Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
kafin daga karshe ya girgiza kai yakoma ya zauna yana yan rubuce rubucensa Sakkowa tayi daga kan fadin tazo tazauna cikin rawar murya tace doctor menene Dagowa yayi yana kallonta nadan lokaci sanann yamika mata takardar yana fadin gaskiya hajiya duk wasu gwaje gwajen damuka mini sun nuna kina dauke da karamin *CIKI* na sati biyu!!!! 😱""""" ?????AK ne yamata 🤔 Kubiyoni taku Maryam Mhd danjin cigaban labarin [19/07, 17:05] Hubbey Frd Ameena Kn: 📚📚📚📚📚📚 👨‍👧 _DOMUN KANWATA_ 👩‍👧 Na( *Maryam Mhd*) 1⃣5⃣0⃣ har wannan lokacin su JJ nayawo acikin daji ganin mangoron dasukayi ayashe da alaman wurinda suka zauna shiyabasu tabbacin suna cikin dajin har yanzu dan haka sukaci gaba da nemansu ganin dare yayi yasa suka yada zango dan su huta se tsinema yaransa yake akan duk su sukaja mishi wannan wahalar ba yanda ahmad baiyiba ba dayansandan akan suci gaba da nemansu tunda sunada torchlights amma sunce gaskiya sun gaji zasu huta gobe suci gaba zaune asma'u take tasa AK agaba se kuka take tana tofa mai duk addu'ar datazo mata Jikinsa yayi zafi rau gashi yana sauke nunfashi ahankali kana ganinsa kasan baccin wahala kawai yake dan da kyar yake Jan nunfashinsa ganin jikinsa nakara zafi yasa ta tafita waje tadibo ruwa aroba sannan tamatso kusa dashi ahankali tafara balle buttons din rigarsa tana kallonsa cike datausayi hawayenta nadiga akan kirjinsa har tagama sannan tafara kokarin cire masa rigar cikin dabara gudun kar ta tasheshi Har tagama cire masa rigar baisan tanayi ba tsoma rigar tayi cikin ruwan tana dora masa akan goshi nan take ruwan robar yadau dumi seda tacanzo wani taci gaba dayimasa hakan har jikinsa yarage zafi sannan ta shanya rigar ajikin runfar wurinsa tadawo ta gyara masa kuanciyarsa tadafa kansa tamishi addu'a Sannan takoma gefe tazauna tana gyara daurin kafarta daya warware tun jini nazuba har ya daskare awurin seda tawanke ta kara gyara daurin sannan tafita tayo alwala tazo tafara jero sallolin da ake binta har tagama tashiga jero nafilfili tana rokammasa sauki awurin ubangiji tana rokon allah yakubutar dasu daga hannun wa'innan mutanen yamaidasu gida lafiya har alfijiri ya keto tana zaune batayi bacci ba seda tayi sallar asuba sannan tasake matsawa wurin AK ta taba jikinsa murmushi tayi jin ba zafi ajikinsa kuma nunfashinsa yafara daidaita jin zai motsa yasa tayi saurin janye hannunta tamatsa baya Gyara kuanciyarsa yayi yacigaba da baccinsa mai cike da mafarkai iri iri marasa kan gado komawa tayi daga gefe ta kuanta nan take bacci yadauketa hasken rana ne yadaki fuskar AK ahankali yabude idanuwansa yana bin runfar da kallo lokaci guda yana tuna abunda yafaru jiya Murmushi yayi da yahango asma'u gefe akuance ta takura wuri guda tana bacci ahankali yatashi zaune yana bin singlet din jikinsa dakallo tashi yayi yadauki rigarsa dayagani arataye yasaka sannan yafita waje Roba yadauka yadibo ruwa arafi yayi alwala sannan yadawo cikin runfar yayi sallolinsa dayagama yayi addu'oinsa sannan yamatsa kusa da asma'u yana duba kafarta daya kunbura yana so yataba kafar amma yana tsoro yatasheta yajima adurkushe kusa da ita yana kallon yanda take bacci kana ganinta kasan atsorace take tashi yayi yafita daga cikin runfar yana bin wurinda suke da kallo asma'u tajima tana bacci se wajan la'asar tafarka zunbur tamike tana kallon tabarmar da AK ke kuance amma bata gansa ba zunbur tamike zata fita kenan ta hango anyi rubutu akasa da mayyan harrufa kusa da inda takwanta Durkusawa tayi tana karanta DON'T GO ANYWAY I WILL BE BACK SOON murmushi tayi tana shafe rubutun cikin siriruwar murya tafurta da wani Abu yasameka jiya zan mutu ina nadamar rashin sanar dakai cewa ina sonka amma nayi alkawarin yau zan Sanar dakai dan bansan mezai faru damu nan gaba ba tashi tayi tafita waje tayo alwala tayi sallah sannan tayi addu'ointa taroki ubangiji ya kamusu karshen wannan wahalar Rike cikinta tayi tanajin wata azababbiyar yunwa na damunta gashi tarasa inda AK yaje cikin wannan dajin jin kamar motsin mutun yasa tayi saurin mikewa atsorace taleko waje ganin AK datayi zaune abakin rafi yasa tasauke wata nannauyar ajiyar zuciya tana murmushi ta nufo inda yake Dagowa yayi yana kallonta da murmushi afuskansa yace kin tashi Kusa dashi tazauna tana dafa kafadansa tace ya jikinka Mangoron dayawanke yamika mata yana fadin naji sauki tundazu yunwa ta tasheni bashiri natafi neman abinci Murmushi tayi tana kai mangoron bakinta tace thank you kafanta yariko da hannunsa yadora kan cinyarsa yafara kwance daurin yana mata sannu dagowa yayi yana kallonta yace kidaina taka kafan kinga ya kunbura sosai yanzu kibarshi haka yanashan iska kar yazame maki babban ciwo Shiru tayi batace komai ba tacigaba da shan mangoronta tana kokarin hada kalmomin dazatayi anfani dasu wurin gayamasa abunda ke ranta Wanke hannunsa yayi shima yadauki mangoron yafara sha suna kallon ruwan dake gabansu bawanda yasake magana Sun jima ahaka secan yadago yana kallonta da murmushi afuskansa cikin sassanyar murya yace Kinkosa ki koma gida ko ? girgiza kai tayi tace nayi kewar gida amma I like it here "Why dagowa tayi tana kallonsa suka hada ido lokaci guda suka tsinci Kansu awani irin yanayin dasuka kasa fassara ma'anarsa Cikin murya mai kaman rada tace ABI aduk lokacinda nake tare dakai banadamuwa da kowane wuri muke cikin dadi ne ko wahala duk hakan baidameni ba indai zan kasance kusa dakai ada nadauka sabone ko shakuwa amma daga baya natabbatar dacewa abunda nakeji shi ake cewa SO Bansan yaushe kuma a ina nafara sonka ba amma abunda nasani kawai shine sonka yajima azuciyata ABI so dayawa mutane suna tsoron fito da sirrin zuciyarsu ne saboda gudun kar su rasa kulawar dasuke samu daga wurin wa' inda suke so Ni kaina abunda nake tsoro kenan amma bazan iya ci gaba da boye sonka araina ba tunda tafara magana yake kallon kwayan idanuwanta ko kiftawa bayayi yana hango tsantsar kaunarsa acikinsu Kauda kansa yayi cikin wani irin yanayi dayayi mai kama da mafarki Hannunta tasa ta janyo fuskarsa saitin tata idonta cike da hawaye cikin sassanyar murya tace ABI I am not asking u to love me base kasoni ba kawai kabarni naci gaba da sonka and please kar kacanza mun nariga nasaba dakai idan kayi nesa dani bazan iya jurewa ba tana kainan ta tashi tanufi runfarsu aguje tana sharan kwalla Da kallo yabita har tashige runfar bai kauda kansaba lokaci guda kalamanta namai yawo akwakwalwa yana tuna rayuwarsu tabaya da wadda sukayi acikin dajin nan mikewa yayi tsaye yasa hannayansa a aljihu yana safa da marwa awurin yarasa meyake damunsa awani hali yake ahin shima yana sonta ko kuwa yana cikin haka kamar daga sama yaji maganar yaran JJ akusa dasu saurin juyawa yayi aguje yanufi runfarsu Zaune ya iskota kan tabarma ta takure wuri guda tana jin haushin kanta datagayamasa tana sonsa yanzu tasan shikenan abunda take gudu ne zai faru zai janye jikinsa daga gareta Saurin karasawa yayi wurinta ya durkusa agabanta cikin rada yace chitti gasunan sun iso kitashi mugudu atsorace tamike tsaye tana zare idanuwa riko hannunta yayi aguje suka fito daga cikin runfar sedai kafin sugudu JJ sun iso wurin shan gabansu yayi ya saitasu da bindiga yana kwashewa da dariyar keta yace Dakata mana AK ina kuma zakuje ai gudu yakare daga yanzu zaku huta muma muhuta da wahalar bibiyarku Cak sukatsaya suna kallonsa ba alaman tsoro atare dasu cike da takaici AK yace to mekake jira kaharbemu mana Wancan karon ma sakacinka ne yasa muka gudu to yanzu ma inkayi wasa guduwa zamuyi kuma kasake nabar nan wurin to daganan nine zanfara nemanka kana guduwa idan kuma nakamaka bazaka taba samun damar dazakayi kwakkwaran motsi bama bare kayi yunkurin guduwa Kallon yaransa yayi suka tuntsire da dariya seda sukayi mai isarsu sannan ya saita bindigarsa kan AK yana kirga uku Kuka asma'u take tana kankame AK ajikinta se rokonsu take karsu kasheshi amma banda dariya ba abunda suke dai daga cikin yaran yasaitata da bidiga yana fadin kar kidamu yan mata ai tare zaku tafi bahaka kuke soba rungumota AK yayi akirjinsa takara kankamesa dakarfi tana runtse idanuwanta JJ na kirga uku yadora yatsansa kan kunamar bindigar zai harba kenan yan sanda suka iso wurin tare da ahmad nan fa aka fara musayar wuta tsakanin yan sandan da su JJ Tundaga nesa ahmad ke kwalama AK kira yana fadin su gudu tsaye AK yayi cike dafarin ciki yana kallon ahmad se washe baki yake yakasa motsawa gashi se harbi ake da bindiga amma ko ajikinsa Jan hannunsa asma'u tayi dakyar yabar wurin suka ruga aguje sukayi wata doguwar hanyar dasuka gani Sunyi tafiya mai nisa kafin suka iso wata kasuwar kauye da mutane dayawa awurin kowa na harkan gabansa tsaye sukayi awurin suna maida nunfashi Cike da takaici AK ya kalli mutanen wurin yana jan tsaki yace yanzu duk wahalar da mukasha ashe akwai dubban mutane anan wurin amma ko tsuntsu bamu gani ba [19/07, 17:05] Hubbey Frd Ameena Kn: 📚📚📚📚📚📚 👨‍👧 _DOMUN KANWATA_ 👩‍👧 Na( *Maryam Mhd*) 1⃣5⃣5⃣ hannunta narawa takarbi result din tana dubawa tajima azaune awurin hawaye natsere akan kuncinta dakyar tamike tsaye tana neman faduwa saboda jirin dake dibarta saurin mikewa doctor yayi yana fadin easy madam are u alright Bata kula saba tafita daga office din tana Jan kafa kamar wacce aka zarewa lakka zama tayi acikin motarta tadafe kai cikin rawar murya tace what....what... have I done ...I am ...such a fool garin ya nabari haka tafaru wane mataki dady zai dauka akaina ya AK zai yi idan yasan ina dauke da *cikin da banashi ba* fashewa tayi da kuka tana fadin *SALIM* kacuceni yanzu yazanyi ni aysha nashiga uku Tajima tana kuka kafin tayi saurin daukar wayar ta takira wata number Tajima tana ringing kafin yadaga cikin muryan bacci yace Baby kintuna dani yau shine zakimun kiran asuba na.... Katseshi tayi da fadin salim kana ina ne we have a problem Dariya yayi yace anzo wurin dama ai bakya nemana se kinada matsala fashewa tayi da kuka tana fadin salim please it's a serious problem I am ..... Saurin tashi zaune yayi yana fadin ohh my god baby are u crying Shiru tayi batace komai ba taci gaba da kukanta Ajiyar zuciya ya sauke yana kallon agogon dakin yace ok ni... ina gida yanzu zakizoni ko inzo insameki tada motar tayi tana fadin a'a ganinan zuwa yanzu daidai wani katafaren estate tayi horn mai gadin yaleko yana ganinta ya washe baki yana fadin ahhh beautiful barka dazuwa .... Harara tamaka mai tana jan tsaki tace kai dallah open the get for me I don't have time for u nonsense Budemata get din yayi tashiga tana gama parking tafito da gudu gudu take hawa stairs ahawa nabiyu tatsaya dadai wani hadadden apartment tayi knocking bata jima atsaye ba aka bude kofar wani dan kyekkyewan saurayi ne atsaye yana mata murmushi ( salim kenan saurayin aysha ne tun tafiyar dasukayi London itada sarah tahadu dashi tun tana wulakanta shi har tafara kulashi saboda tako ina yahadu yasan duk wata hanya dazaibi yashawo kan mace ya iya soyayya gashi yana sakemata kudi kamar hauka Kwararen lawya ne maizaman kansa yanada kudi daidai gwargwado gashi shikadai ne awurin babansa shiyasa yazama dan gata duk abunda yakeso shi akemai Wata rana aysha tazo gidansa tana kuka saboda damuwar rashin kulawar AK dabata samu Garin lallashinta ne har suka wuce gona da iri shine wanda yafara saninta ya'mace kuma daga ranar ciki yashigeta Idan yamata maganar aure setace tana so se ta mallake dukiyar AK gaba daya sannan zata aureshi saboda shine burinta da na iyayenta tun bayaso har tanuna mai irin ribar dazasu samu tagayamai kadan daga cikin kadarorin AK tun daga lokacin shima yafara kwadayin dukiyar ) kauda kai tayi tana share kwalla Janyota yayi ciki yana rungumeta yace baby I missed u so much Turesa tayi tawuce Palo tazauna tana rabka uban tagumi Karowa yayi kusa da ita yazauna yana fadin come on baby banason ganinki haka gayamun damuwarki kinsan uwarki ta haifeki ne dan kikawo matsala nikuma uwata ta haifeni dan na magance maki ita hararansa tayi tace kafara ko??? Dariya yayi yana shafa kai yace sorry namanta ne yanzu gayamun meyake damunki ciro result din tayi daga Jakarta tana nuna masa tace salim inacikin babbar matsala dama na gayamaka banajin dadi to yanzu haka daga asibiti nake doctor ya tabbatar mun inada ciki shiru yayi yana kallon result din nadan lokaci sannan yadago yana kallonta yace look aysha nafasan halinki idan kina bukatar kudi ba abunda bazakiyi ba idan kinsan karya kike to garama kifito kigayamun sannan kinsan ko nawa kike so zan iya baki but don't play games with me riko hannunsa tayi tana kuka tace salim allah dagaske nake idan baka yarda ba muje tare dakai kagani Dafe kai yayi yana tunanin ta inda zai bulloma lamarin kamar daga sama yaji tace Salim nidai tsoro nakeji gaskiya muje acire cikinnan Saurin dagowa yayi yana nunata dayatsa cikin kakkausar murya yace Kar ma kifara aysha bakida hankali ne zubarwa fa kikace to wallahi kinji narantse kar ki kuskura kizubar mun da ciki kinji ko ina son abuna rungumeshi tayi tana fashewa da kuka tace salim tsoro nakeji idan dady yasani zai kasheni sannan kuma .....AK idan yagane inada ciki zai rabu dani kaga bazai aureni ba bare har mucimma burinmu Shafa kanta yayi yana fadin stop crying baby nothing bad will happen kin manta ina tare dake yanzu dai zauna muyi magana Zaunawa tayi tana ci gaba dakukanta Share mata hawaye ya shigayi yana fadin ya isa haka kidaina kuka mana ko kinaso wani abu yasami babynmu ne girgiza kai tayi tana shafa cikinta hannunsa yadora kan nata yana murmushi yace love u my baby tashi yayi yanufi kitchen bayan dan lokaci yafito rike da fresh jus acikin glass cup yamika mata Kusa da ita yazauna yana sauke ajiyar zuciya yace yawwa to yanzu kinsan ya za'ayi Girgiza kai tayi tana ijiye cup din hannunta akan table takureshi da ido takosa taji mezai fadamata murmushi yayi yace ya zancan AK anganshi kuwa ? Kauda kai tayi tana fadin sundawo jiya Kusanta yamatso ya juyo dafuskanta yana fadin kawo kunnenki to kiji wata magana yamata akunne tayi dariya cike dafarin ciki tace wow!!! salim shiyasa nake sonka akwaika da brain kaga daga nan hankalin AK zaidawo kaina munayin aure kuma se insa yaimaida dukiyarsa kan sunan danmu daga nan kuma se..... dariya sukasa suna tafa hannu ta rungumeshi tana fadin thank you dear Shafo cikinta yayi yana murmushi yace gaskiya yau kin zomun da albishir mai dadi kinada kyewta mai tsoka ture hannunsa tayi tace to saura garin rawar kafarka kabari aharbo jirginmu Kara maida hannunsa yayi kan cikinta yana langabe kai yace allah sarki AK uwata ta haifeni dan inmaki ciki shikuma uwarsa ta haifesa dan yazama uban dan sannan yakai bakinsa kan cikinta yana fadin kai kuma baby uwarka zata haifoka dan ka kawo mana kudi mikewa tayi tsaye tana kaimasa duka da pilo tace u will never change salim kafa girma yanzu u are going to be a father yakamata kanatsu dariya yayi yana mikewa tsaye yace baby bari inzo inkaiki wani hadadden wuri kigani antanadeshi ne kawai dan masoya murmushi tayi tace ai kai kam kahadu tawannan wajan shiyasa nakasa hakura dakai Janyota yayi jikinsa yana rungumota tabaya yakai hannunsa kan cikinta bakinsa daidai kunnanta cikin rada yace ohh tanan wajan kawai nahadu ko se antabayi baby yaraba mana gardama hannunta takai baya tana shafo sumar kansa tace kahadu tako ina my Romeo shiyasa nakosa nagama da wa'iccan muyi aurenmu Dariya yayi yasaketa yawuce daki yana dan tsalle yace ohhh I can't wait for that day to come inganki amatsayin matata harda dan babynmu kamar yadda suka zo jiya haka ma yau suka taru gida yacika da yanuwa tamakar gidan biki se raha ake ana murna ya yinda gefe guda khadeeja da ahmad suka tasa AK da asma'u gaba akan se sunbasu labarin abunda yafaru atafiyar su se wasan buya suke tsakaninsu kowa bayason bada labari daga karshe guduwa AK yayi yabuya adakin sarah Asma'u kuma tajima dashiga dakin grany sun rasa inda tayi tana fitowa daga bayi kenan taga khadeeja akan gado juyawa tayi zata fita taga ahmad abakin kofa ya harde hannaye yana murmushi komawa tayi bakin gado tazauna tana fadin ok fine naji zan Baku labarin amma karwanda yamun tambaya harse nagama Karasowa yayi cikin dakin yazauna kan kujera suka sakata agaba suna saurare labarin tafara basu kanta akasa tana murza yan yatsunta har tazo wurinda nunfashin AK kedaukewa sannan ta tsaya tana kame kame Kara matsowa kusanta khadeeja tayi tana fadin se meyafaru ya akayi nunfashinsa yadawo hararanta Ahmad yayi yana danne dariyarsa yace ke batace karmu tambayeta ba sanann yakalli asma'u yana fadin manta da ita aunty cigaba dabamu labarin Sosa kanta tayi idonta arufe tace se..... Nataimaka masa.... katseta khadeeja tayi dafadin dame kika taimaka masa Hararanta tayi tace bansaniba allah se infasa bada labarin Sorry ....tafada tana gyara zamanta Kallon ahmad tayi tace ai kai kagane ko ? Dariya yayi yace sosaima ba irin yadda innunfashin mutum yadauke ba se kasa bakinka ka.... Katseshi tayi dafadin badai ka ganeba to miye kuma nase kafada shiru sukayi suna kallon juna shida khadeeja kamar su tuntsire da dariya amma suna danneta dan sunkosa suji ko tafadamasa tana sonsa Cigaba tayi dabasu labarin har wurinda tagayama AK cewa tana sonsa Ihu sukayi cike dafarin ciki khadeeja tafada kanta tana fadin wow ammah gaskiya kinyi kokari dama ina wajan inga yanda abun yakasance Dariya ahmad yayi yana nikewa tsaye yace to shikuma meyace sunkuy dakai tayi cikin sassanyar murya tace baice komai ba kuma dama ban fada dan inji mezai ce ba kunga ko yanzu abunda nake gudu ne yafaru tunda bama zama waje guda bare muyi fira ko yamun magana Fita ahmad yayi yana fadin karki damu komai zai wuce zaku saba ai ki shirya shima ya kusa cewa yana sonki da daddare bayan kowa ya watse AK yana zaune apalon masa yanason shiga bangarensa amma yanajin kunyar haduwa da asma'u se dannan waya yake yana duban agogo aysha nadaga gefe takira nura tabashi glass cup din jus tace yakaima AK yace inji grany yana zuwa yamika mashi karba yayi yana murmushi yakafa kai seda yashanye shi tas sannan ya ijiye cup din Baifi minti 5 ba kansa yafara juyawa saurin dafe kai yayi yana salati yazo tashi amma yakasa saboda jirin dake dibarsa Karasowa palon aysha tayi takamashi tanufi dakinta dashi Sam baisan duniyar dayakeba tana zuwa takwantar dashi kan gado Seda tacire masa kayansa kap tabarsa dagashi sai boxer sannan tarufa mai bargo takoma gefe tana sauke ajiyar zuciya can cikin dare asma'u tafarka amma bataga AK ba kuma ba alamr yashigo dakin bare har ya kuanta Tashi tayi tafito Palo nan ma wayam daki to koma ta zunbulo hijabinta tasauka kasa Duk inda take sa ran zata gansa taduba bata gansa ba takira wayansa kuma taji tana ringing akan kujerar Palo cike da damuwa ta koma bangaresu tana addu'ar allah yasa lafiya Zaunawa tayi anan Palo dan Sam taji baccin yafita idonta se safa da marwa take tana duba agogo """" [19/07, 17:05] Hubbey Frd Ameena Kn: Cikin baccinsa yake jiyo sheshshekar kuka sama sama kamar amafarki ahankali yafara bude idanuwansa yana dafe kai saboda nauyin dayayi masa cike da mamki yake bin dakin da kallo har idonsa yakai kan aysha dake zaune gefensa daga cikin bargo tana rusa kuka saurin tashi yayi zaune yana kallon ikon allah bakinsa narawa yanaso yayi magana amma yarasa mezai furta sauka yazoyi daga kan gadon yaga kayansa akasa saurin komawa yayi yazauna yana fadin wai meyake faru..... Katseshi tayi dafadin dole katambayi meyake faruwa bayan kagama biyan bukatarka kallonta yayi dajajayen idanuwansa cikin rawar murya yace kamar...ya...banganeba ....aysha wai menake adakinki ne awannan lokacin kuma akan gadonki and why are u crying Fashewa tayi da kuka cikin daga murya tace ba abunda kake adakina zaka tambaya ba abunda kayi adakina zaka tambayeni kukan kuma inayinsa ne saboda kacuceni ka zalinceni ka lalata mun rayuwata ka.... Katseta yayi yana daka mata tsawa yace shut up dallah what kind of joke is this .. "I am not joking AK u raped me saurin matsawa yayi yana kallonta cike da tashin hankali jikina har rawa yake ga kansa dayake Sara masa jinin dayagani kan gadon shiyakara rikita masa lissafi cikin rawar murya yace me....but...how garin ya haka tafaru abunda bantaba yiba ba halina bane ko amatan banza ma bare ke kanwata Cikin sheshshekar kuka tace nima bansani ba jiya ina kuance kawai naji kashigo mun adaki duk yadda naso inmaka bayani baka saurareni ba dakarfin tsiya ka turani kan gado nayi kokarin in kwaci kaina amma nakasa ... takarashe maganar tana fashewa da kuka jiri ne yadibesa yaja dabaya dabaya ze fadi yayi saurin rike kujera zama yayi akai yana dafe kansa wasu hawaye masu zafi suka gangaro kan kuncinsa kokari yake yatuno abunda yafaru amma yakasa abunda yake iya tunawa kawai shine lokacinda yake zaune apalo yana danna waya daga nan kuma baisan meyafaru ba se yanzu dayafarka yaganshi anan ya jima ahaka kafin da kyar ya iya dago kai yana kallonta yanaso yayi magana amma Sam yakasa bude bakinsa tashi yayi yadauki kayansa yasaka batare dayace komai ba yafita daga dakin Tana ganin yafita tamike cike dafarin ciki tafara rawa tana murna tafiya kawai yake amma Sam baya cikin hayyacinsa jiki asanyaye ya nufi bangarensa Yana tura kofar asma'u tamike azabure tanufosa tana fadin ABI are u alright daga ina kake naduba ko ina banganka ba gashi har asuba tayi allah yasa lafiya wuceta yayi kansa akasa batare dayace komai ba yanufi daki Shan gabansa tayi tana riko hannunsa cikin rawar murya tace ABI meyake damunka ya naganka haka kaga..... Kwace hannunsa yayi yana damko kafadunta cikin kakkausar murya yace Akan wane dalili kike tambayar daga ina nake dole ne se kinsan Inda naje da inda nakuana kar kimanta har yanzu bakida wani matsayi awurina so stop acting like my wife .... yana kainan ya turata dakarfi ya wuce daki yana banko kofar dakarfi kan kujera tafada tana binsa da kallo idonta pal kwalla tana mamakin meyake damunsa ne haka zama tayi anan palon taci gaba da kukanta lokaci guda maganarsa namata yawo a kunne bayi ya wuce direct ya sakar ma kansa shawa idonsa arufe hawaye nazuba akan kuncinsa lokaci guda yaji ya tsani kansa wai yarasa wacce zai ma fyade se kanwarsa tajini dakyar yasamu yayi wanka ya shirya ya nufi masallaci acan ya zauna seda gari yawaye sanann yanufo gida yafara shirin zuwa office yana wurin dressing mirror yana fesa turare asma'u tashigo rike da coffee dinsa batare data kallesa tawuce ta ijiye kan bedside drawer sannan tafita Dakallo yabita har tafita sannan yasauke ajiyar zuciya yana ji bai kyewta abunda yamata dazu ba bayan yafito dakin aysha yafara lekawa tana bathroom zama yayi akan gado yana jiranta Tana fitowa tagansa azaune nan take ta hade fuska ta wuce drowan kayanta tana share kwallan munafunci tashi yayi yakarasa wurinta cikin sassanyar murya yace aysha I am really sorry ni kaina bansan ya akayi haka tafaru ba amma ki yi hakuri ki rufamun asiri banaso kowa yaji maganar nan kuma namiki alkwarin duk yanda za'ayi zan yi kokarin ganin anyi aurenmu nan bada jimawa ba banza tayi dashi tanufi dressing mirror yakara binta yana bata hakuri seda kyar ta hakura Tana murmushi tace shikenan insha allahu ba Wanda zai ji kuma nayafemaka ai kasan ina sonka .... takarashe maganar tana kokarin rungumeshi yayi saurin juyawa yafita yana fadin thank you ga magani nan na ijiyemaki kici abinci kisha Da kallo tabisa tana murmushin mugunta tace zan rufamaka asiri har lokacinda cikina zai bayyana daga nan kuma ur name is sorry cikin kuanakinan haka AK yadawo so silent ba um ba um um tun ba aluraba har aka gane kowa yafara tambayarsa sedai yace ba komai tsakaninshi da asma'u kwa ido ne dan har yanzu basu fara gaisawa ba .......lol Sedai zuwa wannan lokacin ya tabbatar ma kansa cewa yana sonta amma bayada kwarin guywar gayamata sedai koda bazai iya gayamata damuwarsaba to yana son ganinta akusa dashi yana Satan kallonta hakan ma ya isheshi Itama tadamu sosai dayana yinsa amma seta dangantashi da cewar datayi tana sonsa

Chapter 22 of 35