Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
albashi ashekarunsa yanzu yaci ace ya daina aiki amma wai....... AK ya katseshi dafadin Ahmad shut up!! Ahmad yayi shuru tare da juyowa yakalli uncle jamilu carab suka hada ido dama suna wucewa ya sauke glass dinsa yabi Ahmad da kallo Murmushin yake Ahmad yamishi tare da daga Mai hannu shidai uncle jamilu se binsa yake da kallo har suka fita kana yamaida idonsa kan jaridar dake hannunsa Suna isa jirgin su Sarah nasauka dagudu suka zo suka rungume AK rumgume su yayi yana dariya Sarah ta juyo da nufin rugume Ahmad yayin saurin jan trolley dinta yana fadin kuzo muje nasan kun gaji Sarah bata damu ba suka bi bayansa suna tafe suna fira banda Ahmad da se ba'a rasa ba yakesa baki Suna isa bangaran grany suka nufah bayan sun gaisa grany tawuce daki Dan ba inuwa daya suke shigaba Wurin dining suka nufa suka AK yaja ma aysha kujera tazauna tare da fadin thank u Sarah tayi tsaye tana jira Ahmad yaja mata kujera taga yazauna baida niyyan kallon inda take baki ta zuburo taja kujera tazauna suka fara cin abinci AK ne yadago yakalli aysha sukayi ido biyu murmushi yayi yakashe mata ido tare dafadin miss you baby Murmushi tayi itama tace miss you too duk abunda suke Sarah DA Ahmad na kallonsu Ahmad naganin Sarah tajuyo zata kalleshi yayi saurin sadda Kai baki ta zunburo cikin muryar shagwaba tace wai ni kan yaya kayi missing dina kuwa AK yayi saurin juyowa yace nayi missing dinki mana kallonshi tayi ta nuna Ahmad tace bakai ba shi AK yayi murmushi ya kauda kai yana fadin ok to kirinka banbanta sunan tunda shi sauranyiki ne kisa masa wani sunan Ahmad yamike tare da fadin nizan wuce Allah huta gajiya ganin Sarah tamike da nufin binsa yayi saurin am...AK muje kadan rakani mana AK yadago da loman abinci abakinsa yace ban gane in raka kaba kai bako ne Ahmad ya langwaba Kai yace kazo mana akwai maganar dazamuyi AK yatashi yana fadin Kai wallahi ka iya katsema mutun jin dadinshi suna fita aysha ta kalli Sarah da mamaki afuskanta tace wai ya naga kaman Ahmad yana avoiding dinki ne Sarah ta zauna jiki asanyaye tace Ashe kema kin Lura ko? aysha ta tabe baki taci gaba da cin abincinta Seda Ahmad yashiga mota yadago yakalli AK yace AK gobe muhadu a office Ina so mu tattauna wata magana AK yaleko ta window yace haba Ahmad be a man mana nasan akan zancan auren nan ne duk kadaga hankalinka don't worry ni zanyi komai kuma ba dogwon lokaci za adauka ba yana kainan yajuya yana fadin se munyi waya Ahmad yadaki stiyarin motar da karfi ya dafe Kai shi yanzu ya zaiyi afili ya furta Kai Ina!!! dasake wayanshi yadauka ya lalubo numban khadeeja bugu biyu ta daga tare da fadin Tarzan ya akayi Ahmad ya jingina jikin kujera ya lumshe ido yana fadin flying Bird kina Ina ne khadeeja takalli Asma'u da takafeta da ido tace Ina gida lafiya ?? Ahmad yatada motar tare da fadin gani nan zuwa khadeeja ta tashi azabure tana fadin gaka nan zuwa Ina? mema zakazo yi ? Ahmad bai jira tagama magana ba yakatse wayar khadeeja ta juyo ta kalli Asma'u tana murmushin yake Asma'u takauda Kai taci gaba da aikinta khadeeja tazo kusanta ta zugunna tace ammah yazanyi tunda naji yace zaizo to Abu Mai mahinmanci zai kawoshi gashi Umma bata nan bata Masan da alakar muba Asma'u tamike tana fadin idan yazo kije in Umma tadawo Zan Mata bayani amma kiyi ahankali ni soyayyar nan taku tsoro take bani duka duka KO sati bakuyi ba da haduwa amma kamar kun shekara tare kuma tun rashin kunyar da kika mishi yafara binki ni hankalina ya ki kunciya Anya bayada wata boyayyar manufa akanki kuwa khadeeja kinsan masu kudin nan basuda tabbas juyowa tayi tadawo wurin khadeeja tare da rike hannayanta duka biyu cikin sanyin murya tace khdy dan Allah ki kula da kanki ki tsare mutuncin ki kar kudi yarude ki kiyada tarbiyar da Umma Tasha wahala tabamu ba wai ban yarda dake bane a'a nasan kinada hankali kinsan Abu Mai kyew DA mara kyew amma shi Dan Adam Tara yake bai cika goma ba hawaye ne suka zubo a idonta tace khadeeja idan wani Abu yasameki mutuwa zanyi zuciyata bazata iya dauka ba Da sauri khadeeja tafada jikin Asma'u tafashe da kuka mai sauti Asma'u ta rungumeta tana shafa kanta cikin sheshshekar kuka khadeeja kefadin shi kenan ammah Allah nabari bazan Kara kulashi ba koda sonshi zaikasheni idan kikace bai maki ba Allah bazan aure shiba Asma'u ta dagota tana goge Mata hawaye tayi murmushi tace khdy bance bana son Ahmad ba duk abunda kike so nima Ina sonshi kawaidai Ina jin tsoro ne amma Zan sameshi muyi magana nakara bashi hakuri akan abunda kika masa kinga daganan se hankalina ya kuanta karar wayan khadeeja ce takatsesu jiki asanyaye khadeeja tadaga Ahmad yacemata gashi akofan gida Asma'u tayi murmushi tace tashi kije amma karki dade kinga Umma batanan tashi tayi ta fita bata ce komai ba akofar gida ta iskoshi karkashin bishiya ya jingina da mota yanda taganshi cikin damuwa yasa taboye tata damuwar takaraso tana kakalo murmushi tamai sallama shima murmushin yayi ya amsa bayan sun gaisa yabude motar yanuna Mata kujera ido tazaro tace menene ? Murmushi yayi yace kin cika tsoro zama zakiyi Ina so muyi wata magana khadeeja tayi murmushi tazauna tana fadin thanks Ahmad yasauke ajiyar zuciya yakalleta yace khadeeja kinsan nataba gayamaki cewa AK hausawee abokina ne ko ? Khadeeja tadaga Kai alamar eh Ahmad ya zugunna ya jingina jikin bishiyar da suke karkashi sannan yabama khadeeja labarin duk abunda yafaru tsakaninsa da Sarah da shirin aurensu da AK keyi ayanzu khadeeja tayi Shuru na Dan lokaci tace gaskiya tun daga farko kayi kuskure duk dacewa awancan lokacin bakada wacce kakeso bai kamata kamata kamata karyan kana sonta ba amma nidai da nice a matsayinta daga reactions dinka ya'isa nagane baka sona sedai shi so makaho ne tunda tana sonka bazata kula da wannan ba Kuma ni banga abunda zaisa kadamu kanka akan wannan ba after all he is just a friend not a father kome takai takawo dai bazai aura maka kanwansa dole ba Ahmad ya girgiza Kai yace khadeeja bazaki gane bane AK ba babana bane amma wani bangarene na rayuwata tare muka taso dashi tun muna primary muka shaku da juna takai har idan dayanmu yake makaranta zai tsaya abakin get har said Dan uwansa yaje sushiga tare dayawa mutane sun dauka gidan mu daya duk ranar da banada lafiya banje makaranta ba AK gidan mu yake dawowa har sai nawarke mutafi tare duk abunda aka sayamasa se ansayamun in ba haka ba kwa to bazai yi anfani da nashi ba Muna scdry school dadyna yarasu alokacin shima abbanshi yajima da rasuwa AK shi yadawki nauyin karatu na har muka gama lokacinda zai je America karatunshi tare muka tafi lokacinda yabude companynsa ni yafara dauka aiki kuma yabani babban matsayi na mataimakinshi khadeeja AK yazama tamkar babban yaya awurina bansan da wane ido zai kalleni ba idan har nace bana son kanwarsa cikin sanyin murya khadeeja tace to ka aureta mana Ahmad yadago dasauri yace aure kuma khadeeja ?taya Zan aureta bayan bana Sonta ni ke nakeso khadeeja kuma ke zan aura baya cikin tsarina zama damace biyu kuma ko na aureta banajin Zan iya adalci atsakaninku so waht is the use of marrying her tunda daga ni har ita bazamu ji dadin auren ba Khadeeja taji wani sanyi aranta dama can karfin hali kawai tayi na cewa ya aureta murmushi tayi tace to tunda hakane ba AK yakamata kagayama cewa baka son sarah ba ita yakamata kagayama kuma kabata hakuri akan wasa da emotions dinta da kayi nacewa kana Sonta alhali bahaka bane ajiyar zuciya ya sauke tare da fadin hakane khadeeja naji dadi kuma nagode da shawarar da kika bani khadeeja tayi murmushi tace bakomai nima nagode daka zabeni amatsayin wacce zaka fadama damuwarka kuma kanemi shawarata hakan yanuna mun cewa inada matsayi arayuwarka Ahmad yamike yana fadin flying Bird Bari na wuce yamma tayi tunda ko ruwan gidanku baki bani ba dariya tayi tace laaaaa Allah namanta duk arude nake kasan bantaba tsayawa da saurayi ba murmushi yayi yace dagaske? kice nidin na daban ne kenan dariya tayi tare da rufe fuskanta da gyale tace u are my first love dariya yayi yace nagode da wannan matsayin and u are Mine too baki ta zunburo tace kaifa second hand ne Ahmad yace kamar ya second hand sekace waya murmushi tayi tace baka riga cema Sarah kana sonta kafin ni ba dariya yayi yashiga mota yana fadin wannan ai iya lebe ya tsaya ke kuma ko yanzu za'a tsaga zuciyata za'aganki aciki tada motar yayi yana fadin Zan tafi badan nagaji da ganinki ba murmushi tayi tana daga mai hannu har yatafi se kuma yayo rebas yadawo khadeeja tace lafiya kankance ido yayi yana kallonta yace wai ma yanaga baki Nuna kishinki akan maganar nan bane harma kike cewa in aureta khade Anya kwa kina sona murmushi tayi tace kazo mun da maganar ne dan kaga kishina Kodan nabaka shawara Ahmad yasosa Kai yace Dan kibani shawara amma kinsan mu maza muna so muga Ana kishinmu ke intakai ma har dambe ayi dariya tayi tace to bada khadeeja za'ayi damben ba yanda kazomun da damuwarka bai kamata na Nuna tawa damuwar ba se abun yama yawa shi yasa kaga na waske amma azuciyata yanda kasan Ana buga ball haka nakeji Dariya Ahmad yake sosai har yatada motar yayi gaba yana fadin I can't leave without you my flying Bird !!! Khadeeja tayi murmushi ta koma cikin gida..... [18/07, 15:03] Hubbey Frd Ameena Kn: πŸ“šπŸ“šπŸ“šπŸ“šπŸ“šπŸ“š πŸ‘¨β€πŸ‘§ _DOMUN KANWATA_ πŸ‘©β€πŸ‘§ Na ( Maryam Muhammad jibril) Dasunan Allah mai rahama mai jinkai....✍ 5⃣0⃣ Yana shiga bangaran Ahmad yatura kofar yashiga Ahmad dake zaune da laptop agabansa at the same time yana waya da khadeeja ganin AK yasa yayi saurin katse kiran yana fadin call u back flying Bird Sannan yadago yakalli AK yana fadin ina kabar wayanka ina kiranka baka dagawa karasowa AK yayi yanufi Dan karamin frig din dake palon yana fadin waye kuma flying Bird? Dasauri Ahmad yadago yakallesa Dan baitaba tunanin yaji abunda yace ba murmushin yake yayi yace 😁tsuntsuwata ce Goran ruwa yadauka afrig din ya zauna adaya daga kujerun Palon sannan yadago yakalli Ahmad yace se yanzu nayarda da zancan momy idan gwabranci yama mutum yawa yana zarewa gashi kafara tabuwa dariya yasa yana fadin inaga Inaga 1 week din danadauka yayi yawa yakamata narage idan ba hakaba naga alamun firstnight dinka a mental hospital zaka yishi yakarashe maganar yana kwashewa da dariya Hade fuska Ahmad yayi baice komai ba yaturama AK laptop din yace duba kaga collection din wannan karon tun dazu ina kiranka bana samu munyi magana da zaid yace mun maybe zuwa yamma zasu iso Lagos Karban laptop din AK yayi yaduba sannan yace sunyi kyew amma yau kaje office ne Gyada kai Ahmad yayi yace eh naje banjima da dawowa ba su mannir ma sun gama bedsheets din sun bala'in kyew se kagani Murmushi AK yayi yace ai nasan mannir baya wasa da aikinsa amma yakaga aikin bashir yana tafiya daidai kuwa Tsaki ahmad yayi yace Dan Allah daina zancan wannan banda wasa da tarin yan mata ba abunda ya ajiye Tashi AK yayi yana fadin muje wurin Momy tace tana son ganin mu hannunsa Ahmad yariko yana fadin come on friend ina kuma zakaje bayan baka gayamun abunda kazo fadamun ba Mezan fadamaka kuma...AK yafada yana kokarin boye damuwar fuskarsa Mikewa Ahmad yayi yashiga gabansa yana fadin haba AK nafasanka fiye da yadda nasan kaina u can hide ur sadness from everyone with ur fake smile but u can't hide it from me coz I know u in and out So please don't waste my time Tell me what is bothering u and let me do my job Zama AK yayi yana sauke ajiyar zuciya Kusa dashi Ahmad yazauna yana kafeshi da ido Wani dogon tsaki Ahmad yaja da yagama jin labarin da AK yabashi mikewa yayi yana fadin wallahi kabani mamaki AK yanzu akan aysha ne ka daga hankalinka so what idan tayi rejecting dinka who the hell is she mata nawa ne agari suke Neman koda pics ne sudauka dakai Wanda ma sunfita komai Dawowa yayi kusa da AK yazauna tare da dafa kafadansa yace AK please be ur self nasan dalilin dayasa kake son auren Aisha sedan kana ganin itace zata zauna da family dinka lafiya saboda ita ma nata ne kuma itace kasan halinta tasan naka Amma shi rayuwar aure ba ruwansa da wannan kamar yanda kukai da grany kabarta tazaba maka kasan bazata zaba maka abunda zai cutar dakaiba I know one day u will thank her for that Harara AK yawatsamai ba shiri yaja bakinsa yayi shuru yana danne dariyarsa Mikewa AK yayi baice komai ba yawuce yana kada key din motar dake hannunsa Bin bayansa Ahmad yayi yana fadin bamu gama maganar ba kuma katafi Bangaran momy suka nufa Tana zaune apalo suka iskota kusan kafanta AK yazauna yana fadin da girman kujeranki momy Allah sadai ba laifi mukayi ba Kauda kai tayi tana fadin laifi kuma ai saidai kar akara Dayan gefenta Ahmad yazauna yana sha sajen fuskarsa yana murmushi Daure fuska tayi tace Ku yanzu saboda Allah kunfiso kuyita gantali agari da girmanku bazaku ma kanku karatun tanatsu ba wai ni idan kunsan bakuda lafiya ne kugayamun insan nayi amma nagaji daganinku haka Dagowa sukayi suka kalli juna sukayi murmushi Kara tamke fuska Momy tayi tace aw dariya ma kuke wato gani mahaukaciya ko AK yace Yi hakuri Momy insha Allah mun kusa nadauka ma Ahmad yagayamaki zancan auren na dasati daya insha allah Tafa hannu tayi tace yaw naji zancan banza shi auren angayamuku wasa ne kai karfa kurainamun hankali Ak yace Momy Allah dagaske to me muke jira tunda ko mata hudu mukace muna so zamu iya aurosu ayau base gobe ba Baki Momy tawashe tana fadin kuma fa hakane amma ai duk dahaka yakamata ace mun fara shiri Murmushi AK yayi yace abunda yakawoni kenan Momy se kije wajan grany zakiji bayanin komai daga gareta Yana kai nan yamike yana fadin mom bari naje sena sake dawowa Ahmad da tunda aka fara magana ya sadda kai sai yanzu Yamike jiki asanyaye yabi bayan AK har yakai kofa momy tace Ahmad idan kadawo kazo inasan ganinka To yafada yana fita daga palon Amota ya isko AK zaune yana jiransa Shiga yayi suka bar gidan Ahankali AK ke driving sunyi shuru ba mai cewa kala kowa ya tsunduma cikin tunani shi ahmad yana tunanin taya zai gayama AK cewa bazai iya auren kanwarsa ba Yayinda shi kuma AK yake tunanin wace yarinya ce grany ta zabamasa wace irin rayuwa zai yi da ita anya kwa baiyi gangancin yanke hukunci cikin fushi ba kuwa Suna isa company office din AK suka wuce gaba daya Mamaki ne yakamasu ganin aysha da sarah a office din Daure fuska AK yayi Yana fadin me kuka zoyi nan Langwabar da kai sarah tayi tace Yaya please give us a chance to explain Kujeransa yanufa Ya zauna yana fadin banada lokacinda zan bata wajan sauraron tatsuniya Cikin muryar kuka aysha tace AK wai meyasa kake mun hakane you've change completely I said I'm sorry kuka ne yahanata karasa maganarta Ahmad da tunda suka shigo ya wuce Drowan dake gefe yana duba wasu files Dogon tsaki yaja tare dazaran wani file yayi waje yana fadin aikin banza bin bayasa sarah tayi tana fadin bari nabaku space Suna fita aysha tafada Jikinsa tafashe da kuka mai ban tawsayi tana fadin AK Dan Allah kayi hakuri komai yawuce Allah nafasa aikin banaso ni kai nakeso bandawka abun zaikai haka ba ko yaune nashirya zan aureka kuka ne yaci karfinta Jiyayi yakasa jure kukanta hannunsa yadawra akanta yana fadin it's ok hanunta Yakama yazaunar da ita kan kujera sannan yazaro farin handkerchief a alijunsa ya mika mata Karba tayi tashare hawayenta cikin rawar murya take fadin ka... Ka hakura...? Kai ya gyada alamar eh Murmushi tayi tace yanzu zamuyi aure ko ? No way yafada yana zama akn kujerarsa Dip murmushin fuskarta yadauke cike da mamaki tace bangane ba Hannanyansa ya ware yana fadin nariga nasamu wacce zan aura kuma awannan satin Afirgice tamike daga kan kujera Tanufesa tana fadin u most be joking right? Kai ya girgiza yace kodaya and don't blame anyone u r responsible for it Kara fashewa tayi da kuka tace ai nabaka hakuri AK why did u do that to me kawai saboda kaga INA sonka kamanta ni shekara nawa nayi ina jiranka shine.... Kukan dayaci karfinta shi yahata karasa maganarta Tawsayinta ne Yakama AK Dan shi kanshi shaidane akan irin sonda aysha kemasa Tasowa yayi yazo kusa da ita ya tsaya kauda kai tayi tana share hawayan fuskarta Kafadunta Yakama yazaunar da ita yana fadin zauna muyi magana zama tayi tana sauke nunfashi idonta har ya kunbura saboda kukan da tawuni tanayi Hannunta yakama cikin muryan lallashi yace aysha I'm sorry nasan ban kyewta ba danayanke hukunci cikin fushi amma zanje insamu grany nabata hakuri ajanye maganar dama itace tazaba mun yarinyar ke kuma se ki kiyaye Nan gaba u need to think twice before u speak Murmushi tayi tarungume shi tana fadin thank u sweetheart Dan Allah kar kace zaka barni bazan iya rayuwa batare dakai ba Kanta yashafa yana fadin I know tashi tayi tace to tunda komai yawuce let's have some fun Ak yace no I am busy Langwabar dakai tayi cikin muryan shagwaba tace kenan baka hakura ba mikewa yayi yadauki jacket dinsa yana fadin let's go Cike da farin ciki tabi bayansa Office din ahmad yaleka azaune yake haushi duk yacikashi ga sarah Tasashi agaba se zancan bikinsu take mishi jiyake kamar ya bibbige mata baki Jin anturo kofa yasa duka suka juya Murmushi AK yayi yana fadin to Mr Romeo se kazo mutafi ai zunbur ahmad yamike yana fadin thank god dama zafi ya isheni Shi duk atunaninsa yadauka shida AK zasu fita ganin sarah tashiga mota yasa ya hade fuska bai gama shan mamaki ba seda yaga aysha ma tabude tashiga AK yatashi motar yana fadin babe se ina? Wani irin kallon kabada maza ya watsama AK tare dajan tsaki Aysha tace wonder life Sarah takatseta dafadin no shopping Yaya yakamata mufara shiri fa basauaran lokaci Ko haka ba D ... Tafada tana kallon ahmad Banza yayi da ita kamar baijita ba Bata damu ba taci gaba da surutunta da AK Dan itama aysha takaici ya isheta itada taso sufita daga ita sai AK Sheraton suka nufa suna isa aysha taja AK sukayi wani gurin ahmad ma kan wani guri yasamu yazauna yaciro wayarsa aljihu ya lalubo wayar khadeeja bugu biyu tadawka tareda sallama lumshe jingina yayi jikin kujera hade da lumshe ido yana amsa sallamarta Shuru sukayi nadan lokaci tadayan bangaran khadeeja tace malam idan bakada abun fada hang up inada abunyi Murmushi yayi yace yaw yan tsiyarne akai kenan Dan ma kinsamu na kiraki Dariya tayi tace to ba dole ka kiraba kana so kaji zazzakar muryar khadeeja ba Dariya yayi yace yabon kai bacinsa Baki tazunburo kamar yana kallonta cikin muryan shagwaba tace to ai kai dayakamata kafada baka fada ba shiyasa natuna maka wai ni kwa Tarzan anya ma kuwa ka iya soyayya Kwashewa yayi da dariya yace taya za'ayi insani bayan bantaba yiba amma aduk lokacinda nake tare dake se inji tamkar awata duniyar nake rayuwa banjima da haduwa dakeba amma se nakejin kamar tunda aka haifemu tare muka taso lokaci guda kika shigo rayuwata amma ayanzu rayuwata batada wani anfani idan har bake Khadeeja tace hmmm ragamun hakanan Tarzan zaka kasheni da lubayya Cikin muryan tsokana yace kufa mata ba'a iya muku kince ban iya soyayya ba yanzu kuma nazage na kwararomaki kalamai maimakon kiyaba sekuma kice ya isa hakanan dariya ta sa tana fadin to yi hakuri kalaman naka ne naji yayi iri daya dana mawakin Indian nan acikin wakar ishq vala Kai yasosa yana fadin ai ina bala'in son wakan ne shiyasa na haddace amma karkidamu indai soyayya ce to ko sharukhan albarka Dariya tayi tace to Allah sa idan baka cikin masu tashin matansu abacci da kafa ko adana musu dundu Dariya yayi yace haba wuce nan yarinya se kin shigo zakiga nawa salon Katse maganar tayi dafadin wai ya kunyi magana da sarah kuwa Nan take fuskarshi tacanza cikin sanyin murya yace a'a tukkuna dai ni bansan ta inda zan fara bane tadayan bangaran khadeeja tace haba Tarzan kar kabada maza mana kaifa namiji ne bai kamata wannan Dan karamin abun yadameka ba Katseta yayi dafadin wannan ba karamun abu bane flying Bird bakaramun karfin hali zanyiba wajan gayama AK bana son kanwarsa Ahasale khadeeja tace to kai ka aureta mana Shuru yayi baice komai ba Cikin sanyin murya tace sorry tarzan inajin haushin kaina ne dakashiga matsala kuma nakasa taimaka maka amma koda ta text ne base kagaya mata ba Murmushi yayi yace nice idea I will try it shiyasa nake sonki akwaiki da brain....jin karan fashewar Abu abayansa da yayi shi yakatsemai maganarsa katse kiran yayi tare da juyowa Sarah yagani atsaye fuskanta sharkaf da hawaye idonta yakade yayi ja ga kwalbar jus nan datafashe akasa jikinta har rawa yake bata damu ba tabi takan kualbar ta wuce harsaida tayanketa akafa amma bata ma san ta taka wani Abu ba saboda tsaban tashin hankalin datake ciki Kusan Ahmad taje tatsaya kallonsa take da rinannun idanuwanta ko kiftawa batayi Cikin sanyin murya ahmad yace sarah I'm sorry I know I hurt u by playing with ur emotions kibani dama namaki bayani Bai yi auneba yaji saukar mari akuncinsa tuni hankalin mutanan wajan yakarkato wajansu dafe kuncinsa yayi cike da mamaki yace kika mareni Cikin rawar murya tace kozaka ramane kabani mamaki ahmad Ashe dama haka kake bansaniba kai wane irin butule ne Rintse ido ahmad yayi hade da dunkule hannu zuciyarsa na tafarfasa wai yau shi aka mara in public kuma wai mace yatabba yau daba sarah bace tamareshi da Allah kadai zai kwaci koma waye ganin mutane na kallonsu yasa ya raba tagefenta yawuce batare da ya kalleta ba Durkushewa tayi awajan tare dasakin wani irin kuka wanda dagaci kasan nabakin ciki ne seda tayi mai isarta sannan ta tashi tana jan kafa da gyalenta ahannu ita tafice basu bi takan su AK kowa ya wuce gida ataxi Seda su AK suka fito basu gansu ba kuma yana kiran wayoyinsu basa dagawa Janshi aysha tayi tana fadin muje mana AK tunda kaga basanan kenan suntafi Aranan sarah wuni tayi adaki banda kuka ba abunda take aysha tayi tambayar duniyan nan amma taki gayamata se fadin take impossible wallahi bazai yiwu ba he is mine and he only belong to me no one can never separate us ..... muryanta harta disashe saboda kuka har banci yadauketa Washegari tunda safe grany tashirya tasami inna da maganar tana so suhada auren zumunci tsakanin Abid da Asma'u Bakaramun farin ciki inna tayi ba nantake ta'aika kiran Abba bayan yazo tazayyane masa komai yayi murna sosai kuma yabada goyon baya saboda yasan AK kuma ya yaba da halayansa na taimakon talakawa da matasa Yabasu tabbacin cewa da yamma zaije yasamu Umma da maganar duk yanda sukayi zasu ji ""''""" Ur's.........✍ πŸ‘©β€πŸ’»Maryam Mhd [18/07, 15:03] Hubbey Frd Ameena Kn: afirgice tadago tana kallonsa da mamaki tace ahmad nizaka mara Wani malalcin murmushi yasaki yace idan har zaki iya sa hannu kimareni to banga dalilin dazaisa nakasa marinki ba Nunata yayi da yatsa yace and let me worn u This isn't ur bedroom so wannan yazama karo nakarshe dazaki shigomun office without my permission Sannan waccan yarinyar da kika kira da karuwa to bari kiji tafiki matsayi da daraja awurina idan har kika kara bude kazamin bakinki kikayi wata maganr banza akanta to wallahi zan baki mamaki ahaka kike so na aureki Hannunsa tarike

Chapter 6 of 35