Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
center table yadauki abincin maryam ya daura akai yafara ci Cike da takaici suke kallonsa Maryam tagaji dazama tafito itama taganshi yanacin abincin hankalinshi kwance Aranta tace kai wannan mutumin akwai isa saikace nashi tazo zata shige yace ke zonan tadawo Tace gani yace zauna muci ta kallisu su aymana da suhaila kafin tadawo da kallonta kan abincin tace nakoshi Ya watsa mata wani banzan kallo dakanta tazauna tare sukayi break fast Tadauki plate direct ta wuce can kitchen din part din dagash tadebo danbun nama tafito tazo tazauna abinta tafaraci Shi dagash ma dariya tabashi yarinyar na matukar burgeshi saboda confidence dinta tashi yayi yakoma part dinshi yashirya cikin suit masu ruwan madara wato milk colour Yayi balain kyau sosai sai kamshi yake fitarwa yana kokarin kulle part dinshi maryam tayi saurin zare key din yace yadai tace kabarshi yaya zan kulle maka Kayi kyau sosai karkayi latti koba komai yaji dadin maganar maryam bai musa mataba yasake mata key din Harzai fita sai yajiyo yace kikira vitrus yagyara koina Maryam tayi murmushi tace karkadamu yaya zanyi komai murmushi yasakar mata baisan lokacin ba itama tadawo mishi da martani Suhaila da aymana suka tashi kaman wasu bosawa waisu gasu mai miji zasu rakashi har gurin mota suka rakashi amma fa bawacce tayi tunanin karbar brief case din dake hanunshi Kafin ya tashi mota aymana tayi saurin rike murfin kofar tace yaya ina bukatar kudi yakalleta a tsiyace yace waiku wasu irin dabbobine Duk zaman danayi agida bai isa kitambayeni kudiba sai da zanfita To bani dasu idan bakinsan yadda ake tambayar miji kudiba kuje kukoya Dan duk haka kuke yayi tsaki yaja motarsa yayi gaba Aymana tana shiga cikin motarta kawai ta dauka tayi gidansu Suhaila ma ganin fitar aymana itama tayi gida **** Hankalin mummuyn aymana yayi dubu to suntashi Jin wannan magana da aymana take fada mata Kiyi shiru kikwantar da hankalinki zamuyi maganinsu sudin banza Nan sukayita kulle kullensu itada mahaifiyarta ** Suhaila ma zancen dayane aikuwa mummyn zayyad tace aikuwa wallahi a wannan fagen kam bazan bariba aci kashi akaina ba dole musan nayi tunkafin lokaci yankure mana ai talaka bashida da dadi suhaila kinga amaryar daddynku itada yarta sun shanye zuciyar mahaifinku da wanku .Dan yanzu zayyad idan ba abincin wannan yarinyar ba bayacin abinci Sannan kuma komai nashi itayakesawa ai ina ganin tashin hankali agidan Saboda bazanbari kema kiji abinda nake jiba nan suma sukayita kulla abin dasu aikata *** Dagash zaune a office din companyn daddy yana dubawasu takaddu Faisal yashigo yace ya mutumina naje hospital dinka bakanan sai doctor Husain yace min kana nan Dagash yace hakane akwai wasu aiyukane danakeson na kammala su shine nazo kawai Akwai labari mana nan dagash yabashi attention dinsa Faisal yafara magana yace wallahi doctor nafada soyayya ne kuma wallahi idan bansame mataba akwai matsala Dagash ya hada rai yace wakenan fa yace kanwarka mana shafa'atu Wallahi yarinyar tana da hankali abani ita insha Allah zanbarta tayi karatunta Dagash yayi murmushi yace banshirya aurar da kanwata ga mutum irin kaba wallahi shafa'atu she is too innocent Kafin yakarasa maganar zayyad yashigo office din yace kaji Dan iska badadi kennan ni nabaka nawa kanwar ko Faisal yace a a abin ma baikaiga hakaba nidai Dan Allah babban yaya kataimakamin Wallahi na Dade da daina halin da kuke tunanin inayi kuma ina kiranku ga hanyar tsira kuzo tuba tare mugudu tare mutsira tare Dagash yafashe da dariya yace yanzu kanso kacemin karabuda su jamcy kenan Faisal sosai makuwa nifa Allah yashiryeni gaskiya shiyasa nake Neman matar are ma na aura saboda nayi tuban gaskiya Zayyad yace wallahi nima aure nakeson yi kwannan gaskiya saboda nagaji da irin rayuwar danakeyi Dagash yace kaikuma wakakeso sauda ce kokuma watace Zayyad yace kai wayake ta sauda kuma anata yar shila yar maryar daddy nakeso rahma Dagash yace what are you in sense mezaka samu a gurin karamar yarinya haka inbanda ciwonkai Zayyad yace bazakaganeba ninaga abinda nagani ai Dagash yace any way is your life amma gaskiya kaban kunya Faisal yace ai a batun soyayya ba wani kunya malam kaji Murmushi dagash yayi kawai baice komaiba yamaidakanshi jikin kujerar shi yana mamakin yadda suke ta magana akan so so Faisal yayi murmushi yace kana ganin shirme mukeyiko kaibakasan so ba saboda kai auran gata aka matako Yanayinka ya nuna kaima kana soyayya amma bakasan kanayiba bakasan shine soba Sosai maganar Faisal yaba dagash dariya duk mamakin farincikin dagash sukeyi basutaba ganinshi yana fara'a hakaba harda buga table *** Bayan isha dagash yayi parking a parking space na gidanshi ya fito yagaji matukar gajiya saboda ya aikatu yau ga yunwa da kwaso Yashiga falon ciki ciki yayi sallama ya wuce suhaila tace sannu da dawowa yace yauwa ya wuce Aymana kam fushi take dashi ko kallonshi batayiba Ba Wanda yayi tunanin karbar brief case din da rigar suit din nacikin suhaila zata biyoshi yadaga mata hanu yace banason adameni nagaji sosai i need to rest please Takoma ta zauna yana un uni yaduba aljihunsa baiga key ba yatuna yaba maryam Maryam tafito cikin duguwar rigar shadda dark green tayi kyau matuka Tayi saurin karbar brief case din da rigar hanunshi tana sannu da dawowa yaya Yace yauwa a takaice amma fa bawai Dan bata burgeshibane sarautace kawai da jinkai Tare suka shiga falon wani sanyayyar kamshi ne yadoki hancinsa yaga ko ina a gyare tsaf ba irin gyaran vitrus ba yana tsammanin zata kaima harsamane sai yaga ta ajiye a kan kujera tace sannu da dawowa kaje kayi wanka ga abinci a dining Ya gaji ne sosai ya fada kan kujera yazauna yace ki haura saman kihada min ruwan wanka Maryam tayi kaman bata jishiba Saidayasake magana cikin tsawa tayi saurin tashi tahaura tashiga bathroom tahada mai tafito Ganinshi tayi tsaye a bakin kofa yakafeta da ido Kanta kasa tazo zata wuce Yadakatar daita ta hanyar kulle kofar da key Kai tofa Next Page Your comment is needed fans Love u love your comment *Signed by ummu afan* πŸ’» [15/07, 1:07 PM] SIS UMMY: πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€ 🎑🎑🎑🎑🎑🎑 πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€ 🎑🎑🎑🎑 πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€ 🎑🎑 πŸŽ€ *BISSIMILLAHIR_RAHAMANIR_RAHIM* *Ummu Afan the Gorgeous writer of the year ,Author of 'YAN BIYAU NE &AKWAI LOKACI* 🌟GORGEOUS WRITERS FORUM🌟 🌟 G.W.F🌟 *Home of gorgeous, intelligent and expert writers we are the best among the rest* I DEDICATE THIS PAGE TO YOU MY ONE AND ONLY HUSBAND INA ALFAHARI DA KAI A MATSAYIN MIJI SOSAI ALLAH YAKARA DANKON KAUNA πŸ’–πŸ’πŸ’˜πŸ’“ ❀ _🎑AL'AMIN DAGASH FANS GROUP_ 🎑 πŸŽ€ *AL'AMIN DAGASH* *PAGE* 2⃣5⃣to3⃣0⃣ Maryam tace yaya zan wuce dagash yace koma kizauna Ta kalleshi kallon mamaki ya za ayi yace tazauna a bedroom dinshi Mehakan yake nufi kenan ita fa gaskiya tana tsoron sharrin giya Dagash yace kobaki bane sai nasake maimata miki ta durkusa a inda take ya wuce yashiga bathroom ya kullo kofar Ya nutse cikin abin wanka kawai sai yayi murmushi dakanshi yatuna da haukan da su suhaila sukeyi ne a waje Kafin yashigo yajisu suna labe shiyasa yakeson ya konasu da ruwan jikinsu tukun Yasan zuwa yanzu dai sungama tabbatar da abinda suke zargi Yayi tsaki wawayen mata kawai yarasa wacce zainema sai yarinyar karama yarinyar dayake kallo a matsayin kanwarshi Shine zasu dinga zarginsa akanta itafa suhaila hardacewa wai ta rantse yana Neman yarinyar nan duk yana jinsu Shiyasa yayi haka Dan ya tabbatar musu da zarginsu Sai daya gama yanganshi kafin yafito da maryam suka hada ido ya sakar mata harara itakuma maryam ganin a haka yasa ta juya mai baya Daga shi sai gajeran wando bugun kofar da akeyine yasa ya dau karamin towel fari Yarataya a kafada yafita Can kofar yanufa yabude wazai gani Daddy king ne baban Aymana wato memartaba kenan Dagash dayake namijin duniyane yace oh my God dad you surprise me ya rungume daddy king ya Daddy king yace zuwa bazatane my Prince yaran nan suka kirani suka fada min abinda ya Daga mana hankali Shine nace lalle zanzo naga mekefaruwane Dagash yasauke ajiyar zuciya yace mukarasa ciki dad Atare suka shiga suka zauna ya kalli mummyn aymana ya gaisheta ta amsa dakyar saboda abinda yarta tafada mata akansa Daddy yace kai kuzo nan Ashe suna lebe suka shigo suka zauna aymana da suhaila kenan Daddy yace my Prince wai dagaske ne mummunar maganar dayaran nan sukafada min Dagash yace mesukace dad memartaba yace wai akan kanwarka maryam Sunce wai kana nemanta narasa wani irin nema Dan har nafara musu fada nace kai ai mijin mace hudune sai me inka neme ta Sai kuma sukazo da sabanin haka Mummyn Aymana tace ranka yadade yakake ta kwanakwane ai yasan abinda muke nufi kafada mishi kawai Aymana tace wallahi daddy yanzu haka yarinyar ma tana cikin dakin tunda yadawo tabishi Dagash bece komai ba Dan yasan hakan ne tunda tana dakin Dad yace tashi kufito da ita tazonan aikuwa aymana ta tashi dasauri hartana cin tuntube tashiga bedroom din dagash bankada kofar tayi da karfi Ga mamakinta bata ga kowaba tashiga bathroom bata nan ba inda bata duba ba amma bataga maryam ba Tafito tace suhaila bata nan fa tashiga dayan bedroom din Kunya Yakama dad dama shiyayi zargin karya sukeyi yadda yasan Prince da tsentsini dakyar zai kula karamar yarinya kamar yarinyar kamar yarinyar amaryar yayanshi ba Cikin takaici daddy king yace kayi hakuri kaji Prince Ina ita yarinyar take tazo mutafi da ita can gidan kawai saboda gudun zargi Dagash yace dad bazan iya rabuwa da maryam ba saboda a yanzu itace madadin mummy dad Kasan bana cin abincin kowa sai na mummy amma yanzu alhamdullila yarinyar tana da tsabta sosai Daddy yayi murmushi irin nasu namayan ya fahimci abubuwa da dama a maganganun Prince Kuma yagane hakan yasa matanshi kishi harsuke zarginsa Daddy yace hakane gaskiya maryam ta ciri tuta tunda har my Prince ya amince da ita Dagash yayi murmushi kawai Daddy yabata rai yakalli su Aymana yace kunbani kunya kukuma kuma mata ace har yarinya karama tafiku sanin abinda yadace To wallahi idan Baku gyaraba zanbaku mamaki zakuce nafada muku Mummyn aymana tace to ai bacewa yayi suna mishi wani abunba Memartaba yace ai game hankali basai yafada ba yace ga abinda suke mishi ba Daga bayaninsa zaki fahimci hakan saboda muzamu koma Allah yabaku zaman lafiya akiyaye zargi saboda yana bata aure Tashi yayi dagash yabi bayansa kafin sukabiyo su har main falon kasa Daddy yace ina ita yartawa maryam dagash ya kalle kofar maryam yana tunanin kar da daddy yace tafito yasan bata nan tana sama Sai kawai maryam tafito cikin doguwar hijabinta ta durkusa har kasa tana gaida memartaba ya amsa cikin sakin fuska yace Allah yamiki albarka kinji ko Kicigaba da kula da yayanki tunda su antyn naki sunkasa Kicigaba maryam Allah yamiki albarka duk wadda yanemi yatakura miki kizo kifada min kinji ko Bakinsan gidan ba maryam murmushi kawai tayi batace komai ba mummyn aymana kam inbanda harara ba abinda take aikwa maryam dashi Daddy yaciro kudi baisan konawa bane yaba maryam yace gashi kisai ice cream ko yata Dakyar maryam takarba sai da dagash ya maka mata harara kafin tasa hanu takarba tayi godiya Hargurin mota suka rakasu Su daddy natafiya aymana da suhaila sukafara rakube rakube saboda rashin gaskiya Ga wani kallo da dagash yake binsu dashi ya shige part dinsa abinshi sosai yayi mamakin yadda akayi maryam taga ne escape door din dayake bedroom dinsa Wanda yasan idan dai ba nunawa muyayi ba bazai taba tunanin kofa bace Yawanci masu kudi sunayin saboda barayi da gobara da dai sauransu Kosu suhaila baya tunanin sun San dazaman kofar nan TV CE plat me kyau dashi bazaku taba dauka koface ba sai Wanda yake da ilimin hakan Shiyasa yayi mamaki yadda akayi yarinyar nan taiya operating din remote din TV din har ya bude mata Yarinya saikace aljana murmushi yayi kawai yashirya cikin kayan bacci ya sauka kan dining table Ya kawashe hadaddan girkin maryam yaji daddin abincin Sosai da mamakin maryam ya kwanta * Washari Yakama monday maryam da wuri tagama abinda zatayi saboda zata school Tahada wa yayanta komai takai mai dasauri tayi break tashirya cikin hadaddan uniform dinta mekaramata kyau yafito mata da yarintarta sosai Tagama dauki matches dinta kawai da biro uku bata dauki school bag ba sai tadauki Dan karamin Jakarta medogon hanu tasaka saboda yau zasu fara exam's wato waec Ta fito taga matan gidan sunfito yan aikinsu sunkawo musu break fast sunayi Tace sannunku anty suhaila taja tsaki aymana kuma ta maka mata muguwar harara Maryam tayi murmushi kawai Dan ita wallahi dariya suke bata sosai bataga aiki su a matsayinsu na matan gidaba Ita ko Dan yangar nan bataga sunayiba Agogo taduba taga time is going yasa ta tashi tabude falon dagash taga be ma sauko ba Tayi shahada ta haura sama tashiga falon sama sukayi kicibus yashirya cikin suit masu balain kyau da tsasada A ranta tace kai shidai wannan mutum kullum cikin irin wannan shigar yakeyi kodan yaga yana mishi kyau ne oho Tace ina kwana yaya yace lafiya Itama Daga wannan bata sake tace yaya naga haryanzu baka sauko bane Kuma zanyi latti yace ba driver ne Maryam tace anty aymana ta aikeshi baice komaiba yasauko idonshi akan table aikuwa yaga break fast farinciki yaji har zuciyarsa Baiyi tunanin zatayi ba tunda yaga yau Monday yazauna yafara cin abincin shi ganin yafara break yasa maryam tayi hanyar kofa Jitayi yace zonan ke Batajiyoba saboda haka kawai sai taji haushin sunan dayake kiranta wai ke saikace baisan sunantaba Tajuyo ta folding hannayenta a kirjinta tace haba yaya haryanzu wai bakasan sunana bane sai dai kacemin ke Yanayin yadda take maganar tana turo baki ya matukar burge dagash Murmushi Wanda shima kanshi baisan yasake taba Yace zonan nace ko takaraso tazauna kasa kusadashi yace wani suna kikeson nakiraki dashi Dan bazan iya kiran sunanki ba yamin tsayi Maryam ta turo baki tajuya mai baya alamun dai taji haushi aranta tace jidan rainin hankalifa wai fadan sunan maryam din yana mishi wahala Kaman Daga sama taji yace baby ya akayi jiya kika fita adakin nan jiya Maryam tayi shiru yace wai badake nake nake maganaba kikayi shiru Tayi shiru nan ma Abinda dayaba dagash mamaki shine yakasa jin haushinta saima burgeshi da hakan keyi Yace Ashe bakyason zuwa school yau kenan saurin juyowa tace toba kai kakirani da sunan yara ba wai baby Dagash dayakai cup din tea baki baisan lokacin daya dawo dashiba Dan idan yakai bakinsa to tabbas zai kware saboda shirmen yarinyar nan Yace kenan keba yarinyabace tace wace yarinya kuma yaufa zamufara exam's Dagash yace ok bazaki fada min yadda akayi kikafitoba Maryam ta ce ai kaimakasan wurin Dagash yace ya akayi kikasan yadda ake operating din wurin Maryam ta ce UNCLE JABEER ne yakoya mana Dagash baisake maganaba har yagama suka fita maryam takullo kofar tana rataye da brief case dinshi dajakarta ta bashi key dinshi Yace kibarshi a gurinki baisake cewa komaiba yafita su suhaila aka taso aka karbi brief case din hanun maryam a gadarance Maryam batayi musuba tabata ganin abin basauki sai na Allah Suna karasawa maryam tabude gaban mota tashiga ta rufe Suhaila kuma akazaga gefen miji ana mishi adawo lafiya baiko kulataba yaja mota suka tafi Dagash yajefawa maryam tambaya tahancewa waye Jabeer Maryam tayi murmushi wata kawarmu ce fareeda Ahmad Yace shima malamine a makarantar Maryam tace a a shiyake zuwa daukarta kullum kuma yana da kirki sosai Dagash yace ok daman bakaratun kukeyiba hirarku kukeyi da maza ko Maryam tajuyo a kidime saboda yanayin da yayi maganar cikin zafin rai Tace wallahi bahaka bane yaya Yaya jabeer yana kirki sosai yanaxuwa gaida daddy ma daddy sanshi Lokacin dayayi ciwo ne daddy yace driver yakaini hargidansu fareeda Da mukaje yana bacci shine fareeda tace mujira mugaisa Bayan ya tashine fareeda tasanardashi zuwanmu shine yace tashigo damu ciki Shine fa mukashiga rahama taga irin TV dakin ka a dakinshi bataganin Abu bata tambayaba tace kai amma TV nan yamata kyau bashida fadi sai tsayi shine abin yaba yaya jabeer dariya yace ai ba TV bane kawai koface na musamman shine yanuna mana yadda akeyi har yabude mana mukagani Dagash baice komaiba har suka isa cikin school din yaciro kudi yace gashi tayi lunch Tace ai inada kudi yaya kabarshi kawai ya watsa mata harara dasauri tasa hanu ta karbi kudin motar ya jabeer ce ta tsaya yakawo fareeda Maryam tayi murmushi ganin fareeda ta iso itama cikin farinciki fara jabawarsu yau Tawa yayanta sallama tafita tunda yaga tafita yaga tayi gurin motar data shigo yanzu yatsaya yake kallon ikon Allah Fareeda tafito itama suka rungume juna fareeda tace ai banzata kebace a wannan babbar mota Maryam tayi murmushi tace Allah sarki yaya nane kinsan nafada miki gidanshi nakoma Ya jabeer ne yakaraso yayi sallama maryam tayi murmushi tace la yaya kaida kanka harnaji kunya fareeda ce tatsareni da surutu ban je gaishekaba Jabeer daya tsare maryam da kallo yace karkidamu maryam yakike Tace lafiya qalau yaya ga yaya na can naga baitafi ba kugaisa Dagash kuwa yana ganin sun nufo motarshi yafige ta da gudu yabar harabar school din Maryam tace ya ilahi watakila waya yake yi yasa bai tashiba sai yanzu kuma na tabbatar baiganmu Ya jabeer yayi murmushi yace karki damu wataran zamu gaisa Nan suka mishi sallama shima yabasu kudin lunch *** Haka rayuwa tayi ta tafiya wa maryam cikin gidan yayan nata kafin wani lokaci dagash da maryam sunyi mugun shakuwa Wanda shi dagash har yana mamakin kanshi sosai A yaune maryam suke gama zana neco dinsu Alhamdullila komai yazo mata dasauki Dan maryam akwai kwakwalwa sosai she is very sharp person Soyyayya kuwa tsakanin rahma da zayyad tayi karfi tun sunayi a boye har anfara ganewa Haka shafa da Faisal kullum yana makale da waya suna hira sosai yake Allah Allah sudawo Mummy kuwa shirun da dagash yayi baimata maganar zaizo ba yadameta sosai Dan tasan dai ba banza yakizuwaba Idan tamishi magana sai yace aiki ne yamishi yawa Baisan su Aymana sunfada mata komai dayake faruwaba kawai tasamishi idone taga gudun ruwansa Anty kuwa soyayya sai abinda yakaru tsakaninta Daddy cikin anty yafito daddy yace yana ganin anty bazata komaba anan zatayi haihu bayan haihu sai takoma gida Anty dai bahaka taso ba tanason ganin yarta farincikinta wato maryam amma kuma bazata iya musu da daddy ba Dan bayan miji Dan uwa take kallon shi Hajiya zabbau tayi bakincikin wannan hukunci na alhaji sai dai kuma dayake daddy ba akawo mishi wargi yasa tayi shiru Tana ji tana gani daddy yarakosu airport su suka hau jirgin Nigeria Mummyn al'amin kuma ta hau girgin libiya Daddy kuma yakoma gurin anty tunda yagama sallamar iyalai To daddy asha amarci lafiya *** *LIBIYA* NEXT PAGE YOUR COMMENT IS NEEDED FAN'S MUCH LOVE TO YOUR NICE COMMENT *signed by ummu afan* πŸ’» [15/07, 1:07 PM] SIS UMMY: πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€ 🎑🎑🎑🎑🎑🎑 πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€ 🎑🎑🎑🎑 πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€ 🎑🎑 πŸŽ€ *BISSIMILLAHIR_RAHAMANIR_RAHIM* *Ummu Afan the Gorgeous writer of the year ,Author of 'YAN BIYAU NE &AKWAI LOKACI* 🌟GORGEOUSE WRITERS FORUM🌟 🌟 G.W.F🌟 *Home of gorgeous, intelligent and expert writers we are the best among the rest* I DEDICATE THIS PAGE TO *masoya Al'amin dagash na group din sis nerjer'at ina alfahari da yadda kuke bin novel din nan daki daki Allah yabar zumunci* πŸŽ€ *AL'AMIN DAGASH* *PAGE* 3⃣1⃣to3⃣5⃣ Mummyn Al'amin ne tana sauka driver din gidansu yazo yadauketa zuwa gida Anata murna da zuwan mummy tana zaune kusada hajiyarta Cikin farinciki hajiyarta ta kalleta tace Aisha ya naganki kekadai ina mijin nawa Mummy tayi murmushi tace ai nima kaina rabona dashi yau wata biyu kenan yana Nigeria Hajiya tayi dariya tace a megidan anfara hankali tunda har ya iya wannan lokacin batare da keba Sai fuskar mom tasauya da tuno abinda matansa suka fada mishi akanshi tsoronta kar talakawar nan suwa Dan ta kwalliya daya illa Dan ita harcikin ranta batason talaka Hajiyar mummy tafara magana tace lafiya kuwa Aisha Mummy tace lafiya kalau ya su yayane banga kowa ba Ina hajiya mami kuma naga kaman bata nan Hajiyar mummyn tayi murmushi tace kin tambayi kowa baki tambayi Imam ba mummy tace ai bangama tambayar ba hajiya kuma kozan manta da kowa bazan manta da yaya imam ba Wai hajiya har yanzu yaya imam yaki yayi aure Hajiyar mummy tace toyazamuyi da matsalar imam Yabi duk ya takura kanshi yaki walwala aikin dayake fitama Dan dole ne Kinsan Allah Aisha rabon da muga dariyar imam agidan namanta lokacin nifa ganinakeyi kaman yarinyar dayake fadi ba mutumbace aljanace Mummy tace gaskiya abin kam Sai addua Allah yakawo mana mafita Kuma fa duk inda matar nan take a yanzu dai tayi aure kusan shekaru nawa yanzu shatara fa kenan 19 years Hajiyar mummy tace nima shinagani fa aisha amma tunda kinzo za a zauna sosai ayi zama akanshi Nagaji da zaman shi ahaka Mummy tace gaskiya kam Sai anyi dagske Abu saikace shafan aljanu Can bayan sallar isha yaya nura yashigo Alhaji nura shine babban yayar su mummy ne yana da mata daya hajiya mami da yaransu Sai mebinsa alhaji Ahmed Wanda ake kiransa da imam shidai har yanzu bashida mata Kuma akalla yanzu yakai kusan shekaru 'arbain da tara zuwa hamsin ma Yayi rayuwa a Nigeria kafin Daga baya yadawo kasarsa Sai dai tunbayan dawowarsa da shekara biyu yake cikin tashin hankali kuma akan mace Wanda koma menene zamuji anan gaba Sai mummy itace kebinsa sunshaku da mummy sosai yana matukar jida ita sosai duk cikin yan uwansa kowa yasan shakuwar mummy da yayanta imam Sai kuma kannen mummy biyu mata Wanda duk suna aure a nan libiyane Wannan kenan Alhaji nura yace a a barka da zuwan 'yan Nigeria ina Dan nawa kuma Aisha mummy tayi murmushi tagaida wanta sannan tace nabarshi a Nigeria nima Daga saudiya nakaraso nan Alhaji nurace kwarai kuwa kinfada min toya hanya yamutan Nigeria Mummy tace kowa lafiya hajiya mami ta ce amma dai wannan karon zaki Dan kwana mana biyu mummyn al'amin Mummy tayi murmushi tace Kai ai sati daya zanyi zankoma amma insha Allah zanzo na huta agida nima kuma tare zamuzo da Son shima yazo yazauna cikin dangina Duk akayi dariya gaba daya Alhaji imam yayi sallama yashigo falon ganin mummy yadan saki fara kadan abinda yake mishi wuyar yi kenan Yace my sis daman kina tafe shine baki sanar daniba mummy tayi murmushi tace mamaki nakeson nabaka my brother Ya karaso yazauna kurar dayake suka shiga gaisawa Ta tambeshi aiki ya amsa da alhamdulla ina 'Dana nakaina Kodayake hafin nashigo gida ma saida mukayi waya dashi amma baisanar dani zuwankiba Mummy tace ai zaiyi tunanin kasani ne Nan hira tabarke dare yayi sosai Alhaji imam yayi bangarensa Ya kwanta bayan yagama duk wani al'ada nashi amma fa Aikin tunanin yacigaba dayi Yana cewa kigarfarceni maryam ina zanganki Dan na nemi gafarki Allah yanuna ranar dazanganki maryam nayi nadamar abinda na aikata miki yashare hawaye masu dumi dake ga garowa kan fuskarshi Can wata zuciyar tace duk inda maryam take yanzu dai atayi aure Wani zuciyar tace kai ina maryam tawace danni aka halliceta bazan iya rayuwa batare da maryam tabbas Sai dai nakoma ga Allah batare da sake yin aure ba Idan har bansamekiba maryam Tashi yayi yadauro auwala yayi ta sallah yana Neman Allah yafiyar abinda ya aikata Alhaji imam shahararren mekudine a kasar libiya sosai arzikinsa yake bunkasa tun bayan rasuwar mahaifin shiyagajeshi sosai Dan kasuwanci yakeyi sosai yafi yayanshi alhaji nura kudi nesa bakusaba Washagri kuwa suka hada meeting sosai meeting yadau zafi Dan bayadda basuyida alhaji imam akan yasamu mata ayimusu aure zairage mishi matsalar dake damunshi Yan uwanshi sunfi shi hujja Dan haka yanemi alfarmar abashi alfarmar shekara daya idan baisami wacce yake nema a shekara dayaba yamusu alkawarin zaiyi aure Ganin bayadda suka iya dashi

Chapter 11 of 18