Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
dinta tana fadin haka kawai kazo shiga bayi kabi takaina Komawa yayi yakuanta yana murmushi Washegari dasafe ahmad yana zaune apalo yadafe kai yana tunani ya kira wayan khadeeja yafi akirga amma taki tadaga jin anturo kofa yasa Yayi saurin dago kai tunaninsa Momy ce zunbur yamike ganin AK atsaye bakin kofa yaharde hannaye akirji yana kallonsa Karasowa yayi cikin dakin yana fadin why are u surprised to see me Zaunawa ahmad yayi yana sauke ajiyar zuciya yace kawai dai naga kajima bakazo bane Kusa dashi AK yazauna cikin sassanyar murya yace har yanzu fushi kake dani ne Saboda na auri budurwarka ko saboda ranan na tureka dakarfi har kafadi ? Shiru ahmad yayi baice komai ba Kamo hannunsa AK yayi yakai kirjinsa yana fadin nasan saboda na tureka ne to Karama seka huce haushinka akaina amma dan Allah nagaji dazama ni kadai ahmad meyasa zaka barni alokacinda nafi bukatarka Kauda kai ahmad yayi yana boye hawayen fuskarsa Jiyo da fuskarsa AK yayi cikin karyayyan murya yace come on friend please stop this drama Tunda muka taso bamu taba irin wannan ba kwana biyu dabana tare dakai I can't handle things I am sorry .... Yafada cikin rawan murya Rungumeshi ahmad yayi Yana kuka shima AK kukan yake yana kara ba ahmad hakuri Cikin rawar murya ahmad yace AK I am ready to marry sarah where and whenever u want Nagane kuskurena Ina wahalar dakaina akan yarinyarda bata Masan inayi ba nadauka tanasona Ashe kudina kawai takeso dataga Wanda yafini kudi da komai shine ta.. Bai karasa ba AK ya rungumesa cike dafarin ciki yace dama nagayamaka ahmad Nagode Allah dayasa kagane gaskiya adaidai lokacinda yadace Hannunsa yaja yana fadin zo muje kagayama sarah inaso naga ya chitti zatayi idan taganka tare da sarah Riko hannunsa ahmad yayi yana murmushin dole yace to ai kabari nayi wanka nashirya ko haka zanje wurin budurwa Dariya AK yayi yace to jeka zanje wurin Momy kafin kagama Dakallo ahmad yabisa har yafita sannan ya rintse ido hade da dafe kai yana tunanin anya yayi ma Kansa adalci Kuwa bayajin zai iya rayuwa batare da khadeeja ba Cike da farin ciki AK yashigo gida yana kwalama sarah kira Kap mutanan gidan nafalo azaune da mamaki suke kallonsa suna tambayar Meyafaru Wurin sarah yanufa yana fadin sarah I have a surprise for u Murmushi tayi tace miye Nuna mata ahmad Dake tsaye bayansa yayi yana fadin nacika maki alkawarinki ga ahmad yadawo gareki yayarda zai aureki kuma nanda kuana biyu ka..... Batajira yakarasa ba tanufi wurin ahmad tana tambayar da gaske yayarda zai aureta Hakuri yaba grany dasauran mutanen gidan akan abunda yafaru kwanaki Nan kowa yafara saka albarkacin bakinsa akan yarinyar data yaudari ahmad grany tace wai Wace yarinya ce wannan Duddubawa AK yayi baiga asma'u awurin ba sama yanufa yana kiran chitti daidai falo sukaci karo Zai shiga ita kuma Zata fito dafe kai yayi yana kallonta yace nagayamiki kina bukatar glasses amma baki yardaba something is wrong with u eyes Sosa goshinta tayi tace alamu sun nuna kaine ke bukatar glasses saboda ..... Katseta yayi dafadin chitti muje kasa akwai abunda zan nuna maki Kallon bayanta tayi dagefenta sannan takalleshi damamaki tace are u okay Daure fuska yayi yace what?? tafa hannu tayi tana dariya tace naga alama matsalan ba a idonka takeba a kwakwalwa ne Tunda kafara gane gane Hannunta Yakama yajata zuwa kasa yana fadin kece dai yau zakiyi mugun gani ur ex-boyfriend is getting married to my sister Kusan ahmad yakaita yana murmushi yace gashi kafadamata taji da kunnenta zaka auri sarah Grany tace meyasa zaice haka Dariya yayi yace haba grany asma'u fa matata ce kuma Yaya awurin sarah so yakamata ahmad yasanar da ita zancan aurensu Murmushi grany tayi tace taji dadi dayafara girmama asma'u amatsayin matarsa Cikin sassanyar murya ahmad yace ma AK idan bazai damu ba yanaso yayi magana da asma'u in private Take ur time... Ak yafada yanama sarah alamar kar tace komai Gefe suka koma tafara tambayarshi meyasa zai auri sarah bayan baya sonta ya khadeeja zatayi idan taji zancan zai yi aure Hakuri yabata akan rashin cika mata alkawarin dayadauka zai auri khadeeja kuma yakula da ita Amma zai auri sarah ne saboda khadeeja .... Nan yabata labarin yanda sukayi da khadeeja Kai ta girgiza cike da tausayin kanwarta tace ahmad nayi kuskure a aurena banaso kayi nadama irin yanda nayi kai namiji ne taya zaka zauna da macen da bakaso ina anfanin auren idan har bazakuyi farin cikiba To asma'u yazanyi khadeeja tadaina kulani tace sena auri sarah ko zan shekara ina kwatantama AK matsalar dake cikin aurennan bayarda zaiyi ba I am doing it for my deeja and nothing can stop me Yana kainan yajuya Yakoma wurin AK Kusa da asma'u AK ya matso cikin rada yace chitti this time ur magic doesn't work on ahmad I feel sorry for u Wane kalan magic kuma anya kwa yau baka sha wani Abu ba bansha ba amma zansha anjima coz I will celebrate abokina yadawo kuma kanwata zata auri Wanda takeso Nakusa rabuwa da kaya Barin wurin tayi batace komai ba tanufi sama tana share hawayenta tasan ahmad yana auren sarah AK zai saketa yazatayi da ummanta Ba adau lokaciba se gata ta sakko da gudu gudu tasha handbag dinta tun tada datana gida Har takusa kofa grany tace a'a asma'u ina kuma zakije haka kamar ankoroki Fita tayi tana fadin grany gida zanje ana nemana yanzu zan dawo Kusan AK da aysha sarah tamatso tana fadin ina kuke ganin asma'u zataje Dariya yayi yace kan cinyar ummanta zataje tarera kukan bakin ciki dariya suka sa aysha tace zataje takona photunan ahmad dake wurinta ne Asma'u tana fita ta tari addedeta se gida Khadeeja ta isko tana wanke wanke Umma kuma na daki Khadeeja na ganinta tazo dagudu ta rungumeta tana murnan ganinta Shafa gefen fuskanta asma'u tayi cikin rawar murya tace deeja kinsan ahmad zai auri sarah Kauda kai khadeeja tayi tana maida hawayen idonta tace eh nasani To meyasa zakisashi ya auri sarah bayan kina sonsa Ni bana sonsa ammah kawai kimanta dazancan karma Umma taji Jin muryan Umma sukayi abayansu tana fadin meye ba'aso naji Bayanta khadeeja takoma tatsaya tana kallon asma'u tace Umma wai kewarki take shine tazo tadubaki amma bataso kisan tazo Kusan asma'u Umma tamatso takama hannunta tana fadin asma'u lafiya naganki haka meyake damunki Anya kwa kina samun kuanciyar hankali agidan mijinki kuwa Murmushi asma'u tayi takai Umma Palo tazauna sannan tazauna kusa da ita tace Haba Umma meyasa kike damun kanki ne akan abunda ba gaskiya ba ina zaune lafiya agidan mijina yan uwansa suna sona suna kula dani to me kikeso Gaskiya zanje nasamu abba yazama dole ki koma wurin inna kuzauna tare ko kya rage kewa in yaso nan se asa yan haya Murmushi Umma tayi tace To shikenan ni dama damuwata bansan wane kalan zama kike agidanki bane Kuantar da hankalinki Umma komai lafiya kalau To shikenan dazu munyi waya da haleema tace tunda basu samu zuwa bikinki ba zasuzo itada Ali suga gidanki Shiru asma'u tayi da alamun damuwa afuskanta Kama hannunta Umma tayi tace nasan abunda kika tuna asma'u kimanta da komai yanzu bagashi kinyi aurenba kinma auri Wanda yafishi komai ai nafiso suzo sugani da idonsu wannan dai asma'un dasuka hana dansu ya aura saboda suna so ya auri yar attajiri gashi ta auri mijin dakowace mace ke fatan samu Tashi asma'u tayi tana fadin Umma bari natafi kar yamma tayi Rakota sukayi har waje da mamaki Umma tace asma'u duk ina motocin mijinki zaki zo a napep Dariya dole asma'u tayi tace ohhh sauri nakene Umma shiyasa banjira ankawoni ba Tana dawowa dakinsu tanufa tayi alwala tayi sallar la'asar tana ninke hijabinta AK yashigo Kan gado yazauna yana fadin chitti kin fara parking ne Da kin kyewtama kanji dan jibi warahaka tuni nayi waje dake daga gidan nan Ijiye hijab din tayi tanufi dressing mirror tana fadin ni ba chitti sunana ba kuma basai ka koreni daga gidanka ba ni zantafi dakaina Kusa da ita yamatso yana fadin ina kika je dazu Jadabaya tafarayi tanakallonsa tace badai sokake na nemi izini awurinka kafin nafita ba Girgiza kai yayi yamatseta da bango suna kallon cikin idon junansu yace inaso namiki kashedi ne idan har kika yi wani abunda dazaisa ahmad yafasa auren sarah se na kwakulo wannan idon dakike yaudaran maza dashi Turesa tayi tawuce batace komai ba amma jikinta yayi sanyi Komawa yayi yazauna yana fadin cigaba da parking nidai zansa ido kar amun sama dafadi da wasu abubuwana Hijabin tasa a drowan kayanta tana fadin base nayi parking ba saboda ba abunda zan fita dashi daga nan gidan Dole kitafi da tsummanki wazaki barmawa Idan ka auro aysha setasa Ba abunda aysha zatayi da kayanki tafi karfin kwance To ai ni duk kayan dakaga inasakawa daga gidanmu nazo dasu nawane bana bukatar Wanda yafito daga hannunka Karya kike kice ba kyason abun hannuna bayan saboda shi kika aureni Kusa dashi tazo tatsaya tana kallonsa tace wai meyasa kakeso ahmad ya auri sarah bayan kasan bayasonta kana tunanin tunda ta auri Wanda takeso zatayi farin ciki kenan Dagowa yayi yana kallonta da mamaki yace wai shawara kike bani ko fada kike mun Kauda kai tayi batace komai ba Wa yagayamaki ahmad baya son sarah ? Suna son junansu ke kika shiga tsakaninsu Yanzu kinga asirinki yatonu shine zaki fara kame kame aurene dai ba fashi kuma daga andaura aurensu ni kuma zan warware nawa dake Fita tayi daga dakin tana fadin nakasa gane wane kala ne kai u keep making the wrong decision [18/07, 15:04] Hubbey Frd Ameena Kn: Tana sakkowa kasa ta isko mutanen gidan zaune apalo kusan grany taje tazauna suna fira Cike da takaici aunty sadiya ke kallonta kusan inna ladidi tamatsa cikin rada tace ladidi natsani yarinyar nan duka duka yaushe tashigo gidan nan amma ji yanda grany tawani jata ajiki ni tsoro na ma kar abata jan ragamar gidan Dariya ladidi tayi tace haba wa ai wallahi bata isaba barima kigani Tana fadan haka tamike tanufi wurin asma'u tana murmushi tace gaskiya yau yakamata musan dandanon girkin surikarmu tunda tazo bamuci abincinta ba koya kuka gani Aysha tayi carab tace wallahi kwa gaskiya yau yakamata tamana girki Daure fuska grany tayi tace dacan wayake maku girki yanda kuke dinnan tukunya nawa zata daura muku Sadiya tace grany tukunya daya ta isa base tayi daban daban ba mudai yayi dadi kawai Shuru grany tayi batace komai ba Tashi asma'u tayi tace ba komai grany zan musu girkin ai dama aiki nane amatsayin surikarsu To shikenan asma'u jeki amma aysha kitashi kitayata Carab sadiya tace a'a grany aysha aikenta zanyi wani wuri Haka tashiga kitchen tafara aiki sauran ma'aikatan natayata se bayan mangariba tagama suka taimaka mata ta jera a dining sannan taje tayi wanka tayi sallah Koda ta sakko suna zaune gaba daya akan dining sunsa kuloli agaba suna hadiyar yawu grany tahana kowa ci wai se wacce tagirka tazo Tana zuwa tazauna kowa yafara ci ana santi AK dashigowarsa kenan shima yaje yazauna kusa da grany yafara ci Lomar farko yace um um um grany amma yau ke kikayi girkinnan ko Bashir yace Yaya narigaka azuci ka rigani afili nifa tunda nabude kular nan nasan abincin nan ba kalar nakullun bane Shiyasa naga uncle jamilu an karkace hula Harara uncle jamilu ya watsamai bashiri yayi shuru yana kunshe dariyarsa Cike da farin ciki grany tace yo ai asma'u ce tayi girkin Shuru AK yayi baice komai ba se bashir ne keta koda abincin Daure fuska grany tayi tana kallon AK tace nace matarka ce tayi girkin kuma kayi shiru Dagowa yayi yana kallonta yace to mezan ce Harara tawatsamai tana kara daure fuska Kallon asma'u yayi yace ohhh Ashe haka kika iya girki darling shine ba kya mana gaskiya daga yau girkin ki zamu rika ci agidan nan Zaro ido tayi tana kallonsa takasa cewa komai Ladidi tace gaskiyarka AK daga yau mun samu kuku Dariya sukayi gaba daya sarah tace tunda takasa wurin daukan wanka da kwalliya se tamana girki mai dadi muci Kallon asma'u AK yayi yaga yanda fuskanta yacanza kamar zatayi kuka suna hada ido tasunkuy dakanta kasa tana wasa da yatsunta Murmushi yayi yace wa yagayamuku hardaku zatayi girkin dani da grany kawai zatama kuma bandamu darashin kwalliyarta ba ina sonta ahaka Dagowa tayi damamki tana kallonsa yayi saurin kauda kai yacigaba dacin abincinsa Shuru sukayi bawanda yace kala aysha kwa tuni ta tashi tabar wurin tana jan tsaki Dariya grany tayi tace gaskiyanka abidi kwalliya bashi kadai ne mace ba girki shine kan gaba Washegari dasafe asma'u na bangaren grany suna shirye shiryen bikin sarah tana gayamata abubuwan da zasu bukata da gyaran gida da sauransu Sarah tashigo tana hade fuska tace grany inaso naje shopping amma kowa yaki rakani gashi banaso naje nikadai Dariya grany tayi tace to ba ga asma'u nan tarakaki ba ... Murmushin mugunta tayi tace to shikenan Da mamaki asma'u ke kallonta tasan dole akwai abunda tashirya Kallon grany tayi tace a'a grany ni bazani ba inada aiki agabana Grany tace a'a asma'u kuje mana daga nan sekiyo ma sauran mutanen gidan sayayya tunda kinga gobe za'afara bikin nan Badan taso ba hakanan ta amince suka tafi Suna isa shop owner din yataresu yana murmushi yace hajiya sarah barka dazuwa Daure fuska tayi tana amsa gaisuwarsa Ina kawarki yau bakuzo tare ba kika zo da mai aikinku kallon asma'u tayi takwashe da dariya Shima dariyar yayi yace Koda yake naji ance yallabai yayi aure nasan ita ya aura ko Nuna mishi asma'u tayi tace to ai ga matar sa nan Dariya yayi yajuya yana fadin aaaa haba kinma rainamun hankali Daure fuska asma'u tayi tana kallon sarah tace idan kin gama cimun fuska se muyi abunda ya kawomu Wucewa sarah tayi tana fadin kije dai kiyi abunda yakawoki ni daban inda zanje Tsaki tayi tanufi wurin atanfofi tafara zaba Mutumin dazu ne yakara zuwa wurinta yana fadin malama lafiya kike tattaba mun kaya kibari uwar gidanki tazaba mana Hararansa tayi tanunasa dayatsa tace Kaga malam kafita ahanyata kajiko inace dai kudi zanbiya ina ruwanka da abunda zan dauka Bayan sun gama sayayya akayi lissafi sarah tace ma asma'u tafita da kayan tajirata awaje Iya nata tadauka tafita tabar na sarah awurin Murmushin mugunta sarah tayi tana kallon shop owner din tace ina so Karage kashi 50 cikin kudin kayanta Da mamaki yace haba hajiya kamar ya kashi hamsin yau kece da Neman ragi haka Damen kudi ta ijiyemai kan table tace kasan Nafi karfin haka ga kufinka kawai kayi abunda nace Dawkan kudin yayi yana dariya yace angama hajiya nan take yamika mata recite na abunda aka kashe amma yarage kudin kayan da asma'u tasaya atanfan dubu ashirin yasata adubu goma Bayan sun iso gida sarah tacema asma'u takawo jakanta tashiga da kayan ita setashigo da sauran Suna shiga ciki ta mika ma kowa nashi sun yaba kyan kayan sunata jin dadi Sarah tace asma'u banga recite dinba muga jakanki naduba koyana ciki Daukan jakan tayi taciro recite din tana dubawa Kallon asma'u tayi cikin daga murya tace wannan wane kalan rainin wayaw ne Damamaki kowa ke kallonta grany tace meyafaru Tsaki tayi Tamika ma grany recite din tana fadin tarage kashi hamsin cikin kudin dakika bata tasiyo kaya masu arha Damamaki kowa ke kallon asma'u har AK dake kwance kan 3siter yana kallo Nan take aysha ,ladidi da sadiya suka dawo dakayansu wai sunfi karfin kayan dubu goma Cikin rawar murya asma'u tace grany wallahi karya takemun ban rage komai aciki ba Karban jakanta sarah tayi taciro bandir din kudi tana fadin su kuma wannan daga ina kika samesu tsiyar talaka kenan daga ansakemaku sekuyi abunda kukaga dama Kusan asma'u grany tamatso tana fadin asma'u dagaske kin rage kudin danabaki Shuru tayi tasadda kanta kasa tana boye hawayen fuskarta Murmushi grany tayi tace se yanzu nayarda nayima abidi zaben daya dace Da mamaki kowa yadago yana kallonta Daure fuska tayi tana kallon su sadiya tace kafin kuji kudin kayanku duk kuyabasu kuma kunce sunyi kyew amma da kukaji kudin daga kuka dawo dasu Yakamata kukoyi tattali adano daga wurin asma'u Dakuna haka dayanzu kundaina family meeting din da kuke kuna tatsar abidi Daure fuska sarah tayi dan ita bahaka taso ba Tashi AK yayi yanufi bangarensa yana waya Dariya aysha tayi tace shikenan komai ya wuce jibi dai sarah zata auri ahmad karyan mutum takusa karewa Sarah tace wallahi kwa gobe ma zamu hada party anan gidan mu ba marada kunya Tsaki asma'u tayi tanufi bangaren grany da sauran kayan da tasiyo Washegari da safe ... AK yana bayi asma'u tashigo bata saniba tana daga labule tagansa atsaye yana balle maballan rigarsa Atsorace tasaki labulan tana rufe fuskarta Murmushi yayi yace kinzo yimun wanka kuma miye na tsorata Bude fuskarta tayi tana fadin malan dan Allah kafita wanka zanyi Cire rigarsa yayi yace Nima ai wankan zanyi kuma nan wuri nane kije ga shower can kiyi Allah yakayewta nayi wanka wuri daya dakai kuma bazan fita ba senayi wankan grany tana jirana Banza yayi da ita yashiga bathtub din da 3quater dinsa yana fadin to kizo muyi wankan tare Juyawa tayi dasuri zata bar wurin santsi ya kwasheta se cikin ruwan tafada saman AK Yar kara yasaki yana dafe bayansa yace Hajiya ai se kishigo ahankali ko Atsorace ta tashi zata fita yakara janyota tafado kansa Kallon cikin idon junansu sukayi nadan lokaci kana ta tureshi ta tashi da gudu tabar wurin Kallonta yake yana dariya har tafita Bayan dan lokaci yafito sanye da kananun kaya yayi kyew sosai Tana zaune ta rufa da bargo tana atishawa Dariya yayi yace tashi kishiga nafito Hararansa tayi bata ce komai se atishawa take jerawa Ruwan dumi ya mikomata batare dayayi magana ba Da mamaki tace don't tell me that u care about me Kauda yayi yace karma kiyi tunanin haka I am doing it for my self Banaso kiyi effecting dina Karban ruwan tayi tasha tana fadin thank u Bai kulata ba yafita daga dakin Murmushi tayi tatashi tashiga bayi Su sarah da aysha anci ado anyi kyew kowa yataru apalo ana party Grany takalli asma'u tace kin gayyato ummanku kuwa Girgiza kai tayi tace a'a grany tace bazasu samu daman zuwa ba se Gobe zasu zo camu amma zata turo khadeeja Dariya grany tayi tace to Allah yakawosu nima yau kanwata zata zo atsorace AK yace badai ameena ba Daure fuska grany tayi tace ita ko kanada matsala ne Dariya asma'u tayi tace meyasa bayaso tazo Daure fuska yayi yace idan tazo zaki sani Gida yacika da yan uwa kowa yazo har ahmad da Momy ga fa'iz da nusaiba sunzo Sedai ahmad Sam baya cikin walwala se waige waige yake kozai ga khadeeja dama saboda ita yazo wurin Kusa dashi sarah tazo tazauna tana murmushi tace honey ya kazauna kai kadai muje mudan taka mana Daure fuska yayi yace I am not in the mood Hannunta takai ta tabashi yayi saurin tashi yabar wurin AK dake gefe yana kallonsu baiji dadi ba amma ya zaiyi Lhadeeja ce tashigo gidan da wata mace mai kama da Umma se kuma wani kyekkyewan saurayi tare dasu suna shigo palon kallo yakoma Kansu Sukuma sebin gidan suke da kallo dagudu asma'u tazo tarungume matar suka gaisa sannan takalli saurayin tana murmushi tace Ali ya kake Murmushi yayi suka gaisa sannan takaisu wurin grany suka gaisa tagayamata matar kanwar Umma ce sawrayin kuma danta ne sannan tanufi kitchen dan kawomusu wani abu Hannu Ali yaba AK suka gaisa yana musu fatan alkhairi a aurensu Ahmad nahango khadeeja ya saki murmushi yana kallonta Kamar ance ta kalla sukayi ido biyu kauda kai tayi kaman bata gansa ba tana daure fuska Aysha da Sarah na tsaye daga gefe suna kallonsu tsaki aysha tayi tace ni wallahi nagaji daganin yarinyar nan kuma ni banga abunda AK yake mata ba banda kowane lokaci suna tare Dafata sarah tayi tace kuantar da hankalinki aysha yanayi ne saboda kar grany ta fuskanci wani Abu amma nafiki tsanar yarinyar nan Suna cikin magana Sega kanwar grany ta iso cike da farin ciki suka gaisa da kowa tun kafin tazauna tafara tambayar ina amaryar AK Murmushi grany tayi tace bari akiramaki sarah kiganta a'a nidai Nafi so naga amaryar AK sarah ai nasanta Daure fuska sarah tayi tana gaisheta Sama sama ta amsa gaisuwar tana waigen waigen mutanan wurin Tunda asma'u tanufo wurin takafeta da ido tana washe baki Tana zuwa suka gaisa tace gaskiya AK kayi dacen mata zuuuuuki Dariya akasa gaba daya banda sarah data bar wurin tana jan tsaki Bayan anyi shagali kowa ya watse aysha ta matsama AK akan seyafita da ita Hakanan suka shirya suka fita yana driving tana mishi shagwabar yadaina kulata tunda yayi aure kamar yadaina sonta Daure fuska yayi yace haba aysha ya isa haka mana yanzu bagashi nafito dakeba Inda bana sonki kema kinsan ko kallo baki isheni ba Ganin ya hasala yasa tafara bashi hakuri banza yayi da ita yana bin wakar da yake sawrare amotar Sunkuyowa tayi gefen fuskarsa wai zata mai kiss Birki yafara kokarin takawa yana fadin aysha miye haka kimatsa bana ganin gabana can't u see I am driving bai karasa ba yaji ya kade wani mutum saurin taka birki yayi yana salati Ganin mutane sun nufi mutumin yasa yayi kokarin Barin motar amma aysha tarikosa tana kuka tace dan Allah sutafi kar agansu mutuncin shi zai zube idan aka ganshi da ita cikin Daren nan Bashiri yataka motar suka tafi amma yanaji abunda yayi baidace ba Suna isa gida yawuce bangarensa yana tunanin wane hali mutuminnan yake ciki Baiga asma'u apalo ba kuma bata daki kayan baccinsa yasa yauna bakin gado yana danna laptop Can anjima tashigo rike da mug ahannunta kan bedside drawer tadora tana fadin nagayamaka idan zaka fita da aysha kasan lokacinda yadace kufita yanzu da grany taga lokacinda kuka shigo mezaka cemata Banza yayi da ita yana duba laptop dinsa da damuwa afuskansa Kusa dashi ta tsaya tana fadin meyake damunka Dagowa yayi yakalleta yace inada damuwan da tawuce kine Murmushi tayi taleka laptop din da mamaki tace Hukuncin tukin ganganci kuma kayi accident ne Banyiba ....yafada atakaice To meyasa kake Neman hukuncinsa ... Kofa yanuna mata yana fadin dan Allah malama je ki kuanta kindameni Talkative girl kawai Dariya tayi tashinfida blanket dinta akasa tace ai ni yau ma nan zan kuana yafi dadi ... Washegari dasafe... Asma'u na goge goge apalo AK yafito cikin shirinsa tsap se kanshi ketashi Kallonsa tayi tana dariya tace wai har kashiraya wannan har kafi amaryar zumudi Harara ya watsamata yafita yana fadin Dan allah dai yau dai kiyi shigar kwarai kar kibani kunya gaban abokanai Yana sakkowa kasa daidai yan sanda sun shigo gidan Dariya yayi yana kallonsu yace malamai ba yau bane daurin auren gobene Karasowa sukayi kusa dashi babbansu yace yallabai ba daurin aure mukazoba munzo tafiya dakai ne Ahasale sarah tace kai karamin da iska mind ur language Kasan dawa kake magana kuwa Katseta grany tayi tahanyar daga mata hannu sannan takalli dan sandan tace akan wane dalili zaku kamashi Shidai AK yayi shuru yakasa magana dan ko ba'afada ba yasan laifinsa Kallon grany police din yayi yace hajiya yaronki yayi tukin ganganci jiya da da daddare har yakade wani mutun kuma bai tsayaba yagudu da motar to acikin mutanen wurin wani yarike numban motarsa shine suka shigar da kara kuma sunyi kashedin idan dai ba abimusu hakkinsu ba zasu yada ma yan jaridu amatsayin sa na Babban mutum kwa hakan ba karamin bakin jini zai janyomasa ba Salati inna tayi tana kallonsa tace abidi yaushe haka tafaru baka sanardani ba Cikin karfin hali yakalli dan sandan yace kunada wata hujjar datanuna ni nayi laifin Murmushi dan sandan yayi yace kwarai kuwa yallabai saboda mutumin daka kade yaganka lokacinda kake kokarin fitowa daga motar kuma ya tabbatar mana akwai wata mace atare dakai cikin motar sedai bai tantance fuskartaba amma kai yashaidaka Kuma muje muna so muduba motarka nasan zamu samu wata shaida tunda mutumin akan mashin ka kadesa dole motarka zata nuna

Chapter 12 of 35