Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
muhimmanci a gurinsa Baidau lokaciba yakawo aikar ganin dagash din baya falon yasa yashiga ciki yakai mai Dagash yace Dan Allah karkayi nisa katsaya a kusa Dan zan iya nemanka yace to yallabai Shima yashiga cikin masu jimamin duk da baisan abinda kefaruwaba duk dai yaga manyan mutane ne Zayyad ne yayi nasarrar ganin anty tadawo hayyacinta Tana farfadowa ta tashi tana banson ganinshi Natsaneshi karkubari yazo kusadani Zayyad yace anty kikwantar da hankalinki a asibiti kike Cikin tsawa tace kamatsa min a hanya nawuce bazan zauna ba wallahi Tafiya zanyi zayyad ganin kaman bata hayyacinta yasa yaketa bata hakuri akan tayi hakuri ruwan da aka samata yakare Harara ta watsa mishi tayi hanyar waje kai ko Dan kwali babu gashin nan hargadon baya gashi yaji gyara amma bata damu a yadda take ba ta fito abinta Dagowar da malam Abdul megadin dagash zaiyi suka hada ido anty cikin dimuwa murya narawa yace maryam Itama cikin kuka tace yaya Abdul duk falon aka mike daddy king ne yayi karfin halin cewa kasan tane Yaya Abdul yace kanwatace anty ta durkushe tana kuka mai bantausayi Yaya Abdul yafito ya matso yakama hanun ta shima yana kuka yace maryam ina kikashiga bayan barin ki gida Kindaga hankalin kowa ba inda bamu shiga nemanki ba maryam innan mu tana can balafiya tun bayan korarki da Abba yayi harta shi kanshi abban ma bashi da lafiya maryam duk adalilin rashinki Dagash ne yafito rike da hanun maryam ganin mutane baisa yasake taba Sai dai ganin anty durkushe itada megadinsa yasa yayi turus maryam ta fisge hanunta tayi gurin anty tarungumeta tana kuka anty kuka yaci karfinta takasa koda maganane Alhaji Dan asabe yataso Yakama yaya Abdul yace malam Abdul kai namiji ne zamu fi samun gamshashshan bayani agunka Kowa ya nutsu bakajin kukan kowa saina maryam da anty Daddy king yace muna sararonka malam Abdul Yaya Abdul yace maryam kanwatace uwadaya ubadaya Nida yayana usman mukatafi Neman kudi cikin garin meduguri Dawowar mu mukasamu mummunnar labarin dayafaru akan maryam Munyi kuka mun nunawa mahaifinmu rashin dacewar abinda yayi kuma ya amsa laifinsa dashi akashiga Neman maryam amma shiru balabarinta Wannan dalilin yasa inna mahafiyarmu takamu da ciwon barin jiki wanda har yanzu tana fama dashi Abban mu dakadan kadan ciwo yakwantar dashi Wannan dalilin yasa mukabar garin gwaza zuwa cikin garin meduguri nan ma zaman badadi ga marasa lafiya har biyu da muke dasu Akamana kwatancen wani memaganin gargajiya a kano Nan mukazo haya muka kama kasancewar yayan mu usman yasamu wani megida dayabashi mota yake tukawa to shiya yasa yaya usman yayi amfani da kudinsa ya kama mana haya gaba kidaya gidan kuwa Kowacce mace da dakinta agidan baruwanmu da nuna banbanci Ana haka watarana nazo wucewa naga anrubuta a neman gate man wato megadi kenan nan naturo application dina Allah dai yabani nasara megida Al'amin yadauki Yanzu nakai kusan shekara goma a asibitin nan wannanshine takai caccan tarihinmu Kowa labarin yagirgizashi sosai anty tabashi tausayi sosai hajiya kuwa inbanda hararata ba abinda takeyi Kowa yakasa magana a falon ganin haka yasa yaya Abdul yace maryam ina abinda kika Haifa bayan barinki da cikin anty cikin kuka ta sake Rungume maryam tace gatanan yaya gatanan yaya takarasa tana kuka mecin rai Gani sukayi alhaji imam yatashi cikin rudewa yace yanzu maryam kina nufin yarinyar nan yatace aikuwa kallo yadawo kanshi Mummy cikin kaduwa da jin zancen yace yaya kasan abinda kake fada kuwa Ya za ayi wannan shegiyar yarinyar bayan agabanka kaji wanta yabada labarin komai kace yarkace Cikin tsananin bacin rai alhaji imam yace ya isa haka Aisha karkisake sheganta min yarinya bashigiya bace nine ubanta Nine mahaifinta ba shegiyabace Duk Wanda kefalon maganar tadakeshi mummy jiri mekarfi ke kokarin kayar da ita dagash yayi saurin kamata yazaunar da ita Cikin sambatu mummy ta rike hanun al'amin tace Son kawunka ya haukace kaje kaduba minshi Dan Allah jama'a kutai makeni yadawo hayyacinsa Alhaji imam yayi gyaran murya yace acikin hayyacina nake Aisha kece bakisani kuma a duk duniyar Wanda mukasan zancen mu goma ne cas Yarana da na aikasu dauko maryam agarinsu su hudu Sai kuma waliyyina da nata dakuma ladan Saikuma ita maryam din sai abokina alhaji sudais saikuma ni kaina Nan yakwashe komai yafada musu Cikin tsananin rudani mummy gumi ne kawai yake tsatsstafo mata takasa magana kanta yamata nauyi sosai maganar ta girgizata Cikin kuka alhaji imam ya tsuguna gaban anty yace maryam ina rokonki da girman Allah kiyafemin wallahi ba ahalinabane kaddarace Anty cikin kuka tace banson jin maganarka dalilinka narasa komai a rayuwata kasa iyayena sunkoreni suntsine min Nashiga gararin rayuwa da rashin gata saboda ba abinda zakafa min nayarda dakai Cikin kuka alhaji imam ya kalli maryam karama yace 'yata kiyafemin nasa muku ciwo azuciyarku Maryam tajuya mai tanaa kuka takasa magana bata kaunar ganinshi ma ita Yaya Abdul cikin kuka yakalli alhaji imam yace Ashe daman Kaine kayi sillar shigar ta gararin rayuwa alhaji Ka aureta bada izinin ta Dana iyayentaba saboda zalunci na masu kudi Daddy king yace haba Abdul kai yakamata ka tayashi bata hakuri da Neman afuwa Shigowar su Aymana da suhaila da iyayensu sunji labarine sukazo gulma Guru suka samu can kusa da hajiya zabbau tashiga basu labari daga farko Sai yanzu daddyn dagash yayi magana yace maryam labarinki akwai tausayi acikinta Wanda nariga nasanidama Amma meyasa kikabari shedan yayi galaba akanki kika aikata abinda kikamin Alhaji imam yace meta aikata Caraf hajiya zabbau tace kwarto takawo daki Alhaji imam yace karya ne wallahi sati daya nayi da maryam na fahimci hallinta bazata aikataba Daddy yace haba imam yazaka ce haka bayan nagani nakuma ji Alhaji imam yace kasake bincike Megadin gidan daddy yashigo shida yan sanda rike da kwarton Megadi yace kugafarceni alhaji tunda ana wai kwarto aka kama agidan nasan badai ta gate ya wuceba Yasa nayi tunanin ta kofar baya yafito shiyasa nayi sauri zagayawa yayi dai dai da lokacin da wannan saurayin take fitowa na damkeshi nabawa security shi Sun mishi duka sosai yace turo shi akayi aikuwa kowa yadau salati a falon hajiyar suhaila tace wallahi bamu yarda ba anbashi kudine kawai Dan ya karyata Alhaji Dan asabe yadaka mata tsawa yace ya isa haka hajiya Zayyad dai kunya yakamashi ganin abinda mum dinsa tayi Hajiya zabbau zatayi magana daddy yadaka mata matsawa Mummyn aymana dai zufa yagama wanketa tas Jiki yadau rawa dagash matsowa yayi kusa da kwarton nan yazabga mishi mari yace yimaga wasu mutane ne suka turoka Cikin sauri yace hajiya zabbau Falon yadau salati anty asiya tafashe da kuka itada shafa'atu saboda takaicin abinda ummynsu ta aikata Nan da nan kwarto yayi bayanin komai yadda suka tsara shida ita Kowa yakadu a falon hajiyar zayyad da mum din aymana duk sunyi tsuru tsuru suna tsoron kar hajiya zabbau ta tona musu asiri tace harda hadin bakinsu aciki Daddy duk dauriyar sa saida yazubar da hawayen rabuwa da anty saboda mace mace ta gari wacce dalilinta yafara ganin haske a rauwarsa Gashi tashi daya ansa ya rabuda ita rabuwa ta har abada Dan babu yadda za ayi tadawo gidansa saki uku yamata Cikin kuka yace zabbau kincuceni kincuci kanki ina mai tabbatar miki kema bazan barki haka banzaba Hajiya zabbau tace Dan Allah alhaji kayafemin wallahi zuciyace hakan bazata sake faruwaba Saiji sukayi daddy yace nasakeki saki uku karkisake kikoma gidana daga asibitin nan Cikin razananniyar kara tace shikenan nashiga ukuna Na wa yasameni Dan haka wallahi kowa ma sai asiransa ya tonu Nan hajiya zabbau ta tona asirin kowa alhaji Dan asabe yayi salati yace au yanzu hajiya duk wannan abinda ake kullawa kece silla Kije nasakeki saki daya bazan iya zama da mai hali irin nakiba Daddy King kam dama ga zuciya cikin zafin rai yayi wa mum din aymana itama saki har uku yace wallahi yayi danasanin hada zuri'a da ita Ya kalli dagash yace ina son kasake aymana yanzun nan saboda uwarta tafara girba abinda tashuka idan ta waye gari taga daga ita har yar tata zaurawa ne hakan zaisa sugane rayuwa umarni nake baka ba Neman shawararka nakeba Dagash kuwa daman jira yake Zaiyi magana daddynsa yace baza ayi ahakaba kabarsu Allah yashiryesu Daddy king yace kabarni yaya Dan Allah karka hanani alhaji Dan asabe yace kamata yayi kabashi umarni yasakesu gaba daya saboda hakan zaikowa musu sanin rayuwa dama tare sukaje gidan kuma tare zasu bari saboda mugun hali na iyayensu mata Muryar anty sukaji tanacewa alhaji kacucemu sanadiyar abinda ka aikata gashi kasa yadawo wa kamillaliyar 'yata Wanda na Dade ina tattalinta Rana daya yatashi a banza Alhaji imam dake zaune jinabinda anty tace hankalinsa yatashi yace nashiga uku mekike nufi da wannan Kalmar Anty cikin kuka tace ina nufin Allah yayi wadan da kazalinta sakkayya tahanyar yiwa yarka ciki Yace innalillahiwainnanirraihinraju'un allahumma ajirni fimusibatihi wakalifni khairun minha Tabbas abinda kayi sai ammaka Wanda yafishi imma nasharri ko na alkairi Bansan inada yarinyaba amma cikin second dasanin hakan sonta ya nunku acikin zuciyata ina son 'yata nayi danasanin aykata abinda na aykata har yau gashi an min ninkin Wanda na aikata wannan jarabawace daga ubangiji nakuma karba Anty tace maryam ina son kifada min waya miki ciki maryam kuka yakwace mata batasan amsar da zata bayarba Dan batasaniba Kaman daga sukaji ance nine Nawa maryam ciki kowa yajuya yana dagash da mamΓ ki Cikin kuka maryam tace a a wallahi karku yarda dashi yafada kawai Dan yataimakeni Asalima ranar da abin yafaru yaya bayagari yayi tafiya zuwa America Dagash yadaga hanu daya sama yace na rantse da Allah ninawa maryam ciki Kan mummy yakasa daukar tention kawai saitazube kasa asume Next page Your comment is needed Much love to your nice comments dear *Signed by ummu afan* πŸ’» [15/07, 1:13 PM] SIS UMMY: πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€ 🎑🎑🎑🎑🎑🎑 πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€ 🎑🎑🎑🎑 πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€ 🎑🎑 πŸŽ€ *BISSIMILLAHIR_RAHAMANIR_RAHIM* *Ummu Afan the Gorgeous writer of the year ,Author of 'YAN BIYAU NE &AKWAI LOKACI* 🌟GORGEOUS WRITERS FORUM🌟 🌟 G.W.F🌟 *Home of gorgeous, intelligent and expert writers we are the best among the rest* *Dedicated to sis su'adat kawar amana ina alfahari dake sosai sis inajin dadin kulawarki sosai aikaina Allah yakara dankon zumunci sosai* _Wannan sakon gaisuwa ummy Al'amin dagash group admin Allah yabaki lafiya yasa kaffarace Mun ba dadi da rashin lafiyarki sosai_ πŸŽ€ *AL'AMIN DAGASH* *PAGE* 6⃣1⃣to6⃣5⃣ Dagash yayi saurin taro mummy Anty asiya dake kuka kaman ranta zai fita tayi saurin nemo ruwa takawo mishi Kan mummy na cinyar dagash yace kiyi hakuri mummy yazama dolene nafadi gaskiya saboda Nima ba ason raina hakan yafaru ba kaddarace Kafin yakara magana Aymana ta taso taje gurin daddyn ta tace kagani ko daddy kunga abinda muke fada muku daman munfada adakinsa take kwana baka yarda ba Wani razanar nan tsawa taji andaka ma dagash cikin tsanin bacin rai yace duk abinda yafaru aikece sila sanadiyar abinda kika aikata hakan yafaru Mummy ce tasake fashewa da kuka ta kalli daddyn Al'amin cikin kuka tace alhaji kaga abinda duk yadawo kaina ko Kaga yadda Allah yake al'amarinsa ko tabbas nayarda ba maiyi sai Allah Ashe abin duk a gindina yake Ashe duk kaina zai dawo tasake fashewa da kuka tace YAYANA da DANA Sai kuka duk wadda kefalon bawanda mummy bata bashi tausayiba sai anty da zuciyarta yadake sosai al'amin yace mummy pls stop crying Nima bayadda kike zatobane mummy dalilin maryam nagyara rayuwata maryam kaddarace ki yarda Dani Kallon takaicin da daddyn dagash yake mishi yasa dagash yaji badadi yace dadi Ba laifi nabane daddy ya daga mishi hanu ba abinda za akacemin Amanar Dana baka kenan asha baza iya rike min amana ba kenan Ashe zaka iya aikata hakan akan kan yar ywarka shafa'atu ko bazaeefa kenan Dagash ya gigice saboda yaji maganar daddynsa ba dadin sauraro Daddyn king yace ya isa haka yaya Prince yimin bayani meyafaru kafin faruwar hakan Nan yakwashe komai yafada musu Ran daddy king yabaci sosai ya kalli aymana yace bazan tsine mikiba kar abin yafi haka amma duniya ce ummu aymana kije gaki gata ya kalli mummyn aymana cikin bacin rai yace kin bata min yarinya bazan taba yafe miki ba Aymana cikin kuka tace wallahi daddy Nima ba laifina bane mummyne tace kaini gidan boka wai akan amin maganin da zaisa Yaya yadaina sauron kowa saini sai yadda mukayi dashi Yazama ko mummynsa yaji bayason gani Saini Daddy da alhaji Dan asabe suka dau salati daddy ya kalli dagash cikin bacin rai yace AL'AMIN ina maka umarni da kasaki Aymana yanzu anan umarni nabaka ba yardaka nake nema ba Dagash ganin Daddy King baitaba kiransa da sunansa na yasa yasan tabbas dagaske yake Daman shima hakan yake nema Yace nasaketa saki daya Aymana ta rusa ihu tace daddy Dan Allah kayi hakuri yamaidani wallahi ina sonshi Daddy king yace Allah yamaka albarka Sai yanzu Alhaji imam yayi magana saboda halin dayake ciki Yace bawanda yayi sanadiyar komai saini Al'amin baka da laifi Ko bakai ka aikata hakan ba dama sai ninkin abinda na aikata yadawo min Sai banso yadawo min akan kamillaiyar 'ya ba amma ba komai Allah yafimusanin abinda yasa yayi hakan nayi nadamar abinda na aikata wallahi Nayi danasanin abinda nayi gashi yau komai yadawo minsabo 'yata da Dan kanwata Wanda nafiso a rayuwata Allah kenan Shiyasan hikiman yin hakan Alhaji sudais yace kayi hakuri abokina Allah yagafarta mana gaba daya Anty datake aikin kuka maryam kwance akan cinyarta zazzabi yarufeta sosai kuka kawai suke sosai Anty ta daga kan maryam ta ajiye a kasan carpet ta karasa gaban mummyn dagash Ta tsunguna tace hajiya ina fatan yanzu kinga matsiyata da dabbo binda idon ki Na tabbatar yanzu dai bawani sauran bashi tsakanin mu donkinga matsiyatan da idon ki Anty na kuka tace ina fatan kinga asalin maryam kice asalinta kinci mana mutunci kintozartamu Duk saboda muna talakawa marasa abin duniya marasa gata kin kyamacemu kin nuna muba mutane bane kece kawai mutum To ina fatan a yanzu kinga matsiyacin uban maryam dakika nema ko Mummyn dagash dai bata iya magana saboda kuka da danasanin abinda ta aikata wa anty da maryam Ashe maryam jininta bata saniba take ta cin mutuncinsu Anty ta kalli hajiya zabbau tace kekam ba abinda zance miki tunda ga sakayya ma kinfara gani Ta karasa gaban daddyn Al'amin ta durkusa ta fashe da kuka tace alhaji ba abinda zamuce dakai sai Allah yasaka maka da gidan aljanna Kasomu a lokacin da ake kyamarmu ka kaunace mu kasu turta mu daga ni har 'yata Wallahi wallahi alhaji ban ji zafinka ba kokadan saboda kowaye Yakama matarshi da wani a haka hukuncin da kayanke zai yanke Kayafe laifukan Dana maka a iya zama dakai mungode sosai Allah yakara arziki Daddy hawaye ne ya sauko mishi yana ta kokarin kar hawayen ya sauko amma ina yariga yasauko yayi rashin mata tagari yama kasa magana Kaman daga sama anty taji anacewa Yakama ta mutashi muje Dan saura awa daya a daura auren Anty tajuya takalli me maganar auren taga daddyn King ne tace aure kuma Alhaji Yace a ai babu Wanda ya isa ya hana daurin auren nan sai Allah saboda kutashi mutafi Anty tayi murmushi tace kayi hakuri alhaji za a iya daura na sauran amma banda maryam bazan taba yarda da auran ta da al'amin don dama Ba ason raina Dana mummynshi za ayiba Idan har auran kukeso kuwa maryam tace kuna da ikon aura mata koda driver zan amince amma ba al'aminba Cikin tsanain gigicewa Al'amin yace Haba anty mena miki haka da zaki rabani da rayuwata lokaci daya Anty tace baka min komai Ba al'amin amma inason na nunawa mummynka muma muna rana talaka ba matsiyaci bane shima akwai abinda za a nema agurinshi har akasa samu Dan kudi basa sayan komai Ta kalli yaya Abdul tace tashi muje ka kaimu gida gurin innata naganta na nemi gafararta Daddy King yace a a maryam kibari akaiku anty tace kayi hakuri zamuje kawai basai ankaimu ba Nan daddy yayi magana yace muje nakaiku gidan da kaina anty zatayi magana yadaga mata yace banason musu maryam Badan anty taso ba ta tasa hanu tadaga maryam a kasa sai anty asiya tayi saurin tayata suka fita zuwa motan Daddy Zayyad yace daddy suhaila fa bazatasan abinda ta aikata illabace itama harsai yasaketa Idan aka yi haka andaure mata gindi tayi ta shirme kenan Alhaji Dan asabe ya kalli dagash yace al'amin mekakejira da suhaila ne Daddy king yace abarta ai ataga aya idan me hankalice Alhaji Dan asabe yace no baza ayi hakaba Yakama ta duk a hukuntasu Saboda haka kasake ta nace Al'amin dakanshi yagama daukan zafi akan kalaman anty datace bazata aura mishi maryam taya zaifara rayuwa ba maryam Yana jin umarnin daddyn zayyad akan yasaki suhaila Yace nasaketa saki daya Suhaila tafashe da kuka takaici daddyn dagash yace duk abinda kukasa ya aikata bashine masalahaba Da kunbarshi kawai ya dau hakuri aishi babbane koba komai watarana rana komai zai wuce amma tunda haka takansance sai muce Allah yakiyaye gaba yakalli mummy yace Aisha kiyi hakuri kitashi kibar kukan haka duk abin da zaifaru yariga yafaru ba yadda muka iya Kinga koba komai kindau darasi akan rayuwa kitashi amaidake gida Ya kalli daddy king yace kutashi kuje nasan yanzu bakin sunkaraso Zanje nadawo yakalli alhaji imam yace tafiyan nan hardaku Yakama ta kutashi mutafi Alhaji imam da alhaji sudais suka tashi jiki a sanyaye suka yi gurin motarsu Mummy dai ba bakin magana Shafa'atu ta taimaka mata suka tashi sukayi motar dagash Wanda acikin zai maida mummy gida Dagash yashiga motar yakasa tada motar zayyad ne yakaraso yace koma kujera kawai barin yi driving din Dagash baiyi musuba Dan yasan bazai iya tukawa ba Yaya Abdul shiyake nunawa daddy hanya harsuka iso kofar wani gida Wanda kaf layin nan ba makaskanci a cikin jerin gidajen layin Dai dai lokacin da yaya nura yayi parking shima a mashin dinsa tsohuwa tasha wahala sosai Yaya Abdul dake cikin motar daddy yace alhamdullila ga yayan ma yadawo Cikin murna anty takama maryam suka fito daga motar Ganin motoci a kodar gidansu yasa yaya usman yatsaya Ganin wacce tafito cikin dankareyiyar mota yasa yakame agun Yace maryam itama cikin kuka tace na'am yaya zata tsuguna yayi saurin dagota yace a a mushiga ciki maryam Ganin yaya Abdul ya fito tare da alhajin dabai sain kowayeba Yasa yace a a Abdul Ashe tare kuke Yace ai dabaki ma dayawa Yaya usman yace a sannunku da zuwa bara amuku iso yakarasa cikin gidan anty suna cikin gidan taga wata mata wacce bata San ko wacece bace Matar nan tace a asannunku da zuwa baki mukayi Jin magana yasa sauran matan suka firfito ganin maryam dawata balarabiyar budurwar yarinya Yaya aliya dake jinyar inna itama tafito ganin maryam taganeta cikin tsananin mamaki tace maryam Anty takarasa ta rungume yaya aliya tana kuka itama yaya aliyar kuka take yi Maryam karama itakanta abin yabata tausayi Cikin kuka anty tace yaya aliya ina innarmu yaya aliya ta nuna mata cikin dakin Anty tashige duk yan gidan sunji mamaki jin cewa wai maryam ce wannan tadawo balarabiya haka Wasu kuma suce Ashe yawon karuwancin ya karbeta Yaya aliya ta kalli maryam karama tace karaso mana 'yata koba ' fada minba ke yar maryam ce Maryam tarungume yaya aliya tana kuka itama nan itada yaya aliya sukayita kuka Anty najikin inna tana kuka Dan inna batada maraba da gawa Tace innan mu kitashi ga maryam dinki tadawo inna kitashi Dan Allah Yaya aliya suka shigo tace ai tana jinki baki ga tana binki da idoba Maganace bazata iya ba Sai ganin hawaye sukayi yana sauka daga fuskar inna Yaya aliya tace Inna dole kiyi kukan farinciki don mucire tsammanin sake ganin maryam araye Kafin wani lokaci anwa su daddy daddy shinfida Anfito da Abba ma danshi jikinsa yafi na inna sauki Nan da nan akabayyana komai gaskiya tayi halinta Abba yafashe da kuka yace ina maryamun take matso kusadani maryam Cikin kuka anty takarasa gabanshi yadafa kanta yace maryam da ina da lafiya Dana saka gwiwo wina akasa nanemi gafara Dan Allah maryam kiyafemin yanke hukunci cikin fushi danayi Alhaji imam yasake magana yace Dan inasake Neman afuwa abisa lafin Dana aikata nine silar komai Abba yace ba komai Allah ya yafemana gana daya Kaddarace Allah ya Riga ya rubuta Yaya usman ya kalli anty yace maryam kiyafewa alhaji Tunda Allah ma ana masa lefi yana yafewa daddyn al'amin ma yace hakane maryam kita maka kiyafe masa kodan yardake tsakaninku Cikin kuka anty tace shikenan na yafe mai Allah ya yafemana gaba daya Wani sanyi da dadi da kuma rashin nauyi alhaji imam yaji yaziyarce shi Wanda yadade rabonda yaji hakan a rayuwarsa Yayi hamdala wa ubangiji Yasake godiya agaresu gaba kidaya Yaya nura yace maganar auren yarinya kuma a daura kar a daga Allah yasanya alkairi Yaya Abdul yace Nima abinda Nagani kenan Shiyasan mutuncinta zai riketa bisa amana Allah yabasu zaman lafiya Anty tace ina rokon ko andaura tarewar abarshi bayanzuba Daddyn al'amin yace ba komai maryam ai auran shine mai wuyan tarewar ko yaushe sai ta tare alhaji imam yace wa yaya usman idan babu damuwa ina son acikin satin nan zan fitar da su Abba da inna jinya kansa waje Daddyn al'amin yace wannan yayi hakan ma Allah yasaka da alkairi Yaya usman yafasheda kuka yace anya innanmu zata tashi kuwa jikin nata yayi tsannani sosai Alhaji imam yace ai rayuwa da mutuwa duk suna hanun Allah ne ballema irin wannan ciwon a kasan waje ba wani bu bane dazai gagaresu da izninin Allah Ya Abdul yace mungode Allah yasaka da alkairi yajikan mahaifa badan sun mutuba alhaji sudais yace sai mu hanzarta muje a daura auran saboda lokaci na tafiya Yaya usman yace to barin shirya Dan dawowata daga kasuwa kenan ma Bayan fitansu ne yaya aliya da anty sukayi ta bawa maryam hakuri anty tace maryam yakikeso nayi ne Nima sanin kanki ne ba ason raina hakan zai faruba Maryam cikin kuka tace anty wallahi a halin yanzu ba mahalukin da na tsana irin yaya Al'amin bana son ganinshi Dan Allah anty karkibari a daura amin aure dashi wallahi bana sonshi Yaya aliya tace Haba 'yata kiyi hakuri dan kinga ai bashi akaduba aka yarda da maganar auren ba mahaifinsane yadda ya rikeku Ba abinda zamu ce dashi sai dai Allah yabiyashi da gidan aljanna Dan haka dole kikoyi son al'amin a ranki kodan babanshi yadda ya rikeki Haka maryam ta yita rera Dan kukokinta mai bantausayi bazasu fahimci yadda take jimabane aranta Karfe biyar da rabi na yamma dai dai Akashaida daurin auren AL'AMIN SU'AD DA MARYAM AHMAD DA KUMA ZAYYAD DA AMARYASA RAHMA DA FAISAL DA AMARYASA SHAFA'ATU Masha Allah ya halarci dumbin jama'a Wanda ba a taba tsam maniba ma yazo Dagash baitaba zaton dashi za adaura ba jin auranshi akafara daurawa yasa ya sauke ajiyar zuciya yaji kaman an mishi albishir da gidan aljanna yayiwa Allah godiya daya mallaka mishi maryam a matsayin mata Zayyad ne ya karo gurinsa yana tsokanarsa yace ango kasha kamshi Dagash yayi murmushi yace wa ni kudai Kune Kunsha kamshi saboda yadda naga kanku na rawa saikace farin shiga Zayyad yafashe da dariya yace za abi na Allah ai farinshigan ne Dagash yace a fannin sunna ba Zayyad yabata rai yace dadina dakai Dan iskane wallahi kai ana sallah ai ba a magana Faisal dake bayan zayyad yace fada mishi dai Dan dama dai shikadai yarage da Vicky nikam wallahi nadade da rabuwa da wannan harkar Dagash yace karma karabu da harkan zanyi maganinka ne ai tunda gashi nabaka kanwata Zayyad yafashe da dariya yace Allah yabaki hakuri da na baka tawa kanwar amma baka rabuda Vicky ba Faisal yace fada masa dai Dagash zaiyi magana

Chapter 15 of 18