fuska kamar yanda yaga tayi
Aysha takasa hakuri seda taje farm house din AK tana isa sani yacemata ai yakoma wurin matarsa nan take taji jiri na deebarta
Tafito kenan tahadu da AK zai shiga dan baisamu damar yin program dinsa ba lokaci yakure
Damamaki yace me kike anan
Kai zan tanbaya daga ina kake
Daga gidan abokina
Kusan shi tamatso tace daga gidan abokin naka ne kasamo turaren mata
Kauda kai yayi baice komai ba
Fashewa tayi da kuka tace AK meyasa zakamun haka kasan ina sonka amma inaga kaina kawai nakeba wahala gara ma kawai nahakura dakai
Saurin rikota yayi yana fadin come on aysha stop this drama please
Me kike tunani wai ina kula waccan yarinyar kome
Kema kinsan she is not my type mezanyi da ita
Kima daina tada hankalinki akan wannan
Da kyar ya lallasheta tayi shiru sannan yajata suka fita shakatawa
Da kyar Umma tashayo kan khadeeja takira mata Asma'u
Bayan sun gaisa Umma ke tambayanta sun isa
Eh ta amsa atakaice
To ina maigidan nanki
Yana bayi ...
Karban wayan khadeeja tayi cikin sassanyar murya tace ammah ya kike
Lafiya kalau khady ...
I hate it when u lied to me
Cike da mamaki Umma tace meke faruwa ne meyasa kika ce haka
Saurin hannunta khadeeja tayi dan Sam tamanta agaban Umma take
Cikin dakewa tayi murmushi tace kai Umma kincika tsoro kawai dai nasan bata zuwaba kuma tayi nesa damu dole zataji badadi
Katse kiran asma'u hade da sulalewa akasa tafashe dawani irin kuka maiban tawsayi """"
Urs....
*MHD*
[18/07, 15:04] Hubbey Frd Ameena Kn: 📚📚📚📚📚📚
👨👧 _DOMUN KANWATA_ 👩👧
Na( Maryam Muhammad jibril)
8⃣0⃣
Khadeeja ce tazo wucewa ta layin gidansu ahmad ta gansa yafito daga masallaci
Karasawa wurinsa tayi tana boye hawayenta
Yana ganinta ya kauda kai yana fadin
why are u flowing me since u have no feelings for me
Sadda kanta tayi kasa tace nazo ne naji wace shawara kayanke akan maganar da mukayi jiya
Khadeeja kigane ni bazan iya abunda kike so ba
Bazan iya auren sarah ba bana sonta
Zaka sota daga baya just try it
Bazai yuwo ba khadeeja mutum baya iya sakama kansa son wani
Kenan haduwata dake da fadan da mukayi duk ke kika shirya
a'a bani nashirya kawai yafaru ne
To kigane so faruwa yake dan na auri sarah bashi zaisa AK yaso asma'u ba
Nace miki kibarni ni zan daw mataki akai
Bawani matakin dazaka dauka abunda AK yayi
Yayishine domin kanwarsa
Nima kuma zan hakura dakai ne saboda yayata kai kuma kahakura dani dan farin cikina idan har kana sona ...
Tana kainan tajuya ta tafi tana sharan kwalla
Dunkule hannu yayi yanawshi iska yana cije lebe
Motansa yashiga yafigeta aguje kamar mai shirin barin gari
zaune suke cikin katuwar runfar gidan suna hutawa bayan sundawo daga shakatawa
AK nifa ina jin tsoro dan Allah kar wannan yarinyar ta rudaka
Wai aysha so nawa zan gayamaki ba abunda zai faru baki yarda dani bane kome
Mezanyi dawannan chitti din kawai jira nake ahmad ya auri sarah nayi waje da'ita
Miye kuma chitti ??
Yaren India ne yana nufin karamin abu
Dariya tayi tace nakosa naga ranar da asirinta zai tonu mu koreta daga gidan
Shiru yayi kamar mai nazari yanaji bai kyewta ba dayama grany karyan yayi tafiya kuma baikamata yakai yar mutane hotel ya ijiyeta ba har tsawon kwana hudu
Dafashi aysha tayi tace kana tunanin matarka ne
Kauda kai yayi yana furzar da iska bai ce komai ba
Asma'u nazaune adaki ita kadai
Bayan AK ya aikomata da kayanta tasa
Jitayi zaman ya gundureta tafito waje tasha iska
Restaurant din wurin tanufa
Daidai yahaya yazo wucewa ya hangota
Cike da mamaki yake kallonta shidai yasan ance sunyi tafiya da AK to meyakawota nan kuma
Wayarsa yadauka ya kira grany yana daga gefe
Bayan sun gaisa yake tambayarta yallabai nagari
a'a bayanan sunyi tafiya da amaryansa kuma kar wanda yadamesa da kira
Lafiya kake tambaya ..
a'a ba komai grany dama wata nagani kamar asma'u shiyasa nake tambayar ko sunfasa tafiyar ne
Cike da mamaki tace a ina kaga asma'u
Bai bata amsa ba yakatse kiran yana lalubo numban asma'u yana daga nesa yana kallonta amma ita Sam bata gansa ba
Tana zaune taji wayanta na ringing mamaki tayi ganin numban yahya
Afili ta furta yahya kuma to lafiya
Tajima kafin tadaga wayar tare da sallama
Bayan ya amsa sallamarta yace dama nakira ne naji kun isa lafiya
Lafiya kalau Yaya...
Kinga Lagos ko? Nasan baki taba zuwa ba ...
Eh Yaya yanzu haka ma muna wurin hutawa gwanin sha'awa Ashe Lagos tanada kyew haka
ya wajansu Umma
Lafiya ....
Yafada yana katse Kiran da mamakin meyasa sukayi karyan sunyi tafiya
Me asma'u take ahotal ita kadai ina AK yake
Dole akwai wani Abu
Wani mutum ne yazo yazauna kusa da asma'u dawata jaka ahannunsa yana leken police din dasuka shigo restaurant din
Tunda tagansa taji bai kuanta mata ba daure fuska tayi tace malam yi hakuri katashi ni matar aure ce
Murmushi yayi yamike yana fadin yi hakuri ban saniba
Karasowa police din sukayi cikin restaurant din suna bincika ko ina
Da manager ya tambayesu suka ce sunsamu labarin anshigo da drugs restaurant din dan haka dole su binciki kowa anan
Suna cikin bincike suka iso wurin asma'u
Daukan jakan yayi yana fadin madam is this urs
Atsorace tazaro ido tace no batawa bace
Bude jakan sukayi sega drugs makil acikin jakar
Murmushi yayi yace kinbani mamaki gaki kamar mutuniyar arziki Ashe ke annoba ce kina matsayin mace da darajarki amma kinwatsar da ita kina cutar ya'yan jama'a
Kuka tafara tana fadin wallahi batawa bace nima seyanzu naganta anan dan Allah kasaurareni
Kiran ogansa yayi ya nuna mashi nan take yabada umarnin ayi arresting dinta
Karasowa yahaya yayi yana rokon sukyaleta yasanta wannan ba sana'arta bace yarinyar yar gidan mutunci ce
Sunkuy dakanta tayi data tuna karyan datama yahya kenan dama yaganta awurin shiyasa yakirata
Ba rokon da bai musu ba amma sunce sedai yabiyosu office yabada shaida
Tana kuka haka suka tasa keyarta har cikin motarsu
Lekowa tayi tana kallon yahya cikin muryan kuka tace yaya dan Allah kar ka gayama su Umma abunda yafaru dan Allah!!!
AK na zaune da aysha suna fira amma baisan meyasa ba Sam baya jin dadi hankalinsa yakasa kuanciya
Kamar daga sama yahango grany tana zuwa
Azabure suka mike gaba daya suna kallonta har takaraso fuskarta adaure kamar bata taba dariya ba
Cikin kakkawsar murya tace mekake anan
Shiru yayi baice komai ba
Badakai nake ba uban me kake anan tare da wannan mara kunyar
Ina ka kai yar mutane kai yanzu baka jin kunya abid yaushe kazama haka ban saniba
Hannu tadaga da nufin wanka meshi mari daidai nan sarah takaraso aguje tana fadin a'a grany
Dakatawa tayi tana jifanta da wani irin kallo
Sunkuy dakai sarah tayi tace yanzu Yaya yakirani yana cikin matsala ne
Yayi signing contract ne dawani company kuma yau ne zasu gabatar da meeting idan har baijeba zasuyi tunanin ya yaudaresu ne kuma hakan zai jamai matsala shiyasa baisamu damar tafiya ba
Kallon AK grany tayi cikin kakkawsar murya tace ina asma'u
Sunkuy da kai yayi cikin rawar murya yace tana hotel dazu nabaro wurinta itace ma tabani kwarin guywar yin hakan tace zata miki bayani dakanta tasan zaki fahimta
Juyawa tayi tana fadin muje ka kaini wurinta dan ban yarda dakai ba
bin bayanta yayi suka fita
Ajiyar zuciya aysha tasauke tazauna kan kujera tana fadin natsani yarinyar nan
Tsaki sarah tayi tana hararanta tace ke bazaki iya hakura da AK na minti biyar bane se kin ruguza mana shiri
Kauda kai aysha tayi tana fadin gwara ni ai...
Suna isa dakin da asma'u take sukaga bata cike da mamaki yatambayi dai daga cikin ma'aikatan wurin shine yake bashi labarin abunda yafaru
Al'amarin ya girgiza shi matuka
Asma'u ce a police station tasasu agaba se kuka take masu tana fadin wallahi batasan komai akan wannan jakar ba
Waya dan sandan yabata yace takira yan uwanta suzo
Karban wayan tayi tana tunanin wazata kira itadai bazata iya kiran Umma ko abba ba
Numban AK takira tana ringing baidagawa
cikin muryan kuka tace ina kira baidagawa
Dariya yayi yace saurayinki ...
Kauda kai tayi tace mijina dai
Yasunan mijinki ...
Konafada bazaka yarda ba
Saboda me koshima dan safaran kayan mayen ne
Girgiza kai tayi alaman a'a
Koshine wanda muka gani a restaurant ...
Nan madai girgiza kai tayi
Ahasale yace to waye
a tsorace tace
AK hausawee
Gaba daya yan sandan suka kwashe da dariya
Seda sukayi mai isarsu sannan dayan officer din yace yallabai kila kowani AK din take nufi
Fashewa tayi da kuka tace shidai wanda kuka sani wallahi shine mijina idan baku yaradaba kuduba social media anyi posting pics dinmu
Dariya sukayi sannan Babban su ya umarci asata a cell idan wani nata bai zoba zai watsata a news kowa yagani
Kuka tafara tana rokonsu amma basu saurareta ba
Umma da khadeeja suna zaune tana tambayarta meke damunta kuana biyu ta sawya
Fa'iz dake gefe azaune yace Umma kila tana kewar asma'u ne
Shiru Umma tayi nadan lokaci sannan tace ni yau inaji ajikina kamar wani nawa yanacikin matsala
Saurin kallonta khadeeja tayi tana fadin Umma duk muna nan waye kuma amatsala
Fa'iz yace to ko asma'u ce
Hararansa khadeeja tayi tace ammah tana tare damijinta ba abunda yasameta
Umma kidaina damun kanki kawai shedan ne kesamaki waswasi
Tana rufe baki suka jiyo sallamar yahya daga waje
Saurin tashi khadeeja tayi tanufi get tana fadin mekuma yakawoshi nan gidan
Lekowa tayi bakin kofa suka gaisa
Sannan yace Umma naciki
Lafiya ....
akan asma'u ne
Saurin fitowa tayi waje tana fadin meyafaru
Dazu naje hotel nahadu da ita to kuma ina nan tsaye sega yan sanda sunzo suntafi da ita
Cike da damuwa tace yan sanda fa kace akan wane dalili suka kamata
Zaiyi magana kenan sukaji Umma nafadin wa aka kama
Murmushin dole khadeeja tayi tace ba kowa
Yahya yamatso kusan Umma yana fadin karya take Umma asma'u yan sanda suka kama
Innalillahi wa inna ilaihiraji'un
Asma'u fa kace yahya a ina
Riko hannunta khadeeja tayi cikin rawar murya tace Umma ki kuantar da hankalinki ba abunda zai sameta bari naje police station din yanzu naji meyafaru
a'a khadeeja shiga ciki kizauna bari ni naje naga ko dagaskene dan ni har yanzu ban yarda asma'u bace
suda sukayi tafiya da mijinta me kuma yahadata da yan sanda
[18/07, 15:04] Hubbey Frd Ameena Kn: Da kyar AK ya lallashi grany takoma gida shikuma ya wuce police station
Asma'u na cikin cell tana kuka fatan ta daya kar Umma tafahimci gaskiyar halin datake ciki
wani dan sanda ne yazo ya fito da ita
Tana zuwa ta isko Umma atsaye da gudu tazo ta rungumeta tana kuka
Rikota Umma tayi tana tambayr ta meyafaru taya tazo nan ina mijinta
Kuka kawai take takasa magana
Jijjigata Umma tayi dakarfi tana fadin asma'u kigayamun meyake faruwa ne
zatayi magana kenan taga AK yashigo office din fuska ahade
Yan sandan sunyi matukar mamakin ganinsa
Cikin kakkawsar murya yace akan wane dalili zaku kamata
DPO ne yace sorry AK banyarda ba lokacinda tace Kaine mijinta
Saboda me ?
bazan iya auren ordinary girl bane
I doesn't judge people by their looks but their character
Juyowa yayi yana kallon asma'u yace meyasa baki gayamusu ke matata bace
Matsowa tayi kusansa tace Nagayamusu amma basuyarda dani ba
Kamar daga sama yaji ta rungumesa tana fadin I am glad u are here
Cikin rada yace ke miye haka
Dagowa tayi takallesa tana mai alama da ido cewa Umma tana kallo
Saurin rungumeta yayi cikin kunne yarada mata
Kindamu da ummanku ni kuma nadamu da grany
Sannan ya dagota yana fadin is ok
I am here
U are safe now
Murmushi tayi tace I am sorry for troubling u
Hannunta yariko yace nagode allah Dana sameki anan
Namiki alkwarin bazan kara barinki ke kadai ba kema kuma kar kikara yin nesa dani kinsan yanda nake sonki idan wani abu yasameki yazanyi
I can't bear it
Rungume juna suka karayi bakinta takai setin kunnensa cikin rada tace
u are over reacting kafitar dani daganan wajan mana
Murmushi Umma tayi tana kallonsu cike da birgewa
Sabanin yahya da abun ya dawre mai kai
Janye jikinsa yayi daga nata yana kallon dan sandan yace akan wane dalili kuka kamata
Jakar yanuna masa yana fadin munsamu wannan jakar akusa da ita kuma drugs ne aciki
Daukan jakan yayi yace yanzu daka ganta ahannuna seka kamani kace ina safarar drugs
Wace hujja kake da ita datanuna jakan tatace
Kasan zan iya yin karar ka akan bata mata suna dakayi
Hakuri suka fara bashi akan basusan matarsa bace shiyasa
Hannunta yaja suka fito daga police station din
Su Umma nabiye dasu
Wurin Umma yazo
Yace Umma meyasa kika zo nan kinsan yanda asma'u tadamu da lafiyarki yanzu gashi kindaga mata hankali ni kuma natsani gabinta cikin damuwa
Naji ance asma'u tana nan ne shiyasa nazo
Hannunta yariko yana murmushi yace Umma ki kuantar da hankalinki asma'u matata ce hakki ne akaina na kula da ita wannan ma dayafaru kaddara ce amma namiki alkawarin zan kiyaye
Murmushi tayi tace ba komai abid nidama nasan bada saninka haka yafaru ba allah yatsare gaba
Ameen yafada yana kallon yahaya yace kamaida Umma gida tana bukatar Hutu
Sallama suka musu yahya yaja motar suka tafi
Cikin siriruwar murya tace I am sorry
Juyowa yayi yakalleta takara cewa
Sorry
Baice komai ba yanufi motarsa
Binbayansa tayi suka shiga tare
Khadeeja nagida hankalinta atashe jin shiru Umma batadawo ba
Fitowa tayi da nufin binsu taga ahmad akofar gida
Daure fuska tayi ta kauda kai kaman bata gansa ba
Karasowa wurinta yayi yana fadin yawwa dama ke nake jira
Ya akayi kasan zan fito
Kawai dai naji ajikina ne
To me yakawoka wurina
Cikin sassanyar murya yace gaskiyanki ne nagane nine mai laifi kuma ina so na gyara kuskuren da nayi
na amince zan auri sarah !!!
She was shocked
Ni dai nasan mace daya nakeso arayuwata kuma bana tunanin zanso wata bayan ke
Juyawa tayi takoma ciki tana danne kukanta
Tana shiga tasaki wani irin kuka mai ban tausayi
Tundaga waje yana jiyota runtse ido yayi yana jin zafin kukanta har kasan zuciyarsa yajima atsaye kafin ya juya jiki asanyaye yabar layin
Seda Umma tadawo tabata labarin abunda yafaru a station tana fadamata tayi farin cikin ganin yanda AK ke kula da asma'u
Shiru khadeeja tayi tana tunanin meyasa AK yake yaudaran kowa kawai saboda kanwarsa
Suna isa gida bangaren grany suka nufa
Tana zaune itada sarah suna jiran dawowarsu
Tana ganinsu tamike tana Cike da farin ciki tanufo asma'u tana fadin
Ba abinda yasameki dai ko meyasa baki kirani ba kinsa nashiga damuwa
Riko hannunta AK yayi yace shikenan grany ba gashi na maidomaki ita ba
Fizge hannunta tayi tana fadin dallah yimin shiru duk bakai kaja ba meyasa baka barta agidaba zaka kaita hotel
Riko hannunta asma'u tayi tace
Grany yi hakuri kidaina mishi fada laifi nane ni nace yatafi wurin aikinsa
Kima daina goyon bayansa dan ba yarda zanyi ba yana kokari wurin aikinsa amma yakasa wurin kula da matarsa
Nadauka idan yayi aure zai canza ashe nayi kuskure
Shidai AK yana tsaye kansa akasa yakasa cewa komai
Ba dole ne yadamu dani ba amma yazama dole yadamu dake amatsyinki na matarsa
Juyowa tayi tana kallon AK tace
To bari kaji nagayamaka idan har kasake maimaita irin wannan kuskuren zan dauki asma'u mubar maka gidan
Kudi dai suna iya karewa daga karshe duk watsewa zasuyi subarka kai kadai matarka ce kawai zata zauna dakai
Sekayi shawara...
Tana kai nan tanufi hanyar dakinta rai bace
Dagowa yayi yana kallon sarah da rinannun idanuwansa cikin wata iriyar murya yace
Yaune karo nafarko da grany ta taba mun magana haka
Juyowa yayi yana kallon asma'u yace
are u happy now
Kinsamu abunda kike so
Dafari kin rabani da ahmad yanzu kuma kindawo kan family na gashi ta dalilinki grany tamun abunda bata taba mun ba wallahi jinake kamar....
Hannunsa yadaga da nufin marinta sarah tayi saurin rikoshi tana fadin calm dwon bro
Kibarni kawai nakasheta all my problems will be over
Dafashi tayi tace easy yaya abun bai kai haka ba
tunda na auri yarinyar nan nayi ban kuana da kuanciyar hankali
Kallon Asma'u yayi yace uban wa yace kifita daga dakin mekika jeyi a restaurant
Nataimake ki a station saboda farin cikin ummar ki amma ke kin ruguza mun nawa
banza ...shashasha...
Rikoshi sarah tayi tana fadin yaya kabarta kawai
Zama yayi yana fadin bazan barta ba ita dai zata barmun gidana...
Fita asma'u tayi daga palon tana danne kukanta ...
dafashi sarah tayi tana fadin relax Yaya wannan yarinyar tana anfani da grany ne wajan samun abunda takeso
Kafin mu iya mata wani abu dole se grany tasan gaskiyar wacece ita
Girgiza kai yayi yace I don't think that is possible
Murmushi tayi tace kabar komai ahannuna nidai kawai kasa ahmad ya aureni
Tashi yayi yafita yana fadin zan dawo maki da ahmad rayuwarki nikuma kifitar mun da wannan daga tawa rayuwar....
washegari dasafe...
Cikin bacci takejin music natashi bude idonta tayi taga AK agefe yana motsa jiki (exercise)
Yi yayi kamar bai ganta ba yaci gaba da abunda yake
Cikin muryan bacci tace wanna wane kalan abune ...
exercise...
Yafada atakaice
To kacanza kidan ko ka kashe music mana
Haka nasaba yin abuna kuma da rock music
tashi tayi tadauki blanket din ta zata wuce ta bige da exercise Weight dinsa yar kara tayi hade da dafe kafa
Dariyar keta yayi yana fadin Inada medical glass idan kinaso zan taimaka miki
Banza tayi dashi ta wuce daki tana dingishi
Knocking akayi awaje yaje yabude
Rebeka yagani atsaye
Bayan sun gaisa tace yallabai yau tun safe grany bata fito kuma bata bude daki ba ....
Bai jira ta karasaba ya fita aguje ya sauka kasa yanufi bangaren grany
Asma'u da fitowarta kenan tayi saurin bin bayansa
Yana zuwa ya isko gaba daya yan gidan akofar grany suna bubbugawa
Saurin karasawa yayi yafara buga kofar yana kiran grany
Nan take hankalinsa yatashi guba kofar yake kamar zai ballata yana kwala mata kira
Ture asma'u dake gefensa yayi yana fadin bari nazagayo ta window naga
Karsawa tayi jikin kofar cikin siriruwar murya tace grany!!!
AK har yakai bakin kofa ya tsaya cak jin anbude kofa
Saurin karasowa yayi wurin grany cikin rawar murya yace
Grany duk ihun da nake kina jina kika yi banza dani...
Katsesa tayi dafadin ni banji ba asma'u kawai naji takirani
Kuma daga yau muryanta kawai zanji tunda kuma ba kwajin maganta duk mai son wani abu yagayamata tagayamun
Grany meyasa kike mun haka bayan kinsan bazan iya yin komai batare dake ba ke kika San komai nawa menake ci menake sha ....
Kanada kudi ai zaka iya dawko wa'yanda zasu kula dakai konawa kake so
Juyawa yayi yakoma bangrensa rai bace
Yanaso yacigaba da exercise dinsa amma yakasa hannayensa biyu yasa yadafe kansa
Daidai nan asma'u tazo wucewa ya fizgota dakarfi
Hannayensa biyu yasa yariko dantsenta dakarfin gaske
Atsorace tadago tana kallonsa yanda idonsa yayi ja kamar bashiba
Cikin kakkawsar murya yace
Wai me kike shirin yine
Ina tsananin kaunar grany ta shiyasa nake kiyaye macin ranta tun ina karami bata taba gayamun maganar danaji zafinta ba se yau
Tunda kika shigo rayuwata kika lalata mun ita
Idan kika sake kika shiga tsakani na da grany sena....
Katseshi tayi dafadin
Ba abunda zakamun da yawuce wannan zama na anan kadai ya isheni
NI ba abunda nafadama grany
Burina shine na hadaku wuri guda
Nafahimci yanda kake son grany kuma nasan akwai zafi idan Wanda kake tsananin so yayi fushi dakai
banji dadin yanda grany tamaka fada akaina ba
Alhali ni ba kowa bace face bakuwa acikin familynku
Zanje namata magana nabata hakuri kuma na kuatanta mata nasan zata fahimta
Tunda tafara magana yake kallon kwayan idonta ko kiftawa baiyi
Riko hannunshi tayi cikin rawar murya tace u are hurting me
Saurin sakinta yayi yaja dabaya yana fadin sorry ....
Fita tayi daga palon tana share kwallan datazubo mata karo sukaci da sarah zata shigo
Karasowa tayi wurin AK tana fadin yaya meyafaru
Abunda asma'u tagayamasa ya maimaita mata yakare zancan dafadin
Kuma danakalli kwayan idonta zalla gaskiya nahango acikinsu inajin tsoro kar ace ....
Shiru yayi bai karasaba yana nazarin maganganunta
Dariya sarah tayi tace Yaya kabani dariya sekace ba wayayye ba
Bakasan halin yan mata mayaudara ba kenan
Idan kuna magana zasuyi kokarin hada ido dakai to daganan zaka yarda da duk abunda yafito daga bakinsu
Natabbata dawannan take anfani wurin ahmad da grany shiyasa tasiye zuciyarsu
Gyada kai yayi yace shiyasa danake kallon idonta ba abunda nakeji se sautin muryanta
Kice nadaina kallon hada ido da ita kenan
Fita tayi tana fadin idan baka hada da ita ba ita zata hada da kai kawai kasan yanda zakayi kafitar da ita daga gidan ne gaba daya ...
Yana zaune adaki ta shigo rike da mug ahannunta yana ganinta yakauda kai
Mikamishi mug din tayi tace ga coffee dinka
Kin karba yayi yace bayaso
Ta juya zata fita
Yace ta ijiye akan dressing mirror
Girgiza kai tadora akai
Tasowa yayi ya nufota yana kauda kai
Yana so yadauko mug din yadako kwalban turare
Da mamki tace wai mekake hakane kwaban turare fa kadauka
Ijiye kualban yayi yadauki mug din yana fadin nasani dama gwadaki nake naga ko kina bukatar glasses
Kauda kai tayi tace kafini bukatar su
To zaki iya tafiya
Karasawa tayi cikin dakin tana fadin inada abun yi
Juyawa yayi yafita yakoma Palo
Dakallo tabishi tana fadin mutum sekace aljani ...
Urs....
*MHD*
[18/07, 15:04] Hubbey Frd Ameena Kn: 📚📚📚📚📚📚
👨👧 _DOMUN KANWATA_ 👩👧
Na (Maryam Mhd)
8⃣5⃣
Daddare AK na kuance akan gado yakurama TV dake jikin bangon dakin ido yana kallon wani horror film mai ban tsoro
Kwance yake duk ya takure wuri guda gashi yakashe fitila se hasken TV kawai yadan haska dakin
Yanajin anturo kofa yayi saurin kallon wurin adan tsorace ganin asma'u ne yasa ya hade fuska yacigaba da kallonshi
Bata kulashiba tawuce bathroom
Bayan wani dan lokaci tafito sanye dakayan baccinta dogon wando da riga mai dogon hannu kalan pink
AK da yadukufa yana kallo yaji tasaki wata kara atsorace ya diro daga kan gadon yana tayata ihun
Ganinta dayayi atsaye tana kallonsa yasa yawaske hade da daure fuska
Cikin rawar murya tace dan ...dan Allah kacire wannan film din tsoro nakeji
Tsaki yayi Yakoma kan gado yakuanta yana fadin ai ba danke nasaka ba bare kice nacire
Yanda kike din nan ai bai kamata kiji tsoron aljanu ba
Dan allah kacire ba kyewfa kallon irin wannan da daddare
Dogowa yayi yakalleta sannan yamaida kallonsa kan TV can kasan makoshi Yace
Saboda me
Suna fitoma mutum dagaske ko kayita mugun mafarki
Banza yayi da ita yaci gaba da kallonsa
Towel tasa tana goge gashin kanta tanufi saitin gado zata dauki pilo da blanket dinta
Sam baysan tabar wurin ba sedai yaji kamar Abu kusa dashi afirgice yamatsa daga kan gadon yana kunna bedside lamp
Dariya tayi tace sekace dole kanajin tsoro ka kashe mana
Blanket dinta ta dauka tayi hanyar fita tana fadin nidai in sunzo maka ziyara kar ka kirani
a'a tsaya mana ina kuma zakije
Juyowa tayi da mamaki tace kamar ya ina zanje ko kamanta inda nake kuana ne
Daure fuska yayi yace ba inda zakije yau nan zaki kuana
akan wane dalili
Malama ba yanda zakijamun matsala awurin grany haka kawai tazo taganki kina kuana a Palo takara yin fushi dani dama da kyar ta hakura
Buga kafa tayi da kasa kaman tafashe da kuka tace Allah ni bazan kuana anan ba Palo zan kuana haka kawai
hahaha yarinya sama zuciyarki ruwan sanyi ba abunda zanyi dake
I have better things to do
Dawowa tayi tana zunbura baki tace wai kodai tsoro kakeji ne dan nace aljanu zasu zo maka ziyara
Harara ya watsamata yana nuna mata gefen gadon daga kasa yace kishinfida blanket dinki anan coz I can't share my bed with u
a'a ni gaskiya bazan shinfida anan ba
Dayan gefen takoma tashinfida blanket
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 11 Chapter of 35