nusaiba se Ku kawo daga baya mayi magana
tashi tayi jiki asanyaye tafito daga wurin tana sharan kwalla
Karo sukaci da ahmad zai shiga atsorace yace deeja menene yanaga kinfito meyasami Umma
Banza tayi dashi taje jikin mota takifa kai tana rera kuka
dawowa yayi wurinta yana tambayar meyafaru
Daidai nan su sarah suka iso asibitin aguje tanufo inda suke ta matse khadeeja jikin motar tana fadin allah yakamaki munafuka wallahi yau nizanyi ajalinki
Kokarin rabasu ahmad keyi amma yakasa
Kamar mahaukaciya haka sarah tadawo gashi tarike wuyan khadeeja gam taki sakinta
Ahasale yafizgota daga jikin khadeeja yayi wurgi da ita gefe seda tafadi sannan yanunata da yatsa yace wallahi kika kara tabata se tattakaki awurin mahaukaciyar banza kawai
Tasowa tayi tanufosa tana kuka tace eh nayarda ni mahaukaciya ce ahmad amma kuma kai kahaukatani
Riko hannunsa tayi tana nuna khadeeja tace dame wannan tafini ahmad mezakayi dawannan karamar yarinyar dabata masan miye soba
Nice nakesonka da gaske ahmad zan iya mutuwa in narasaka
Kwace hannunsa yayi yabudema khadeeja mota tashiga sannan shima yazaga yashiga suka wuce
Da kallo tabisu baki bude se hawaye dasuka wanke mata fuska
Jan hannunta aysha tayi suka koma mota suma suka bar wurin
Bayan dan lokaci Umma tafarfado tana kiran asma'u
Aguje suka fada dakin su duka kusanta asma'u taje tazauna tana kuka tace na'am Umma
Shafo gefen fuskanta tayi cikin muryar mara lafiya tace asma'u dagaske ne AK yasakeki da gaske khadeeja tagudu da ahmad
Shiru asma'u tayi takasa cewa komai se hawaye dake diga daga idonta
Damamaki grany tace wane saki kuma take magana kodai tayi mafarkine
Shuru kowa yayi adakin bawanda yabata amsa
Juyowa tayi tana jifan AK da kallon tuhuma
Saurin matsawa yayi kusan gadon yakamo hannun Umma yana murmushi yace haba umma wace irin magana ce wannan taya zan saki asma'u haka kawai batayimun komai ba bayan ina sonta koma wa yafadamaki karyane kidaina damun kanki yan....
Bai karasaba takatseshi dafadin amma dagaskene ahmad yafasa auren sarah sun gudu da khadeeja ko
Kauda kai yayi ya zare hannunsa daga nata yana fadin Umma kibar wannan maganar khadeeja tana nan bataje ko ina ba yanzu dai kina bukatar hutu kidaina daga hankalinki
fita yayi yana fadin bari naje doctor nason ganina kudan barta tahuta
Binbayansa asma'u tayi sukashiga office din doctor din
Bayan yagama yan rubuce rubucensa yadago yana murmushi yace waye nata acikinku?
Atare sukace ni..
Juyowa sukayi suka kalli juna sannan AK yakalli doctor din yace muduka ya'yanta ne meyafaru
Cire glass din idonsa yayi yana sauke ajiyar zuciya yace well
Wato zuciyarta ce tabuga sanadin ji ko ganin wani abunda yadaga mata hankali dama kuma tana fama da ciwon zuciya to yanzu dai munyi nasarar yimata aiki amma akiyaye nan gaba kar irin haka takara faruwa zaku iya rasata duk wani abunda zai bata mata rai akiyayeshi
sannan akula sosai da maganinta
Bayan yagama yimasu bayani yabasu list din magungunan daza abukata da sauran abubuwan sannan suka fito
Wurin Abba AK yanufa yabashi takardar sannan yace zaije mota yadauko kudi se asiyo maganin
Gudiya yamasa yana samai albarka
Murmushi yayi yace Abba bana bukatar godiyarku ni Dane awurinku kome nayimaku addu'a kawai zakumun ita nafi bukata ba godiya ba
Yana kainan yaraba tagefen asma'u yawuce batare da yakalleta ba
Da kallo tabisa tana murmushi yar yabacema ganinta sannan tazauna tana sauke ajiyar zuciya
Washegari da yamma aka sallami Umma gaba dayansu suka koma gida harda su grany
Bayan sunci abinci sundan yi fira suka shirya zasu tafi
Ganin asma'u batada niyyar tafiya yasa Umma tace asma'u kitashi kutafi mana
Langwabe kai tayi tace Umma kidan barni nazauna har kiji sauki
"a'a tashi kitafi ni naji sauki alhamdu lillahi kuma ga inna da Ummi ai ba nikadaibace
Shagwabe fuska tayi tana kallon grany tace grany kirokammun Umma tabarni se gobe
Murmushi grany tayi tace a'a ni ba ruwana tashi ga mijinki can awaje kitambayeshi idan yabarki ba matsala
Ganin dagaske suke yasa bashiri tafito waje Neman AK
Cikin mota ta iskoshi zaune yana jiransu
Karasawa tayi jikin motar tatsaya kanta akasa tana tunanin mema zatacemasa
Sauke glass din motar yayi yaleko yana fadin kinada magana ne
Sosa kai tayi tace dama dama sonake inkuana anan harzuwa gobe
Kauda kai yayi yana maida glass din motar yace u don't need to ask me dama zaki zauna gaba daya sonake
Shuru tayi takasa cewa komai kuma takasa motsawa seda tadan jima kana tajuya takoma ciki tana mamakin meyasa taji zafin maganarsa bayan tasan ba sonta yakeba
[19/07, 16:58] Hubbey Frd Ameena Kn: 📚📚📚📚📚📚
👨👧 _DOMUN KANWATA_ 👩👧
Na( *Maryam mhd*)
1⃣0⃣5⃣
Washegari dasafe AK yasauko daga bangarensa yana naman sarah dan tun jiya rabonshi da ita aysha ya tambaya tace sarah tana dakinta tun jiya take kuka har yanzu bataci komai ba
Dakinta yanufa ahankali yatura kofar yana sallama
Can karshan gado ya iskota zaune tasa kai aguywa tana aikin kuka
Yajima atsaye bakin kofar yana kallonta kafin ahankali yataka zuwa inda take
Kusa da ita yazauna yana shafa kanta cikin sigar lallashi yace
Sarah idan nace nasan halin dakike ciki nayi karya saboda duk yanda ake fadin soyayya ni bahaka nasanta ba
nakanyi mamakin yanda mutane keshiga tashin hankali idan suka rasa masoyansu
Nasan zakaji zafi amma bansan yazafin yakeba
Ni hasali ma banyarda akwai wata aba ba wai soyayya
ganinki awannan halin yasa nafara tawsaya ma masoya kuma hakan yasa tafita araina tunda ba komai acikinta se kunci dawahala
Nasan kina son ahmad kina kaunarsa kina son rayuwa dashi amtsayin mijinki
Amma inaso kigane akan yima mace auren dole tazauna amma ba namiji ba
ada nadauka ahmad zai iya aurenki yazauna dake ahakan amma lokacinda nagansa da khadeeja natabbata koda kin auresa bazaki ji dadin zama dashiba saboda nafuskanci bakaramun so yakemata ba
Dan haka kiyi hakuri kimanta da ahmad kiyi addu'ar allah yabaki miji nagari Wanda yafi ahmad kuma yasoki fiye da yanda zaki soshi
Ko kuma ni kibani dama cikin abokanaina nazaba miki Wanda nayarda dashi nasan zakiji dadin zama dashi
Tunda yafara magana bata dago takallesa ba sema kukanta dayakaru
seda yasa hannu yadago kanta sannan tabude jajayen idanuwanta tana kallonsa
Handkerchief yaciro a aljihunsa yafara share mata hawaye yana fadin kinyi shiru bakice komaiba ko kinbani damar nazaba miki ne
Kauda kai tayi cikin dasashshiyar muryanta tace
Yaya ni nagirma nakai lokacinda zan tantance abunda yadace dani da Wanda baidace ba basai kazabamun ba
Ko limamin kasar maka zaka kamun bana bukatarsa kuma bazan so shiba ni ahmad nakeso kuma shi kadai zan aura idan bazaka sa ya aureni ba leave it to me ni zan iya ...
Cike da mamaki yake kallonta tunda tafara magana
Cikin wata iriyar murya yace sarah ni kike gayama haka
Ni kike gayama kin girma kinsan abunda yadace dake
Koda yake ba laifinki bane ni nabata ki
tun kina Karama nareneki da hannuna duk abunda kikeso shi nake maki baki taba Neman wani Abu kinrasaba sedai inyafi karfina
nayi kokarin bata abotar dake tsakanina da ahmad duk saboda ke
amma yanzu ki kalli kwayan idona kina gayamun wai basai nazabamaki ba kinsan abunda yadace dake
Tashi yayi yanufi hanyar fita daga dakin yana fadin
Fine nabarki kizabi abunda yadace dake amma karki kara sakani cikin duk wata damuwarki
Saurin tashi tayi tarungumo shi tabaya tana rusa kuka tace Yaya dan allah kayi hakuri bahaka nake nufi ba raina ne abace I am sorry
janyeta yayi daga jikinshi yafita batare da yace komai ba
bangaren grany yanufa bayan yayi breakfast yakwanta anan Palo yana kallo
Fitowa grany tayi daga daki tazauna daga gefe tana fadin abidi yau kaje kaduba Maman su asma'u kuwa
girgiza kai yayi alamar a'a
"Bangane a'a ba to tashi kaje daga can ma kabiyo da matarka
Pilo yasa yarufe kansa kamar zai yi kuka yace ooooo grany dan allah kibarni nadan huta ita batasan hanya ba da intaje ni nake zuwa dawkota
Haba tarike tana salati tace yau naga abunda yafi karfina ni mairo
Kai yanzu abidi matarka bata kuana gida ba amma kana mitar zuwa dawkota
anya kwa abidi kanada cikakkiyar lafiya kuwa
tashi yayi yana yarfa hannu yafita daga Palon
zaune yake abayan mota driver ketukasa har suka isa
fa'iz dake filin gidan yana buga kwallo ne yazo yabude masu get
bayan yashiga yayi parking AK yafito daga motar yana kallon fa'iz dayayi kamar baisanshiba
Murmushi yayi yakarasa wurinsa yafara buga ball din
tsaye fa'iz yayi yana daure fuska yagaidashi ciki ciki kamar mai koyon magana
Dafashi AK yayi yana amsa gaisuwarsa yace come on boy wai fushi kayi dan namareka ranan
Kauda kai fa'iz yayi baice komai ba
"OK I am sorry bansan meyakaika dakin ba amma nasan abunda tafada karyane
She is my sister kaga bazanso hakan yafaru da ita ba
Kaima kuma kanina ne bazan so ace ka aikata hakan ba
Amma nagane rashin fahimta aka samu tsakaninku
Karkato da kuncinsa yayi yana shagwabe fuska irin nayara yace
Idan kuma kana fushine dan namareka to gashi Karama
Dariya fa'iz yayi yana fadin haba yaya allah ya kyewta
Dariya shima yayi ya wuce cikin gidan yana fadin bari nagaida Umma nazo muyi kwallo
Yana tura kofar palon yahadu da khadeeja tafito daga kitchen rike da plate din indomie ahannunta
Sunkuy dakai tayi tana gaidashi
Bayabo ba fallasa ya amshi gaisuwarta yana zama apalon
Ciki ta wuce ta sanardasu ga AK yazo
Bayan sunfito suka gaisa yakoma kusan Umma yazauna yana fadin Umma ya kike ji yanzu bawata matsala daiko
Murmushi tayi tace ba komai abid nagode da kulawa allah yasaka da alkhairi
Ameen yafada yana kallon inna yace inna kefa
nifa harmukaje asibiti banyarda Umma ce batada lafiya ba nadauka kece
Daure fuska tayi tace ni makiyiyarka ko to ta allah bataka ba
Dariya yayi yace allah baki hakuri daga magana ai ni masoyinki ne
kallon khadeeja Umma tayi tana fadin Ashe abunda wainnan sakarkarun yaran sukayi kenan ai da kazanemun ita wallahi khadeeja bataji ko ina ita ina ahmad oho
Tashi tayi tafita idonta cike da kwalla
Murmushi inna tayi tace harkan yara se hakuri
Sannan takalli AK tace kungaisa da Abba kuwa
Girgiza kai yayi yace a'a ni yanzu nashigo yana nan ne
"eh yana bangarensa
Tashi yayi yanufi bangarensu Abba
yana Isa ya iskosu zaune apalo suna fira harda asma'u
Bayan sungaisa yashiga firan anayi dashi sedai jifa jifa yana kallon ALi da asma'u dasuka koma gefe suna tasu firar
kiran khadeeja tagani yashigo wayanta da mamaki tatashi tafito daga palon
karo sukaci da khadeeja zata shigo fuskanta sharkaf hawaye
Gefe tajata tana fadin lafiya khady meyafaru kike kuka AK yamiki wata maganar ne
Daidai nan AK yazo wucewa yatsaya yana sauraronsu
Cikin rawar murya khadeeja tace baicemun komai ba amma naji kunyar hada ido dashi
Gaskiya koda son ahmad zai kasheni dolene nahakura dashi saboda bandace dashiba
Sarah tana sonsa idan ya aureta ahankali zai fara sonta
Farin cikin sarah shine na AK ni kuma naki shine nawa
Gaskiya dole ne ahmad yazaba ko ya auri sarah ko yahakura damu gaba daya amma ni bazan iya aurensa ba
Barin wurin AK yayi yanufi motarsa yashiga
fa'iz yabudemasu get yana fadin Yaya har zaka tafi bakace zamuyi kwallo ba
Murmushi yayi yana daga mai hannu harsuka fita batare da yatankasa ba
Yana fita yakira ahmad awaya seda takusa katsewa yadaga
Bayan sungaisa sama sama AK yace kana gida ne
eh.....
Yafada atakaice
Katse kiran yayi yagayama driver gidansu ahmad zaikaishi
Numban sarah yakira amma har yamata 5 missed call bata daga ba
Shuru yayi ya jingina da kujera hade da lumshe ido yana tunani kala kala aransa har suka isa
yana isa bangaren ahmad yatura kofar yashiga zaune ya iskosa apalo
Ahmad naganinsa yamike tsaye
Kusa dashi yamatso yadafa kafadarsa yace
Friend inaso ka rufe idanuwanka kamanta lokacinda muka fara samun matsala dakai kamanta lokacinda sarah da khadeeja suka shigo rayuwarka katuna lokacinda muke dagani sekai kana kirana supper hero ina kiranka supper man
Lokacinda dayanmu baya iya bacci se yatabbatar da lafiyan dan uwansa lokacinda za'a dakeka amma nine zanyi kuka lokacinda banada lafiya amma kai ne kejinya lokacinda zanji ciwo amma sekafini jin radadinsa
Shuru ahmad yayi idonsa arufe yana tuna duk abunda AK kefada seyaga kamar lokacin abun ke faruwa baisan lokacinda hawaye suka fara zuba daga idonsa ba
Cikin rawar murya AK yace
Yanzu gani agabanka ba amtsayin AK hausawee ba
amatsayin supper hero dinka
shin zaka amince ka auri wacce nakeso takasance matarka ??
Rungumesa ahmad yayi yana fashewa da kuka yace na amince supper hero nayarda zan aureta ko yanzu kake so muje adauramana aure wallahi zan zauna da ita kuma zan kula da ita
Jan hannunsa AK yayi yana sharan kualla suka fita daga gidan
Kofar gidansu khadeeja driver yayi parking
da mamki ahmad yace amma wannan ai gidansu khadeeja ne nan nakawota jiya meyasa muka zonan
Murmushi AK yayi yace inaso mubasu hakuri ne kuma kuyi bankuana da khadeeja kagayamata ka amince da auren tunda itama haka takeso
Bude kofa ahmad yayi yafita baice komaiba
Murmushi AK yayi yafito suka shiga tare
tunda AK yafita sarah ke kuka tana ganin kiransa amma taki dauka aysha dake kusa da ita tace sarah AK yamiki 5missed call amma baki daga ba
Kauda kai sarah tayi tana sharan kwalla
Daukan wayan aysha tayi takira numban amma yabarta amota har takatse ba adaga ba
Zama tayi kusa da sarah tana fadin meyasa baki dauki kiransa ba kikasan kome zai gayamaki
Numban drivernsa takira bugu biyu yadaga yana gaidata
Bata ansa ba tace kuna tare da AK ne
"Eh munatare dashi amma yanzu sunshiga wani gida shida sir ahmad
" ahmad fa kace wane gida suka shiga kenan
"bansani madam amma naji suna zancan wai sir ahmad ya amince zai yi aure
wurgi tayi dawayan tana daka tsalle tace sarah barka natayaki murna ahmad ya amince zai aureki
Saurin tashi sarh tayi tana washe baki tace allah dagaske wa yagayamiki
Kama hannunta tayi tana jujjuyata tace yanzu driver yacemun AK natare da ahmad kuma ya amince zai aureki
tsalle sarah tayi tafada kan gado cike da farin ciki tana kankame pilo
zaune suke apalon inna sunyi jigum jigum suna jiran abunda AK zai fada
ajiyar zuciya ya sauke yana kallon Umma yace
Umma kintabbata bakida matsala akan duk hukuncin da nayanke
Gyada tayi tace kwarai kwa abid nabaka dama kayanke musu duk hukuncin dayadace
Murmushi yayi yana kallon inna yace inna kefa
Tabe baki tayi tana juya furar dake hannunta tace yo ni meruwana dasu
Fa'iz dake kusa da ita se hadiyar yawu yake nabin furar dakallo
harara tabankamai yayi saurin kauda kai yana hade fuska
sunkuy da kai AK yayi yace
To ba wani Abu bane dama ahmad nazabama mata kuma ya amince da aurenta to shine nazo Baku hakuri akan abunda yafaru
Dagowa ahmad yayi yakalli khadeeja suka hada ido tayi saurin kauda kanta tana share hawaye
Murmushi AK yayi yana kallon ahmad yace
Friend zan baka auren kanwata kariketa amana da gaskiya ka kularmun da ita yanda yadace idan kacutar da ita to zan manta kai abokina ne nayima rashin mutunci
Shuru sukayi gaba daya ba Wanda yace wani Abu
Idon asma'u ne yakawo kwalla tana kallon kanwarta cike da tawsayi Umma ma haka kawai dai juriya take
Maida kallonsa yayi kan khadeeja yace
Deeja ga abokina nan nasan kina sonsa to kiyimai biyayya kuzauna lafiya banda rashin ji idan har kika muzguna masa to kema zanmanta cewa kanwata ce ke zan iskoki har gidanki nahukuntaki kinji ko?
Gaba daya suka dago suna kallonsa cike da mamaki
Murmushi yayi yace yakuke kallona ko baku gane menake nufi bane
cike da farin ciki ahmad yace friend kana nufin ka amince na auri khadeeja
Gyada kai yayi yace bama amincewa kadai ba nizan shirya komai kuma agidana za'ayi komai
Rungumesa yayi yana dariya mai sauti har yakasa magana
Cike dafarin ciki asma'u tadaka tsalle tafada kan khadeeja suka rungume juna suna murna
Ganin kowa ya rungume dan uwansa fa'iz yajuya yana washe baki garin rungume inna yabige furar dake hannunta tawatsamata afuska
Sadap sadap yatashi yabar wurin tun kafin tabude idonta
Sunjima ahaka kafin kowa ya natsu juyowan da AK zaiyi yaga fuskan inna sharkaf da fura har ba'aganin komai se idonta atsorace yamatsa gefe yana salati
Se alokacin kowa yalura gaba daya suka kwashe mata da dariya seda sukayi mai isarsu tana zaune tana binsu da ido
Daure fuska tayi tace kun gama ai kamar ta ce suci gaba suka kara sa wata dariyar
Tashi tayi tafita tana kwalama fa'iz kira
Umma tace amma abid idan akayi haka ba'ama sarah adalci ba
Murmushi yayi yace Umma nasan zataji wani iri amma kuma hakan shine yadace
Idan taga ahmad zai auri khadeeja dole tahakura dashi tunda tace batason kishiya
" to shikenan amma gaskiya ba agidanka za'ayiba abun seyamata yawa
Kusa da ita yazauna yana fadin ohhhh Umma kefa kikace duk hukuncin danayanke bakida matsala kuma tun ba'aje ko inaba kinfara complain
Murmushi Umma tayi batace komai ba tana gode allah dayabata suruki irin abid Wanda yadauketa tamkar uwa
Kallonsu Asma'u take da murmushi afuskanta tana jin wani yanayi datakasa fassara shi
Daki tawuce khadeeja nabinta
Abaya
Rungumota tayi tabaya tace ammah I am so happy gaskiya AK daban ne what a wonderful surprise !!!
Juyo daita asma'u tayi tana murmushi tace nima nayi farin ciki kanwata zata auri Wanda takeso
Murmushi khadeeja tayi cikin sigar tsokana tace
hmmmm kodai abunda kike ma farinciki daban ba ammah nahango wani Abu a kwayan idonki kamar kinfara son.....
Bata karasaba asma'u tayi saurin fadawa bayi hade da banko kofar da karfi kamar mai tsoron akamata
Dariya khadeeja tayi tafada kan gado tana ma allah godiya
Mutanan gidan kowa nazaune apalo sarah da aysha suka sauko cike dafarin ciki aysha tace kushirya fa zamu sha biki ahmad ya amince zai auri sarah
Carab grany ta amsa da fadin to in yakara guduwa fa
Dariya akasa gabadaya
Inna ameena tace nidai nashajin amarya tagudu ranan aure amma ango kam se akan sarah
Bashir yace gaskiya wannan karon inyagudu za'afara tsoron sarah
sadiya tace sedai muba dai cikin ma'aikatan mu
ahasale sarah ta dakatar dasu akan zata gayama AK inyadawo bashiri sukayi shiru
tashi AK yayi yama Umma sallama suka fita ita kuma tawuce daki kiran asma'u
Suna bakin mota ta iskosu
Bayn mota AK yashiga yana kallon ahmad yace muje ko??
dariya ahmad yayi yajuya yana fadin muje ina ??
Hahaha kuje dai ni sena gana da masoyiyata
Kofar asma'u takama zata shiga yarike yana fadin malama ina zaki shiga
Nan ...tafada tana nuna gefensa
Harara ya watsamata yana nuna mata daga gaba kusan driver yace ga wurinki can inzaki shiga inbakyaso kuma dama kinsaba da hawa mashin
Ganin ba alamun wasa afuskansa yasa tabude gidan gaba tashiga suka tafi
[19/07, 16:58] Hubbey Frd Ameena Kn: 📚📚📚📚📚📚
👨👧 _DOMUN KANWATA_ 👩👧
Na( *Maryam Mhd*)
1⃣1⃣0⃣
suna isa sarah tazo dagudu tarungumeshi tana fadin Yaya u are the best thank you so much
Dagota yayi daga jikinsa yace banganeba why are u thanking me
menayi
karasowa wurinsu aysha tayi tana dariya tace hmmmm kana so kamana surprise ko to nariga nasani Ahmad zai auri sarah yanzuma daga wurinsa kake
Kusa da grany yaje yazauana yana fadin
Ahmad zaiyi aure amma khadeeja zai aura ba sarah ba kuma nariga nagama magana karnaji wani yace wani abu
Cak sarah tatsaya tana kallonsa da mamaki bakinta bude amma takasa magana
Juyawa tayi wurin asma'u dagudu tahadata da bango cikin gunjin kuka tana fadin wallahi basu isa ba sedai bayan ranta
Saurin tasowa yayi yabanbaro sarah daga jikinta yana fadin sarah wai meyake damunki ne wai yaushe kika zama so stubborn ne
Kwace hannunta tayi takara nufan asma'u tana surutai
Fizgan hannunta yayi yanufi sama da ita yana zuwa dakinta ya wurgata kan gado cikin kakkausar murya yace wallahi kika kara tabata se nasabamiki what is wrong with u
Da mamaki take kallonsa cikin rawar murya tace Yaya ...ni...akan waccan ..
Katseta yayi dafadin ba laifinta bane sarah tayi kokarin hadaki da ahmad amma hakan baiyuwu ba ni nashirya auren dakaina badan nakuntata miki ba sedan kihakura da ahmad kinema wani
Saurin dirowa tayi daga kan gadon tanufi hanyar fita tana fadin wallahi banyarda kai kayi hakan ba Yaya itace tashirya komai kuma wallahi bazan barta ba
Janyota yayi tana kokarin kwacewa baisan lokacinda yadauketa dawani gigitaccen mari ba jikake tasssss
Cak sukatsaya daga ita harshi kamar gumaka
jadabaya tafarayi tana jifansa dawani irin kallo mai cike da mamakin abunda ya aikata
Hannunsa yakalla sannan yakalleta yana matsawa kusa da ita cikin rawar murya yace sarah I am sorry bansan...
Katseshi tayi dafadin karkatabani katafi kabani waje kai ba Yayana bane Yayana bai taba kai hannunsa ajikina danufin dukana ba
Tabata yaje yi tayi saurin shigewa bayi hade da banko kofar da karfi tana kara fashewa da kuka
Fita yayi daga dakin yanufi bangarensa
Dakarfi yatura kofar yashiga hade dazama kan kujera yana dafe kai
Kusa dashi asma'u tamatso adan tsorace tace
Ya....sarah...take...
is she ok...
Girgiza kai yayi yace she is not amma komai zaiwuce dama nasan sarah zatayi abunda yafi haka idan tarasa ahmad
Ruwa tazubomai mai anyi akopi tamikamai
ahankali yakai hannu yakarba yasha sannan yamika mata sauran
Zama tayi kusa dashi cikin siriruwar murya tace karka damu nasan tayi fushi yanzu amma zata sauko daga baya
abunda zakayi shine kasamu wani Wanda kayarda dashi kasan zai iya jure wulakanci daga gareta kuma kasan yana sonta seka....
Katseta yayi da fadin se inyi me wai inhadasu aure ? nifa natsani hade haden nan..
Dawawa tayi gabanshi tazauna daga kasa tana fadin ha'an to kabari kaji mezan ce mana ai bangama ba
Kauda kai yayi yace to inajinki
Murmushi tayi tace yawwa idan kasamu sawrayin sekasan yanda zakayi kahadashi da sarah batare da saninta ba shi kuma kagayamasa idan har yana son kabasa auren kanwarka to seyanemi soyayyarta kafin nan
Juyowa yayi yana kallonta yace to amma miye hikimar yin hakan
Gyara zama tayi tana murmushi tace uhmmm kaga yanzu matukar sarah tana ganin ahmad kawai amatsayin saurayinta to bazata taba hakura dashiba amma idan taga Wanda yake haukan sonta tun tana wulakantashi tana koransa har tafara sawraronsa daga nan kuma bazama tasan lokacinda ahmad zai fita aranta ba
Murmushi yayi yace wow!!! what a brilliant idea chitti
dan kwalinta ta turo gaban goshi tana kauda kai tace ahh dabakaki saurarena ba
Murmushi yayi yace hmmm I am really impressed amma kintaba soyayya ne
Saurin joyowa tayi tana kallonsa tace no bantaba yiba banmasan ya akeyiba
dariya yayi yace shiyasa naganki gaki ga kamarki amma wannan Ali din nagidanku ai nadauka saurayinki ne
" ina ba saurayi na bane cousin dina ne da dai yaso ya aureni iyayenshi suka hanashi
dariya yayi yace kice kema kintaba kwantai shiyasa kika samu experience akan rasa masoyi
Hade fuska tayi tace allah ba kuantai nayiba kawaidai wai suna so ya auri wata yarinyane babanta yanada kudi to daga baya kuma yarinyar tafasa auren
zaiyi magana kenan sukaji anturo kofa
Aysha ce tashigo taci kwalliya tana taunan cingam
Juyowa AK yayi yana kallonta yace ohhh hello babyyyyy!!
Karasowa tayi cikin yanga tazauna kusa dashi tana hura hanci
Kallonta asma'u tayi takwashe da dariya
atare suka kalleta aysha na hade fuska
Daure fuska AK yayi yace ke kinada hankali kuwa me akayi nadariya
tashi tayi tawuce daki tana dariya
hade fuska aysha tayi tace wallahi AK kasakema yarinyar nan dayawa tagama raina mutane
Shiru yayi baice komai ba yana kallonta
Da daddare AK na zaune bakin gado yana danna laptop ga Earp akunnensa yana jin waka se gyada kai yake yana bin wakar
asma'u tashigo rike da coffee dinsa kan bedside drowa tadorashi tana fadin ga coffee dinka nan
Baimasan tanayiba yamika hannu zai dauki wani Abu kawai yajishi cikin zazzafan coffee
Yar kara yasaki yana yarfa hannun cike damasifa yace wayace ki ijiye anan baki gayamun ba
Karasowa tayi tana duba yatsunshi tace bakajiba nace ga coffee dinka anan
Kallon bakinta kawai yake yana motsi amma baijin metake fada
Kuace hannunsa yayi yace dubawan me zakiyi bayan dagangan kikayi dakika kawo ai sekibani ko kigayamun
"Wai bakaji menace bane
"Jiki kawai bawani hakurin dazaki bani
damamaki take kallonsa secan tahangi Earp akunnensa hannu takai tacire Earp din tawuce dressing mirror tana maimaita mishi abunda tafada dazu
Painkiller tadauko takama hannunsa zata shafamai
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 15 Chapter of 35