Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
sukaga zugar abokansu sun tahowa tashi sukayi suka karbesu nan danan zayyad masu rabon take away sukafara Komai na girma akayi Shafa'atu takira wayar daddy yadaga yace shafa'atu ya akayi tace Daddy junior yana ta kuka Daddy yace asha fito gamunan kofar gida kikawa minshi Nakaiwa mahaifiyarsa Haka kuwa akayi dadddy ya shiga mota sai gidansu anty Yanazuwa kuwa akakirata tafi cikin doguwar hijabinta kamar yadda tasaba yace maryam shine kotakan Dana bakyayi kinmanta dashi Anty tace Haba ya zanyi namanta da duk wani abunda yashafeka a rayuwa ina sanedashi Ai nasan yana hanun da bazai wahala ba koba agun shafa'atu ka karboshiba Daddy yayi murmushi yace kwarai na yarda yana ranki tasa hanu ta karbe lil al'amin daga hanun daddy Yace maryam kiyafemin kaddarace wacce bamu isa mukauce mataba Zabbau ta cuceni cutar da bazan taba maida kamanta ba Asarar mace kamarki ai babban abune a rayuwar kowane magidanci Haka kuma samun ki sa ace babban a rayuwa Anty bazata iya tsayawa jin maganganun daddy ba yasa tashige cikin gida tana kuka Shima daddy mota yafada yatayar Allah ne kawai yakaishi gida Anty nashiga yaya aliya tayi saurin karbar lil al'amin ganin yadda anty tashigo a rude Tace maryam lafiya anty tace yaya aliya nayi rashin miji da bazan taba maida kamarsaba alhaji yakaunaceni ya nuna min kauna tashi daya sunrabamu rabu ta har abada Dan ina mai tabbatar miki da ace saki daya yamin nidakaina zankoma gidana Amma kash ya yanke alakar my gaba daya bazan taba samun wadda zai nuna min kauna kamarshi ba Gani sukayi hanun inna na motsi alamun magana takeson yi Washagari misali karfe Tara safe yaya Abdul yatafi gurin aikinsa wato gadinsa Yaje yakarba agurin abokin aikin nasa Yana zaune Al'amin yashigo da motarsa cikin asibitin yana tiyata ne karfe goma shiyasa yashigo amma dabazai shigo ba Ganin ya Abdul a gate Al'amin bai karasa parking dinba yafito yace Haba malam Abdul mekadawo nan gurin kuma ai kafi karfin nan kuma yanzu Kayi school ne yaya Abdul yace ai tunda daga secondary school bankaraba Yallabai kabarni kawai wallahi ina jin dadin aikina Dagash yace kajirani zanfito daga tiyata by 12 pm zamuyi magana amma banason kacigaba da budewa mutane gate Yadauki mukullin office din shi yace gashi kaje office kajirani Yace ina shi malam haladun yacigaba da aikin kawai Kafin asamo wani *** Bayan kwana biyu Alhaji imam yagama komai na tafiyan su inna da malam jinya Anty da yaya aliya da yaya Abdul dasu za atafi Yayin da maryam zatabi mahaifinta zuwa libiya Dansuma sunji komai yanzu maryam kawai suke dokin gani barinma hajiyarsu mummyn dagash Tana ta Allah Allah taga jinin imam dinta **** Hajiyar dagash ne zaune kan kujerarta da carbi a hanunta tana lazumi sai daddy yashigo Yaga tana ta aikin tunanin nata nafama yace Wai bazaki daina wannan damuwarba Aisha yakikeson nayi ne narasa maryam Kema kina son kisawa kanki damuwa Mummyn al'amin tace to yakakeson nayi alhaji dawani ido zan kalli maryam harta yafemin Alhaji yace wata maryam din ai maryam tadade da yafe miki ai bata da ruko kedai Yakama ta idansun dawo ki je hargida kisake Neman afuwa Mummyn tace inasukaje daddy yamata bayani komai tace hakan ma Yayi To ina maryam akawo min 'yata tazauna dani koda na yan kwanakine Wallahi alhaji tunfarkon danaga maryam naji tashiga raina kawai dai naringa karyata hakan ne saboda tazo a matsayin yar talakawa Daddy Yayi murmushi yace tashi kikawo min coffee zanshiga ciki Yatashi yahaura samanshi itakanta mummy mijin nata yabata tausayi tabbas yana son matarshi Dan gashi harda wasu raman wahala jinyar zuciya sukafito mashi **** Dagash kwance cikin falonsa shikadai yana tunanin Maryam wai yaushe ne za abashi dama yaje yaganta yaushe ne zasu bashi matarshi Daddynsa king yace karyaje gareta a yanzu harsai ta huce shin yaushe ne maryam dinsa zata huce ta fahimceshi Shidin masoyinta ne nagaskiya Kai ina bazai iya watannin da akaniba mishi Kafin yagantaba saboda gone zaitafi libiya Next page Your comments is needed fan *Signed by ummu afan* πŸ’» [15/07, 1:14 PM] SIS UMMY: πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€ 🎑🎑🎑🎑🎑🎑 πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€ 🎑🎑🎑🎑 πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€ 🎑🎑 πŸŽ€ *BISSIMILLAHIR_RAHAMANIR_RAHIM* *Ummu Afan the Gorgeous writer of the year ,Author of 'YAN BIYAU NE &AKWAI LOKACI* 🌟GORGEOUS WRITERS FORUM🌟 🌟 G.W.F🌟 *Home of gorgeous, intelligent and expert writers we are the best among the rest, Dedicated to lovely son afan Allah ya albarkaci rayuwarka my son much care 😘😘😘😘😘😘 Talle talle talle πŸ‘‡πŸΌπŸ‘‡πŸΌπŸ‘‡πŸΌ *KAI NE SILA* Shahararren novel dake zuwa muku daga alkalamin *sis sameehat* Marubuciyar littatafan soyayya domin nishadinku Karkusake a Baku labari yanan a social media masu bukatar littafin *KAINE SILA* sumata magana da wannan number din ta watspp 08033975309 _🎑AL'AMIN DAGASH FANS GROUP_ 🎑 πŸŽ€ *AL'AMIN DAGASH* *PAGE* 6⃣7⃣to7⃣0⃣ Maryam kwance kan cinyar kakanta hajiyar su mummy kenan Tunda maryam tazo gidan tazama yar gatan kowa Kowa na cikin gidan jida maryam yake kaman su lasheta Barinma kakarta hajiyarsu mummy ai tana matukar kaunar maryam sosai tunda ta ganta kullum suna tare Haka alhaji nura babban yayan su mummy ma shima yana nunawa maryam kulawa sosai yayinda matarshi hajiya mami itama bakaramin gatantawa maryam takeba Maryam dai tazama yar lelen kowa shiyasa shagwaba yakaru Maryam ta kalli kakarta tace hajiya ina da tambaya wai Ku asalinku larabawane Hajiya tayi murmushi tace sosai kuwa maryam asalin yan saudiya kuwa Neman kudi yafito da kakanku kasar libiya Maryam tayi murmushi tace haba ai dagani ba tambaya hakan ya nuna ma Hajiya tayi murmushi tace meya nuna miki hakan maryam tayi murmushi tace caf kinganki kuwa hajiya kintsufa amma har yanzu kyanki nanan Hajiya tayi murmushi tace kayya maryam ina wani kyau to mamanki ta Aisha kuma kice mata me itada ubanki ai duk sun kwashe kyan Maryam tayi dariya tace kai hajiya wannan ai zagine dawayo sukayi dariya gaba dayansu Ameelat tashigo agajiye tazauna sharaf gaban su Maryam tace yan makaranta andawo ameelat tace wallahi kinsan sabon shiga wallahi gaskiya university yana da wuya Maryam tace a a fa banyardaba wallahi sai dai kekikeson yamiki wahala Ameelat tace a zakice haka mana tunda ke kinsamu kinyi aurenki da mijinki kinga kuwa koyanzu kika koma school wallahi bazai baki wahalaba saboda bakida fargabar komai a gabanki Maryam ta watsa mata harara tace zakifara ko ameelat tace to karya akayi ba matar auren baceke Hajiya tace to zaku farako ameelat tace rabuda da ita hajiya bata son gaskiya Tasamu handsome guy kaman brother Al'amin tadinga mana yanga wallahi tanasonshi Tana fada haka tadauki jakarta ta gudu Maryam tabita da gudu aguje suka shiga ciki da gudu Ameelat tashige dakinta ta kulle kofar Maryam tace wallahi zaki fito kisameni zanyi maganinki Ameelat yar alhaji nura ce ta hudu a mata subiyu suka rage da ameelat da kanwarta suhaima meshekaru takwas Ameelat zasuyi sa'oi da maryam kuma itama yanzu take shekarar farko a university ameelat takasance yarinya me hankali sosai Bata da burin da yawuce tayi aure kafin tacigaba da karatu sai dai kash abbanta yaki yace sai taje two hundred level kafin ya aurar da ita Tunda maryam tazo gidan ameelat tasamu kawa kuma yar uwa tare suke komai Ameelat takancewa Maryam wallahi kinyi sa'ar miji yar uwa samun mutum kaman brother ai sai an tona Maryam zata hada tace batason hirarshi shiyasa abin yazama tsokana a tsakaninsu Bayan sati biyu Dagash zaune a falon daddy yana rokarsa akan yabarshi yaje libiya daddy yace bayanzu bafa son Kasake hakuri sai lolacin daya dace kaje zansanar dakai kaje kaga matarka Mummy tace to alhaji muje tare mana ya rakani Daddy yace kedai kawai kice zaki min wayo kikai danki yaga matarsa Mummy tayi murmushi tace kodaya nidai banason tafiya nikadaine .daddy yace shikenan badamuwa kuje din amma danaso sai ita yarinyar tagama saukowa daga fushin nata kinsanfa abinda ciwo sosai Mummy tace hakane kam amma ai gwamma yaje can suhadu yabata hakuri Nan dai dagash yaji dadin barinshi da akayi sutafi da mummy Mummy tace saikaje kashiraya mana komai nanda jibi sai mutafi dagash yace that's my mom Dadddy Yayi murmushi yace kai dai bazaka girma ba tsofai tsofai dakai karinga shagwaba Mummy tace aifa ai yanzu lil al'amin Yakama ta kabarwa shagwabar haka Dagash yace ai harkintuna min boy Insha Allah harcan zanje naduba su antyn Daddy dai baice komai ba Direct office dinshi yawuce ya bar komai hanun zayyad Zayyad yace wai dagaske ne zakabi maryam tokabari akawo maka itamana Dagash yace caf waya fada zan iya hakurin harsai lokacin da akaga damar kawomin mata wallahi bazan iyaba Tunda aini ba dutsebane ina bukatar matata Kusadani Zayyad yace to yanzu kokaje ma ai dagawa kanka hankali zakayi kawai Dan idan kana ganinta damuwar taka zatafi yawa Dagash yace wayafada maka sata agaba zanyi ina kallo tana halal dina intsaya kallonta haka kawai Zayyad yace amma dakacika marakunya dagash yayi murmushi dake kara masa kyau da kwarjini Yace zancen kakeso wayasanima komudawo da Dan libiya Zayyad yace ai zaka rina wallahi kai ba Sai a hankali Allah yasa taki bada hadin kai muga ta rashin kunyarka Murmushi kawai dagash yayi kafin ya dialing number din wani abokin business dinshi Yanagama wayar zayyad ya kalleshi yace muje gidana mana ko rahma tana da sako gurin kawarta Dagash yace kudai dason saka yara su raina mutum Nifa kaga inason maryam ko tobazan taba bari ta rainaniba saboda banason raini Zayyad yace lalle bakasan soyayya ba ina ruwanta da raini Niyanzu kaga rahama sai yadda tayi dani wallahi binta nakeyi kamar rakumi da akala Kuma kaima bazaka gane hakanba sai randa katare dataka amaryar ka kwashi zumarta da kyau kashiga hanunta Dan wallahi auran yaran nan alkairi babba atare damu Dan yanzu gaskiya nasamu nutsuwa ban nemi komai daga matata na rasaba Dagash yace lalle nayarda kayi nisa a soyayya zayyad wannan irin zance haka Wai ina Faisal ne yace caf aina kwana banganshiba Dagash yace barin kira number dinshi muji Yayi ta ringing ba adagaba saida yakusan tsinkewa aka daga Faisal ne yace wai kai Dan iska mutum yana hutawarsa kadameni da kira haka Zayyad ya karbi wayar yace ato fada masadai wai tambayata yake ina kakene kwana biyu Shine nace nima banganka ba Dan idan nafada mai amarya ce arikeka zai tsaya min wasu maganganune nasu na gauraye Faisal yace ina dagash din zayyad yace gashi yamika wa dagash wayar dagash ya watsawa zayyad banzan kallo yace duk kugama Badai iskanci bane abin naku duk kugama wai damma nima inada matar Zayyad yayi murmushi suka gamawa Faisal yabawa dagash wayarsa yace mukarasa ko Dagash baiyi maganaba yaje sukashiga motar zayyad suka nufi gidan zayyad Mortar zayyad na parking rahama tafito cikin kwalliya tatsaya tana jiran karasowarshi shima ganin matarshi ya manta da dagash suke tare motar yabude yafita yanufeta itama karasowa tayi tarumgemeshi cak zayyad ya dauketa zuwa cikin gida Dagash ya rintse ido yace God help me tare da dafa goshinsa Yace duk abinda kuke kucigaba zanrama shiwanyancan Dan iskar nakirashi wai yazan katse wa mutum jindadinsa Shikuma wannan yadauketa suka shige Key din motarma a Jiki zayyad yabari saboda ya rude ganin kwalliyar matarshi Murmushi dagash yayi yatada motar yayi gaba abinsa yace kazo ka karbi motarka agida A ranar yagama musu komai saboda a yadda yakeji bazai iya kai jibin da mummy tace ba Gaskiya yana cikin wani hali na matukar bukatar matarsa Gidansu ya koma yace mummy nagama komai jirgin karfe goma zamubi Mummy ta takalleshi tace haka nace maka ya marairaice yace haba mummy ai dagobe da jibin duk dayane a gurin Allah Mummy Dan nata yabata tausayi tagane abinda yake damunsa tabbas Dan ta yashiryu da tana kyautata zaton yabar wanann yarinyar Victoria take ko wa Zatasan yadda zatayi abashi matarsa sudawo gida gudun komawa ruwa Ta kalleshi tace shikenan Allah yakaimu goben dagash yace Yauwa mummy kokefa Nazeefa da afnan nesukadawo daga anguwa dagash ya kallesu yace kai kuzonan daga ina afnan tace gurin ummy muke Dagash ya watsa mata wani banzan kallo ubanwa kuka tambaya dazaku fita Duk suka rikice dagash yace barin fada kafin nadawo daga tafiya acikin samarinku da kuke Tarawa mutane akofar gida kufitar da na aure Wallahi kokuma duk nabadaku ga masu gadi kunsan zan iyako suka daga kai dasauri Yace kutashi Kuban guru guri shashai kawai Washagari jirgin su dagash da mummy yadaga zuwa libiya Maryam zaune falon hakiya mami itada ameelat hajiya mami tafito da kula tazauna itama cikin yaranta ta kalli maryam tace Yauwa 'yata gawannan maza cinye kiban kulan inakallonki Maryam tace Yauwa mamana ta kalli ameelat ta mata gwalo itakuwa ameelat dariyar maryam takeyi Dan kwata kwata talura maryam bata Masan abinda maminta take dirka mataba Maryam tace zodai muci badan halinkaba ameelat Ameelat tace wa ni aisaike yargatan mami kedai akace kici nima dai nasan kitchen din zanje nadiba Hajiya mami tace a munjidai sauki Kofi kidebo mata madara a fridge maisanyi Ameelat ta tashi tana dariyar mugunta dantasan yadda mutane suke kyan kayan maminta sosai kwararriyace akan harkar maganin mata Taje tadebo madarar da maminta take nufi Takawo Maryam taci iya cinta tace mamina nakoshi Mami tace daure kikarasa yar mami haka dai maryam take fama dakayan ciye ciye da shayaye shaye Dana wanka Sosai hajiya mami take gyarata saboda tasan komai dayafaru da ita taji komai agurin mamin dagash Sosai maryam take ganin canji ajikinta amma saitayi la'akari da canjin rayuwa datasamu ga farincinkin haduwa da danginta ga tsananin soyayyar families dinta suke nuna mata Jikin yasake tsanain kyau ,laushi ,tsantsi dasheki Gacikowar datayi ta kotaina kirjinta suncika fam ga diri mezaman kansa Itadai maryam har tsoro kyan datakeyi yakebata gashi duk sati saitaje Saloon gyaran gashi itada ameelat sosai maryam tasake gogewa da wayewa sosai Ameelat na zaune tace tana shiryarwa tace Dan Allah maryam kifito kefa idan kinshiga wanka kamar zakisake fata maryam ta fito tana goge ruwan jikinta tace wai harkingama shiryawane Ameelat tace mezanjira tunda saloon zamuje ai a can zamuyi makeup din Maryam tace hakanefa kinga kuwa ai shirina bazaiyi wahalaba Ameelat ta kalli agogo tace Dan kiyi sauri tunda kinsan daga saloon zamuje gidan anty naila kinsan tace muje ko Anty naila kanwar su mummy ce dake aure cikin libiya itama akwai autar su mummy kuma mesuna nasreen itama tana aure a cikin garin libiya Maryam tazabo wani doguwar Riga ja mai adon ash ajinta na duwatsu mai tsadar gaske sosai Anty nasreen ce ta takawo mata lokacin dataje India da mijin baifi ma satiba Tasaka tayu Rollin da mayafin batayi kwalliyaba saboda a saloon za a musu Tadauki bag dinta da high heel dinta ash colour tabalain kyau sosai duk da ba kwalliya komai a fuskarta Tana fitowa ameelat tace kai maryam kinga yadda kikayi kyau kuwa inama brother nanan yabiya kudin kwalliyar nan Maryam ta zabga mata harara tace kekuma bakida aiki sai shirme motar ameelat suka nufa maryam tubude tashiga Ameelat kuma taja motar suka fita Zuwa saloon anmusu gyaran gashi sosai masu saloon suka yaba da kyan yan matan nan kamar su sacesu bakamar ma maryam tayi balain kyau sosai gashi anmusu makeup tayi kyau sosai Gaskiya Wanda yasan maryam ada yanzu idan yaganta zaisha wahala kafin yashaidata Ta hana acika mata makeup a fuska gira kawai aka gyara sai power sai jambaki maroon black kai tayi kyau matuka Direct gidan anty naila suka wuce Sunsha hira sosai da ita sai da suka kai kusan karfe takwas nadare kafin nan suka mata sallama tayi tayi sutsaya su kwana amma ameelat taki tace gobe tana da test a school *** Suna parking ameelat ta fito itakuwa maryam tana chart ne ma abinta saidata gama yangarta kafin ta fito Tafiya takeyi tana chart a waya tana dariya alamun dai abinda take karantawa yana bata dariya Batayi tsama niba kawai taci karo da mutum Wayar tafadi Tadago da sauri Dan tabada hakuri tasan lefintane suka hada ido hudu itada PRINCE AL'AMIN DAGASH Next page Your comment is needed fans *Signed by ummu afan* πŸ’» [15/07, 1:14 PM] SIS UMMY: πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€ 🎑🎑🎑🎑🎑🎑 πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€ 🎑🎑🎑🎑 πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€ 🎑🎑 πŸŽ€ *BISSIMILLAHIR_RAHAMANIR_RAHIM* *Ummu Afan the Gorgeous writer of the year ,Author of 'YAN BIYAU NE &AKWAI LOKACI* 🌟GORGEOUS WRITERS FORUM🌟 🌟 G.W.F🌟 *Home of gorgeous, intelligent and expert writers we are the best among the rest* Dedicated this page to masoyan maryam da maryam wato anty da maryam karama 😘😘😘😘 Talle talle talle πŸ‘‡πŸΌπŸ‘‡πŸΌπŸ‘‡πŸΌ *KAI NE SILA* Shahararren novel dake zuwa muku daga alkalamin *sis sameehat* Marubuciyar littatafan soyayya domin nishadinku Karkusake a Baku labari yanan a social media masu bukatar littafin *KAINE SILA* sumata magana da wannan number din ta watspp 08033975309 _🎑AL'AMIN DAGASH FANS GROUP_ 🎑 Much love to you 😘 πŸŽ€ *AL'AMIN DAGASH* *PAGE* 7⃣1⃣to7⃣5⃣ Cikin tsananin mamaki da rudewa maryam take kallon dagash yayin dashikuma dagash ya hade rai kamar baitaba dariyaba Prince sak kawai Cike da takaici maryam tafasa daukar wayartata dafadi kasa Takauce zata wuce abinta Jitayi ya riko hanunta yace dawo nan batareda ya kalletaba Maryam kuwa tace lafiya malam kasake min hanu mana Cike da mamaki dagash ya kalleta yaga ba alamun wasa a fuskarta Yace what mekikace maryam cikin dauriya tace saboda banaso Cikin tsananin mamaki dagash ke kallonta yace nikikefadawa wannan maganar maryam tace a mana batare da takalleshiba Saboda yadda zuciyarta kematukar tsoron dagash amma tadaure Dan samawa kanta mutunci Kallonta yayi tsaf batayi tsammaniba taji bakinsa cikin nata ya hada tayi yinkurin kacewa amma takasa ameelat ce tabiyo bayanta ganin ta Dade batada shigoba ga mummyn na tambayarta Ganin abinda kefaruwa yasa ta tsaya turus bata karasaba A hankali takoma cikin sanda takoma shiru Mummyn dagash tace ina maryam din ameelat tarasa mezatace wa mummy tace am am am tashiga in ina dai mummy tagane Ameelat tace tana waya a waje ne Mummy tace ok hajiya mami tace shine zata tsaya a waje a daran nan Ameelat tace yanzu zata shigo Dagash baisaketa ba sai dayaji horn din mota alamun alamun dai motace zatashigo Sai yasaketa yana saketa maryam tafasheda kuka tayi cikin gida da gudu Murmushi dagash yayi yadauki wayarta a kasa yayi part din dayake sauka idan yazo Itakuwa maryam batasan da mutane a falonba tashigo da gudu zatayi dakinsu ganin mummyn dagash yasa tayi turus ga hawaye nan caba caba a fuskarta Hajiya mami tace a a maryam ya dakuka kuma meyafaru Karasowa tayi tatsuguna tagaida mummyn da mami Suka amsa Mummyn dagash tace zonan yar albarka zogurin mummuynki taji duminki Maryam batayi musuba ta matsa kusada mummy Mummy ta rungumeta tace Allah yamiki albarka 'yata kiyafewa mummynki abinda ta aikata abisa rashin sani Maryam tace bakomai mummy nibantaba rikeki a raina Mummy tace yauwa yar albarka Allah yayi miki albarka Maryam tayi saurin dafa kanta alamun yana mata ciwo mummy tace lafiya tace kaina yake ciwo Hajiya mami tace subahanalla tashi kije kikwanta yanzu ameela zata kawo miki magani aikuwa maryam batayi musuba Dan daman hakan take bukata Daki tawuce tafada kan bed dinsu tana kuka ameelat data fito daga wanka tace a a amarya ansha kamshi Wannan irin soyayya haka lalle kunyi missing dinjunanku tunda abinma ankasa hakuri tundaga waje Maryam tadago kanta ta watsa wa ameelat harara Ameelat tace wallahi dariya kike bani kema fa kinasonshi kuma kinawani kaiwa kasuwa Maryam batace komaiba tana kukanta tashiga bathroom tayi wanka ta fito tashirya cikin sleeping dress dinta fari tas dashi me tsantsi takwanta taja bargo abinta Ameelat tace yau ba hira kenan tun yanzu zaki kwanta maryam tace bansani ameelat tayi dariya tace ai shikenan sai nashigo natafi falo Kowa ya hallara a falon ana al'amin yace inason nabiya ma naga su anty asibiti Alhaji nura yace ai babanka imam ma yanacan yau kwanansa biyu datafiya dubosu Ance jikin nasu dasauki sosai Wai ina my daughter ne Banga tazo wa Abba oyoyo ba Hajiya mami tace kanta naciwo shine nace taje ta kwanta Abba ashsha tasha magani ko Ameelat tace a nakaimata dagash yace wani irin magani kikabata ameelat tace panadol Yace ai bakowani ciwonkai akeshan panadol Barin dubo jikin nata Abba mummy tace a a son ai tayi bacci kabarta kawai sai gobe kuma Abba yace a a barshi yadubota ko akwai taimakon da za abata kafin safiya Hajiyar su tace ikon Allah lalle maryamu yargatan kowace yanzu ciwonkai ne yatada hankalin Ku haka nikam ba abinda yadameni Ameelat tace caf ai wallahi watakila ma kinfi kowa damuwa duk akayi dariya Abba yace dubo ta kaji al'amin Sum sum dagash ya wuce zuwa bedroom din ameelat inda ya tabbatar nan zaiga maryam Yana shiga yaga dakin da duhu sakamakon kashe wutar dakin da akayi Sa hanu yayi ya kunna wutar Idonshi yasauka akan maryam dake bacci cikin nutsuwa tayi kyau sosai Karasawa yayi yahau gadon yashiga cikin bargon shima Cikin bacci maryam taji kaman ana lalubata tabude ido zatayi ihu ina ai ya hade bakinsu guri daya Sai dayayi ra'ayi kafin yasaketa maryam tamaida numfashi tafashe da kuka tace nifa banason irin abinda kakemin banaso Yanzu idan wani yashigo fa yace suzo mana kawai mekike nufine da ni Yakike Neman haramta min abinda Allah ya hallatamin ne Kobakisan kedin halas dinabace Oyo bakyasona ko to meye dalilin ki nakina Baki maryam tasake tana kallonshi tace Tana ganin karfin hali irin na mutumin ne Yace yes kalleni da kyau nimijinki ne al'amin Maryam tadafa kai tace ya Allah tasauko daga kan bed din sai batakai ga daga kafaba ta koma tazauna saboda bazata iya tafiya da wadan nan kayan a gaban dagash ba Ganin haka yasa dagash murmushi tareda lumshe ido Tace Dan Allah kafita zankwanta al'amin yace idan kikasake cewa nafita anan zan kwana kitashi kawai kizo muyi magana Maryam ta kalli dakin dakyau ta hango zurmukeken hijabin ameelat me hanu ai kuwa tasura tayi waje Tasaka tana fita falo taga su Abba ne da sauri takarasa tace sannu da dawowa yace yauwa yar Abba ya kannaki Murmushi maryam tayi tace nasha magani Abba yayi sauki Hajiya mami tace a kodai daman na rashin ganin Abba ne Murmushi alhaji nura yayi yace wai haka maryam Murmushi kawai tayi Mummy kuwa maryam nafitowa tasan al'amin ta guduwa saboda a razane tafado falon ganin mutane yasa ta dai daita nutsuwarta Mummy tace zo yargidan mummy naji kan naki maryam ta matsa kusada mummy Mummy tace tashi muje ciki 'yata Dakin da mummy take sauka nan suka shiga Mummy tace nasan bacci kikeji maryam son ne yadameki kika gudu Hau kikwanta a gado bazaki komai dakinba zai zo yasameni Kunya Yakama maryam Dan batayi tunanin mummy taganeba Murmushi tayi ganin maryam takasa dago kanta Tace kisaki jikin dani maryam nima mahaifiyarkice kinjiko Maryam tadaga kai alamun to Ba musu ta hau takwanta abinta Next page Love u love your nice comment *Signed by ummu afan* πŸ’» [15/07, 1:14 PM] SIS UMMY: πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€ 🎑🎑🎑🎑🎑🎑 πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€ 🎑🎑🎑🎑 πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€ 🎑🎑 πŸŽ€ *BISSIMILLAHIR_RAHAMANIR_RAHIM* *Ummu Afan the Gorgeous writer of the year ,Author of 'YAN BIYAU NE &AKWAI LOKACI* 🌟GORGEOUS WRITERS FORUM🌟 🌟 G.W.F🌟 *Home of gorgeous, intelligent and expert writers we are the best among the rest* Dedicated to all my fans wadan da nasani da Wanda bansaniba ina alfahari da kaunarku a gareni Talle talle talle πŸ‘‡πŸΌπŸ‘‡πŸΌπŸ‘‡πŸΌ *KAI NE SILA* Shahararren novel dake zuwa muku daga alkalamin *sis sameehat* Marubuciyar littatafan soyayya domin nishadinku Karkusake a Baku labari yanan a social media masu bukatar littafin *KAINE SILA* sumata magana da wannan number din ta watspp 08033975309 Jinjina agareki Ummy khaleel marubuciyar GIDA DAYA wannan page din naki ne Allah yakara basira ya yaraya zuri'a πŸŽ€ *AL'AMIN

Chapter 16 of 18