Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
dashi Maryam na tsugune har shafa takawo yace oya jeki abinki shafa ta tafi tana tauasayawa maryam Dagash ya kalli maryam yace ke tadago manya mayan idonta tazubamishi masu rikitar da mekallonsu Dagash gabanshine yafadi yayi saurin dai daita kanshi yace dauki tsintsinyar nan ki share compound din nan yanzu Maryam tace to batare da sake kallon inda yakeba Tafara sharanta Faisal yace haba dagash yazakayi haka kuma baka ganin yanzu tadawo daga school dan kabarta taje huta Zayyad gaskiya hakan baidace ba itafa batasan ma abinda tayiba ganizatayi mugunta ne kawai Dagash yayi dariyar mugunta yace kungama nawa kukagani banataba Tafi karfin tabada hakuri saboda girman kai tana chick little girl din ta hartasan raini zankoya mata hankali agidan nan Zayyad yagane DAGASH dai sokawai yakeyi tabashi hakuri itakuma yarinyar tanuna batasan wannan ba Faisal yace Maryam yakirata tana sharar tabari tazo yace bashi hakuri kitafi kiyi huta Maryam tayi murmushin takaici tace yaya duk da bansan sunankaba Ban wa yaya al'amin komai ba kawai dai yasani aikin ne saboda ya isa yasa ni dan yana matsayin babban yayana saboda haka zanyi zangama insha Allah Ta wuce su abinta yacigaba da shararta ta Zayyad ya bushe da dariya yace wa Faisal yaufa maza ya hadu da dai dai dashi Magaanrsu ce tadawo dashi daga tunanin dayatafi yace haryanzu ba haifi yarinyar da zata min raini inkyaletaba dani da ita zanga metaurin kai idan na zaneta Zayyad yace a a mutumina kar ayihaka kaganyarinyace karama Karkabari raini yashga tsakaninku da ita kΓ ja girmanka kawai please Maryam tagama dan dama gidan Ba datti kawai muguntace irin nashi Ta isa gurin ta durkusa tace yaya nagama Cikin fusata yace dan ubanki waye yayan naki Ba maryam ba harsu zayyad rasa bakin magana sukayi Maryam tayi shiru zakin yabata mata rai sosai saboda bata son tsawa antynta bata mata Tadaga kai tace haba yaya bakasan allah yatsine wa Wanda yazagi iyayensa ba Karasa abinda zaka sakawa daddy dashi saizagi Danni a yanzu banida wani ubanda dayawuce daddy a rayuwata kagakuwa dan kazageni kaman shikaga tunda ubanmu daya Tana kawowa nan tayi gaba abinta Dagash yatashi dasauri zayyad yayi saurin shangabansa yace haba man be a man mana Kuma fa yarinyar nan gaskiya tafada kai dan'uwantane danme zakazageta Bayan nafada maka karkabari raini yashiga tsakanin Ku Idon al'amin yakada yayi ja saboda bacin rai bai taba irin haka koda daga gurin abokanshiba sai akan yarinya karama yar talakawa Juyawa yayi gurin mota yanufa abinshi yafada yayiwa motar key yafita daga gidan Maryam nashiga part dinsu taga anty a falo tayi kwalliya cikin material doguwar Riga Tayi kyau sosai Maryam tayi murmushi tace anty kinyi kyau sosai Anty tace Yakika dade sosai haka yanzu karfe shida da minti ashirin Kafin maryam tayi magana shafa yashigo cikin falon maryam tayi saurin cewa anty tace Bakomai anty kinsan sabuwar zuwa sai a hankali Shafa tagaida cikin ladabi anty ta ansa mata ya school tace alhmdll anty Tanemi guri tazauna anty tace shafa'atu tashi kije kici abinci gashican a dining Shafa tace to anty batayi musu taje dining din taja tazauna tafara serving kanta abinci maryam kam tuni tashige wanka Tashirya cikin Riga da wondo Pakistan tafito tayi dining taga anty shafa a dining din taje zauna sukaci abin suna dan taba hirarsu Sosai shafa taji dadin abinci sakwarace da miyar egusi da naman rago Anty tayi kasancewar yau itace da daddy tayi mishi. Special food haka **** Al'amin na isa gidanshi yayi parking yafito abinshi cikin zafin rai da kunar zuciya Su aymana suna ganinshi sukatashi sannu da dawowa Ya daga musu hanu ya isa bayason surutu Suhaila tace to , suka nemi guri suka zauna aymana tace yau kuma kowa yataboshi Suhaila tace wayasan mishi Nan kowacce tacigaba da abinda yake gabanta Prince kuwa bayan yafito daga wanka yasa kaya marasa nauyi saboda zuwa sallah magriba Yana fitowa yawuce mosque abinshi **** Daddy kwance kan cinyar anty a bedroom din shi kusan karfe goma nadare Yana lissafa mata abubuwan da yamallakane da kadarorinsa Saida yagama zaiyyana mata komai anty tace allah yakara daukaka ya sa kafihaka alhajina Ameen Ameen maryam Can tace amma Alhaji kagama lissafomin banji kace kanada gidan marayuba kokuma malarantun islamiyya da daisauran aikin lada Daddy yayi shiru yace bantaba wannan tunaninba maryam amma yanzu ya kikeso ayi Tace yauwa alhajina inason acikin filayenka da kake dasu a akowani state mezai hana ka ware kwaya daddaya a Gina maka gidan marayu Sannan kabi anguwan wannin talakawa kagina musu masallatai da su Bohol da fanfuna Nasan dan kayi wannan na komai bane acikin arzikin da Allah yabaka ko yakace alhajina Daddy yatashi daga kwanciyar dayake yace hakane maryam insha Allahu zakiji amfara duk aiyukan nan dakika lissafa nan ba da dewaba Anty tace kai amma naji Sosai daka dauki shawarata alhajina allah yakara budi Dad yace ameen daddy yadade Yana nazarin maganar anty yagane kuskurensa sosai yagodewa Allah dayabashi anty a matsayin mata **** Shafa tana zaune a part din su tana karatun waec su nazeefa kuma kallo saboda suna hutun semester Sai maryam tashigo falonsu nazeefa da sallamarta Afnan tajuyo taga maryamce tace meyakawoki nan kekuma Maryam batareda ta kallesuba kafinma tayi magana shafa'atu tace a a maryam ya akayi maryam tace anty assignments zanyi nazo ki aramin laptop dinki danyi design din page din zansaka water mark ne Shafa tace OK badamuwa bara na dauko miki ta tashi zata dauko mata sai nazeefa ta tareta tace mezakiyi shafa Shafa tace zandauko mata laptop dina ne kobakuji bane Afnan tace baza a bayarba a Ba ubanta tane yasai laptop dinba Shafa ranta yabaci tace yasakuke Abu kaman wasu kananan yarane Afnan tace shafa akan wannan agolar kike mana rashin kunya Shafa tace nayi din kuma nagani data shigo gurina tazo bagurinku ballantana kuce baza a bayar ba nawane bana kuba Shafa batayi aune aune ba taji saukar mari a fuskarta tas Tayi saurin rike gurin takalli me marin ummynsuce Hajiya zabbau tace wawiyar yarinya Mara kishin kai Yanzu saboda wata yar matsiyatar kikewa yayunki rashin kunya wato bazakiji magana ba ko Shafa tajuya ta kalli inda maryam ketsaye taga bata gurin Ran shafa yabaci sosai tawuce dakinta cikin fushi tana jiran daddy ya dawo Maryam kuwa ranta yagama baci tayi alkawarin bazata sake tambayar komaiba saboda gudun fituna *** Washagari Yakama asabar dad yana zaune ya falonsa shafa tazo tazauna tagaisheshi Ya amsa yace shafa'atu ya akayi ne tabashi labarin abinda yafaru dad yace jeki kiraminsu nazeefan Ta tashi taje kiransu DAGASH ne yashi cikin kananun kaya kamar kullum ya gaida dad ya amsa yace son ya akayi ne maganar ayyukan nan amfara ko dagash ya yace ai tunda kabani umarni nasa akafara aikin a kowani state kuma zasu gama lokacin da aka diba musu Amma dad wai meyasa kake wasting dukiyarka hakane kwata kwata bangane makaba dad Dad tayi murmushi irin nasu namanya yace Al'aminu kenan kaima zaka fahimta amma sai nangaba Dagash ya daga kafadu irin alright allah yakaimu lakacin dazaka fahimtar dani din Mum ce tashigo dagash yagaisheta tace son ya duk karame ne meyake damunka ne Yace mom yanzu dai yunwa nakeji break fast please tahado mai komai atirai Yace mom nifa yau kezakibani Dad yayi murmushi yace ai daman kasaba yau yanshagwabar suna kusa kenan Mom murmushi tayi tace yazanyi wai ace mutum yagirma besan yagirma ba Da yaranka zanji koda kai dad dai dariya yake musu Shidai bece komaiba yadauko tiren abinci tazauna gaban mummy tafara feeding dinsa su nazeefa da afnan ne suka shigo Suka zauna gaban daddy Daddy yahada rai Ashe bakuda kunya Ashe haka kuke zakusa kanwarku agaba kuna zagi harda ce mata gidan ubanta bane Ku kinsan yadda naku rayuwar zata kasance nan gaba idan akace yaubani kuma ba dan uwan naku dakuke takama dashi Yanuna Dagash Yace Ashe haka kuke Karin yayi wata maganar Hajiya zabbau ta fito daga part dinta Tace amma alhaji aibahaka ake shariyaba ita munafukar agolar data fada maka karya da gaskiya har kazo kahau yaranka dafada ai ba Gaskiya tafada dan ba haka akayiba Daddy yace to ita wacce kike zargin ba ita tafada Mehankalin yarkice tafada komai yakalli shafa yace jeki kira min maryam Shafa maryam suka fito maryam sanye da katon hijabi harkasa ya balain mata kyau tayi shirin zuwa islamyya ne Ta zauna tagaida daddy ya amsa tagaida mum ta amsa bayabo ba fallasa tagaida uban gayyar wato dagash Sai alokacin yadago ido yakalleta gabanshi ne yasake fadauwa wai meyasa idan yaga chick little girl din nan sai yasamu wannan feelings din ne Ya watsama harara Wanda ita batamasan yanayiba Dad yace maryam kiyi hakuri kinji da abinda yan uwanki suka miki inafatan baki fada wa antynki ba maryam tayi murmushi tace la haba daddy ai ba komai Yakamata anayi nafada wa anty ba daddy bata saniba Hajiya zabbau ta dau salati tace mezangani Wato damuwarka ma kar uwarta tasani [22/06, 6:35 PM] SIS UMMY: Daddy ya kalleta cikin takaici bayason fada mata maganganu a gaban yara ne shiyasa yake kyaleta Yace wa maryam allah yamiki albarka kinji tace amin daddy ya kalli shafa yace shafa'atu allah ya miki albarka yasa kidure da da halinki nagari tace amin daddy Ya kalli dagash da mom take ta bashi break yace Son tunda ba inda zakaje inaso kakai maryam tazabi laptop da waya Kowanne ta dauka abata da resit Yace shafa'atu idan bakya komai kuje tare kema kicanzo wayarki daga nan Shafa tace to daddy mungode Maryam tayi godiya shafa taja hanun maryam suka fita Gudun kar ayi irinta ranar yaya ya tafi yabar maryam gwamma suje gurin motar sujirashi Sai da yagama yangarshi yagama Jan ajinsa kafin yatashi yayi waje cike da takaici abinda yasa daddy yake yawan hadashi a lamarin wannan Mara kunyar yarinyar ba Shafa tabude gaba tashiga maryam tabude gidan baya tashiga abinta Yana zuwa ya kalli maryam ta madubi yace ina zanje dake da wannan labulen haka .maryam duk da tasan da ita yakeyi hakan baisa tadago ido ta kalleshi ba Next page Naji dadin adduarku akaina kuma allah ya karba dan nasamu lafiya nagode da kaunarku agareni allah yabar zumunci Your comments is needed fans More comment more typing *Signed by ummu afan* πŸ’» [26/06, 11:55 AM] SIS UMMY: πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€ 🎑🎑🎑🎑🎑🎑 πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€ 🎑🎑🎑🎑 πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€ 🎑🎑 πŸŽ€ *BISSIMILLAHIR_RAHAMANIR_RAHIM* *Ummu Afan the Gorgeous writer of the year ,Author of 'YAN BIYAU NE &AKWAI LOKACI* 🌟GORGEOUSE WRITERS FORUM🌟 🌟 G.W.F🌟 *Home of gorgeous, intelligent and expert writers we are the best among the rest* I DEDICATE THIS PAGE TO YOU AGAIN SIS FATIMA SUNISI SANATA (TEEMERH MAKEOVER) GASKIYA INA ALFAHARI DAKE OVER SIS ALLAH YABAR ZUMUNCI INAJIN DADIN NICE COMMENT DINKI KEEP IT UP ❀ _🎑AL'AMIN DAGASH FANS GROUP_ 🎑 Ina matukar alfahari da comment dinku gaskiya sosai da sosai Comment harda read more πŸ€”much love to your love and care πŸŽ€ *AL'AMIN DAGASH* *PAGE* 1⃣3⃣ Dagash ganin yana mata Magana tayi shiru yace ke wai badake nake ba ne Shafa'atu taga alamun horn din mota tamaida hankalinta kan motar dake shigowa akuwa bakuwar mota suka gani Wazatagani wadanda sukafito da ga motar ne yasata fatinciki Ta kalli yaya al'amin tace yaya ga friend dina sunzo Yace to mezan miki tayi shiru tunda tasan amsar tafito tazagayo ta gurin maryam tabude tace maryam ga mayafina tunda duguwar rigace ajikin ki Maryam tadago kai tace a a anty meyasa zansa wannan kuma tace au bakiji me yaya yace ba Maryam tace au yayi maganane banjiba Shafa hankalinta yatashi dan karyace marayam tamishi rashin kunya Nan shafa ta maimaita mata mata abinda yace Maryam tace OK banji bane ai Dana koma ciki na dauko wani Shafa tace a a basai kinkomaba ganawa kuje kudawo nayi bakine kizabo min wayar mekyau kawai Maryam tace OK shafa tabata mayafin takarba ta manta kanta ba dankwali sai gashinta da takama shi da riborm gashi har yawuce gadon bayanta Shafa taji mamakin gashi irin na maryam dan bata taba ganin gashinta Tadauka kullum acucine takesawa Shafa tace maryam saikin koma gaba yaya bazai yarda kina baya yana Jan mota ba Maryam tayi murmushi tace to anty zankoma Maryam tafito tabude gidan gaba tashiga takauda kanta tana kallon window nagefenta Dagash kuwa saidaya gama wayarsa Sannan ya tashi motar sukatafi Tafiya yake a hankali yana sauraran wakar Akon Suna gurin dagash yayi parking nan da nan maikata suka fara zuwa kwasar gaisuwa Agurin megidansu amma babu Wanda dagash yadaga ido ya kalla bare ya amsa mishi Takaici Yakama maryam tace yanzu wannan wulakancin dame yayi kama haka harda wadanda suka girmeshi amma yake wulakanta dan Adam haka amma insha Allah anan sai ta nuna mishi bakowa zaiyiwa haka yabishi ba Tana zaune a motar tacigaba da zama taki fitowa shikuma Dagash yake waiwayowa Dagash yashiga ciki anbashi masauki yazauna amma yarinyar bata fitoba wai metake nufine Kojiratake yace tafito aikuwa saidai sukwana anan Maryam takira daya Daga cikin maaikatan tabashi sako yazabo mata latest phone da akeyayai yanzu guda biyu iri daya Sai kuma laptop mekyau shima yace angama ranki Dade kozakishiga kizaba da kanki Maryam tace karkadamu kazabo min kawai Ba afi minti goma ba saigashi yakawo mata su daga kasan manyan bwayoyine shima laptop din kansa abin kallo ne Tayi godiya yatafi wayar yamata kyau sosai iridaya Dana shafa tasa aka kawo musu Dagash yagaji dazama cikin zafin rai yataso yafito yabude kofar motar gefen da Maryam yace kewai dan zaikarasa zagin kome yatuna kuma yafasa zaginta oho Yace ni sa'an wasankine kokuma jirakike nace kifito saboda kin isa kome Maryam tafito tace haba yaya kai meyasa kullum acikin zafin rai da nuna kowa banza ne a idonka Duk girman mutum bai isa ka amsa gaisuwarsaba Ninadauka wa mu yara kakewa Ashe harda wadanda suka girmeka Gaskiya naji kunya sosai shiya naji bazan iya jerawa dakai ace tare muke ba a yi tunanin halinmu daya Tashin hankali ran maza yabaci wai yau shine mace zatace tana jinkunyar jerawa dashi macen ma karamar yarinya Cikin tsanin bacin rai yafigeta har mayafinta yafadi saboda santsin gashinta ga yawa amma baibita kan mayafinba Maryam cikin tashin hankali kanta ba dan kwali gashi duguwar rigar dake jikinta yabude daga wuya sosai har ana iya hango lafiyayyun dukiyar fulaninta dasuka hade da juna Yashigo maryam tace dan allah yaya kayi hakuri dan allah wallahi bazansakeba Dagash yajuyo yaga abinda yasa takebashi hakuri haka da wuri Maryam hartafara kuka ita damuwarta ma jikinta ne taya zatakoma gida a haka mezatace wa anty idan taganta a haka Dagash besan sanda yataka burki akan titiba Saboda ganin surar dabe taba ganiba Cikin tashin hankali ya dafe Kanshi Yafara maganar zuci yace wai mehakan yake nufi Karamar yarinyar kaman wannan ta mallaki abinda manyan mata baigansu atare dasuba Kukanta ne yadawo dashi daga duniyar tunin da yafada ga shi hada wani uban go slow a hanya Sai ya ankara ya ja motar sukayi baitsaya koina ba sai wani boutique dinsa yashiga da kanshi yadauko mayafi babba mekyau sosai shibai tsaya duba colour ba yadauko Yashiga motar ta saka kanta acikin cinyo tana kuka Cikin tsawa yace enough malama wannan kukan naki yacika min kunne Tadago daniyar tasake bashi hakuri saitaga yana miko mata mayafi cikin farinciki ta karba Yayi tsaki yace ashe rashin kunyar nakarya itadai bata kulashiba tunda tarufe jikinta ai shikenan abinda yabashi mamaki duk kukan datayi baisa idonta yacanza launi ba Har yanzu sunan kaman madara dan haske Suna isa gida tafito a motar takwashe kayanta tabar mishi motar abude Yace ke zonan kotasan allah yayi mutum Cikin mamaki dagash OK munzo gidako zakishigo hanuna Itakuwa maryam tayi alkwarin bazata sake shiga motar Dagash ba *** Bayan wata uku soyayya tsakanin alhaji dan asabe da maman rahama abin ba ace komai har antsaida ranar aure nan sati daya za adaura auren Mum din zayyad bakaramin hauka tayiba amma wannan karon alhaji dan asabe yayi nisa baya jin kira Sosai ake shirye shirye biki Maryam da rahma sunji dadi sosai kasanewarsu gari daya Anyi bikin maman rahama da dad din zayyad ta tare agidanta Sai dai muce allah yabada zaman lafiya *** Shekaru sunja dan shafa'atu tana nan a university level two Yayinda maryam kuwa da rahma suna SS3 karatu yafara zafi sosai Dagash kuwa abun tunbaya damunshi yanzu yafara damunshi yanzu Wai meye dalilin daya yana yawan tunanin wannan maraya kunyar yarinyar ne Yarasa meke damunsa Aymana da suhaila kuwa haryanzu ba cikin kobatan wata bawacce ta tabayi Kuma dukansu zugan kawayene acewarsu haihuwa da wuri zaisa mijin ya tsanesu Gashi kowacce ya bude mata tafkeken boutique yanzu sunzama manyan mata Business kawai suka agaba ba abinda yadamesu Komai suke so suna samu ***** Daddy zaune suna cin abinci da anty sai anty ta tashi dasauri tayi bathroom aikuwa daddy yabi bayanta yaga amai take dakanshi ya taimaka mata tashirya yace suje asibiti Suna zuwa kuwa gwajin farko akamishi albishir da cikin anty Daddy yaji dadi sosai saikace ba ataba mishi haiuwa ba Bayan sundowa gida yace Yakama ta muje umara gabakidayan mu mutanen gidan Dan nagodewa allah akan ni'imar daya karamin Anty tayi murmushi batace komai ba Duk ilahirin mutanen gidan kaf daddy yasa akamusu visa Mum din al'amin itadai abin mamaki yakebata canjawar mijinta lokaci daya haka Maryam tace anty yanzu ni yazakuyi dani kenan saurafa sati daya mufara exam's Anty tace ai daddynki yagama komai maryam gidan yayanku zaki koma har saboda jarabawar Ku Maryam ta zumbura baki tace kai anty kinsan allah matan shi basu da kirki Kawai kubarni naje gidansu rahma Anty tayi murmushi yace maryam kenan ai nan alhaji yazaba miki kinga bazaki ce mishi bazakijeba ko Maryam tace anty kuma zaku dade a can ko Anty tace a a tunda naji yace fa zamukai two months a can Maryam ta gwalo ido tace Kai yanzu wata biyu zanyi banganki ba Anty tayi murmushi tace karkidamu kinga ke exam zakuyi idan kuma bakyason zama kedai a gurin yayan naku zan fasa tafiyar sai muzauna Maryam tayi murmushi tace a a anty na karki damu allah yadawo daku lafiya Kuma kimin addua allah yacika min burina nazama BARRISTER MARYAM insha Allah anty tayi murmushi tace maryam ai kullum cikin addua nake miki insha Allah zaki barrister Maryam ta rungume anty tana me alfahari da ita Next page Your comments is needed fans More comments more typing *Signed by ummu afan*πŸ’» [26/06, 11:55 AM] SIS UMMY: πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€ 🎑🎑🎑🎑🎑🎑 πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€ 🎑🎑🎑🎑 πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€ 🎑🎑 πŸŽ€ *BISSIMILLAHIR_RAHAMANIR_RAHIM* *Ummu Afan the Gorgeous writer of the year ,Author of 'YAN BIYAU NE &AKWAI LOKACI* 🌟GORGEOUS WRITERS FORUM🌟 🌟 G.W.F🌟 *Home of gorgeous, intelligent and expert writers we are the best among the rest* I DEDICATE THIS PAGE TO YOU SIS FATIMA ZAHRA ❀GASKIYA INA ALFAHARI DAKE OVER SIS ALLAH YABAR ZUMUNCI INAJIN DADIN NICE COMMENT DINKI🧑 KEEP IT UP ❀ _🎑AL'AMIN DAGASH FANS GROUP_ 🎑 Jinjina gareki sis ummy allah yasaka da alkairi kina kokari wajen ganin komai yatafi dai dai allah yabar zumunci sosai❀❀❀ πŸŽ€ *AL'AMIN DAGASH* *PAGE* 1⃣4⃣TO1⃣6⃣ Yaune girgin su daddy zai daga karfe goma nadare zasu tashi Shiyasa tunsafe suke ta shirye shirye Dagash yana dakin mom dinsa yace yanzu mummy shikenan haka zanyi ta rayuwa da snack da juice ba cin abinci Mummy tayi murmushi tace to kozaka shirya mutafi ainima basan barinka nakeba Kawai dan dai kaizaka cigaba da kula da business dinku ne tunda daddynka yadauki hutun almost two months zamuyi a saudiya Kuma ina ganin ni daga can ma zanyi gida naga nawa yan uwan Al'amin yace gaskiya zanzo nima nan da sati biyu Da banzan iya zaman wahala ba mom Mummy tace shikenan ma saikazo din yanzu dai ga danbun kaji da danbun nama duk namaka Sai kuma snacks Dagash yace that's my mom allah yakara miki lafiya mum Mum tayi murmushi tace amin Son Mummy tazauna jikin gadonta fuskarta yacanja Tarike hanun al'amin tana son yin magana Al'amin yace lafiya kuwa mom meyasa fuskarki yacanja Mom taja nunfashi tace Kaine son wallahi nayi tunanin auren dakayi zaisa kacanja kadaina shan giya kadaina Neman mata amma bako daya son Al'amin yace oh my God mom kicigaba da min addua mummy zan daina kodanke ma tunda bakyaso amma fa mummy wannan yarinyar nan dakikasani itace dai Vicky bana naman mata barkate mom Mummy ranta yabaci tace yanzu son har ka dubeni kace wai har yanzu wannan wacce nasanine baka canja wataba Anfada maka Abu mai kyau kakeyi ne Wannan halin naka yana daga cikin abinda yasa nakeson tafiyan nan saboda nayi ma addua a kaba dakin allah nayi addua sosai allah yashirya min kai Al'amin yace mummy insha Allah adduarki takusa karbuwa Zandaina mom amma kinsan sai a hankali Mummy tace to allah yasa kadaina din Gashi mahaifinka yadauki son duniya ya daura maka baya iya ganin kayi badai dai ba yama magana al'amin yayi murmushi yace ai ina alfahari daku a matsayin iyaye mom allah yadawo mundaku lafiya Mum tace amin amin son ** Maryam tagama shirya wa anty kayanta tsaf Itama tashirya nata akwati biyu tadeba Anty tace yauwa maryam kingama to zonan Maryam taje kusa da anty tazauna Anty tace kinga dai gidan dazakije maryam duk ba sa'anki dan allah kimusu biyayya karki rainasu idan sunsaki Abu kiyi kinji ko Sannann kuma kikama kanki dan yayanki ne amma fa ba muharraminki bane Kinajina ko maryam tace inaji anty na anty tace allah yamiki albarka maryam tace amin amin antyna *** Su shafa'atu kuwa suma sunata shirye shiryen su kowacce tagama shirya kayanta Hajiya zabbau baki harkunne Za'ayi tafiya gabakidaya family ba barmata 'ya'ya kogudayaba Inba asiya ba itakuwa asiya suna India da mijinta ma Sun gama hada komai suka fiffito falo Dagash yafito da kayan mummynsa daga part dinta Karfe Tara nadare kowa yashiga mota zuwa air port Al'amin shiyake jan mummynshi da daddy Anty kuma suna motar driver itada shafa da Maryam Hajiya zabbau ma su uku da ita da nazeefa da afnan Jirgin su yatashi karfe goma dai dai maryam batasan zatayi kuka ba saida taga da gaske ne fa anty ta tafi Al'amin takaicin kukan yakamashi yace ke wai wace irin dabbar yarinyace Ke yarinyar goyece dan anyi tafiya zakikama yiwa mutane kuka Maryam kuwa ba abinda tafara tunawa sai labarin da shafa'atu tabata akan yayan nasu idan mummy zatayi tafiya Aikuwa batasan lokacin datafashe da dariyaba sosai Takaici Yakama al'amin ya danko ta yace ke ubanme mekikewa dariya Maryam taji matsa tace badakai nakeyiba Natuna da wani kato ne kaman kai idan maman shi zatayi tafiya Yashiga damuwa kenan wani lokacinma harkuka yakeyi Dagash abin yabashi dariya dan yasan dashi takeyi Take raina mai hankali Baibari taga dariyar ba saboda bayason raini Yace oya shiga mota mutafi Batayi musu ba tashiga Dagash yadau hanyar gidan shi Suna isa tabude tafito yana gaba tana binshi abaya suka shiga falon Aymana kwance kan 3sitter ansha kwalliya cikin matsatstsun Riga da wando dan burge megida Haka ma suhaila cikin duguwar rigane itama ya matseta sosai Ganin dagash da Maryam suka hada rai dan ita aymana ma tun farkon ganinta da Maryam bata mata ba bata sake mata saboda kishin kyau da allah yamata Suhaila tace sannu da zuwa bai amsaba ya wuce abinshi aymana tagaisheshi bai amsa ba Maryam tasamu daya daga cikin kujerun falon tazauna abinta tace sannunku anty Aymana tace kekuma suwaye anty naki Suhaila tace tambayeta dai Suhaila tace towaima meyakawoki gidan nan ba dai dagaske bane anan zaki zauna ko Maryam batace komai murmushi kawai ta tashi suka ga tayi part din dagash Aykuwa Aymana tace kutuman uba wabaki daman shiga wajen mijinmun Maryam tadafa goshi tace ya ilahi wallahi bana son magana kubarni mana please Jin haya niyar aymana dagash yafito yaga sunsa maryam a tsakiya Ya hade rai yace kukuma lafiya Cikin muryarta medadi tace yaya bacci nakeji kuma kayana yana bayan motarka kuma bansan inda zan kwanta Baka nunamin dakina ba takarasa maganar cikin shagwaba Batare da yayi maganaba ya komaciki yadauko key din motar yace gashi maza kije

Chapter 9 of 18