Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
kidauko kayanki Maryam ta gwalo ido waje Wanda hakan bakaramin kyau suka kara mataba cike da shagwaba Tace yaya bazan iyaba da nauyifa sosai Tsaki ja yayi hanyar waje ya nufa suhaila da Aymana mamaki yakashesu a tsaye Suhaila tace Aymana menake gani badai kayan nata dagash yaje daukowa bako Aymana tace gashi kuwa kina gani bata gama mishi karuwanci da ido ba Maryam najinsu tace subhanallah Allah yamana tsari da wannan Kalmar Zasuyi magana Dagash nashigowa da akwatuna biyu yashiga dakin dake cikin falon dakayan ya ajiye Ya kalli maryam yace ga dakinki maza wuce ki kwanta bana son hayaniya Maryam tawuce abinta tabarsu da bake sake kallon idonsuba Aymana tace ai wallahi za ayi tashin hankali a gidan nan caf Suhaila tace gaskiya kam dasake kiga yarinya hartasamu darajar doctor da kanshi yadauko mata kaya Aymana tace wallahi ko asiyace bazai dauko wa Abu haka direct ba sai dai yasa masu aiki Suhaila tace kisani koba banzaba tunda su mummy ma suna kuka da uwarta Nan dai sukayi ta Neman mafita Washagari maryam ta tashi sallar asuba tayi sallarta tayi karatun alkur'ani megirma wayar yafara kara taga bakuwar lamba ce tadauka aiku wa taji muryar antyce Cikin murba tace antyna Nayi ta Neman layinki bansamu anty beshigaba Anty tace ai bazai shiga ba amma yanzu gasabon layina ki saving Nan sukasha hirarsu ta ya da uwa Tana kashewa shafa'atu takirata nan sukayi hira Maryam bata koma bacci ba saida tagyara dakinta tas ko ina yadau kamshi hadadan turaran wuta Kafin tafito zuwa kitchen ta shirya lafiyayyar break fast dan kadan Dankali soya sai soyayyar kwai da soyayyar bread dayaji kwai gurin suyar Saita dafa hadaddan shayinta tadauko flask mecin cups biyu tazuba tadauko tacika Irish potatoe chips tashinfida soyayyar kwai akai Wanda yasha albasa da attaruhu Tadauki kofuna biyu tasa kan tiren da spoon Haba nan da nan gida yakaure da kamshin abinci Dana turaren wuta Lokacin karfe Tara da rabi su aymana an fita gurin business dinsu dan wataran ma acan suke break Maryam taje part din Dagash falon kasa tayi sallama taji shiru sai ta je tsakiyar falon taja center table ta ajiye mai akai Tafita abinta kitchen ta koma ta hada nata tafito takai dakinta ta ajiye tashiga wanka Dagash kuwa yana tashi yayi wanka yashirya cikin kananun kaya kamar yadda yasaba Kitchen din cikin part din shi yashiga yadebo danbun nama da da snacks Ya dauki hollandia milk yasauko falon kasa yazauna idonshi kai kan center table Tashi yayi yabude da mamaki yaga abindake ciki girgiza kai yayi yasan wannan yarinyar ce Shi beci abinci masu hankali ba saina wannan chick little girl din zaici Fitowa yayi yaganta zaune a falo ta na break tayi kyau sosai sanye take cikin Riga da zani na atamfa zanin 6 piece ne ya mugun zama akugunta sosai Gashi tayi daurinta nagaban goshi tadaure gashinta da farin ribom kasancewar atamfar pink ce da fari Zane ajiki Hankalinta kwance take break fast dinta saijin maganar ya al'amin tayi acikin kunnenta Ke ni sa'an wasankine zakiyi jagwalgwalonki kikai min falo Maryam kuwa bata jiyoba sai biyo shida gaisuwa ma datayi Tace yaya antashi lafiya Yace aranshi lalle yarinyar nan ta tarainani wato magana natake ignoring Zanyi maganinki ne yace kafin nabude ido na rufe kizo kikwashe jagwalgwalon abincinki a falona Maryam najinshi tayi banza dashi abinta yakoma falon yakai dabun naman bakinsa Sai kawai suffar Maryam yake aiyanawa a ranshi yadda tayi kwaliyarta tamishi sosai yarinyar saikace aljana gata karamar yarinyar amma dakayan manya yayi tsaki shikadai Wai me yasame shine yake yawan tunanin wannan yar mitsitsiyar yarinyar Tashi yayi kawai dai yace bari dai yadansha tea kadan ya hada tea din can kuma kamshin dankali da kwai yadaki hancinsa Nan yabude yakai kadan baki aikuwa shidai bude ido yayi yaga yacinye tas yasake hada tea din yasha sosai yaji dadin abinci Yace ashedai yarinyar ta iya abinci ga tsabta dan tsabtarta yasa ya dan Dana abincinta aikuwa ba abinda yabari Danbun naman barinshi yayi ya haura sama yadauko Abu Maryam tayi sallama tashigo direct gurin abincin ta wuce tabude taga wayam ta jijjiga flasks din tea shima babu abin yabata mamaki toko zuburwa yayi Saukowarsa suka hada ido da Maryam Tace yaya banga abinci dakace nafitar ba Harara yadankara mata yayi waje abinshi tazauna kan kujerar tafara dariya kaman allah ya aiko ta har dan kwalinta yafadi bata damu ta mayarba saboda tasan bakowa Dan ta tabbatar shiya sha saboda ga cups din nan sun bata amsa Cikin dariyar tace kai amma yaya akwai pretending Abinda maryam batasaniba tunda tafara mishi dariya yafasa fitar yadawo yaji dalilin dariyarta Dagowar dazatayi suka hada ido da PRINCE AL'AMIN DAGASH Next page Your comments is needed fans Love u love your comments fans *Signed by ummu afan* πŸ’» [26/06, 11:56 AM] SIS UMMY: πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€ 🎑🎑🎑🎑🎑🎑 πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€ 🎑🎑🎑🎑 πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€ 🎑🎑 πŸŽ€ *BISSIMILLAHIR_RAHAMANIR_RAHIM* *Ummu Afan the Gorgeous writer of the year ,Author of 'YAN BIYAU NE &AKWAI LOKACI* 🌟GORGEOUSE WRITERS FORUM🌟 🌟 G.W.F🌟 *Home of gorgeous, intelligent and expert writers we are the best among the rest* I DEDICATE THIS PAGE TO YOU SIS SURRY BABY GASKIYA INA ALFAHARI DAKE OVER SIS ALLAH YABAR ZUMUNCI INAJIN DADIN NICE COMMENT DINKI KEEP IT UP ❀ _🎑AL'AMIN DAGASH FANS GROUP_ 🎑 Ina matukar alfahari da comment dinku gaskiya sosai da sosai Comment harda read more πŸ€”much love to your love and care πŸŽ€ *AL'AMIN DAGASH* *PAGE* 1⃣7⃣To2⃣0⃣ Cikin tsoro maryam ta hadiye dariyarta Dagash yace dawakike wannan dariyar Maryam cikin rashin gaskiya tace ba dariya nayi ba yaya kwarewa nayi nake tari Yace OK yanzu zakiga kwarewa idan na fasa miki jiki da belt Maryam ta gwalo ido tace nashiga uku dan allah yaya kayi hakuri bazan sakeba Taga dai tabbas dagaske yakeyi aikuwa ta tashi takoma bayan kujera Tana rokonshi yayi hakuri Shikuwa ina dariyar ta yabata mishi rai sosai dan ta rainashi zata zauna tana mishi dariya yanufoto aikuwa suka shiga zagage dakin nan Baisamu nasarar kamo maryam ba yatsaya yace kina karawa kanki lefine fa kina wahalar dani Da wayo tazo gurin kofa aikuwa tabude tayi waje da gudu dakinta ta fada ta banko kofar Sallamar da akayine ya hanashi zuwa kofar dakin Zayyad ne da Faisal suka shigo Zayyad yace kaikuma mezakayi da wannan belt din haka a hanu Dagash yace wannan Mara kunyar yarinyar mana Faisal yayi dariya yace kai Prince shine karike belt saikace zaka daki babban mutum Wannan yarinyar ka zuba mata wannan belts din ai saita suma maka Dagash yace ai maganin takenan amata dukan dazataji ajikinta Zayyad yace kokuma maganinka ba Dagash yace mekace zayyad yace bance komaiba Dagash ya kalli Faisal yace kaikuma dan rainin wayo bazaka dena kirana. Da sunan gargajiyar nan ba ko Faisal yace tuba nake ranka yadade Suka yi dariya gaba dayansu Dagash yace ya zanyi daku yadaafa kanshi Shigowar rahma yasa dagash ya kalli Faisal yace daman Baku kadai bane Wannan yar karamar yarinyar kuma daga ina kuka samota Zayyad yace kai kanwatace fa rahma yar gidan amaryar dad ce fa Tace zatazo gurin kawarta maryam shine nace tashirya nakawota Rahma ta durkusa tagaida da al'amin amma baiko daga ido ya kaleta ba saboda sarauta Zayyad yace tashi kinji rahama nemi inda maryam din take wannan yayan naku haka yake sai hakuri Dagash ya watsa mishi harara Rahma kuwa cikin ikon allah dakin maryam tanufa direct dan tafara dubawa konan ne Tana bugawa taji a kulle maryam tace waye dan tayi tunanin yaya al'amin ne Aikuwa rahma tace itace maryam ta kwalla wani ihu tabude suka rungume juna Duk yan falon idonsu yadawo kan gashin maryam Maryam tace kai amma naji dadin zuwanki yar uwa juyawar dazatayi taga su yaya zayyad aikuwa tasake rahma tayi dakin ta dauko hijabinta taje tagaishesu Zayyad yace maryam yagidan ya hakuri da yayanki Maryam tayi murmushi zatayi magana taji an damki kunnenta tace Dan Allah yaya kayi hakuri bazansake ba Yace ina wasa dake ne ta girgiza kai yace ok bakida baki ko Zanyi maganin ki tayi saurin cewa a a yaya Dan Allah natuba wallahi Yace nonsense tashi kibar nan Dasauri ta tashi tayi dakinta Faisal da zayyad sukayi murmushi Faisal for the first time a rayuwar dagash ya playing very nice game da baby Zayyad yace Dan rainin hankali ba yasamu dai dai dashi Dagash yace kuna wannan maganar fa zakuja wa yarinya duka Dan zankirata na faffasa mata jiki Zayyad yace Allah huci ran yarima Amata afuwa Dagash yayi tsaki yace kutashi mushiga konan ya muku Faisal yace a a muje dai abamu abin tabawa Dan na San mum zatayi tafiya bata barinka ba snacks da danbun nama Dagash yayi murmushi kadan dansun tuno mishi da draman su da yarinyar nan Maryam" tace rahma amma kwana zakiyi ko rahma tace wa ni baruwana wallahi kafin anty suhaila tadawo ta zazzageni kinsan munzo sodaya wai inga yar uwata daddy yasa driver yakawoni Tazazzageni harda ce agola yan cin arziki rahma ta fashe da kuka Maryam kaicin kukan yakamata tace to saimeye idan sunce miki agola kinsan Allah abinda ake miki Wanda ba amin Kawai abinda zakiyi idan anmiki kinuna su da banza duk daya suke kebaki basu amsa ba kebaki nuna musu kinji haushiba Rahma ta goge hawayenta tace kinsan agidan yaya zayyad yafi kirki wallahi har yakan daukeni yazaga dani inga gari Bayanshikam duo sauran mutan gidan basu da kirki Maryam tace karkidamu kiyi hakuri kinga nimkuma suk gidan anty shafa'atuce mekirkin gidan sosai Dan tana mugun kaunata kuma nima haka kinga wannan yayan Dan rainin wayone waishi bayason raini Koda kannenshi ma bantaba ganin yayi wasaba fa sai uban jinkai Maryam tace muna ta surutu ban baki komai rahma tayi murmushi Maryam ta tashi tabude Dan karamin fridge din dakin nata taga bakomai aciki ta fita fridge din falo nan ma babu direct kawai tayi falon yayan nata cikin sallama Bata ko kallesu ba tayi hanyar fridge din falon direct Zayyad da Faisal da dagash suka kalle juna at the same time Cikin daure fuska dagash yace ke mezakiyi anan bata ko saurareshiba tabude abinda tagani ya mugun razanata Bakomai bane face giya kala kala Dan duk ta karanta sunansu daga gefe kuma drinks ne kamansu maltina, exotic fanta ,etc Ta juya takallesu taga ita suke kallo taga gabansu duk kwalaben giyan ne Tajuyo abinta tasa hanu tadauki kwalban giya biyu zata fita dagash yayi saurin shan gabanta yace inazaki da wannan Tamishi wani irin kallo dashi kanshi baisan yazai fassara kallonba Tace zamuje musha ne nida rahma yace kuma wadan nan kadai kigani acikin fridge din Maryam tace a a ganinayi shikuma kukesha wataki la yafi dadine Yamika hanu yace banisu nan maryam tamatsa tace a a haba yaya kabarmu mana musha muma Cikin tsawa yace bakida hankali ne zakisha whisky Takalli su zayyad ta kalli kwalban dake gabansu Tace kenan yaya sai marasa hankaline suke shan wannan Babu kyau kenan me hankali yasha To shikenan zan mayar tunda na marasa hankaline Cikin bacin rai tawuce fridge din ta ajiye tadauko musu holandia milk mesanyi abinsu Bata sake kallon inda suke ba dagash kuwa kusan mutuwan tsaye yayi Da kyar yaja kafarsa yakoma Zayyad yace shikenan mutuncinmu yazube a idon yaran nan Faisal yace rana ta farko Dana fara danasanin shangiya a rayuwata Zayyad yace kaiko ni na tabbatar sai tafadawa rahma Rahma tana kallona da mutunci sosai O my God ! Yadafe kai cike da takaicin halinsu Dagash kam tsaban miskilanci bai fadi komaiba dayake cikiba karshema tashi yayai ya haura sama abinshi Maryam tashiga dakinta jiki a sanyaye tazauna rahma tace lafiya kuwa maryam kinfita bada wannan yanayinba kindawo da wannan yanayin Maryam ta kalli rahma tace rahma Ashe suyaya mashayane Rahma tadafe kirji tace mekikagani Maryam tabata labarin komai Sannan maryam tace kince yaya zayyad yana daukanki kufita ko tadaga kidaina yadda saboda babu abinda mashayi bazai iya aikatawa ba saboda wani lokacin ba a hayyacinsu sukeba Kiringa taka tsantsan da rayuwarki Rahma cikin tsoro tace insha Allah nadaina kogyaran dakin shin dayake sani nadaina Maryam tace a a karkiyi haka sai kitabbatar yanan kafin kishiga dakinshi ki gyara mishi Rahma itadai duk ta tsorata da jin wannann magana Can sukaji zayyad yanakiran rahma sufito sutafi Har gurin Mota maryam taraka rahma sukayi sallama dagash yana daga can farandar shi nasama yana kallon maryam Takomo ciki abinta direct bathroom ta wuce tayi tasake wanka tayi alwala tayi sallar azahar taroka wa yayan nata Allah yashiryesu Tasaka duguwar riga kasancewar bacci zatayi yasata tasaka duguwar rigar baccinta Ta kashe wutar dakin Dan tana baccin rana dama tasaba Saida ta tabbatar ta kulle dakinta Sannan bacci mai nauyi yadauketa Dagash kuwa yama rasa meyake damunshi Suhaila ce tashigo gidan yana ganin motarta ya yi tsaki yadauki waya yakira mummy sukayita hira abinsu Nan yadauki wayarshi da key din motarshi yafita abinshi daga gidan gaba daya Suhaila tace sannu doctor yace yauwa kawai tace inazakaje kuma daga dawowata gidan Yakalleta yace ok idan zanfita saina sanardake ko Ya wuce abinshi suhaila tace nikam wannan wani irin miji Allah yabamu haka Ace tsakaninka da miji ba gana medadi Amma shine jiya harda dauko wa wannan kodaddiyar yarinyar kaya Tayi tsaki tayi ciki Dan ta huta Maryam tashi tayi sallar la'asar tashige kitchen abinta ta dudduba taga ba nama ba kaji tasan kuma saboda ba anfani da kitchen dinne yasa ba akula anzuba komai ba Fitowa tayi taje ta aiki driver yasiyo mata kaza fresh guda daya da kayan cikin rago Nan da nan kuwa yakawo mata tashiga sarra fawa Macaroni tadafa Wanda yasha kayan lambu da kayan ciki kafin ta gyara kazarta tayi shawarma dakanta abinta Dan tana shawa'ar shi sosai Ta gama ta hada kunun ayarta Wanda madarar ruwa ta kai fridge din dakinta Komai ta kwashe takai dakinta tasamu kula mekyau sosai Dan karami tazubawa dagash abincin a ciki shawarmar kuma tasamu dish bowl me murfi tasaka aciki ta ajiye a oven ta barshi warm saboda bata bukatar yayi sanyi Tashiga tagyara dakinta ko ina yadaukamshin girki da abinci kishi ya turnuke su Aymana dake zaune a falon Suhaila tace ke zonan maryam ce zata wuce maryam kota juyo ta kara gaba abinta kaman batasan da ita akeba Aymana sarkin zuciya ta tashi tajuyo da maryam kawai ta bata mari Maryam kuwa batayi tsammaniba taji mari a fuskarta kau akuwa ta dafa gurin Aymana tace Dan ubanki kina da right da zamu kiraki agidan nan kidaga mana kai Ko kannen megidan ma basu da wannan damar bareke agola Maryam tayi murmushi takaici tace tabbas kinshammaceni kin mareni amma ina maki gargadi da babban murya karkisake kasadar daukar hanu kimareni Suhaila ta task jin amsar da maryam takeba Aymana Suhaila tace mezakiyi idan ansake marinki zaki ramane Maryam tayi murmushi tace kodaya bazan ramaba amma shiwanda nake zamanshi agidan dakanshi zai ramamin kunga kuwa ai kunji kunya tunda akan agola mikinku zai Baku mamaki Kuma kugwada kugani tayi tsaki tawuce tabarsu da mamaki Aymana tace suahaila anya kuwa Ba abinda yashiga tsakanin wannan yarinyar da yaya al'amin kuwa Suhaila tace da alamar tambaya kam Dan idan bahakaba yaushe zata samu damar fadin magana haka da kwarin gwiwa Aymana tace idan hakane kuwa munshiga uku gaskiya yakamata mu aje zuwa kasuwar nan haka muga meke tafiya acikin gidan nan idan ba ma nan Suhaila tace da dai yafikam nan suka zauna suna ta tufka da warwara Bayan sallar isha maryam ta idar da sallarta tayi adduointa datasaba sanye take cikin Riga da skirt din material ja ya mata kyau sosai Ta saka jambaki maroon colour shikenan sai giranta data gyara sai tsadaddiyar powdar din Zata fara cin abinci kenan taji tsayuwar mota ta leka window taga dagash ne Ta koma tadauki abincinshi saida tajira yashigo tukun ta bude kofarta Kallo suka bita dashi kosu dasuke mata kwalliyar maryam yaburgesu bare dagash Shawarmar tadauko tasa kan tire din tayi part din dagash Aymana zata bita suhaila tayi saurin kamota tace mezakiyi Aymana tace zanyi maganinta mezai kaita falon mijinmu inba iskanciba Suhaila tayi murmushi tace kwantar da hankalinki yanzu zai mana maganin me ruwankai ai ai takwashi abinci takai mishi a tarihin rayuwar doctor baitaba cin abinci ako inaba idan mummynshine tadafa ba Sainata zaici Dan itace wa kwantar da hankalinki Aymana tace kuma ma fa hakane to bari muzuba ido yadda zasu kwashe Maryam tana shiga ta ajiye mishi a tsakiyar falon tafito zata tafita tana fita dagash na saukowa kasa Idonshi yakai kan abincin data ajiye mishi Karasawa yayi bude nan da nan kuwa abincin ya attracting dinshi yazauna Yafara ci sosai yaci Dan bairageba yabude shawarmar nan ma yaci yasha kunun aya Yana kai baitashiba su suhaila suka shigo gulma abinda idonsu yagani yabasu mamaki kuma yadaga musu hankali ganin dagash zaune a kasa yanacin abincin Next page Your comment is needed fan's More comments more typing Voted & share *Signed by ummu afan* πŸ’» [15/07, 1:05 PM] SIS UMMY: πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€ 🎑🎑🎑🎑🎑🎑 πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€ 🎑🎑🎑🎑 πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€ 🎑🎑 πŸŽ€ *BISSIMILLAHIR_RAHAMANIR_RAHIM* *Ummu Afan the Gorgeous writer of the year ,Author of 'YAN BIYAU NE &AKWAI LOKACI* 🌟GORGEOUS WRITERS FORUM🌟 🌟 G.W.F🌟 *Home of gorgeous, intelligent and expert writers we are the best among the rest* I DEDICATE THIS PAGE TO YOU SIS SHAFA'ATU GASKIYA INA ALFAHARI DAKE OVER SIS ALLAH YABAR ZUMUNCI INAJIN DADIN NICE COMMENT DINKI KEEP IT UP ❀ Gaisuwarki dabance my twins sis Allah yabar zumunci sosai ina alfahari dake over wallahi _🎑AL'AMIN DAGASH FANS GROUP_ Jinjina agareku kawayen amana πŸ‘‡πŸΌπŸ‘‡πŸΌπŸ‘‡πŸΌπŸ‘‡πŸΌπŸ‘‡πŸΌπŸ‘‡πŸΌ Sis Ummy Ummu farhan Fatima sunusi sanata Mummyn jidder Fatima zahra Nana Suryy baby Mom imam and hanifa Mom isqah e t c Adda khady Da dai sauransu Wanda insha Allah zakuji sunan su saboda very hot comment da sukeyi 😘 πŸŽ€ *AL'AMIN DAGASH* *PAGE* 2⃣1⃣to2⃣5⃣ Cike da mamaki aymana da suhaila suke kallon ikon Allah Aymana tace menake gani yaya dagash yadago kai yamusu wani matsiyacin kallo Ya tashi ya haura sama abinshi Suhaila tace munshiga uku aymana yanzu meye abinyi Aymana tace abinyi shine muci ubanta tafada mana meke tsakaninsu kawai suhaila da aymana suka nufi dakin maryam itakuwa maryam ta baje ne tana karatunta Saboda jibi Monday zasu fara waec Sosai take jin dadin karatun yana shigarta yadda yakamata Kamardaga sama taji muryarsu aymana suna cewa sainaci ubanta sai fada min meketsakaninta da mijinmu aikuwa maryam ta tashi tayi bayan kofa Suka banko da karfi suka shigo aikuwa shigewa maryam ta falla da gudu tayi Falon dagash bataganshi anan ba ta haura saman da gudu Yayi shirin shiga wanka kenan dagashi sai gajeran wando ya daura towel a kan kafada yaji anbanko kofar dakin Maryam yagani kai va dankwali dama baigantaba gaskiya wannan yarinyar Allah yayi halillta anan tana zuwa tayi bayan dagash Kafin yakai ga tambayarta abinda yakorata su aymana sun banko kofar sunshigo Suhaila tana kokarin fisgo maryam daga bayan dagash aikuwa maryam bata San lokacin data rungume dagash din ta baya ba Itada take cikin tashin hankali ba abinda taji amma shikuwa gogan naku wani shocking yaji Wanda baitaba jinsaba Saikace Wanda mace bata taba tabashiba haka yaji Maryam tace Dan Allah yaya kabasu hakuri wallahi bansan menamusuba Bazansakeba aymana tafara surfo ruwan ashar tana saukewa akan maryam sosai maryam ta tsorata dasu saboda yanayin kerar jikin Aymana na yan dambe ne Itakuma suhaila daga zatayi zafi hanu gurin duka gashi maryam anty bata taba dukanta ba Ita wallahi zata iya lissafa dukan da akama ko school ne bare tabari wadan nan su saka hanu ajikinta Dagash yayi karfin halin janyo maryam daga bayansa ba dukanta zakuyiba gata kudake ta Tunda bakuda kunya ta gudo harnan kubiyota zakudaketa saboda kun rainani ko Yace gata kufara dukanta mana Aymana cikin zafin nama ta zabga wa maryam mari Saboda tsananin zafin marin maryam ta kwalla kara ta zube kan gadon dagash Cikin tsananin bacin rai dagash yace what Aymana raini tsakaninmu bazaiyuba Ya danko ta yakasheta da mari yadauki yaci ubanta da kyau tuntana bashi hakuri harta kasa Suhaila uwar wayo tana ganin aymana ta mari maryam ta gudu Aymana dakyar tasamu ta kwaci kanta ta gudu daga part din shi Yajiyo yaga maryam haryanzu ajiyar zuciya takeyi Yace saura ke wato bakida kunya ko yakamo kunnenta yace matan nawa kikewa raini Mekika musu harsuka hadu zasu dakeki Cikin kuka maryam tace nima bansaniba nikawai ka maidani gidansu rahma Bazan iya zama anan ba wallahi tsoronsu nakeji suna bani tsoro Dagash yaso yayi dariya saboda yadda take baganan harcikin zuciyarta ce gaskiyarta take fada Yace tsoro horo ne su dazakiji tsoaronsu inkina tsoron duka kidaina abin dazaisa sudakesu Maryam tadaga kai ta kalleshi tace haka kace yadaga mata gira yes tace shikenan nadaina insha Allah bazan sakeba Ta tashi tayi waje fuuuuuu abinta dagash yanemi guri yazauna yarasa dalilin dayasa baya iya tsawatar ya yarinyar nan Ya rasa dalilin dayasa yake iya dogon surutu akan lamarinta Wani zuciyar yace kawai Dan tana da tsabtane shiyasa Ya yarda da zuciyarshi baitaba jin jiki mailaushi irin maryam ba hanunta datasa ta rungumeshi jiyayi yafi audiga laushi ya tsinci kanshi da lumshe ido yana murmushi dakyar yaja kafarsa zuwa bathroom saboda tashi daya kasala ya dirar mai Maryam kuwa tana fitowa falon taga suhaila da aymana suna fada Aymana tana ta zagin suhaila wai zasuyi Abu tare saita zame tabarta Bazasu hada kai su yaki Abu tare ba saboda haka kowa tashi ya feshsheshi Suhaila kuma tace kinfiye saurin hanu haka kawai naga yana jibgarki sainasa baki Sosai fada da ca car baki Maryam kuwa ko kallon India suke batayiba tashige abinta Washagari maryam ta tashi ta hada lafiyayyan break fast dinta ita kadai dai cikinta tayi wanka ta shiyar cikin Riga da wando amma na India wato Indian dress Sai da tagama gyaran dakinta tas sannan tadauki break fast din tayi main falo dashi akuwa Matan gidan suna nan bata ko kalli inda suke ba ta ajiye a tsakiyar falon ta zauna akasa ta nade kafafunta Zata fara break kenan sai sukaji a nocking a kofa Maryam ganin itace karama yasa ta tashi taje tabude kofar aikuwa ganin mata tayi cikin wasu arnan shiga Maryam tace to kikekuma fa cikin gadara Vicky tace matsa min nawuce Maryam tayi murmushi tace ba inda zaki wuce wallahi dubekifa gurinwa ma kika zo tukun Ta kalli su aymana tace anty kokunsanta aymana tayi tsaki suhaila kuma ta maka mata harara Maryam tayi murmushi tace kinga wannan ya tabbatar basusankiba may be wrong address akabaki Vicky tayi murmushi tace idan kebakisanni ba aisu sunsanni sunsan karonmu dasu Dagash ne yafito jin hayaniya ganin Vicky da maryam yasa yatsaya ya rike hanu a kirji yana kallon ikon Allah Vicky tace hello sir dagash ya watsa mata harara yace you again ? Ya yakaraso cikin tafiyarsa na kasaita yanuna wa Vicky hanyar waje if i ever see in my house again kinsan sauran nonsense oya get out before a get u there Jiki a sanyaye Vicky tasha kunya tafita Suhaila da aymana kuwa sunjike da ruwan jikinsu ganisukeyi kaman maryam zata kwashi kashinta a hanu sai ganisukayi ya rufe Vicky da fada Dagash yajiyo kan maryam ya watsa mata harara yace wato kekuma bazakiji maganaba kowa kika dama saikin mishi rashin kunya Ya rike kun nanta yayi part dinshi da ita haba suhaila murna yakamata Ashe ba barinta zaiba Dagash kuwa yanashiga falonshi nakasa yace maza yi neel down Maryam ta zube a kasa tace to yaya mena maka kuma dan Allah yace au baki ma San abinda kikayi Tadaga kai yace meyasa bakiyi abincinba maganar yazo mata a bazata tace abinci kuma caf Nayi dakai matan ka sunmin duka beside ma ai kai kace karnasake yimushu laifi a iya sanina kuma lefin danayi kenan Dagash bakin kawai yake kallo tana maganar Baice komaiba yace ina naki abincin tace yana falo Baicemata komaiba ya tashi yafito falon su aymana yan labe suna jikin kofar sukaji alamun fitowarsa suka koma gurin zamansu Gani sukayi ya nemi guri ya zauna yajanyo

Chapter 10 of 18