yayi jikinsa asanyaye yace shikenan friend ka kula dan allah idan kaga wurin da hadari kar kashiga kajira se munzo kaji
To yafada yana juyawa yafita bin bayanshi aysha tayi har yafita tarikoshi tana fadin AK wai mekake shirinyi ne
Juyowa yayi yana fadin abunda yadace
fashewa tayi da kuka AK yaruwarka fa zakasa ahadari saboda asma'u to gaskiya sedai kazaba ko ita ko ni idan har katafi wurinta sedai kahakura dani
Shiru yayi nadan lokaci sannan ya kwace hannunsa daga nata ya juya yana fadin nabarki lafiya
Saurin shangabanshi tayi tana kuka tace AK dagaske tafiya zakayi
Gefen fuskanta yashafo yana murmushi yace aysha nasan kindamu dani shiyasa kike haka amma kiyarda dani ba abunda zai sameni insha allah
Yana kainan yayi gaba dakallo tabisa har yashiga mota yatafi sannan tajuya ahasale tanufi dakin aysha
tana shiga ta isko sarah na Neman JJ awaya hankali tashe yana dauka tace JJ wai kai wane kalan sakarai ne to kasani ga Yayana nan zuwa kuma wallahi kasake yakamaka kai kasani karma ka ambaci sunana
tsaki yayi yace to seme inyazo ke nifa banason takura kingane ko inace ko gama biyana bakiyi ba kinzo kin isheni da surutu kibarshi yazo mana alqur'an ana kamani sunanki zan fada banza yar tasha kawai
saurin katseshi tayi dafadin yi hakuri JJ raina ne abace yanzu kasan meza'ayi
Kawai kasaki yarinyar kubar wajan kafin ya iso kunji
dariya yayi yace ni banda matsala kawaidai kituran sauran kudina ni kuma zan sallameta
tsaki tayi tana katse kiran tazauna bakin gado tana share zufan da takaryo mata se tsinema JJ take
Juyawa aysha tayi tafita batare datace komai ba tanufi bangarensu
Haduwa tayi da jamilu zai fita aiki fadawa tayi kan jikinsa tana kuka
Rikota yayi atsorace yana tambayar meyafaru
Cikin kuka tagayamasa duk abunda yafaru da tafiyar AK wurin asma'u
zama yayi kan kujerar Palo yana cire hularsa yace ina bazai yuba gaskiya haka kawai muna gani munaji Abu zai rikice mana wallahi natsani yarinyarnan ga dukkan alamu AK yafara sonta
Sadiya dashigowarta kenan palon tace yana fara kulata kuma zata fara zazzago Ya'ya daga nan kuma muntashi aiki daga karshe ayi waje damu
Kallon aysha yayi yana fadin kinsan Wanda sarah tabama aikin
gyada kai tayi tana share kwalla
murmushin mugunta yayi yace jeki satomun numbansa amma karki bari tagane
Fita tayi cike dajin dadi tanufi dakin sarah da dubara tasamu tadauki numban JJ tadawo bangarensu
Karban numban uncle jamilu yayi yakira bugu biyu yadaga yana fadin waye ne
Canza murya jamilu yayi yafara fadin
Sunana basiru nasan sarah tabaka aiki akan kasace khadeeja bai mistake kasaci yayarta yanzu kuma tace maka kasaki yarinyar yin haka kuma hadari ne babba awajanka
Katseshi yayi dafadin to malam basiru kake ko wa ??
abunda kakira ka gayamun kenan ?
Dariya uncle jamilu yayi irin tasu tamanya sannan yace JJ nima fa dan ahnnu ne saboda haka aiki zanbaka
bansan konawa sarah tabaka ba amma zan linkamaka konawane ka kashemun yarinyar kafin AK yaje wurin
Dariya JJ yayi yana hura sigari yace angama yallabai irinku mukeso masu bamu aiki kai tsaye
dariya jamilu yayi yace kardamu JJ yanzu zakaji alert narabin kudinka sauran kuma ina ganin gawarta zakagansu
cike da farin ciki JJ yagayamasa kudin da account numban daza'a turamasa kudin sannan suakayi sallama nan take ya dibi yaransa suka nufi dajin da asma'u take
kallonsa aysha tayi da mamki tace dady meyasa kace sunanka basiru
Dariya yayi yace yarinya ai awannan harkar wawayene kawai ke fadan sunansu nagaskiya kinga yanzu koda wani Abu yafaru yansanda suka tuhumeshi zaice basiru ne yasashi to waye basiru??
Dariya sukasa gaba daya cike da farin cikin burinsu yakusa cika
gudu AK yake amota kamar zai tashi sama yana mamkin nisan dayayi amma har yanzu arrow din baidaina nuna hanya ba seda yakai inda motarsa bazata Shiga ba yayi parking dinta yafara tafiya akafa yana ma Ahmad kuatancen inda yake
Yayi nisa sosai adajin ahmad yakirasa awaya yace gaskiya ya jirasu gasunan zuwa sun isko motarsa awani wuri shi sam bai yarda da .....
Hello hello AK yafarayi dan baiji karshen maganar ahmad ba
Jin shiru yasa yadago wayar yaduba zaro ido yayi ganin wayar amace yakunna kuma taki tashi
Hannu yadora akai yana fadin namutu ni Abidi yanzu taya su ahmad zasu San inda nake cikin wannan dajin
Jiyayi kamar yakoma wurin motarsa se kuma ya tuna baisan halin da chitti take cikiba
Kallon agogon yayi sannan yayi shahada yabi hanyar dayake nuna masa
har yamma tayi amma AK baikaiba har yafara sarewa da lamarin yana tsinema agogon ahmad shikadai se magana yake gashi ya gaji fatanshi daya allah d
Sa ba banzan agogo bane wannan yabi ta karyan turawa zai kashe kansa
jin karan agogon yakaru yasa yayi saurin kallonsa dariya yayi cike da farinciki yanufi inda yanuna mai baiyi tafiya mai nisa ba yahango runfar du JJ kuma nan agogon ya nuna masa
Cikin aljihu yasaka agogon cikin sanda da dabara yakarasa wurin kwance suke suna bacci suduka bayan sunsha giya sun bugu
ahankali yake takawa har yatsallekesu yashiga runfar can gefe ya hangota azaune tacusa kai aguywa tana kuka saurin karasawa yayi wurinta yana murmushi cikin rada yace chitti!!!
kamar amafarki taji muryansa saurin dagowa tayi dan ganin koda gaskene
zagayowa yayi tabayanta ya kuance mata daurin kamar jira take tafada jikinsa tana fashewa da kuka rungumeta yayi nadan lokaci sannan cikin rada yace kinga tashi mutafi idan munbar nan wajan se kiyi kukan
dariya tayi ta tashi tana fadin ya akyi kazo nan Jan hannunta yayi yana mata alama tayi shiru
suna fitowa sukaga ba yaran JJ awurin zaiyi magana kenan yaji ansamai bindiga abayan wuyansa cikin muryan mashaya JJ yace sannu da kokari AK
hannayansa yadaga sama yana juyowa ahankali itama asma'u tayi yanda taga yayi atsorace jikinta se rawa yake
kara saita bindigarsa yayi yana dariyar keta yace kayi Babban kuskure daka shigo gonata doka tace idan har nakama mutum yayi kokarin guduwa to kisa ne hukuncinsa saboda haka
saita asma'u yayi da bindigarsa yana dariya yace kiyi addu'ar karshe yan mata
saurin shiga gabanta AK yayi yana kallon JJ yace
dakata dan allah kayi hakuri kabarta ta tafi lafina ne nizaka kashe ba itaba katausaya mata mana mace ce fa mezaka samu idan ka kasheta tukunna ma akan wane dalili ka kamata kafada konawa kake so zan baka amma kabarta ta tafi
Kallon yaransa yayi suka kwashe da dariya seda sukayi mai isarsu sannan yasaita bindigar kan AK yana fadin to ai kaima ba kyaleka zanyiba tunda har kaganni kuma kaga mabuyata to dele kamutu
janyo hannunsa asma'u tayi tadora bindigar kan goshinta cikin kakkawsar murya tace zaka iya kasheshi amma sedai kafara kasheni tukkuna
saurin janyota AK yayi tafado jikinsa yana fadin chitti mekikeyi hakane
Dariya JJ yayi yana kallon yaransa yace haba tundazu ina mamakin meyasa AK zai sadaukar da rayiwarsa yashigo wannan dajin saboda wata yarinya Ashe masoyane hahahhaha
juyowa yayi yana kallonsu yace Romeo da Juliette banada isashshen lokaci kuazabi wazan fara kashewa acikinku ko kuma ni nazaba
Shiru suakyi suna kallon juna hawaye nabin kuncin asma'u tana tuna halin da iyayensu zasu shiga idan suka ga gawarsu atare
Shima AK abunda yake tunani kenan
Dariya JJ yayi ya umarci yaranshi dasu rike mashi AK shikuma yasaita bindigarsa kan asma'u
Sam bata damu da bindigar ba hankalin nakan AK dake kokarin kwace kansa daga yaran yana rokon JJ dayarabu da ita
kallon juna suke lokaci guda suna tuna rayuwar dasukayi abaya hawaye nazuba akan kuncinta amma da murmushi afuskanta tana kallon AK
kallonta yake shima baisan lokacinda hawaye ya zubo mashi ba cikin rawar murya yace JJ dan allah na rokeka kabarta ta tafi idan ma zaka kasheta dan allah kafara kasheni tukkuna I can't watch her dying
dafe goshi JJ yayi yana kallon AK yace
aK kamun shiru ni idan ina aiki banason hayaniya
Kallon yaransa yayi yace gayu gaskiya tunda nake bantaba kashe masoya ba kuma gaskiya bazan iya barinsu sutafi ba dole ne su mutu ya za'ayi
dariya sukasa dayan yace oga to mezai hana kabani bindigar nagama musu aiki
Shiru yayi nadan lokaci sannan ya tuntsire da dariyar mugunta yace gawata dabara
Bishiyar kusa dasu yanuna musu yana fadin kudauramun yagiya ajikin waccan bishiyar zamuga idan dagaske bazai iya ganinta tana mutuwa ba
Nan take suka daura yagiya kamar yadda yace hannayensu yasa suka daure sannan suka nufi wurin bishiyar dasu
duk yanda AK yayi kokarin kwace kansa amma abun yagagara sarkin yawa yafi sarkin karfi ga bindiga ahannunsu ita dai asma'u tuni ta saduda tagama sallamawa kawai mutuwa zasuyi to meyasa zata dami kanta
Banda kuka ba abunda take se rokonsu take surabu da AK sukasheta amma ko kallonta basuyi ba
har dare yayi ahmad nayawo da yansanda adajin amma sun rasa ta inda zasu nemesu gashi wayan AK akashe ba yanda baiyi da yan Saddan ba akan suci gaba da nemansu amma sunki wai dare yayi bazasuyita shiga cikin daji ba zasu koma idan sun shirya zasu zo aci gaba da nemansu
Bayanda ya iya haka yahakura jiki asanyaye yakoma gashi khadeeja se kiranshi take tana tambayar yagansu sedai yabata hakuri yace zasu gansu
acan gida kuwa gaba daya hankalinsu yakara tashi ganin ahmad yadawo batare dasu AK ba Umma ma seda ahmad yakira doctor yamata alluran bacci gudun kar ciwonta yatashi Abba kuma tuni yafada amasallaci atayasu da addu'a
Khadeeja kwa banda kuka ba abunda take da kyar ahmad ya lallasheta tayi shiru
Haka ma bangaren grany da inna ameena abinci da kyar sukeci dan gaba daya gidan ba dadi
Ita kanta Sarah tashiga damuwar rashin AK dan tasan JJ bayada mutunci zai iya hadasu gaba daya yakashe gashi tana kiransa baya dauka daga karshema yayi blocking numberta
Aysha ma tadamu ganin AK baidawo ba amma da jamilu yakira JJ seyacemasa AK baijeba asma'u kuma yakasheta kawai yajira gawarta nanan zuwa
Se alokacin hankalinsu ya kwanta sukaci gaba da nuna fake damuwansu akan rashin dawowarsu
kama asma'u sukayi suka ratayeta ajikin yagiyar ga hannayenta adaure
Dai cikin yaran yana rike da kafafunta wanda daga yasakesu wuyanta zai sarke ajikin yagiyar
Kuka AK yake kamar karamin yaro bashiri yasa karfinsa gabadaya yakwace kansa aguje yakarasa wurinta yana kuka yana rokonsu dan allah sukwanceta
dariya sukasa gaba daya suna kallonsu
yaron dake rike da ita yace oga nagaji pah yasin zan saketa
karasowa JJ yayi kusan AK yana fadin zaka iya taimakonta ai dasauran dan lokacinda yaragemuku kafin wahala takarasaku
durkusawa AK yayi akan guywowinsa aka Dora kafafuwan asma'u akan kafadunsa tayi tsaye
Dariya sukayi dai cikin yaran yace oga kana ganin zai iya juran daukanta kuwa
"To ai hikimar abun kenan shi dakanshi zai kasheta idan kuma bai kasheta ba ita zata kasheshi
Haka zamu barsu su kwana har gobe idan basu mutu ba dasafe zamu kashesu kafin mu barnan
juyawa sukayi suka koma gefe guda suka fara shan giyarsu suna fira
Hawaye ne ke zuba akan kuncin asma'u kamar anbude panpo har suna diga sama kan AK
ahankali yadago kansa yana lekenta yace chitti yayyafi akene kece asama zaki fini sani naji Abu nadiga akaina
Cikin muryan kuka tace ABI why did u come
"aw abunda ma zakice kenan maimakon kigode mun nazo taimakonki shine zaki ce meyasa nazo ko
"To yanzu me zuwannaka ya anfanar ni bantsira ba gashi zamu mutu gaba daya
murmushi yayi yace bazaki mutu ba chitti kafin Nazo nan wurin seda nabiya wurin Umma namata alkawarin zan maidaki gida to koda zan rasa raina insha allahu se kinkoma gida karkidamu
sautin kukanta ne yakaru tace ABI ni nafiso namutu karayu akwai mutane dayawa akarkashinka ga grany da sarah wane hali zasu shiga idan wani Abu yasameka
"Kema ai kinada responsibility ga Umma ga inna da khadeeja kece mai kula dasu yazasuyi idan bake
Cikin sheshshekar kuka tace idan har kana nan bandamu ba nasan zaka kulamun dasu amma idan baka ni bazan iya komai ba ABI
runtse idanuwansa yayi dan tuni kafadunsa sun fara zafi cikin muryan wahala yace yanzu dai abar zancan meyasa kincika surutu ne kina gabar mutuwa ma bazakiyi shiru ba to nidai ki kyaleni inyi istigfari dan nafara hango barzahu
Shiru tayi hawayenta nakaruwa tana ji dama itace akasa dan tasan shikadai yasan meyakeji ahalin yanzu
Har dare yayi su AK na ahaka tuni yafara gajiya dan har wani jiri jiri kedibansa kawai taimakon allah ne da jarumta irin tashi yasa har yanzu yake durkushe awurin amma guywowinsa da kafadunsa jiyake kamar ana Sara mai gatari gashi yanada asma tuni yaji tafara kokarin tashi
asma'u ma haka tagaji da tsayuwa jikinta har rawa yake tun tana kuka har tagaji tayi shiru tana addu'a sedai jefi jefi AK yakan tsokaneta wani lokaci takulashi wani lokaci kuma sedai tafashe da kuka har takai lokacinda suduka sukayi shiru bamai magana """""
[19/07, 17:04] Hubbey Frd Ameena Kn: ππππππ
π¨βπ§ _DOMUN KANWATA_ π©βπ§
Na( *Maryam Mhd*)
1β£4β£5β£
Kokarin janye kafarta tafarayi daga kan kafadunsa tana fadin ABI
katashi katafi kabarni anan kawai koban mutu yanzuba anjima mutuwa zamuyi gaba daya dan natabbata bazamu iya kai safe ahaka ba kuma koda munkai ma kashemu zasuyi
Kaga damu mutu gaba daya gara kai katsira koba komai abun zaima su Umma sauki
Kokarin kuance hannayensa yafarayi yana fadin chitti miye haka kike kokarin yi stop moving ur legs dan allah u are hurting me kina so kikashe kanki ne idan natafi nabarki anan miye anfanin zuwana mezan gayama su Umma idan nakoma
Cikin Sa'a kuwa ya kwance hannayansa har takusa sauke kafanta yayi saurin rikosu cikin rawar murya yace
Chitti kinga na kuance hannayena kiyi kokarin kwance naki abun baida kwari sosai
Shiru tayi hawaye nacigaba dazuba afuskanta yana rike da kafafuwanta akan kafadunsa yana cigaba da lallashinta har tafara kwance hannayenta da taimakon allah tayi nasaran kwancewa sannan tafidda yagiyan wuyanta atare suka fadi awurin suna maida nunfashi
Cike da tausayi ta sunkuyo saitin fuskar AK cikin rada take jera mai sannu
Yajima ahaka kafin dakyar ta taimaka mai yatashi yana runtse idanuwa saboda azaban da kafadunsa da guywowinsa kemasa
Hannunta Yakama yana leken su JJ dake sharan bacci kaman matattu sunsha sunyi tatil
Cikin sanda suka fara tafiya seda suka dan yi nisa sannan suka fara gudu suna kara shiga cikin dajin batare da sunsan inda suka dosa ba
Sunyi nisa sosai asma'u taci birki tana fadin ABI gaskiya nagaji bazan iya cigaba da gudunnan ba mudan zauna mu huta mana
bai musa mata ba dan shi kanshi juriya kawai yake amma bayajin zai iya tafiya mai nisa bai fadi ba
Zaunawa sukayi suka jinginu da katuwar bishiyar dake wurin suna maida nunfashi sun jima ahaka kafin suka fara bin wurin dakallo se alokacin suka fahimci ba karamin daji suka shigo ba dan gaba daya wurin manya manyan bishiyoyi ne azagaye dasu kasan kuma ciyayi ne da ramummuka iri iri
Adan tsorace asma'u tamatso kusan AK cikin rada tace ABI nan ina ne
jinginar dakansa yayi jikin bishiya yana lumshe ido cikin dasashshiyar muryansa yace da a maiduguri muke dase ince wannan shine dajin sambisa
amma yanzu bansan mezan cemaki ba
shiru tayi nadan lokaci tana kallonsa sannan ahankali tadafa kafadansa cikin sigar tausayawa tace kanajin zafi ko
Dagowa yayi yakalleta suka hada ido sannan yaballe bottom din rigarsa yafito dakafadansa yana murmushi yace ba sosaiba nagode allah bakida nauyi sosai da yau namutu
Murmushi tayi da hawaye afuskanta tadora hannunta kan kafadarsa tana shafawa ahankali
Jinginar dakansa yayi jikin bishiya idonsa alumshe yana jin dadin shafawar dakate kaman tana Sosa mai wurin ne
juyo dakansa yayi yana kallonta ahankali yace kinajin tsoro ?
Gyada kai cikin rawar murya tace eh amma basosai ba
Kaifa?
Murmushi yayi yana kallon wurin dasuke baice komai ba
maidamasa wuyan rigarsa tayi tana maida masa maballan alokaci guda suna kallon junansu suna jin wani yanayin dasuka kasa fassara shi
Mutsa bakinta tafarayi ahankali tana ji kamar tagayamasa tana sonsa amma kuma tana tsoron mezai biyo baya
Suna cikin haka sukaji wani gurnani gurrrrrr
atsoarace suka kalli juna cikin rawar murya asma'u tace ABI did u hear that ??
Kai ya gyada mata yana waige waige sekara shigema juna suke
gurnanin suka kara ji anyi atsorace asma'u tarungumeshi da karfi tana jero addu'a
Dariya yayi yana rike ciki yace chitti ba komai bane ciki nane fah
Kallonsa tayi da mamaki tace cikin ka fah ABI wannan fa kamar zaki ne ko damisa
janyeta yayi daga jikinsa yana shafa cikinsa yace cikina ne yunwa nakeji yau ba abunda naci tun jiya rabona da abinci
itadai bata yarda ba se bin wurin take da kallo tana karanto duk addu'ar datazo mata tun yana mata dariya har shima yafara tsorata dayanayin wurin yafara tasa addu'ar
Washegari dasafe dai daga cikin yaran JJ yafara tashi yaga ba su AK hankali tashe yatashi sauran yasanar dasu
afusace JJ ya hausu dafada kamar su suka kwancesu bashiri ya rarrabasu acikin dajin suje su nemosu hankali tashe suka bazu nemansu hardashi JJ kuma yayi alkawarin yana ganinsu zai kashesu kowa yahuta
tun safe ahmad yaje police station suka fara shirin fita Neman su
agidama haka sun dage da addu'a tun suna kuka har sun hakura sun barma allah gidajan biyu sunzama tamkar gidan mutuwa Sam ba walwala ba farin ciki acikinsu
lokaci guda khadeeja tarame tafita hayyacinta kowa yaganta seya tausayamata kowane lokaci suna waya da ahmad yana kara kuantar mata da hankali
bangaren sarah ma abun yafara damunta saboda bata San halinda AK yake cikiba dan tasan idan dai JJ yagansa bazai kyaleshi ba
aysha ma haka tana mamkin rashin dawowar AK tunda JJ yacemusu yakashe asma'u gashi kuma sunji shiru suna kiransa basa samunsa
Kuance suke suna bacci hankali kuance AK yadora kafansa kan cikin asma'u ita kuma tayi reran dayan hannunta kan kirjinsa
ahankali tafara bude idanuwanta tana bin wurin da kallo saurin tashi tayi tana ture kafan AK daga jikinta tafara tashinsa
gyara kuanciyarsa yayi cikin muryan bacci yace chitti bring my coffee kafinnan zantashi
Dariya tayi tana daddabashi tace wane kalan coffee kuma ABI kamanta inda muke ne
janye hannunta yayi daga kan kafadarsa idonsa arufe yace jiya nayi wani mafarki mai ban al'ajabi idan kin kawomun coffee dina se inbaki labari
Ganye ta tsinko tadora akan bakinsa tana dariya tace ba coffee sedai dambun nama inzakaci
saurin tashi yayi zaune yana kakkabe bakinsa lokaci guda yana bin wurin da kallo
Runtse idanuwansa yayi yakara budesu yanaso yatabbatar ko dagaske ba marfaki yayi ba
tashi zaune yayi dakyar yayi mika yana salati kamar daga sama sukajiyo
Tafiyar yaran JJ suna nemansu
atsorace suka kalli juna suna mikewa tsaye asma'u ta cakumo rigarsa cikin rawar murya tace
ABI... mun ..shiga uku za.....
Bata karasaba yaja hannunta aguje suka cigaba da gudu suna kara kutsawa cikin dajin seda sukayi nisa sannan suka fara tafiya suna Jan kafa kamar bugaggu ga kishi da yunwa dasuka addabesu karfin hali kawai AK yake amma tuni yafarajin asman shi na kokarin tashi
Tafe suke shi agaba ita abaya sekara kutsawa cikin dajin suke
Karasowa asma'u tayi kusa dashi cikin dasashshiyar muryanta tace ABI I am hungry
baijiyo yakalleta ba yace gani kici
Dariya tayi tace ai koda inacin naman mutane ba'abunda zanyi danaka dan dagani ba dadi zai yiba
Shiga gabanshi tayi tana rike cikinta kamar zatayi kuka tace
ABI dagaske yunwa nakeji kuana biyu fa ba abunda naci ko ruwa bansha ba
Kafadunta Yakama ya juyar da ita sukaci gaba datafiya yana fadin chitti ki kalli nan wurin da kyew kigani banda ciyayi da bishiyoyi ba abunda keda kwai
Idan bamuyi gaggawan barin wurinnan ba mune zamu zama kalacin namun daji
Saurin juyowa tayi tana fadin π§namun daji fa kace kana nufin akwaisu anan
Dariya yayi yawuce gaba yana fadin awannan dajin miye baza'a rasa ba kima kula da inda kike sa kafanki kar ki taka maciji
saurin bin bayansa tayi tana riko hannunsa tace to wai aganinka suwaye wa'yannan kuma meyasa suka kamani
"Ke baki sani ba taya za'ayi ni insani
Shiru tayi batace komai sukaci gaba datafiya batare da sunsan inda suka nufa ba amma kowane da tunanin dayake aransa
Tuni ahmad da yan sandan suka shigo dajin sedai abun takaicin basusan ta ina zasu bi sufara nemansu ba hakanan dai suka rarrabu gida uku sukashiga dajin dafatan ganin su ko ko sukama yan daban
agida kuma tun safe grany da inna ameena suka je gidansu asma'u aka taru acan ana taya juna jaje da addu'ar allah yabayyana su
har yanzu JJ nacigaba da nemansu AK acikin dajin nan saboda yanada tabbacin bai isa sunfita daga dajin ba dan yanada girma sosai za'ajima kafin akai kyawyukan dake kusa dawurin
suna cikin tafiya asma'u tarangada ihu atsorace AK yajiyo yana duddubata yaga ko wani Abu yasameta
Tsalle tafara cike dafarin ciki tana nuna mai bishiyar mangoron datahango
tace ABI kalla kaga mangoro acan wallahi mangoro ne
tsaki yayi yana kallon bishiyar mangoron shi kanshi tabirgeshi bai San lokacinda yasaki wani lallausan murmushi ba suka nufi wurin
dutse yadauka yafara jifan mangoron amma yakasa samun koda guda dayane
labace baki tayi kamar zatayi kuka tana kallonsa tace ABI haka bazai yiba kahau mana katsinko
Baki yasaki yana kallonta yace nahaufa kika ce wannan katuwar bishiyar nasan miye akai haka kawai ke ki hau mana
tureshi tayi daga wurin tana fadin yo se in hau mana ai ba yau nafara ba bishiyar ma dako tsawo batada
Matsawa yayi yabata wuri tafara kokarin nawa se dariya yake yana tafa hannu yana fadin chitti!!!chitti!!!chitti!!!
Tafara hawa kenan tayo kasa zata fadi yayi saurin tareta tafado kansa suka fani kasa tare
Dafe bayansa yayi yana runtse ido hade dasakin yar kara atsorace ta riko gefen fuskarsa tana fadin ABI are u ok kaji ciwo ne ?
Bude idanuwansa yayi yasaukesu cikin nata suna kallon juna nadan lokaci sannan yatureta yana fadin
Dallah malama tashi sama na dama nasan dagangan kikayi
Saurin tashi tayi tana Sosa kai
Dakyar yatashi yana dafe baya yace dama zan samu naman dajin dazai cinye mun ke koba komai kashi hamsin na matsalolina zasu ragu
Nuna mai mangoron tayi tana lashe baki tace please ....
Bata karasaba yatattare kafan wandonsa yahaw bishiyan yafara tsinko mangoron yana jefomata
Ita kwa se dauka take tana Tarawa ga daya ahannunta tana sha
Lekowa yayi daga saman bishiyan yana kallonta yace to kijira insauko mana asha tare haka ake ni da wahala keda jin dadi
seda suka Tara mai yawa sannan ya sauko suka zauna awurin Sunasha suna fira
gutsuran mangoro yayi yadago yana kallonta yace
Chitti acikin namun daji wanne yafi hadari
Dgowa tayi tana kallonsa da mangoro abakinta tace me kadaukeni ne ABI ai kowa yasan zaki yafi hadari
Dariya yayi sannan yakai mangoro bakinsa yana lumshe ido yace
to shi zaki baida wani hadari saboda idan dai zaki iya dake nunfashinki kiyi kamar kinmutu to sedai yayita zagayeki ba abunda zaimiki kinsman bayason mushe yafiso yakashe dakansa sannan yaci
tunda yafara magana take kallonsa baki bude seda yagama sannan tayi dariya tace kaidai kawai sha mangoronka amma wane dauke nunfashi mutum zai iya yi ga zaki na kewayashi
dariya yayi yace to kindai fadi wannan fadi wani
Zari ido tayi tana kallon macijin dake bayansa cikin rawar murya tace ma.....maciji
Dariya yayi yace kaji wai kuma maciji yo miye hadari awurin maciji ai shi kina ganinsa kawai kiyi kokarin taka kansa se kisa hannunki ahankali ki kamo wuyansa kirike gam to kin gama dashi ba'abunda zaimiki
Mikewa tayi tana wurgi da mangoron hannunta atsorace tace ABI ....maciji....abayanka
zunbur yamike yana duba bayansa yana ganin macijin yadaga uban tsalle yabi tagaban asma'u aguje har yatafi yajiyo yaganta atsaye takasa motsawa se yarfa hannu take bashiri yadawo yaja hannunta suka bar wurin
seda sukayi nisa sannan suka tsaya ai kwa nan asma'u tahau kwasan dariya tana tsokanarsa banza yayi da ita yayi gaba yana jinyar kirjinsa dake masa azaba amma ko kadan bayaso asma'u tagane halin dayake ciki
suna cikin tafiya ta taka wata gundumemiyar kaya durkushewa tayi awurin tana sakin yar kara tana kallon kafar
Saurin dawowa AK yayi wurinta yana mata sannu
Hannu yakai zai taba kafar amma taki bari se rike hannayansa take
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 20 Chapter of 35