You Cannot Download this book untill you login but you can read it .
Login Register
mutum ba tashikibani guri nan da wata zan daura miki aure da mutum daya acikin mane manki
Aikuwa cikin tashin hankali natashi nayi dakinmu inazuwa nafada jikin innarmu
Tace ya akayi maryama nace innan mu nashiga ukuna wallahi Abba zai aura min Wanda banaso
Inna tace kiyi shiru maryama insha allahu aliyu zaki aura
Yau idan yazo kice ina nemansa nace to innan mu Dan ina yadda damaganar innanar mu Dan tana sadaukar da farincikinta saboda yaranta
Aliyu yazo kiran innan mu
Bayan sungaisa tace mishi aliyu idan dagaske kake yakamata katuro magabatanka gashi mahaifinta har yafara shirin bada ita gawani
Aliyu cikin tashin hankali yace inna Dan Allah kar amin haka wallahi idan na rasa maryam zan iya rasa raina
Inna tace bazaka rasata ba aliyu kawai katuro magaba tanka asan abinyi
Haka kuwa duk abin abbana burinshi na aurar dani baicikaba saboda magabantan aliyu sunzo
An tsaida magana nan da wata biyu za ayi bikin mu da aliyu
Hakan yasa aliyu tafiya Neman kudi kafin lokacin yazo
Munyi bikin kawata deeje yarage saura nikadai shiyasa ma nadaina zuwa ko ina
Wata ranar alhamis ranar da bazan taba mantawa dashiba a rayuwata takarasa maganar tanakuka
Dad ya miko mata robar ruwan swan water batayi musuba tasan tana bukatar ruwan kam
Bayan tasha ruwan tacigaba da basu labarinta
Ina cikin tafiya kan hanyar zuwa islamiyyata naga wata bakar mota sun tsaya agabana naga sunbude kofar motar sunfito
Duk fiskarsu a rufe yake
Suka nuna min bindiga sukace wuce muje ganin bindiga nayita basu hakuri sukaki karshe kawai ma sai suka fesa min wani Abu
Bude ido kawai nayi naganni a wani hadaddan gida mai kyau sosai da haduwa
Kuka nakarka dashi hankalina yatashi can sai naga anbude kofar anshigo
Wani alhaji nagani fari mai mutunci dashi a fuska
Yafi zubin larabawa haka dashi
Yayi dariya yace barka da tashi yake kyakykyawar yarinya
Nace Dan Allah alhaji kaiyi hakuri kafitar dani daga gidan nan
Wasu ne suka satone daga kauyenmu
Wani dariya naga alhaji yayi yace ke yarinya dena hadani da Allah kicuceni Dan kozaki kukan jini ba kyaleki zanyiba
Tabas ninasa akawo minke gidan nan saboda tun ranar danaganki nakwadaitu da surar da Allah yamiki da kyan hallitarki duk da acikin hijabi naganki
Hakan bai hanani ganin wasu sirrika atare dake ba
Na nunawa yarana ke sukaganki shine yau nace akawo minke na huta dake saboda bani da niyyar aure a yanzu Dan da inada niyyar aure zan aureki kodan kyau da Allah ya miki
Cikin tashin hankali nace Dan Allah alhaji kar keta min haddi
Wallahi niba yar iskabace alhaji aurena ya kusa alhaji
Kabarni naje da mutuncina gidan mijina karka bata abinda nayi shekeru ina tattalinsa alhaji karufa min asiri Dan Allah
Alhaji yace wayafada miki nima ba auranki zanyiba
Ai bazan yadda na hada shimfida dakeba sai an daura min aure dake saboda kikwantar da hankalinki auren sunna zakiyi
Sannan kuma kiraya sunna da ni mijinki
Aikuwa nasake shiga tashin hankali sosai yace yanzu dare yayi amma zuwa gobe karfe tara za a daura min aure dake a masallacin anguwar nan
Zanbaki sadakin ki gobe yasa aka kawo min abinci da ruwan sha nisaboda tashin hankali ko yunwar ma da kishin ruwan bana ji
Yadda naga rana haka naga dare saboda tashin hankali ba abinda nakeyi sai salloli da addua
Dasafe karfe Takwas alhaji yashigo yace 'yanmata sunanki saboda liman ne yake zai miki wakilci
Ban dago ba bare naga fuskarshi saboda babu mutumninda natsana a duniya sama da wannan alhajin
Alhaji yayi magana yaji shiru yace toshikenan daman bana son kusantarki batare da aure. Bane tunda kinfi son hakan shikenan bari kiga aiki da gamawa yafara cire kayansa
Cikin tsananin kuka da tashin hankali nace sunana maryam
Yayi murmushin mugunta ya ce Ashe kina da wayo yarinya
Bayan daura auren Alhaji da maryam yadawo cikin gidan yabata sadakinta dubu ashirin
Bata karba ajiye mata yayi yace hakkin kine fa idan baki karba kinyi wa kanki
Har video din daurin auran yakawo mata dan ta tabbatar da andaura
Sati na daya agidan Alhaji a matsayin matarsa
Abinci inacinsa ne kawai Dan yunwa karya kasheni
Amma bawai Dan tana jin dadin komaiba
Ina zaune a falon gidan Dan Alhaji kullewa yake idan zaifita
Sai naga yadawo da wuri yabani takarda yace nasake ki saki daya
Tunda nazo gidan banyi dariyaba sai daya bani takardar sakina
Yace zan koma kasan mu saboda amin waya mama na bata da lafiya
Ina so kisa a ranki baki taba sanina ba a rayuwarki
Saboda bazaki sake ganinaba maryam
Nayi murmushi nace Alhaji nima bana fatan na sake haduwa da mutum kamarka a rayuwata
Nisakin da kamin ma yafi komai dadi a rayuwata
Sai dai kacuceni Allah ya isa bazan taba yafe maka ba Allah ya isa
Murmishi yayi yace wannan damuwarkice kinji nabaki hakuri ne to bana bukatar hakurinki
All what I know dai banyi zaman zina dakeba auranki nayi
Dakin na koma namaida kayana da yasato nidashi harda hijabin da da jakar makarnta nawa tunda nazo nafito yace yauwa ai sai an maidake tace bana bukatar sumaidani
Kafada min kawai nan inane
Alhaji yayi murmushi yace ai abinda bazaki sani ba kenan Dan haka ma ko compound din gidan nan bazakiganiba yadda kikazo hakazi koma
Banyi aune aune ba naji sunfesa min wani Abu aikuwa
Sai bude ido nayi naganni a dakin innata sunata min fiffita ancika akaina
Yaya aliya tace inna ta bude ido sunyi murnan farkawata
Ruwan zafi inna tasa aka hada min nayi wanka suka hada min kunun gyada mai dadi
Ina zaune a kan gadon innata yayuna duk sun zagayeni
Abba yashigo yace sannu maryama nace yauwa Abba sannu
Yace wai ina sukaiki ne wannan tambayar da Abba yamin yadaga min hankali Dana tuno da abinda yafaru dani
Nasan idan nafadi gaskiya Abba bazai amince min ba
Sai kawai nazabi da nayi karya akaro na farko a rayuwata
Nace Abba masu garkuwa da mutane sun tambayeni ko babana mai kudine nace musu a a nafada musu sana arka shine suka min duka suka saka naketa musu wanke wanke kullum muna dayawa Wanda aka kama amma yawancinsu iyayensu masu kudine shine sukace bazasu smdawo damu gidaba sai randa iyayen yaran nan suka kawo musu kudin da suka bukata
Ba a gama turo musu kudinba sai jiya shine duk suka fesa mana wani Abu Dan kar muga inda za a fito da mu
Abba yayi ajiyar zuciya jin cewa ba a musu komaiba
Nan da nan kowa yashiga fadin albarkacin bakinshi na ta tatsallake rijiya da baya
Abba yace Allah yarufa asiri yafita
Innan mu tace kai munshiga tashin hankalin rashinki maryama dagani har mahaifinki ba maici ba maisha
Har gurin hukama ankai maganar amma dayake bamu da gata ba awani damu a yi bincikenba
Yaya aliya tace sannu kinji maryam allah yadada karewa to ai tunda yanzu dai dama can kinsauke kinyi hadda ki hakura da zuwa islamiyyar nan
Har sai kinyi aure kuma sai ki fara zuwa na matan aure
Innan mu tace wannan haka yake tunda ai an kusa ma
Maryama na ki hakura kinji da zuwa makarantar nan har sai kinyi aure kuma sai kicigaba da zuwa makarantar ko
Na daga kai nace to innan mu insha Allah
Yaya sumayya tace ikon Allah duniya ya lalace ace sace mutum ba abin komai bane a gurinsu
Na dawo normal kamar yadda nake da sai dai ansamu canji saboda innan mu ta lura dayawan damuwar Dana ke ciki
Bayan sati uku da dawowata lokacin al'adata yayi banga komai ba hankalin yatashi sosai
Ga kuma yawan tashin zuciya danakeyi
Ina zaune innar tayi miyar taushe yana ta kamshi nikuwa cikin yana ta juyawa aikuwa sai amai amai sosai nayi inna hankalinta yayi matukartashi
Kishiyoyinta suka taso sukayi wa maryam ca suna salati wai kardai zarginsu ya tabbata akan maryam
Inna ta taimaka wa maryam sukashiga daki
akuwa uwargidan tace wallahi bazaa haifama na cikin shege a gida Anje anyi abin kunya za azo ana rurrufewa to bari malam din yadawo dole aje asibiti a tabbatar da abunda muke zargi
Innan mu gabanta yafadi ras jin sun ambaci ciki
Ya ma za a yi hakan takasance da maryam yarinyar arziki kamila baruwanta da duniya
Abba ne yashigo har sun guntsa mishi aikuwa yabanko kofar dakin innan mu yace ke maryam meke damunki tace ba komai Abba
Yace maza dauko mayafinki muje asibiti innan mu hankalinta ya tashi tace malam yadaga amai sai ace za aje asibiti kobaka yarda da yarkabace
Abba yayi murmushi yace halima kenan 'Dan yau ai ba abin yarda bane balle yarinya baliga irin maryam shekarar ta shatakwas ba aure kuma muga tafara amaye amaye acikin gida ai dole hankali ya tashi
Harda innna akaje asibitin aka min duk wasu gawaje gwaje dayawa kamata amin muka zauna jiran sakamoko
Yaya aliya da taje gidan bata samu kowaba ance duk suna asibiti
Itama tayo asibitin
Antyn maryam data kawo nan sai kuka ta fashe da shi mai tsuma jiki harda sheshsheka
Maryam kanta kuka takeyi na tausayin mahaifiyarta daddy da megari ma duk jikinsu yayi sanyi dajin labarin maryam mai ban tausayi
Daddy yace Ashe daman haka masu kudin mu suke basu da imani kokadan
Megari yace hakane abinkam ai sai addua
Megari yace maryam muna sauraronki cigaba da bayaninki
Next page
Your comment is needed fans
Love u love your comment
More comment more typing
*Signed by ummu afan* π»
[26/06, 11:54 AM] SIS UMMY: πππππππ
π‘π‘π‘π‘π‘π‘
πππππ
π‘π‘π‘π‘
ππππ
π‘π‘
π
*BISSIMILLAHIR_RAHAMANIR_RAHIM*
*Ummu Afan the Gorgeous writer of the year ,Author of 'YAN BIYAU NE &AKWAI LOKACI*
πGORGEOUSE WRITERS FORUMπ
π G.W.Fπ
*Home of gorgeous, intelligent and expert writers we are the best among the rest*
I DEDICATE THIS PAGE TO YOU MAMAN IMAM allah yabar kauna ina matukar alfahari dake over sis keep it up wajen nice comment din ki β€
_π‘AL'AMIN DAGASH FANS GROUP_ π‘
π *AL'AMIN DAGASH*
*PAGE* 9β£
Anty maryam tacigaba da ba su dad labarinta
Tace nurse tafito dauke da sakakamakon gwajin da aka min
Gaba na yafadi dan nasan yau kam asirina ta tonu ga mutanen gidan dam asibitin sai kace wacce nakashe mutum
aikuwa tana karasowa Abba yace yauwa malama yadai tace baba a sakamakon da gwajin yabamu yarka tana dauke da ciki harna tsawan wata daya
aikuwa guri yadau salati da maganganu
Yaya aliya juyawar dazatayi taga innan mu tana shirin faduwa tayi saurin zuwa ta tare ta fadi ajikinta sumammiya
Akayi cikin asibintin da ita
Abba kuwa durkushewa yayi a inda yake zaune yana salati duniyar yashiga juya mishi
Yace halima kincuceni Dakika bari na aurar da yarinyar nan kamar yadda nake aurar da yan'uwanta
Uwargidan Abba tace daman bawani saceta da akayi yawon iskancinta ta tafi za a rainawa mutane hankali wai ansaceta
Abun yasake tu zura baba na ya taso yafara kaimun duka yana tsine mun yana cewa yacireni daga cikin 'ya'yansa
Ina kuka incewa wallahi Abba bacikin shege bane ina gani yake ma na raina mishi hankali
Da kyar mutanen anguwar suka karbeni a hanun abban mu yace daga nan kuma karna koma mai gida ya koreni
Ya sallamawa duniya ni kwatata kwatata yaki yabani daman nayi magana
Haka yatasani agaba yana dukana yana korani har bakin titin garin yace natafi inda aka min ciki shiya yafeni
Nazauna agurin nacikuka nakoshi bansan inda zan nufa ba danni ba bazan iya komawa kauyen muba saboda babu Wanda zai yadda dani
Ina cikin kukana naji andafani na juyo da sauri naga ko waye sainaga deeja ce kawata tana kuka ganinta sai na rungume ta muna kuka sosai
Mijinta ne yakawota a mashin dinsa sunji abinda yafaru tace lalle tasan ina hanya sai dai yakawota kozata ganni
Nace deeja kinga yadda allah yayi daniko deeja tace karkice komai maryam wallahi na yarda dake nasan akwai wani Abu amma bazaki taba aikata abinda wannan abinda kunyar da ganganba
Nayi murmushi nace nagodewa allah dayasa nasamu mutum daya data yarda dani
Nan nabata labarin komai abinda yafaru sosai deeja tayi kuka tace kizo mukoma gida mumu su bayanin komai
Nayi murmushi nasan daman zakice haka amman sai dai kufara zuwa kumusu bayani inan idan sun amince to na yarda saikudawo mukoma gida
Cike da doki deeja takoma inda mijinta yake dan daman yana jinsu tace yakaita gida suje suwa su abban maryam bayanin komai dan allah
Suna tafiya nayi murmushi na duba lalitar innan mu Dana dauko dan daman nike sayar da komai akazo siya shiyasa tabani lalitar na daura saboda bada canji
alokacin da abban yace nafito muje asibiti dama lalitar tana jikina baciireba
Ina ganin haka nayi hamdala natashi da kyar na tari muta akace ina cikin gari
Wato meduguri kenan
Muna isa tasha akace kowa yakawo kudin mota
Bayar danawa
Daga can gefe naga kawai mota na Lodi naje nashiga mota yacika aka dau hanya
Tunda muka fara tafiya ba abinda nake tunani sai bansan ma me motar take ciki ba
Sai ji kawai nayi anacewa kowa yafito na fito natambayi kudin mota
Akafada min nabayar nakara gaba sai kuma tunanin yazomin na wai a wani garima nake
Juyawa gurin motar nayi nakarewa wa memotar kallo
Can na nufa daga gefe naga wata mata da alama akwai abin da take jira ta Tara kayanta a gefe
Namata sallama ta amsa nace baiwar allah Dan Allah nan wani garine
Tambayar Dana mata yabata mamaki dan na fahinci hakan a fuskarta
Tace yanzu kebaiwar allah Ashe bakimasan wani gari kikazoba
Na daga mata kai alamun bansaniba tace to abuja kike tarayyar Nigeria
Mamaki yacikani wai abuja
Matar tace idan bazan damuba zata min tambaya akan rayuwata dan kuma inda zanje
Nan dai na takaita mata kadan tace idan ta fahimceni dai bani da inda zanje kenan nace kwarai kuwa tace idan bazan damuba zata tafidani gidan nace nayarda
Nafara zama da anty hassana me abinci ina tai maka mata a wajen sana'arta tana bani gurin kwana da abinci sai sabulun wanki haka amma ba albashi hakan ma nagode
Ina nan ina rainon cikina har yakai watan haiuwarsa
Tsakar dare natashida nakuda anty hasssana ta kira ungurzoma dan bazata iya da tsadar asibin abuja ba
Akullum addua ta shine allah karyabani yarinya mace saboda renon 'ya mace akwai hatsari musamamn ma a wannan rayuwar danake ciki na rashin gata
Idan kuma yabani macen yabani mummuna yadda bazata ja hankalin mutane har su cutar da itaba
Na haihu lafiya na haifi 'yata kyakkyawa allah bai karbi addua taba don yarinyar harta finima sosai
Anty hassana tana tayaba kyan yarinyar gata fara Sol da ita
Nayi kuka danaga yarinyar da allah yabani saboda ina tsoron abinda yafaru dani yafaru da ita
Ranar da nacika kwana bakwai da haihuwa nawa 'yata huduba da suna na Maryam
Sosai nake kokarin kula da ita dan anty hassana kullum tana kasuwa
Nikuma sainayi arba'in zanfara zuwa nima kasuwar
Muna haka ina ta renon maryam yarinya me wayo da farinjini itama tun tana karamarta
anty hassana gaskiya ta taimaka min a rayuwata duk da bawai tana biyana albashibane
amma zanci zansha zata sai wa maryam gwanjo masu saukin kudi idan tasamu dama amma fa nima ina bautuwa a wajenta
Muna haka shekarar Maryam hudu aduniya anty hassana tafara ciwo bayan kwana biyu kuwa allah yama ta rasuwa
Nayi kukan rashin anty hassana sosai bayan makokin anty maryam narasa abin yi Gashi maryam tayi wayo kullum setamin maganan makaranta insata amakaranta
Ina zaune nida maryam ina bata abinci abaki aiki naje nayi nasamu akaban abincin
Sallama naji shugowa kawai sukayi Ashe wai dillalan gidan ne sunbani nan gobe na kwashe komai nawa zasu zuba wasu agidan ba tausayi a fuskokinsu
Shiyasa ma bansamu damar basu hakuriba
Haka washagari mukabar gidan na tattara mana kayanmu naja hanun maryam muka fita tafiya kawai nakeyi amma bansan inda zanje ba
Bamuzame koinaba sai kofarwani asibiti kawai nasa kai nashiga cikin asibitin
Har dare yayi bansamu abinda zanba maryam taciba Gashi bani da kosisi
Muna zaune kusada wata mata da alama jinya yakawota saita fito shan iska ta shimfida taburma sunata hira da masu zuwa gaisuwa
Wani katon kula ne agabansu kuma wai anemo musu almajiri yakarbi abinci
Banyi sanya ba nace musu inaso da mamaki matar ta kalleni tace to bawair allah dauka kijuye to
Jikina har bari yakeyi nadubo bakar Leda a jakarmu najuye shinkafa ne haddadiya da miya
Harda nama ma aciki
Nan naje fanfo na wanko flask nakawo mata na mata godiya kafin nadawo gurin maryam natasheta a baccin wahalar datakeyi nabata abinci sosai maryam taji dadi nagani a fuskarta
Tabani tausayi sosai kukanayi sosai saida ta koshi da kanta nadebo mata ruwa fanfo nabata tasha sai bacci kuma na shimfida mata zani ta kwanta kafin naci abinci nima
Anan muka kwana abinmu kasancewar akwai masu kawana a wajen ba Wanda yadamu damu
Inatashi naga wata guntuwar tsintsinya nashare asibintin nan tas kaman jaka
Haka dai har mukayi sati a asibitin nan kuma kullum allah baya hanamu abinci idan mutane suna Neman almajirai zankarba kuma kullum ina share asibitin nan tas
Muna zaune da maryam ina mata tatsuniya sai naga wata ma'aikaciyar asibita tazo tace baiwar allah waikizo inji likita nace nashiga uku badai sungaji damu bane zasu koremu
Nan dai nakama hanun maryam mukabi bayan nurse dinan
Muna zuwa muka zube akasa likitan ma ba musulmi bane
Dakyar hausar tashi yake fita
Yace sannu ko nace yauwa likita allah yasa ba laifi mukayiba
Yace a a no karkidamu kece mesharemana hospital kullum ko nadaga kaina yace good
Ya kalli maryam Yace beautiful girl zonan maryam taki zuwa dan bata yadda dakowa sai antynta kamar yadda take cemin
Murmushi yayi yace idan kina so zakicigaba da aikin zamu daukeki murinka biyarki zamu baki dakin dazaki zauna da yarki acikin hospital din nan
Dan farinciki ma rasa mezanyi nayi saboda dadi
Sosai ma mishi godiya yace karkidamu malama zamu ringa biyarki dubo goma kafin muga kokarinki akan aki sai mukara miki albashi zuwa dubu goma shabiyar sosai nayi godiya yace bakomai
Yacewa nurse ta Nina mata dakin dazata zauna acikin reception tace OK sir
Har munyi gaba yace am malama najiyo yace amma kiringa kula da lafiyar babynki karkibarta tacikomai a hanun mutane kinji ko sosai naji dadin shawarar dayabani
Takaimu ta nuna mana dan karamin dakin da toilet aciki da alamu ma office ne suka maidashi daki nan tace to baiwar allah ga dakin nan dazaku zauna ga toilet nan akwai ruwa aciki saiki tsabtace dakin
Sosai naji dadi itama namata godiya nashiga gyaran o koina yayi fes dashi
Likita yakirani yabani Rabin albashina wato dubu biyar wai kozan bukata naji dadi dan muna bukatar abinci
A da lilin aiki a asibitin nan nasa maryam a makaranta tana zuwa school din ta sosai mukejin dadin rayuwarmu a asibitin nan
Munaki kusan shekara goma zaune a asibitin nan munsaba da likitan nan sosai dan yana temaka mana a arayuwa kaman wani musulmi
Shekarar goma sha hudu sukayi sauka a islamiyyarsu tana Jss two sakamakon rashin shiga makaranta da wuri
Kwatsam muna zaune nida maryam tana min kitso sai mukaji hayaniyya a waje naje mukatashi gaba dayanmu mukafita wazamu gani doctor Patrick ne mukaga 'yansanda sunsashi a mota suntafi dashi
Nayi tambaya meyayi akace min wai ana zargin asibitin nan da saida sassan jiki mutane
Kuma ana zargin dasa hanunsa aciki
Nafasheda da kuka nace ya Allah kasa yazauna a matsayin zargi allah karka tabbatar da wannan Abu haba mutumin kirki irin doctor Patrick
Mukazauna cikin jimami abinda za azo a fada mana
Bayan sati daya naji wai za a rufe asibitin har ankai doctor fursuna
Haka muna ji muna gani mukarbar cikin asibin doctor Patrick dake garki village
Maryam tace anty yanzu ina zamuje nace mata sai inda allah yayi zaman abuja kam bazai mana ba saboda tsadar rayuwa
Haka muka hau motar mararrabar abuja dan inayawan jin sunan a bakin mutane
Munje kuwa alhamdullahi munkarbu dan gidan nan ina magari muka fara sauka na nemi da megari yabamu waje zamufara Sana'a shine yabamu wannan runfar Wanda muke zaune acikinta
Yanzu dai shekarar mu daya da wata biyu agarin nan
To wannan shine takaicaccan tarihin rayuwata
Takaarasa tana share hawayenta maryam matso cikin kuka ta rungume anty tace antyna allah ya isa miki allah saiyasaka miki
Danasan abinda zanji kenan na labarin mahaifina da banbiyokiba kuma ina rokonki gafara akan kiyafe na matsamiki danakeyi kibani labarin babana
Anty dai takasa magana sai kuka kawai
Megari da dad sunma kasa magana saboda tausayin maryam da yarta
Megari yace to Alhaji yanzu zabi ya rage naka akan maryam
Dad yayi murmushi yace ai wato wannan labarinta data fada min yasake samin tsananin sonta a raina
Saboda maryam zan aureki zan rike maryam tamkar 'yata zan hadata 'ya'yana narikesu tsakanina da allah
Sannan kuma bayan bikin zan dauki maryam muje garinsu dan ama iyayenta bayanin komai
Anty maryam ta tashe da kukan murna tace mungode Alhaji Allah yabiyaka duniya da lahira
Daddy yace ai bake zaki gode minba maryam nizan gode miki da kikayarda zaki aureni
Megari yace kai amma naji dadin wannan Abu Alhaji allah yasa masu kudin irinku su yawaita aduniya
Daddy yace amin amin
Abinda nake Neman alfarma niba yarobane dan haka banson maganar auren ya wuce nan sati biyu
Megari yace masha Allah hakan ma yayi amma bari muji ra'ayun malama maryam din
Anty maryam tace ba amince amma ina rokon wani alfarma da abari sai bayan maryam tayi jarabawarta na makaranta
Daddy yayi murmushi yace wannan kadai uzirinki anty tadaga kai alamun a
Daddy yayi murmushi yace ai yanzu baki da iko da maryam nikeda iko da ita a matsayina na mahaifinta saboda haka karma tasake zuwa wannan ma karanta zan canjamata
Wani a kano anty da maryam suka kalli juna maryam tace nagode daddy Allah yakara girma
Daddy yace amin yar daddy
Nan dai daddy da megari sukagama shirya komai
Daddy yace kai zakazama waliyyinta idan allah yaimu nan da sati daya zanturo kanina da abokina sukuga juna
amma yanzu inaso amatsayinka na waliyyin maryam inaso zanbiya sadakinta a yanzu
Megari yace masha Allah hakan yayi kyau sosai kuma ya nuna min kai babban mutumne alhaji baka magana biyu
Daddy yaje mota ya dauko brief case dinshi yadawo yaciro bandry din yan 1000 ya ajiyesu agaban megari yace wannan kuma kudinkuma na menene
Dady yace sadakin maryam ne dubu Dari biyarne
Yace zanturo za amaka gyaran gidan nan gone gobe insha ga cheque na 5 million kasa aljihunka
Yajiyo yace gurin maryam zanturo driver yakaiki kihada lefenki da kanji maryam 'yatama inason kimata sayayya yadda takeso
Ya tura mata kudin dake cikin brief case din
Anty kusan suman zaune sukayi itada maryam
Ganin yadda suke kallon kudin cike da rashin yadda da kuma tsoro
Megari yayi malama maryam kokinajin sunan hamshakin mekudin nan dayashara a kafafen yada labarai na duniya wato AL'HAJI SU'AD BABANGIDA
anty Maryam tace kwarai kuwa jin sunan abakin jama'a
Megari yace to yau baki Gashi
Ya nuna Alhaji da hanunsa
Anty maryam cike da mamaki tace yanzu alhaji daman Kaine wannan shaharraren mutumin amma meyasa kaboye min kanka
Daddy yace saboda ba matsayina nazo infada miki ba soyayyarki nazo nema
Nan dai komai ya kammala tsakanin anty da daddy amma fa da temakon megari dan anty dataji waye dady tace allanfur yafi karfin ta
Hartaba daddy dariya ma sosai
Daddy dakanshi yakaisu gida yace oh my God maryam daman airin wannan gidan kukeciki anty murmushi kawai tayi zatafita yace tsaya bansallamekiba
Maryam karama tafito da brief case din da alhaji ya basu cikin dogon hijabi
Tace daddy yar dady Allah yayi miki Albarko tace amin dady
Ya miki mata wata Leda yace ga tsarabarki
Maryam takarba tayi cikin gida
Daddy yace wa anty maryam to amaryata nizankoma kano yau sainasake dawowa kafin ranar daurin auren
Anty maryam kunya yakamata takasa tace to shikenan agaida yayuna
Daddy yayi murmushi