan jirani daga waje AK yakasa fita seda aysha taja hannunsa tafita dashi Cike da takaici yace wai tun kika ji shiru adakin meyasa baki kirani ba Nakira mana amma wayanka akashe Ina mutanen gidan suke Bansaniba tafada tana ware hannayenta Bangaran inna ladidi yanufa ahasale yafara buga musu kofa rai bace tafito tana fadin kai lafiya wayene natsani.....ganin AK datayi atsaye fuskarnan a murtuke yasa ta hadiye sauran maganarta tana fadin oh AK Ashe Kaine Fuska ahade yake fadin kinji karan knocking din danamaki amma bakiji lokacinda nake balla kofar dakin sarah ba Meyasamu dakin sarah da ake balla kofar Mutuwa tayi Afirgice tace mutuwa kuma AK subhanallahi yo idan ma mutuwar ce fisabilillahi haka zaka fadamun ita salan zuciyata tabuga Kai yakauda hade da cije lebensa nakasa sannan ya juyo yace Ankayata wancan babban palon ne badan yazama na ado ko na family meeting ba a'a sedan yazama cibiyar kara donkwan zumunci da kaunar juna manufarsa kenan amma dazaran kunbiya bukatar Ku acan shikenan se kowanne yashige bangaransa bawanda zaisan halin da dan uwansa yake ciki Kuma nagayamaki kanwata tamutu amma har yanzu dai ke takanki kike wai kada zuciyarki tabuga bana tunanin ma kinada zuciyar ajikinki Hade fuska tayi tace to wai meyasamu sarah ne naga duk kafita hayyacinka ne Idan kinso sani kizo kiduba da kanki .... Yafada yana juya baya yakoma Dakallo tabisa seda yabace mata sannan ta tabe baki takoma ciki tana fadin dama kasaba ai idan wani Abu yasamu sarah to ko bacci hanamu kake wai mutayata jaje bare kuma ance batada lafiya ai munshiga uku shiyasa na guanmace ni nayi ciwo akan sarah koba komai nasamu nayi bacci mtswwwww Suna tsaye abakin kofa shida aysha doctor yafito dasawri AK yakarasa wajansa yana fadin doctor ya jikinta meya sameta hop she is OK Dafa kafadansa doctor yayi yace be strong man kanwarka lafiyarta kalau kawai dai damuwa ce tayimata yawa kuma da alamum tajima rabonta da abinci Juyowa yayi yakalli aysha saurin sunkuy dakai tayi tana wasa da yatsunta maida kallonsa yayi kan doctor yace To yanzu ya jikinta Jiki dasauki yanzu dai namata allura tana bacci ga wannan idan ta tashi

Chapter 7 of 35