Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
tsara komai Wayar daddyn ce tayi kara yadaga yaga babban danshi ne zayyad Yace a a mutan Spain kodai kana hanya ne zayyad yace yes dad zamu yi landing by two so aturo driver yadauko ni Daddynshi yace that's my boy ai kanwarka zata zo ta daukoka yace OK dad Mom dinsu tayi murmushi tace sarkin rigima zai dawo kunnen mu ba sakat kuma Daddyn suhaila yayi murmishi yace ina ruwanki da rigimarsa dan daddy ne Tace shima sai yazo yafito da nashi matar a hadasu da yar uwarshi Daddyn suhaila yace da dai yafi kam Dakyar mom din suhaila ta rarrasheta akan tayi shiru ai kowacce da salonta zata zauna kuma ba abinda AYMANA zata nuna miki Kema ai kina da kyau sosai nasan idan har kika aureshi zaisoki fiye da yar uwatasa ma Murmushi tayi jin abinda uwarta ce hartasami kwarin gwiwa ***** Zayyad yakira wayar AL'AMIN alokacin al'amin yashiga wanka sai da yafito yaga miss call yabari idan yagama shiryawa saiya kirashi Yana kan goge kanshi da hadaddan towel din shi Wanda ba abinda yake fitarwa said kamshi danzan iyacewa al'amin kamshi nature dinshi ne Wayarce akasake kira da yadauka yana murmushi zayyad yace DAGASH DAGASH DAGASH AL'AMIN yayi murmushi kawai yace to dan iska zakafara ko Zayyad yace aikaji matsala ta dakai kaikuma to by 2 pm zanyi landing a airport AL'AMIN yace waw amma naji dadin dawowarka sosai but yau ina da theater a hospital by two da sai nazo airport din na dauka Zayyad yace no bad don't worry your self suhaila zatazo ta daukeni Daganan al'amin baisake cewa komai ba sukayi sallama Yana gama shirinsa cikin wani suit mai balain kyau sosai dan bazan iya fada muku irin kyau da AL'AMIN yayi ba Ya dauki farin glass din shi Wanda yakara bayyanar da anihin kyau da Allah yaba al'amin Yadauko brief case din shi ya rataye yayi waje ****** Bayan sati biyu Al'amin zaune a office dinshi yana duba patience dinsa bayan aiki yayi sauki ne sai yaji anyi nock yace yes come in Bakowabane sai zayyad yashigo da sallama AL'AMIN ya amsa yace kaji dan iska saikace wani mutumin kirki Sukayi dariya gaba dayansu tare da tafa hanu Zayyad yace da nabanzane Zayyad yace wai harkura zatace wa kare maye Al'amin murmushi kawai yayi Wanda dama baya yin abinda yafi haka Zayyad yace ango ango amma kasan Allah dasu daddy zasu ji magana ta subarka kazabi mata da kanka amma suntashi sunhada ka da suhaila da Aymana duk da suhaila kanwatace nasan bata cikin tsarin macen da kake so tazama mallakinka AL'AMIN yadago yakalleshi kadan yace kaifa kafiye surutu Zayyad yace ba surubane nasan waye kai nasan irin macen da kadade kana lissafa min Wanda duk cikin su babu wacce takeda wannan qualities din DAGASH baice komaiba yaduba wristwatch din shi yace kai yakamata muje muyi lunch fa Zayyad yace wai har yanzu baka dena komawa gida yin lunch ba bazaka bar mom ta hutaba DAGASH yace idan nabarta ta huta nikuma sai inci abinci a ina Zayyad yace common Ga wurarancin abinci nan bila adadin agari DAGASH yace Allah yasauwake Inzaka ta tashi katashi idan kuma bazaka tajeba natafi abuna Zayyad yace zaka Rina ai dan ba mutunci kaganiba dan iska Suka fita zuwa gidansu al'amin Mummyn al'amin nazaune a daya daga cikin kujerun falonta taji sallamar dan nata Ta amsa tace Son baka gajiya da zirga zirga a hanyar nan wai kai kazo abinci ko Zayyad yace kema dai kyafada mom nace mishi muzabi restaurant mai kyau murinka zuwa lunch yace Allah yasauwake Mom tayi murmishi tace aikuwa nakusa hutawa nan da two months dai ai sai dai yaje gidan shi yaci ko DAGASH ya yamutsa fuska yace Allah yasauwake naci jagwalgwalon yara kullum gunki zanci abinci Mom tayi murmushi tace wa zayyad kaji wata sabuwa kuma wai su suhaila ne yara To suhailar ce yayarin ya kokuma Aymanan ce yarinyar dukansu babu wacce bata kai 25 years ba DAGASH yace amman dai ai agurina yarane tunda babu wacce ta girmeni acikinsu Zayyad yace uban son girma Mom tayi murmushi tace kai son wai ina zaka kai wannan murdaddan halin nakane DAGASH yace mom am hungry fa Tace kuje dining area your food is ready That's my lovely mom yabata kiss a kumatu ya wuce abinshi Mom tace wato son kagama rainani ko zayyad yayi murmushi yabi bayan abokinshi **** Aymana zaune cikin bedroom dinta tana waya da kawarta dake Dubai mai suna sauda Sauda tayi dariya daga wayar tace amma gaskiya kawata na tayaki murnar samun gwarzon namiji Kaman wannan gayen da kika turo min hotonsa Kuma kikace dan yayan dad dinki ne amma nibantaba ganinshi ba Aymana tayi murmushi tace a ina zaki ganshi tunda kogidan mukaje bama haduwa Sauda tace hakane saidai maganar suhaila yanzu miji daya zaku hada da suhaila yar jiji dakai din nan Aymana tayi murmushi tace to Allah na tuba wazata ja wa ajin bayan babu abinda zata nunamin Kawai kowatata tafish sheta Sauda tace hakane amma kawata akwai magana amma sai na dawo zamuyi maganar Aymana tace OK Allah yadawo dake lafiya sukayi sallama Aymana tashiga tunanin ya al'amin acikin zuciyarta Allah yasani ta Dade tana kaunar ya al'amin dama rashin ganin fuska ne yasa ta kama bakinta Dan zata iya rantsewa bata taba ganin dariyar bawan allahn nan ba kullum fuska a murtuke Kaman wani boss Tashi tafito falonsu kuyanginta suka zube suna kwasar gaisuwa ta watsa musu harara tace dan uwarku kuna jiran nasa takalmin da kaina ne kafin tarufe baki wata daga cikin su tadauko sifas din nata tashiga saka mata Wasu kuma Allah ya huce ran gimbiya Tace nikumin shiru wawayen kawai tawuce fuuuuuuu Tana shiga falon mummynta taga bakowa dan haka ta wuce zuwa bedroom kawai direct Tana shiga ta tarar da ita zaune kuyan ganta suna mata massarge din kafar Ganin Aymana ta shigo yasa sukafita dan sunsan halinta yanzu saitaci mutunci su Mummynta tace lpy kuwa aymana tace wallahi mummy yanzu dan Allah dan daddy yabawa ya al'amin ni sai yaki zuwa ma mudan gana Kuma wallahi nasan yana zuwa wajen waccen banzar suhailar nice dai bayaso tafashe da kuka Mummynta tace wayafada miki yana zuwa gurin dayar itama fa bason ta yakeba Kinga ai gwamma kema yar warsace ko A hankali zaifara sonki Itadin banza kuma indai al'amin ne zaizo ki kwantar da hankalinki Naji abban ki namagana dashi dazu akan yazo Ku gana Aymana tayi murmushi tace Yauwa mumyy wallahi har hankalina ya kwanta *** AL'AMIN zaune a office din daddynshi dama duk Thursday da Friday yana zuwa office din daddynshi idan yadawo daga aiki dan 12 yake tashi Bayan sungama hada duk wasu file daddy yace Son kaje gurin yaran kuwa Kasan anriga an tsaida lokacin bikin ko Nan two months za ayi AL'AMIN yace nasani dad zanje insha Allah idan nasamu dama yace alright kayi kokari kajiko Yana kwance akan godonshi yanashan whisky wayarshi tadau kara yadauka yaga Vichy ce cikin tsawa yace wayace kikirani by this time a round Tace am sorry sweet heart dama nakiraka ne naji lafiyarka yace kina ina ne tace gida yace kijirani zanzo yanzu Baijira ta ce wani abuba yakashe wayar shi Murna ta kama Vicky dan tasan tayi missing din shi sosai Dan idan abin baya kanshi saiyafi wata be nemeta duk da dama itatake nemanshi nan da ta tashi ta shirya cikin wasu matsatstsun kaya Wanda tasan zeyaba dasu sosai Sannan kuma ta fesa turarrukan dayabata tadinga amfani da su idan zaizo gareta danshi mutumne me tsafta sosai Haka kuwa akayi ranar a hotel suka kwana da Vicky Ya tashi da asuba yayi wanka yaje masallaci daganan kuma ya wuce gida abinshi Vicky koda ta tashi taga bayanan tasan badawowa zaiyi ba dan haka halinsa yake Kudi taga yazube mata kan bed din ta kwasa tana murna Ita tasan daga ita DAGASH baya kula kowacce yarinya kuma yana kashe mata kudi sai dai tana tsoron ranar da zaisan ba shikadai take kulawa ba *** BAYAN KWANA HUDU Al'amin yashirya danzuwa gidansu suhaila da umarnin dad Zayyad daman baya gari shiyasa kawai yashirya tsaf cikin wasu suit mai kyau golden colour na cikin fari sai necktie dinma golden kai gaskiya yayi kyau sosai Yafito ya wa mum din shi sallama Tace waw Son wannan kwalliya haka lalle agaida suhaila ta ciri tuta Baice komai ba ya wuce abinshi saboda yasan tsokanarshi kawai takeyi Danshi ko yaushe cikin kamshi da ado yake Mom tayi murmushi tace miskli wannan matan naka ma ai su shiga ukunsu Hajiya zabbau ce ta fito tana waya tanemi daya daga cikin kujerun falon tazauna Tsakaninsu bamai cewa wata kala haka suke zamansu Suhaila kuwa tunda mom din Al'amin takira mummynta tace yau Al'amin yana zuwa gurinta Dadi yakasheta sosai aka hau gyaran jiki tasaka 'yan aikin gidansu suka shirya mata abinci na musamman karfe biyar na yamma Al'amin yayi parking a gurin ajiye motoci na gidan Bai fito a motar ba dan kasaita da jinkai Suhaila ta karaso cikin yanga da yauki da rashin kamun kai Riga da wando tasaka sun matseta gashi taci kitson attach Ga kwalliya da musamman ta dauko me kwalliya tamata na musamman Tayafa dan karamin mayafi Wanda dashi da babu duk daya Hanu tasa tabude mishi kofan tana sannu dazuwa doctor Sai daya dau lokaci kafin yasa kafa a waje yace Yauwa Tace mushiga daga ciki kugaisa da mummy Yamata wani wawan kallo yace kezaki fada min abinda zanyi Tayi saurin girgiza kai yace stupid Da kyar yaja kafa zuwa cikin gidan cike izza da kasaita Tana biyedashi har falon gidan nan anriga an ajiye komai na motsa baki a yatsine yake kallon komai Kaman yaga kashi duk da haduwa irin na falon Tazauna tana son magana amma tana shakka hakan yasa tayi shiru Tayi karfin hali tace yasu mummy Wani kallo yamata Wanda tarasa gane na menene kallon Yacigaba da latsa wayarshi Tashiga serving din shi abinci ganin bai hanata serving dinba tayi tunanin zai iyaci ne Sai da tagama tace doctor have a food bai kalleta ba ballan tana tasamu amsarta Can dai kusan minti goma yakalli agogon hanunshi Yasa hanu a aljihunshi yacire band's na kudi 'yan dubu dubu ya ajiye akurar dayake yatashi Yakama hanyar waje Takaici ya ishi suhaila ta tashi gwiwa a sanyaye tabi bayanshi kafin yakarasa fita suka hadu da mummyn suhaila Yadan sake fuska kadan yace mummy an wuni lfiya tace lafiya kalau al'amin .wato dan ba abokinka shine zaka wuce batare da mungaisa bako Yace ba hakabane mom dama Inda niyar shiga mugaisa Tace bakaci kamaiba zaka wuce yace bakomai mummy Yanzu ma gidan daddy king zanyi shiyasa nake sauri kar akira magrib ban karasa ba Tace OK to agaishesu ta kalli suhaila ta mata magana da ido akan tarakashi mana Tarakashi har gurin motar shi yasa hanu yabude yashiga yatada motar yayi gaba abinshi kota kanta bebiba Da kuka ta dawo falon tafada cinyar mum dinta tana kuka tace mumyy nashiga yafison Aymana kinga wai har sauri yake zaije gidan su Mummy tayi murmushi tace yaro dai yaro ne waya fada miki yafi sonta dayafisonta ai gurinta zaifara zuwa amma gurinki yafara zuwa kafin zaije gunta Gakuma makudan kudin daya ajiye miki Wanda bana tunanin zai bata kamarsu Idan kika kwantar da hankali bakaramin dukiya zamu taraba dan kisan koshi AL'AMIN yafi dadinki kudi nesa bakusa ba Ballan tana kuma uwa uba kuma mahaifinsa Wanda komai nashi al'amin ne akai Murmushi suhaila tayi tace kuma hakane maganarki mum Suka kirga kudin dubu Dari biyu cas Suhaila tayi wani ihu yace waw AL'AMIN yana isa ana kiran magriba dan haka sai da yatsaya sukayi sallah a masallacin gidan sarki tare da memartaba suka fito suka karasa cikin gidan Mummyn Aymana tace a a manya baki yau yarima ne agidan namu Yadanyi yake kadan danshi idan akwai abinda yatsana to akirashi Prince Aymana ce ta fito da gudu tana mummy ina ya al'amin din Kunya Yakama memartaba dan tanuna zumudinta a fili Hakan yasa yatashi yayi sama abinshi Mummyn Aymana ma ta tashi tayi cikin gidan akabar Ayman da Prince Yana ta aikin danna wayarshi Tace yaya sannu da zuwa Bai kalleta ba ballan tana ya amsa mata Nan da nan ta kira kuyanginta tashga zaginsu tace waiku wasu irin dabbobine bakusan abinda Yakama ta kuyiba Dayar tace ranki yadade kekikace sai kinbamu umarni zamudinga yi Tayi tsaki tace kushirya wa ya Prince abinci Aikuwa suka watse dan cika umarnin ta Wani wawan kallo da DAGASH ya watsa ma ta yace how there you zaki kirani da Prince dan ubanki ni sa'an wasanki ne Dama Kaman jira yakeyi ya huce takaicin masu kiranshi da Prince akanta Ganin yadda yataso yasa taja dabaya sai takai bango kafin yabita ya wanke ta da mari Yace dan ubanki insake jin sunan abinki ki sha sha beside ma wazaici Kazamin abinci na masu aiki Yasa kafa yataketa a kafa Yacire kudi kamar yadda yaba wa suhaila itama haka ya wurgeta da su yayi hanyar waje Da gudu tayi hanyar dakinta tafara kuka Kaman Allah ya aikota Mummy tasauko dan daukar Abu taga kudi turus akasa Tasa hanu tadauka tasan bazai wuce Al'amin bane yabaiwa Aymana Tayi hanyar dakin Aymana tanashiga tasameta tanata kuka tace meyafaru Aymana nan aymana taba mummynta labarin komai Mummy tace lalle ma al'amin yacika dan wulakanci shine harda mari akan abinda baikai yakawo ba Kwantar da hankalinki duk abinshi nasan yana sonki wazaiki kyakkyawar mace kamarki Aymana kobaki Ga kudinki dayabar mini bane Aymana tace aini kotakan kudinma banyiba dan takaici nan dai suma sukayi ta murnan samun kan al'amin DAGASH zaune kan daya daga cikin kujerunsa na part din shi yana ganawa da managers din sa na companies dinsa Akwai manager na DAGASH AIR LAND Dan Al'amin yana da jiragen sama a gida da wajen Nigeria shida ma haifinsa Sai kuma manager din DAGASH BUILDING CONSTRUCTION COMPANY shima ba abinda basayi na harkar gine gine da kawata gida Sai kuma DAGASH SHOPPING COMPLEX Wanda babu state din da bashi branch Sai kuma DAGASH BARBING SALOON NA MAZA DAGASH RESTAURANT wato gida jen abinci masu tsada duk nasane shida mahaifin Bazan iya fado muku dinbin dukiya da wannan 'da yatara shida mahaifinsa ba Bayan sun gama zaman ne ya sallamesu Kafin yashiga wanka yana fitowa yashir ya cikin kayan training dinsa yayi waje Yaje wani hadaddan gurin training ne na musamman Wanda aka kayatashi acikin gidan Yana isa yaga kannan shi mata suma suna motsa jikin Suna ganinshi sukafara wucewa daya bayan daya Nazeefa tace sannu yaya Yace yauwa abin yabasu mamaki dukansu yau yaya al'amin ne da amsa gaisuwa Batare da ya kallesuba yace ke afanan da shafa kuzo nan Dan uwarku yaushe nafara wasa daku dazaku wuce Baku gaisheni ba Afanan da shafa jikinsu yadau rawa sukace Dan Allah yaya kayi hakuri wallahi bazamu sakeba Cikin tsawa yace will u keep quite my friend Shiru sukayi harda kama bakin da hanu Yace oya kuje kudauko tsintsinya kushare compound din nan gabadaya Da mamaki suka kalli juna Dan basu taba sharaba Yasake daga musu wata tswar tukun suka watse da gudu zuwa cika umarninsa ***** Al'amin kwance yana charting a wayarsa yaga massage yashigo yaduba yaga sabuwar number ce Aka rubuta good morning my suld mate Tsaki yayi yacigaba da abin yakeyi Suhailace tamishi kusan kullum sai ta mishi massage Ita kuma Aymana kira take dayake ita tana da private number dinsa Sai yaga dama yake dagawa Idan baiga dama ba kozata kira sau hamsin ba zai dauka ba *Next page* *Tofa masu karatu koyazata kaya Ga wadannan gidaje guda biyu Wato Aymana da suhaila Kowacce da tunanin ta akanshi Kubiyo ni ummu afan dan yanzu fa akafara fans duk wannan shimfidane Pls your comments is needed fans More comment more typing Ina alfahari daku over Sign by ummu afan* πŸ’» [26/06, 11:52 AM] SIS UMMY: πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€ 🎑🎑🎑🎑🎑🎑 πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€ 🎑🎑🎑🎑 πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€ 🎑🎑 πŸŽ€ *BISSIMILLAHIR_RAHAMANIR_RAHIM* *Ummu Afan the Gorgeous writer of the year ,Author of 'YAN BIYAU NE &AKWAI LOKACI* 🌟GORGEOUSE WRITERS FORUM🌟 🌟 G.W.F🌟 *Home of gorgeous, intelligent and expert writers we are the best among the rest* I DEDICATE THIS PAGE TO YOU MOM IMAN &HANIFA love your comment sis Allah yabar zumunci 😘😘😘😘😘 πŸŽ€ *AL'AMIN DAGASH* *PAGE* 3⃣ DAD din Al'amin zaune a office dinsa shida wasu baki da yayi suna tattaunawa Can yaji alamun sakon waya yashi go phone dinshi Sai yaduba yaga sakon wani general meeting ne na manyan mutane Wanda za a yi a gudanar a garin Abuja nan da sati uku azama cikin azumi kenan Dan nan da sati biyu za akama azumi Bayan ya salla mesu ne yadauki wayarshi yakira amininsa alhaji Dan asabe yace kasamu sako kuwa Alhaji Dan asabe yace na maganar meeting ko Dad din al'amin yace yes hakane Wai nan da 3 weeks cikin azumi kenan ko Alhaji Dan asabe yace kwarai kuwa Yace to Allah yakaimu ****** Bayan sati biyu Dagash da iyayensa suna zaune a falonsu suna kasafin zakkan da zasu cire sukai masallaci Inbanda zakka ba abinda suke yi wa talaka wanda zasu jidadi shima zakkan inaga Dan dole ne yasa suke fitarwa Suna mugun kyamar talaka sosai Dad yakalli mom din al'amin yace hajiya Aisha kaman nawane zasu isheki hidiman azumi da ma sallah baki daya murmushi tayi tace konawa kaban nasan zasu isa Murmushi yayi Dan yasan wayonta baya taba cemata ta yanke kudin dazai ba ta tafada sai dai tabarshi da zabinsa Yakalli hajiya zabbau yace kefa hajiya zabbau nawa kike da bukata tabata rai tace 10 million murmushi yayi yace OK zan miki transfer a accounts dinki Tace bakatambayan na yara ba Daddyn al'amin yamata wani kallo yace da kekadai mezakiyi da million goma keda yarinkine zan tura miki kimusu abinda suke da bukata Al'amin dai kala baice ba danshi kam dama sai suyi magana sau Dari baice komai ba Mom din al'amin tace am al'haji kaga bikin nan dad matsowa yakeyi kasan Bayan sallah ne da sati biyu Yakamata acikin azumin nan zamu Dubai da ni da suhaila da Aymana kowacce ta hado lefenta da kanta abinda ransu yakeso su dauka koya kagani Dad din Al'amin yace badamuwa afara nema muku visa sai kuje ko azumi da sati dayane ko Tace yauwa hakan yayi Daddy ne ya kalli Dagash dayake ta danna wayarsa kaman baya jinsu Yayi murmushi yace kai son anya kuwa baka da ciwon magana kuwa tunda muka zauna muke ta magana amma kai bakace komai ba Dagash yayi murmishi yace dad to mezance komai kayi yayi ai Dad yace to ya maganar order din shaddo din danasa ayimana zadai kasa ko karkasa nayi asarar kudina fa Dan suna da tsada kuma akalla zau kawo har yadiddika kusan talatin na mana order nida kai Kuma is over 5 million kaga kuwa ba banzan yadi bane da kake siya dubu hamsin dubu sittin DAGASH yayi dariya yace kai dad meyasa zaka bata kudin ka haka Bayan kasan basawa zanyiba Mom tace aikuwa baka isaba auren ka guda kasa kananan kaya a a badaniba shiga zakayi me kyau Dan ina buri sosai a wannan biki Allah dai ya nuna mana DAGASH murmushi yasake wanda har kumatunsa suka lotsa sosai Dan sai yayi murmushi suke lotsawa nashi Yace kai mom rigima yatashi yayi hanyar waje abinshi Mom tayi murmushi tace kagani ko yagama rainani wai nice ma rigimar gabadaya Dad murmishi yayi yace ai gaskiyarsa ne kedin wasace tace au harda kaima kabi bayansa Takaicine Yakama hajiya zabbau ta tashi tayi cikin gida fuuuuuiu Tana ta nanata kayan daya musu order nasawa kawai ajiki shine wai har na million biyar kuma wai guda talatin kenan Gaskiya tana danasanin rashin samun 'da namiji da Alhaji su'ad Dubi fa yadda yake rawan jiki akan komai daya shafi Al'amin ***** Washagri akatashi da azumin RAMADAN Al'amin ne zaune a office dinshi yana aiki sai akayi nocking door yace yes come in Akashigo bakowabace sai Vicky Yana ganinta ya hada rai yace who ask to come with out my permission Cikin sanyin jiki tace am sorry sir wallahi nazo nace maka ina son zanyi tafiyane zan je garinmu Nayi takiran wayarka baka dauka that's why I decided to come here and meet u Ya watsa mata harara yacigaba da aikinsa Vicky dai ta gaji da tsayuwa shikuma bece tazauna ba Kuma idan tazauna tashiga uku dashi harsai yabata umarnin zama suna haka Zayyad yashigo ganin Vicky a office din yasashi kallon DAGASH yace man Ana azumin ma baza bar wani abunba Dagash ko dagowa beyiba ballan tana zayyad yasamu amsarsa Zayyad yayi murmushi yace yaufa abin sun motsa Sai daya gama abinda yakeyi yadago ya kalli Vicky yace oya fada mishi abinda ya kawoki office din nan Vicky ta kalli zayyad tamishi bayani yace OK I understand yajiyo yacigaba da kallon dagash yaga shima shiyake kallo Dagash yace Dan iska kaji abinda yakawota ko zayyad yace a naji abinda fada min amma kasan jin dai dole yadda kuma ba dolebane ko yakarasa yana dariya Dagash yace kar Allah yasa kayarda ma mana Dan uwarka Zayyda yayi dariya Abinshi Dagash ya kalli Vicky yace jeki zan miki transfer ta account tace nagode Sai anjima koya kalleta tana fita tayi gidan saurayinta daman karya take taga lokacin azumine yazo ba ma.ganin AL'AMIN zatayi ba harsai Bayan sallah to itakuma bazata iya hakurin one months ba shiyasa kawai suka shirya da saurayinta zasutafi gida shakawa tunda duk yan Enugu ne su Zayyad yace ya dagash zakaje meeting din nan kuwa Dagash ya ce a a idan dady ma yaje ai ya wadatar mezanje namusu Zayyada yace nazata zakajene ai Nima na shirya amma tunda bazaka ba shikenan normal ne wai kunyi waya da Faisal kuwa Dagash yace nadai ga miss call dinshi dazu ina son sai na koma gidan zan kirashi Zayyad yace ai kaji matsalata dakai wai muma sai ka nuna mana halin naku 'ya'ayan sarauta Haba ai kafin yarufe baki Al'amin yadauki trowing pillow akasa ya wurgeshi dashi Zayyad yayi dariya yace ai kaji kuma gashi bakason gaskiya **** Suhaila zaune itada mom dinta suna rubuta abinda suke bukata a game da shirye shiryen bikin Sallama sukaji mom ta amsa driver din gidan su AL'amin ne yagaishe da mom da harda suhaila amma suhaila bata amsa ba yace daman hajiyace ta aikoni nakawo wa suhaila wanann Yabasu mom ta bude taga Visa ne da passport Tace zata kira taka muku bayani mom din suhaila tace to agaisheta Yana fita suhaila ta hau murna tace waw mom Allah yakashe yabamu wallahi zasuga diban kayan hauka dazanyi Mom dinma tace au da kiragama mana ayi bake ai zagewa zakiyi kidebi abubuwa masu tsada baruwanki da kudin sunyi yawa zasu iya biya Nima kimana tsaraba nida kannanki Suhaila tayi murmushi tace karkidamu mom ai kema akwati daya zanzaba miki na fitan biki Shewa sukayi kaman wasu kawaye suka tafa abinsu duniyar tamusu dadi **** AYMANA kuwa da Visa dinta ya iso hanun ta itama murna sunyi sosai ganin anga na banza Mom dinta tace tare zasuje itama zataje sayan kayan kitchen din amarya haka kuwa akayi akashirya tafiya harda ita Ranar rabara Yakama takwas ga watan Ramadan a ranar ne su mum din Al'amin da su suhaila da aymana da mom dinta suka wuce Dubai Washagari kuma su dad suka dauki hanyar abuja shida amininsa dad din zayyad Mota daya suka dauka driver kawai yajasu suka tafi batare da security ba Dad din zayyad yace suje kawai amota basai sun jirgiba Dadyn al'amin tunda yake ya manta rabon da ya je abuja amota a DAGASH AIR LAND suke tafiya amma wannan karon dai yabi ra ayin abokin nashi alhaji Dan asabe suka tafi a lafiyyan mota me tsadar gaskiya sai da aka dauko bakanike yasake ma motar check up mekyau ya tabbatar musu ba matsala Kafin suka dau hanya ba a son ran dagash sukatafi a mota ba Ganin daddyn

Chapter 2 of 18