Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
yace taya akayi kikasan inada feye da daya Anty maryam tayi murmushi tace ai bakayi kamada memata dayaba alhaji Sosai taba daddy dariya yace OK hakane to bakice agaida 'ya'yankiba anty tayi murmushi tace afuwan to suma aigaishemin dasu Daddy yace sufa gudawane yakamata ace inadasu yaran Tambayar taba anty dariya tace shahudu zu wa shabiyar Daddy yayi dariya sosai yace hakane gaskiya kikafada amma fa kezakibani goman ko taran Dan dai yarana biyar ne a yanzu daya namiji hudu mata Babban Dana ma yayi aure matansa biyu anty da boye fuskar ta tadago tace Ashe babbane Daddy yace a yagirmeki anty tayi murmushi tace kai amma gaskiya kana da jiki mekyau alhaji kaman baka ajiye me wannan shekarunba Daddy yace ko tonagode gashikuma zan auri yarinya kinga nadawo yaro kenan ko yayi maganar yana kallon fuskar ta aikuwa anty kau da kai taki kallon daddy tana murmushi da tunanin kirki irin na daddy kaman name kudiba Daddy yakatse mata tunani tahanyar ajiye mata kwalin waya sabuwa dal metsadar gaske yace kisamu kiyi charging zankiraki da zaran na sauka Anty tayi murmushi tace nagode sosai Allah yakaika gida lafiya Daddy yace amin amin amaryata anty tayi murmushi batace komiba sukayi sallama Daddy na isa kano DAGASH. Yazo air Port ya dauko dad dinsa Next page Your comment is needed fans More comments more typing *Signed by ummu afan*πŸ’» [26/06, 11:54 AM] SIS UMMY: [19/06, 10:32 AM] SIS UMMY: πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€ 🎑🎑🎑🎑🎑🎑 πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€ 🎑🎑🎑🎑 πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€ 🎑🎑 πŸŽ€ *BISSIMILLAHIR_RAHAMANIR_RAHIM* *Ummu Afan the Gorgeous writer of the year ,Author of 'YAN BIYAU NE &AKWAI LOKACI* 🌟GORGEOUSE WRITERS FORUM🌟 🌟 G.W.F🌟 *Home of gorgeous, intelligent and expert writers we are the best among the rest* I DEDICATE THIS PAGE TO YOU SIS MOM ISQAH GASKIYA INA ALFAHARI DAKE OVER SIS ALLAH YABAR ZUMUNCI INAJIN DADIN NICE COMMENT DINKI KEEP UP ❀ _🎑AL'AMIN DAGASH FANS GROUP_ 🎑 Ina matukar alfahari da comment dinku gaskiya sosai da sosai Comment harda read more πŸ€”much love to your love and care πŸŽ€ *AL'AMIN DAGASH* *PAGE* 1⃣0⃣ Anakiran isha dagash na parking a cikin gidan da sauri security suka bude wa daddy kofa suka budewa dagash ma Suka wa alhaji sannu da dawowa ya amsa ba yabo ba fallasa mutuminki kam hada rai yayi idan da sabo sunsaba da rashin sakin fuskar da dagash yake musu Kaitseye cikin gidan suka nufa mom din al'amin ansha gayun tarbar daddy ko ina masu aiki su gyara tsaf sai kamshi yake Ta tashi barka da zuwa daddynmu Al'amin yayi murnushi yace hardake a a mum kinemi daddynki Dad yayi murmushi yace rabuda ita son ai bana baban da ita Mom tayi murmushi tace tace wato dai ka bada min kasa a ido kenan ko Kasancewar ba adakinta daddy zai kaba shiyasa daga gaisuwa sai tanemi guri ta zauna abinta daddy zama yayi Yasan da itace da yanzu tayi da shi part dinshi yayi wanka tukun yaci abinci Su afnan ne naxeefa suka shigo yiwa daddy sannu da zuwa Sai ummy tashigo falon tace sannu da dawowa daddyn afnan Dan haka take kiranshi bazatace daddyn al'amin ba saboda kishi Yace yauwa nasameku lafiya tace lafiya kalau ga abinci a dining yace no sai nayi wanka zanci tace OK ta cigaba da kallonso Dady ya kalli nazeefa yace nazeefa jeki bathroom dina kihada min ruwan wanka tace to daddy Al'amin yace daddy saida safe mom saida safe mom tace kadauki abincin naka kadawo min da kulata Al'amin yace gwamma da kika tunamin wallahi Dan danaje ma.zan dawo Wani hadaddan food flask ya dauka yayi waje daddy yace ina Allah yakaimu goben kazo ina da meeting daku Al'amin yace OK dad nice dream ya kashe wa dad ido daya Daddy yayi murmushi yace nazama kakanka ai Mom tayi murmushi tace ai son sai a hankali Daddy na fitowa daga wanka bayan ya goge jikinsa yasaka jallabiya ya dauki wayarsa ya kira anty Sai yayi ringing ba adauka Can yakusa katsewa tayi sallama cikin zazzakar muryarta Daddy yanemi guri yazauna Dan abin saida zama Yace kobakya kusada wayarne tace a a wayar na hanun maryam ne bata daga bane saida takawo min Alhaji yace oh nayi mistake fa naman yartawa ma ta isa rike waya zan kawo mata tata Anty tace a a alhaji na sai tagama secondary sai abata waya daddy yace good idea Daddy zuciyarsa yasake masa fes yace da sake fadin sunan da kikakirani da shi ma Anty tayi murmushi tace alhajina Yace kai maryam komai naki special ne tace godiya nake alhajina Ka isa da lafiya dafatan kasamu kowa lafiya Yace kowa lafiya amaryar alhaji Murmushi anty tayi ina fatan dai kaci abinci kahuta yace yanzu nake shirin cin abinci Tace a to barin barka kaci abinci ka huta kafin daddy yayi magana anty takashe wayar murmushi yayi yana bin wayar da kallo Dai dai lokacin hajiya zabbau tashigo taga yakura wa waya ido yana murmushi ta kebe baki tace to sabon salo kaikuma da waye haka daddy yayi murmushi yace nida kanwarki ce Hajiya zabbau tayi murmushi tace alhaji kennan akwai da son wasa Muje kaci abinci sukafito falin atare a lokacin mom tayi part dinta ta kwanta Bayan daddy yagama cin abinci hajiya zabbau tawuce bedroom din daddy Dan yau itace a dakin Daddy kuma dakin mummyn Al'amin yayi yaga harta kwanta abinta dakin da duhu saboda bata son kwanciya da wuta ita kona bacci bata so ya kunna wutar dakin yashiga Ganin bacci take sosai yasa bakinshi dai dai goshinta yabata kiss kafin yaja mata bargon yafito abinshi Daddy kasa bacci yayi tunanin anty Shidai yasan bawai kyaune ya rudeshiba saboda yasabaganin kyau agidanshi Dan mom din al'amin akwai kyau kaman itatayi kanta Kasa tantancewa yayi tsakaninta da anty wacce tafi kyau Dan abinda hango kawai anty tafi mom da yarinta amma kowacce tana jida nata kyan Hajiya zabbau sai sharar bacci take miji yana ta fama da soyayyya DAGASH na isa gidanshi yasamu matanshi a falon kowacce an kure adaka ana jiran miji Suhaila ce da kwanan turaka Dagash nashigowa suka mishi sannu da zuwa yasanma Allah yayi ruwan tsiron su Dan har sunsaba da kalan wulakancisa sosai ga shakkarsa da sukeji da tsoronsa da akwaishi da gida baya son raini kokadan Yanayin yadda ya wucesu da flask a hanunshi yasa duk suka ga kaman yafi na kullum Aymana tayi murmushi tace wa suhaila kitashi kije mijinki yadawo Suhaila ta kalleta a yatsune tace ba yanzuba sai anjima Aymana dariya yakwace mata batasan lokacinba Suhaila tace dadin abinma bani kadai yakewa hakan ba kema ba sha kikayiba Ta tashi tayi part din Al'amin taji shi a kulle tadawo tazauna itafa gaskiya wulakancin mutumin nan yayi yawa wallahi Suna zaune sukaji anyi nocking suhaila tace yes waye ne muryar mace sukaji tace is Vicky Suhaila ta tashi tabude kofar sukaga Vicky tasha matsatstsun kaya Riga da wando ga uban gashin dokin nan ya tsaya caak akan wato Afro tayi Suhaila tace mezangani kekuma daga ina Vicky tace sorry ma nazo sir ne Jin abinda tafada aymana tataso taganta kutuman uba ubanwa baki daman kishigo mana gida harma kizo Neman mijin Dan ubanki Vicky tsoro yakamata Dan Aymana saida tshinke ta da mari Marin ne yajawo hankalin DAGASH dake falonshi na kasa yafito yace kai lafiya kukemin iskanci agida Ganin Vicky rike da kumatunta durkushe akasa alamu dai sun mareta aikuwa yace wacece ta mareki acikinsu ta nuna Aymana yadaga hanu ya tsinke Aymana da mari Yace next time kusake ciwa bakona mutunci kuga abinda zanmuku da kikai kawai Yajuya kan Vicky itama bata tsiraba yace kekuma Dan ubanki wayabaki izinin zuwa gida Jikin Vicky na bari tace am sorry sir na Dade da dawowa daga tafiyan ne shine bangankaba naje office nakane akace min kana gida akamin kwatancen gidan nazo Yace stupid girl tashi kibiyoni aikuwa jikina bari tabi bayansa suhaila cikin takaici ta sha gaban Vicky tace gaskiya muna ji muna gani baza kashiga mana da karuwa cikin gida ba Wannan ma ai zaluncine Karfin halin suhaila yabawa DAGASH mamaki aikuwa ya nufota tagudu bayan Aymana dake sharbar kukan takaici Vicky dai tasamu tashige Ya matso da daf dasu yace mekuke nufi ne kuna nufin kun isakusa na canja rayuwatane daga yadda nakeyi To Baku isaba bakuda wannan damar da mutuncin Kuma zanfada magana kunga wannan maganar kurike azuciyarku idan wata acikin kutayi dogon bakin kai karata ta to zauna a inda takai karata din nasaketa Duk suka kalli juna yanzu akan karuwa har zai iya rabuwa dasu Yace nadai mafada muku duk wacce takai karana to tayi zamanta kawai acan dan ta saku sannan kuma bazan taba dawo daitaba Yana gama fadin haka yayi part dinsa abinsa ya kullo kofar Ya ga Vicky a tsaye ya watsa mata harara Ya haura saman yaga tana biyoshi yace heeeeeee stop there kaman banza kazaman wofi kekin isa kishigo min daki oya ga guri can kije kizauna wawiya kawai Jikinta yayi sanyi sosai kai wannan mutum akwai masifa Ta zauna adaya daga cikin kujerun falon Anan ta kwana shikuma yakwana a sama Amma suhaila yadda sukaga rana haka sukaga dare saboda tsananin kishin mijinsu da karuwa a daki Washagari bayan al'amin ya yaje masallaci yayi sallah yadawo yashiga wanka yafito tsaf da shi kaman shiga yayi wasu kananun kaya masu masifar kyau sunkarbi jikinsa sosai Yafito yaga Vichy karfe Tara amma bata tashiba yasa hanu yadaka mata duka aikuwa a firgice ta tashi tace Jesus Yace agidan ubanki kike dazaki kiramin Jesus anan tace am sorry sir yace tashi muje nakaiki gidanki tace sir banyi brush ba yace a inazakiyi brush din a bazaki min anfani da toilet kodaya agidan nan ba muje nakaiki gidanki kawai tace OK thanks sir Ya wuce tabiyoshi yau bakowa a falon kowacce tana bangarenta tana jinyar zuciyarta Amma har fitansu duk suna kallon ta window dinsu Duk a tunaninsu dagash ya kwana da Vicky ne DAGASH yayi sallama a falonsu yaga daddynshi yana break fast Al'amin yagaisheda da dad ya amsa kafinn nan yagaida hajiya zabbau da kyar ta amsa gaisuwa tashi yariga yasaba bata damunshi kokadan Mom ta fito itama cikin Shiga ta alfarma tayi kyau sosai doguwar rigar shaddace tasha aiki a jikinta sai kamshi take fitarewa Kallon da daddy kemata yasa hajiya zabbau tayi kicin kicin da ranta Kishin ya tashi sosai Mom ta tace a a Son sammako akamana ne yace yes mom ba muna da meeting da daddy ba Mom tace yes exactly kayi break ko Al'amin yabata rai yace a ina zanyi tace a gidan ka mana baka da matane Al'amin yace haba Mom kibani break please am hungry Ta koma part dinta tahado mishi komai da komai yaci ya koshi Daddy yace to mukoma falo sai muyi maganar [19/06, 5:54 PM] SIS UMMY: Duk sunzauna mom Al'amin hajiya zabbau Daddy zaifara magana hajiya zabbau tace alhaji naji kaman kace meeting ne Kuma banji kace a korasu nazeefa da afnan ba Daddy yayi murmushi yace kirasu suma tunda hakan kikeso Aikuwa ta dau waya takirasu Kowacce tanemi guri ta zauna Daddy yafara magana yace nasan duk zakuyi mamakin abinda yasa natara mu anan ko Sukace kwarai kuwa yace to za adaura min aure nan sati biyu Baigama fada ba hajiya zabbau ta tashi tace aurefa kace alhaji ai daman cemin dakayi kanawaya jiya da gaske ne To wallahi ba agidan nan ba bazai taba yuwaba kokadan haba alhaji mekakenema aduniya kuma haka bayan rufin asirin da Allah yamaka To agaskiya bazaka kawo mana wata yar iska cikin gidan nan ba Dariyar DAGASH ita taba kowa mamaki suka kalleshi Dad yace kaikuma fa DAGASH yace wallahi dad Bakomai kawai dai abin ne yaban dariya wai aure dad haba dad Dad yace oh lefine kenan ko DAGASH yace no dad Bakomai kuma nima ina bayanka wallahi tunda ai dama saura biyu aciki gidan Dan nima fa dad mata hudu ras sainacika su Kaga like father like son kennan ko dad Kafin ya rufe baki mom dinsa tace rufe minbaki kaida nake tunanin zaka sabaki yabari Wani aure ne beyishi tun tuniba sai yanzu tsofai tsofai damu yace zaikawo mana kishiya haba alhaji gaskiya kasake tunani DAGASH yace haba mummy ai ba haramun bane kuma ma ai cewa yayi yadaina sonkuba haba mum kallon da ta watsa mishi yasa hanu ya kama bakinsa alamu wai yayi shiru Allah yabata hakuri Hajiya zabbau tace karma kasake amma wallahi dai ba agidan nan Daddy yace kingama yace ai ba zan taba gamawa indai akan kishiyace alhaji Yace to madalla Ya kalli mom.yace lokacin da zan auri zabbau wani irin tashin hankali ne bakishiga ba Mom tace gaskiya kam naji badadi amma ai yanzu dai alhaji muntsufa ai haba Dan Allah Ya ce muntsufa kikace tace sosai ma yace OK tsoho baya aure kenanko .to ni za afara daga kaina Kekuma zabbau barinfada miki duk abinki inzaki kwantar da hankalinki ki kwantar aure sainayi shi gida gidane ikonane So ba bu Wanda ya isa ya taka min burki beside ma ba a Karin auren zan aureki Keba wata kikashigo kikasamu ba kuma tayi hakuri kukazauna To yazama dole kema kizauna da wata kuma lafiya Wannan dalilin yasa bankira su nazeefa na saboda nasan abinda zaije yadawo zakiyi abin kunya agaban yaranki ne kawai Hajiya zabbau tafashe da kuka tsakanin ta ada allaha tace daman nasan tun ba yauba baka kaunata baka kaunar yarana agidan nan Bakomai amma kasani wallahi yau bazan kawana agidan nan ba gidan mu zantafi Daddy yace ina maitabab atar miki kikasa kafa kikbar gidan nan kozakiyi shekara ne bazanyi bikonki ba infact ma babu Wanda ya isa yasa nadawo dake zabbau Jikinta yayi sanyi tayi hanyar dakinta afnan tabita Nazeefa kuma tazauna anan Mommy tace Allah ya rufa asiri A ina kasamu matar yace a mararrabar abuja Tana da yarinya daya kuma dukansu zan rike Ya kalli DAGASH yace ina son kawa company masu furniture's din Anna suzo sugyara dayyan part din can ya nuna bangaren da bakowa daman tsarin gidan mata hudu ne Ya kalli mummy yace dake da hajiya zabbau kowacce ta rubuto abinda takeso na fadar kishiya Akwai abinda banfada muku ba yarinyar basu da komai infact talakawa ne sosai aikuwa Daddy baiga tashin hankali ba saida yace yar talakawace DAGASH yace why dad duk matan dasuke duniya masu da jidakansu karasa wacce zaka kawo susamana tsiya da talauci sai fakirai Mom tace alhaji nida ban hada kayi aureba amma ban amince ka kawo mana talaka cikingidan ba Muna zamanmu lafiya kakawomana balai Dan shi talaka ba abinda yasani sai kyashi da bakinciki DAGASH yace nima gaskiya dad anan kam ina bayan mommy Dan Allah kanemi wata banda talaka please I hate them dad Daddy yace kagama ubana dagash yace yes yace to bazan canba kuma ina son acikin satin agama zubu komai a part dincen Kaji na fada maka dad yatashi yabasu waje mom ta kalli dagash tace. Son munshiga uku bantaba ganin dad dinka yaki jin maganarkaba sai yau Kafin dagash yayi magana hajiya zabbau tace ai bazai taba jinsaba kuwa tunda yace talaka ze aura Mom tace bangane abinda kike fada ba hajiya zabbau tace aisu talakawa ba abinda da sukasani sai asiri sumaka asiri su mallakeka surabaka da mijinka da yaranka Dagash yace kai nifa ban yarda akawai wani asiriba sai anjima zan dawo amma niba ruwana da wani maganar asiri duk karyace .hajiya zabbau tace ai daman nasani bani da mutunci a idonka da zanfadi magana ka gaskata Al'amin yayi waje abinshi hajiya zabbau dabasu taba zama da mom suna hiraba saigashi yau hajiya zabbau tazage tana bawa mom illar talakawa da kuma hatsarin dake tattare dasu *** Mom tagama tsorota da lamarin ga alhaji yadage sosai ake suba gyaran gida kaman baza a mutuba Hajiya zabbau kuwa kawayenta sunbata shawarar ta zauna ta gallazawa a amaryar hartagaji ta gudu Mom kuwa tayi alkawarin bazata ta taba shiga harkar amaryar alhajiba kuma bazata Bari tashigo nata ba kowa yazauna a matsayinsa Alhaji Dan asabe zaune suna magana da dad yace gaskiya abokina kai din namijine Dad yace har yaushe zanzauna nida gidana ana juyani Wanda nake shakka dama al'amin ne kuma da nuna mishi bazan hakuraba yace shikenan Allah yasanya albarka Yanzu maganar da nake fada maka shiyasa akayi komai na part din amayar akazuba komai Alhaji Dan asabe yace to Allah yasa mu adanshinku Dan wallahi ina son nashigo sahunku Duk da dai kai yanzu na uku zaka kara Niko dayar ma nasamu nakara Daddyn Al'amin yace saikacire tsoron hajiya a ranka Alhaji Dan asabe yace insha Allah zanyi kokarin ganin na gyara gidana sosai Kafin nayi tunanin Karin aure .dadadyn al'amin yace abinda yakamata kenan Dan a yanzu ka kai wata gidan zata sha wahala sosai Dan zakaga ana mata wani abun kayi magana ba bazaka iyaba Alhaji Dan asabe yayi shiru yana tunanin maganar abokinshi yasan gaskiyace Rana bata karya gobe daurin auren anty da daddy Anty tana zaune itada kawarta zainaba maman rahma tace kai amma gaskiya antyn maryam kigodewa wa Allah kiga fa kayan da musiyo amma duk da hakan alhajin naki wai baimishiba Zaikara miki wasu anty tayi murmushi tace zainaba ni wallahi har rasa bakin magana nakeyi ma alamarin alhajin yana bani tsoro wallahi kaman besan ciwon kudine ba Zainaba tace maryam kennan ai a kudi irin na bawan Allah nan Dan ya miki wannan bakomaibane Nan tafara lissafata iya abinda taji anacewa ya mallaka Anty tace ai ba wannan ne damuwata ba ya mutanen gidanshi zasu karbeni Wannan shine matsala ta kinsan fa bana son tashin hankali saboda ban iyaba Zainaba tace a ina zaku hadu ballantana su tanka miki ai banbancin mekudi da talaka kenan agida daya ake amma saiki shekara bakiga kishiyarki kowa tana nata bangaren Anty tace nidai kitayani addua Dan Allah maman rahma tace insha Allah kullum acikin adduarki nake karkidamu Allah yakareki daga sharrin makiya Kiga fa Dalilin ki yadda akagyra gidan nan acikin sati biyu ai ba abinda zamuce dake sai addua kedin alkairice ataredamu Gidan ma yanzu yazama mallakarmu Allah dai yabiya mungode Anty tace haba maman rahama ai mun zama daya godiyar ta isa haka Suna cikin maganasu maryam da rahma sukashigo Maryam ta raka rahama kitso itakuma maryam kanta baya kitsuwa ma saboda yawansa dama kuma ba gwanar kitso bace Maryam ta gaida maman rahama kafinta gaida antynta tafada jikinta tana washa antyna nagaji Rahama tace Dan Allah daga ta karki karya mana uwa Maryam tayi murmushi tace ai wallahi idan zan zauna banzauna jikiin anty ba bana jin dadi sai naji kaman faduwa zanyi Rahama tace ai wallahi baki isaba katuwa dake kikaryata tajanyo maryam daga jikin anty Anty tayi murmushi tΓ ce nagode miki rahama dabiki jata ba haka zata gajiyar dani nima ita ma takwaso gajiya tarabama na Maman rahma abin yaburgeta matuka Dan idan anty da Maryam suna wasa bazaka taba dauka uwa da 'ya bane zaka dauka irin ya da kanwartace Maryam tace anty kiban aron wayarki Dan Allah Anty tace dauka kufita magana mukeyi ko ta dauki wayar suka koma dakin su rahma suka zauna Rahama tayi shiru tana kallon maryam Maryam tace ya akayi ne rahama irin wannan kallo haka Rahama tace wallahi maryam idan natuna wai gobe zaku bar gidan nan bana jin dadi wallahi nasaba dake sosai Maryam tace haba rahama ai zanbaki number din anty nima kiban na mamanki zandinga kiranki muna gaisawa Rahama tace duk da haka bakaman yadda muke tareba Maryam tace hakane nima fa rahma nadamu da rashinki da zanyi saboda zamana dake nagane ke me amanace kina da kirki sosai Rahama tayi murmushi tace ai duk zama dake nakoya maryam kinga kuwa dole nayi rashin kawa tagari ko Sukayi murmushi gaba dayansu rahama tace wayasani ko sai bikin ki zansake ganin ki Maganar ma taba maryam dariya tace aure kuma ni maryam Bana fatanta yanzu sai nacika burina aduniya da yardar Allah inason zama bbabbar lauya mefada aji aduniya Kafin nayi aure Rahama tace Allah yacika miki burinki BARRISTER MARYAM Maryam tayi murmushi tace kai kawata har faranta min rai wallahi Allah yakarbi adduarki Washagari daurin auren garin marrabar abuja yacika makil da jama'a dam kuma manyan mutane Yakama shugaban kasa mate makinsa memartaba sarkin kano kanin daddy da sauran sarakuna da yan majilisu Kai ranar garin mararraba maki yake da jamar annanbi tako ina kazaga yansanda ne da sojoji koina an bazasu Antaru akatafaren gidan megari Wanda daddy yasa akagama komai Kafin ranar yau Megari ganin jama'ar dake cikin garinshi kuma wai duk wani babban acikin Nigeria to yana wannan waje Sai kawai yafashe da kukan farinciki Dakyar akabashi hakuri yace wannan yarinyar alkairice agareni Allah.mata albarka Kowa tace amin nan akadaura aure daddy da amaryarsa DAGASH yana daga cikin mota yaki fitowa su zayyada sun sunyi yace shifa bazai fito ba tunda yake a rayuwarsa betaba taka kazamin gari irin wannan Ba Faisal yace ai shikenan dan iska saikayi tayi mukam munshiga sukashige abinsu DAGASH kawai yaji ana an daura auren ALHAJI SU'AD BABANGIDA DA AMARYARSA MARYAM AHMAD GWAZA DAGASH yakebe baki yace kai daddyma akwai rigima Yacigaba da danna wayarsa abinshi har mutane suka fito akashiga gaisawa da juna Dagash yace to malamai aisaikuzo mutafi ko Faisal yace a a bazamuje muga antynta muba .yayi tsaki yace wallahi zantafi inbarku kwabiyo su daddyn Faisal yace wa zayyad kaga kazo muje Dan iskane sai yatafi gashi da muta daya mukazo Haka suka dau hanya abinsu Daddy kam saida yasallami bakinsa ya rage dagashi sai amininsa alhaji Dan asabe sai mutan daukar amarya wata hadaddiyar lemozin ce doguwa tayi parking a gefe Dan tunda dare matan megari sukaje suka dauko anty zuwa wajensu Daddy yasa akira mishi amaryasa anty tafito cikin shiga ta alfarma wato lifaya ce me tsadar gaske kana ganin kasan ta hadu iya haduwa Dan tasha gyara sosai maman rahama ta dauko megyaran amare acikin abuja Bayan kyau da anty tayi harda wani yarinta karara zakagani a fuskarta Bazaka taba cewa ta ajiye kaman maryam ba Daddy ya bude mata gidan gaba tashiga da kanta kafin yazaga yazauna shima alhaji Dan asabe sunyi matukar burgeshi yana daga bayan motar yace barka dai amaryarmu Anty tayi kasada kanta tace barka dai alhaji nan suka gaisa yasa musu albarka a auransu daddy yace mungode sosai da adduarki abokina nan dadi yace a a yanaganki kekadai ina kawar taki Anty tace itatarokini amma daga bakin gate ta tsaya yace a a kirata mugaisa sugaisa da abokina Anty tace to tafita tafiyarta ma kawai abin kalloce Alahi Dan asabe yace kai abokina Gaskiya kasamo yar shila dole karikice .dad yayi murmushi yace kai meyakai idonka kan matar aure Yafada yana murmushi alhaji Dan asabe yace ai amarya take yau dole akalleta sukayi dariya gabadayansu Anty suka fito da maman rahma itakuma maman rahama suka gaisa da daddy yace ga abokina can kugaisa yanuna mata motar daukar amarya Abin yaba anty mamaki tace a a yaushe yakoma can koma Daddy yace ai waya yakeyi maman rahama takarasa gurin alhaji Dan asabe suka gaisa zata tafi yace a haba zainab yazaki tafi Kuma kibarni nikadai bayan abokin nawa yana tare da amaryarsa Maman rahama tace kai alhaji kana da abinda dariya suma nan hira sukayi sosai Alhaji Dan asabe dai ya kyasa mman rahama sosai Daddy yace to maryam zamu koma saikun karaso nifa da dahalima da anbani amaryata ma kawai nayi gaba da ita Anty tayi murmushi murmushi bata ce komaiba Yace wai maryam meye siirin wannan kyau da kikayi haka na yau yafita daban Anty tayi murmushi kawai yau ba bakin magana *** Can gida Kuma gida yacika makil da mutane yan gulma ne gasunan dai Mummy dai yan uwanta daga libiya suka zo mata kannan ta mata sai Kuma kanwar maman ta sai matar yayar mommyn Suna

Chapter 7 of 18