Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
sadinba Al'amin yace waiko kuma kunga yadda manyan kayan sukai mukune yakamata kucigaba sawa ai ko Yan sa ido kawai dariya sukayi gabadaya Dan sunsan suma fa ba ma'abota saka k Mayan kayan bane Dad da mom sun yaba kwalliyar Dan nasu al'amin yace mom zomuyi pic harda da dad duk suka dauka sosai hotunan sunyi kyau Nazeefa da suke gefe tace yaya nima nazo gira yadaga mata alamun yes tazo Dadi yakamata taje suka daddauka su afanan ma sukace yaya mufa yace nahana kune Suma da murna sukataso sosai sunji dadin hotuna da Dan uwan nasu ansauko daga sallar idi anci ansha ***** Saura sati daya bikin shirye shirye ta kowani bangare Yau ake shirin kai lefe akwatuna kwacce shabibbiyu amma fa dunkiyar dake cikin shabiyu dinan yafi karfin daukar hankali Dan ba abin kasa da dubu hamsin sai sama Hmmmmmmmm Next page fans Your comment is needed *Signed by ummu afan* πŸ’» [26/06, 11:53 AM] SIS UMMY: πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€ 🎑🎑🎑🎑🎑🎑 πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€ 🎑🎑🎑🎑 πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€ 🎑🎑 πŸŽ€ *BISSIMILLAHIR_RAHAMANIR_RAHIM* *Ummu Afan the Gorgeous writer of the year ,Author of 'YAN BIYAU NE &AKWAI LOKACI* 🌟GORGEOUSE WRITERS FORUM🌟 🌟 G.W.F🌟 *Home of gorgeous, intelligent and expert writers we are the best among the rest* I DEDICATE THIS PAGE TO YOU SIS NANA LOVE YOUR COMMENT ❀❀❀❀keep it up πŸŽ€ *AL'AMIN DAGASH* *PAGE* 5⃣ Dagash zaune a dakin Faisal shida zayyad suna sana'arsu wato shan barasa Zayyad yace gaskiya Faisal Yakama muyi event kamar biyar haka saboda auran dagash guda ace ba wani shirin da muka fara Faisal yace oho kadawo kan hanya kenan danayi magana cewa kayi sai yabamu hadin kai ayi komai Kai sanin kankane idan dantashi sai dai muji kunya ace mungayayyaci friends ba wani event me dadi da za a dan Shana Zayyad yace to yanzu dai yakamata mutsara komai Nan suka shiga tsare tsarensu Ba abinda suke da matsalarsa kusan komai ma companies din su dagash suna producing komai Hatta hall din da decoration din hall din duk suna da mai'akata Sannan abincin da za'aci ma yana da restaurant masu tsada kowani state amma na kano yafi yawa So order kawai zasuyi amma zayyad yace shizai biya komai Dagash ya watsa mishi wani kallo yace banyi niyar samuku baki ba amma yanzu zansa dan kunyi order a restaurant dina shine zaka biya Zayyad yace yes wannan shine gudilumawata da zanbaka please karkasake cewa komai kai ba abinda zan baka na burgeka komai kana dashi amma dai kabarni na biya su please Al'amin baisake magana ba dan bayason dogon zance Faisal yace nikuma nadau nauyin event uku Zayyad yace a a ai gaba daya events din nizan dauki nayinsu Kanemi wani abun kuma Faisal yace sai dai kawai namishi liki amma Bayan haka ai bansan me zanyi ba ***** Mom din al'amin dai uwar biki ta gayyaci hamshakan kawayenta na gida Dana wajen dan tayata murnar auran danta tilo Dagash Sosai suke shirin bikin nan dan mother's night mom tashirya wanda ba atabayi yin irinsaba a fadin Nigeria gaba daya makudan kudi take shirin narkarwa a mother's nigh din Hajiya zabbau kuwa kishi da takaicin wannan aure yasa ko alamun shirin bikin ma batayi Sai yaranta kuwa su afnan da nazeefa anko kusan kala goma suka fitar kuma duk dagash ne ya musu Yayarsu ansiya dake aure a Zaria itama ta zo bikin sosai dagash yawa kan nanshi kaya masu kyau da tsada Anty asiya itake kebin dagash ya wurin daddy itama tana murnan auran dan uwan nata sosai Ba abinda zata bashi saboda Ba abinda bai mallakaba Shiyasa kawai itama tazo da niyar manni wato liki kenan wa ango da amare Anty siya ce tashiga bedroom din Maman hajiya zabbau tace Haba ummy yanzu dan abinda kikeyi aisakisa mutane suga kaman bakinciki kike da auran yaya Duk fa abin mom din yaya bata taba hanashi yamana alkairi amma ke saiki kasa boye tsanar dakike mishi a idon kowa Toma wai muna da allah yabaki a matsayin 'ya'yane bakyaso saboda muna mata haba dan allah mummy karkibari shaidan yashiga rayuwarki mana 'ya'ya mata rahmane mummy Yaya Al'amin dan uwan mune duk abinshi shine ubanmu bai isa yacanja hakan ba Takarasa maganar tana kuka Hajiya zabbau jikinta yayi sanyi tace haba asiya wallahi banbancin da akenunawa tsakanunku da Al'amin a gidan nan yayi yawa wallahi a matsayina na uwarku dole abin yadameni sosai Asiya tayi murmushi tariko hanun hajiya zabbau tace ummy wani irin banbanci kike nufi Abinci maikyau ne dad baya bamu kokuma sutura kokuma zama yayi hira damu kokuma makarantu maitsada ne baisamuba iye ummy kifada daya dabaya mana acikin wannan ummy Hajiya zabbau tace duk abinda kika lissafo yana muku amma duk wani kadarorinsa ai na al'amin ne Asiya tace ok yanzu na gane abinda kike nufi akan dukiya ne ko ummy To ai ummy abinda bakisaniba yaya Al'amin yafi dadi dukiya nesa bakusaba Kuma dakike maganar duk dukinyar dady tana hanun yaya ai hakan shine dai dai ummy Dukiyar yaya ai tamuce dan na tabbata ba abinda zamuzo da bukata yakasa yimana ke shaidace dan allah ummy kisaki ranki ayi bikin nan kamar Bakomai Nifa ummy da nice ke har walima zanhada maikyau aci asha Hajiya zabbau ta maka mata harara tace bazanyin ba tunda ba ubana bane Asiya takunshe dariya dan ganin yadda ummy tayi harcikin zuciyarta Aymana zaune cikin kawayen ta sauda ce daman babbar kawa itace ranar dinner zata fadi biography din kawartata Sunyi anko masu tsada da kaloli na alfarma su da amryarsu Mom din Aymana itama fa kai yayi zafi anashirin aurar da ya ga Prince shirin datakeyi saiku rantse bata taba aurar da 'yaba **** Suhaila manyan mata itama hadaddun kwayenta yan boko ne zasu Mara mabata baya Sunma ansha anko kala kala nagani nafada masu tsadar gaske duk wani shirye shiryensu sunyi dan Sufi sauran amaren Mom din suhaila kuwa daman akanta zasu aurar wa shiyasa akayi shiri sosai Gidan da Al'amin zai zauna babban gidane kokuma nace mansion din sosai ya hada komai na rayuwa haryafi gidan dady kyau nesa bakusaba Bayan guraren shan iska da lambu masu bansha'awa dake kewaye da wanann gida Harda wani gurin wasan yara wanda ba irin lilon da kayan wasan daba asaba agurin harda wani dan karamin ruwa wanda akacika shida balloons domin dai wasan yara Ka kekuna kalala acikin gurin kai maikaratu zanso kuga wannan gida danake Baku labari gaskiya kudi sunyi kuka babu abu daya na Nigeria acikin kayan gidan kaf Kowa yaga gidan saiyayi santinsa Hajiya zabbau datazo itada yaranta suka ga gidan kwana tayi batayi bacciba saboda kishi Sai tafara tunanin anya kuwa ba asiri mom din al'amin take wa alhaji ba yake nunawa danta wannan mugun son ba Tafkeken falone wanda iya tsaruwa ya tsaru part hudune a ciki Kowani part upstair ne wato bene Acikin falon kowani part yake duk za ayi iya haduwa a wannan falon in fact ma tafalon kowa hanyar part dinta yake Kujeru set uku ne a falon gefe daban daban kuma kowanne fannin da kujerun suke akwai tafkeken TV ga kuma makeken dining area wanda akalla zaici kujeru shabiyu daga gefensa kuwa wani tafkeken fridge wanda ba abinda babu aciki Daga can gurin din erea din kuwa akwai wani tamfatsetsen kitchen wanda babu kayan nau far girkin dababu aciki Daga gefe kuma store na wanda acika shi da abincin da koshekara biyar zasuyi bazasu sunye Kai wani Abu sai masu kudi baruwansu abinda sukayi niyya shisukeyi abinsu πŸ€¦πŸ»β€β™€πŸ€¦πŸ»β€β™€πŸ€¦πŸ»β€β™€ Kowacce a part dinta iyayenta sun zuba mata kaya masu tsadar gaske ba karya bikin na yan karyane Kowacce tana da katon falo biyu da Ku 3 bedroom acikin part dinta sai kuma kitchen da store din abinci wanda kowacce iyayenta suka cika mata da gara Wato dai da alamu store din kansan nan na megidan nan kenan hmm sebaduniyaba πŸ€” Part uku na gidan duk iridayane sai dai daya ya ban banta sosai wato dakin megida rangida kenan Wato shi anashi part daga can gefe yayi wani daki ne ban sha'awa wanda acikin falon sa na sama zakashiga dakin kwanan yarane kai gaskiya wadan nan mutane basu San zafin kudiba harda yaran da basu zo duniyaba anriga agama hada musu komai na rayuwa komai da dakin yaran farine tas gwanin sha'awa saboda Al'amin akwai son farin Abu sosai yakeson yara arayuwrshi sai dai saboda jinkai baza a fahimci hakan ba Sai da yabada plan din yadda yakeson komai na gidanshi dakin yara maza daban na yara mata daban haka yayi su asashinsa dan gata Shikuma bedroom dinsa yana saman na biyu kenan amma shikdaine tsarin nasa haka wato two upstairs kenan na farkon na yaranshi ne harda falon duk saboda su yayi su Nabiyu kuma nashine shima akwai komai kamar yadda yake na farkon Kai gaskiya iya haduwa gidan ya hadu sosai Kuzo kuga rawar kai gurin amare suma tun da akazo musu Jere suka biyo yan Jere suka taho ***** Maryam zaune tana cin tuwa itada anty Taga anty tayi shiru tana tunani Maryam tace anty lafiya kuwa dan allah anty kidaina yawan tunani wallahi anty banajin dadin ganin ki a haka Anty tayi murmushi tace to maryam nabari ci abincinki Maryam tace kema kici tace ai inaci maryam Maryam tace yauwa anty dan allah meyasa kikaki amince dasu wanannan alhaji tunda sunce suna da niyar taimakon mune Sunzo sunzo anty kinki kulasu akwai zuwan dasukayi nakarshe ma anty harda kuka kikayi wai surabuda mu dan allah karsu sake da dawowa Anty wallahi nidai jikina yanabani kaman ba cutar damu zasuyiba dan allah anty kibasu daman su mana tambayar dasuke sonyi kinji anty na Wallahi inason ganin cikin farinciki anty na tunda nayi wayo nake ganin wahalar dakikeyi dani anty Dan Allah kibari kiji abinda alhajin nan zaice miki wataki yataimaka mana anty kisamu kema kihuta Anty tayi murmushi tace maryam haryanzu ke yarinyace bazaki fahimci komaiba amma nasan nan gaba zakisan abinda nake nufi Maryam tace ai anty wai ni har yanzu yarinyace Bayan kema kinsan niba yarinya bace kwananan fa zanshiga Senior secondary school amma kice yarinya Anty tayi dariya wanda ya bayyana kyawawan hakwaranta farare tas tace oh maryam shagwabar nan taki batayi yawa ba kuwa Yanzu dai ya hakuri kici abincinki Kiyi wanke wanke sai nagyara miki gashin ko sarkin tsoron kitso Maryam tayi murmushi wanda yasake fito da zahirin kyanta Kai maryam akwai kyau masha gata yarinya karama amma komai yaciko ajikinta Ga hips da kirijin na acike suke tam sai daga cikin ta ashafe yake kaman bata sama cikin abinci Ga Gashi hargadon baya ga baki ga santsi Ga fararen ido tas har yafi madara haske ga jerin hakorinta dai dai kaman ita tajera wakanta Ga dan siririn wushirya dayake tsakanin hakorinta ga tada gashin gira dan siriri sai kudauka cewan tana shaving ne nata haliitace daga allah Ga gashin ido wato sai kudauka ta taje salloon ne tana da round face dai dai ita Kai wallahi bazan iya lissafo muki kyau na hallitar irin na maryam ba Shiyasa a duk lokacin da anty ta kalli maryam bata samun kwanciyar hankali Tana matukar tausawa yartata Dan kyau masiface ita zata bada labarin hakan akaran kanta Tana iya bakin kokarinta ganin taba maryam tarbiya da kulawa dan ayanzu maryam ko adaki take tana cikin hijabi tariga tasaba Idan zata fita to da nikaf da suck wannan ra'ayintane Dana antynta Gidan sukasamu gidan matan aure kusan mata hudune a gidan kowacce da mijinta Sai dai kuma bandaki daya sukedashi agidan gasu da tarin yara kazamai Ranar dasuka koma gidan da zama maryam taje bandakin aikuwa da gudu tadawo kafin takaraso kofar dakinsu tafara amai saboda kazantar dake bandakin Anty ta zo hankalinta atashe tace meyasameki maryam fada min meyasameki Maryam tace anty bandakin ne wallahi bazan iya shigaba Anty tayi shiru tace daman megidan yace min badaki dayane agidan sai dai wai idan munaso tunda akwai wani bandakin zamu iya biyan kudi a gyara mana Maryam tace anty nawa yace wai zamu kashe dubu talatin nakuma bashi kudin dan haka kiyi hakuri kishiga nayau kinji Maryam tace ai anty nafasa idan naje islamiyya nayi a can Dama fitsari ne Anty tayi murmushi tace kai maryam wannan kyankyamin naki da tsafar sun yawafa inazaki kaisu haka Maryam ta yi murmushi tace ai nawa ne kawai yafito fili wallahi yadda nasanki ko nawa akasa kishiga bayin nan bazaki shigaba Anty tayi murmushi tace maryam zakiyi lattifa nidai baruwana Tafada tana komawa cikin dakin Murmushi maryam tayi tadauki hijab dinta da suck tasaka da nikaf ****** Biki yayi biki yau mom take mother's nights gaskiya bakarya mom tayi kyau sosai dan me kitso ce tazo tazubawa mom kitso in fact ma mom tayi kara'i Dan harda me kwalliya ta dauko Tazuba wani tsadaddan less ne meshegen kyau da tsada Doguwar Riga akazuba mata yasha aiki Ga nadin gwagwgwaro da nasawa akafada Gawasu zenare wato Gold kenan data zubasu wuya da hanu da kunne Hardasu mom din Aymana da suhaila tace suhada taron kawai Kowacce uwar amarya ta cigayu kaman bagobe amma fa duk cikinsu ganin mom din al'amin da irin shiigarta yasa duk suka raina Kansu kayi Mummy takira dagash a waya tace son kuna inane maza kukaraso anfara fa Dagash yace mummy muna hanya tace ok Amare kowacce anzaunar da ita a kujerarta wanda suka saka kujerar angon a tsakiya Kowacce tasha ado anci artificial make up Shigowar ango da abokansa yasa kallo yakoma Kansu duk Kansu sunsha wani hadaddan tsadaddan yadiddika sukasha Al'amin cikin wata lallausar yadi baki wanda duk yana daga cikin kayansu da daddy ya musu order Kai gaskiya yadin ya karbi jikin al'amin sosai Yasha hula akalan aikin dake jikin kayan Abokan kuma duk sunsha anko cikin farin yadi kowanne yana farinciki dan harsunfi angon ma farinciki dan shi fuskar nan a hade amma fa hakan bashi ya hana kyanshi fitowaba Mom da kanta ta taro danta sukafara rawa aikuwa aka dau tafi RAF RAF RAF Tawa amaren alamun sutaso suma cikin yanga da kwarkwasa yanga ga uban dogon takalmi da Aymana tasaka Sai sauri suke dan kowacce tana son tsayawa kusada ango aikuwa Aymana tajita timmm akasa aikuwa kalloyakoma kanta Dan kowa yaga saurin dasukeyi Kawayen ta sukayi saurin dagota suna mata sannu kunya ne yarufe Aymana gashi suhaila tarigata isa gefen dagash dole gefen tatsaya Suhaila saiwani iyayi take itaga amaryar gefen miji Sukayanka cake dagash yayi saurin yankawa ya nufi bakin mom dinsa haba guri kaure da tafi Mom ta yanka taba dagash a baki kai gaskiya dai sunburge mutane sosai Aymana dai tunda tafadi akasa jiki yayi sanyi iyayin ya ragu Suhaila ce dai kanta yaki zama tadauki wukar ta yanka cake din kowa idonshi yadawo kanta ganin wazata baiwa cake din ai kuwa tanufi bakin DAGASH zata samishi cake wani banzan kallo yayi mata wanda batasan lokacin da cake din yafadiba cike da kunyar disgin abinda Al'amin yamata Gaskiya hartafi Aymana data fadi kasa jinkunya aikuwa Aymana taji dadin abinda yafaru dan koba komai sunyi ziro ziro kenan Mom din al'amin tace haba son meyasa kayi haka Kayi hakuri kabasu cake din mana son Next page Your comment is needed fans More comment more typing *Signed by ummu afan* πŸ’» [26/06, 11:53 AM] SIS UMMY: πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€ 🎑🎑🎑🎑🎑🎑 πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€ 🎑🎑🎑🎑 πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€ 🎑🎑 πŸŽ€ *BISSIMILLAHIR_RAHAMANIR_RAHIM* *Ummu Afan the Gorgeous writer of the year ,Author of 'YAN BIYAU NE &AKWAI LOKACI* 🌟GORGEOUSE WRITERS FORUM🌟 🌟 G.W.F🌟 *Home of gorgeous, intelligent and expert writers we are the best among the rest* I DEDICATE THIS PAGE TO YOU mummyn Jidda Allah yabar zumunci ina son nice comment din ki over sis ❀❀❀❀❀keep it up πŸŽ€ *AL'AMIN DAGASH* *PAGE* 6⃣ DAGASH yakalli mum yace no mum kibarni kawai Bana son yaran nan surainani Mom tace shikenan son karkabata fuskarka yayi murmushi kadan Takaici Yakama iyayen amare Da amaren ma gabadayΓ  Anty asiya tazo ta yanka cake din taba wa DAGASH abaki yabude bakin yace that's my sis aka dauke da tafi gabadaya haka kananshi sukabashi yabude baki yaci Abin mamaki sai akaga ya dau wuka shima ya yanka cake din yanufi bakin anty asiya dashi abin yaburge mutane yadda yanunawa kannanshi kulawa yabakowa sha'awa sosai Mum din al'amin ta yanka cake din taba wa amare sudai sunkunyata agurin ace Wai ango bazai ciyar da su cake din auransu ba sai dai uwarsa tabasu Washagari asabar akadaura auran DOCTOR AL'AMIN DA AMARENSA SUHAILAT UMAR (DAN ASABE) SAI KUMA UMMU AYMANA MUSA BABAGINDA bikin da halarci manmayan kasar nan dama wajenta Ango na hango cikin wata dakakkiyar farrar shadda da babbar Riga da hula kai gaskiya Al'amin ya hadu iya haduwa bakarya sai dai fuskar kamar kullum hakatake Ankai amare gidansu kowa ya watse yabar amare da kawayensu saboda siyan baki Can wajan karfe goma na dare amare sukaji shigowar motocin angwaye Nan da nan masu kara powder nayi masu fesa turare nayi saboda kozasuyi kasuwa Shikuwa zayyad dama tunda yaga sauda kawar Aymana yamakale mata itama kuwa nan da nan yasamu karbuwa gunta A babban falon farkon suka zauna gaba dayansu kowacce amarya na gefe daya da kawayenta Angwaye suka shigo da sallama Nan da nan kawaye kowa tashiga amsa wa da kwarkwasa Abokan ango suka zanzauna can sauda kawar Aymana tace a a ina angon Zayyad yace kanshi na dan ciwo amma yanzu zaishigo ai Aymana da suhail suka hada ido suka sakarwa juna harara Nan dai Faisal yace nawa zamubaku ne kudin sayan baki ne ko meye Zulaihat kawar suhaila 1 million is OK Nan da nan Faisal yaciro cheque yayi signed yace gashinku ai kuwa kawayen amare sukace waw sunga banza Faisal suna da niyyar tashi sai kawayen aymana su sauda sukace a a yazaku tafi Baku sallamemuba Faisal yace daban daban nefa ko tace sosai ma Yace kukuma meye balance dinku sauda tayi fari da ido tace gaskiya dai mu amaryar mu mai tsadace so 2 million zaku bayar Faisal yace OK nan da nan shima yayi signed cheque yabasu Ai kuwa su zulaihat haushi yakamasu dan ganin sunfisu samun kudi sosai Nan dai abokan ango suka fita zuwa mota kawaye suka bisu Akabar amare gaba dayansu kowacce tana jinkai Aymana ta dauko waya tashiga chart Suhaila ma haka Can wajen shabiyu na dare suhaila bacci ya kwasheta sai Aymana ita taki baccin Itama suhailar saceta yayi baccin DAGASH yashigo ko sallama baiyiba bare yasan Allah yayi tsiransu Aymana dasauri ta tashi barka da zuwa yaya Bai kalletaba yayi hanyar part dinshi tabi bayanshi Yana gaba tana baya har cikin bedroom dinshi cire kaya ya hauyi da zaishiga wanka Aymana ta zauna a bakin gadon tana jiranshi Har yafito yashirya yasaka kayan baccinsa masu kyau da kamshi Ya haye gado yaja blanket Aymana ganin bashida niyyar kulata yasa ta haye gadon itama ta kwanta Dagash yace what's zaki kwanta kusada ni shine ba wanka common shiga bathroom ki wanke dattin jikin kinne Mara kunya kawai Aymana ganin yabata damar kwanciya adakin nashi yasa bata ji haushin fadanba kokadan Cikin doki ta tashi tayi bathroom tayi wanka ta dauro towel ta fito Ya kaleta tana goge jiki yayi tsaki yajuya mata baya Tana gamawa da tawul dinta ta haugadon yatashi yace Oh my God waike wace irin dakikiyace zaki kwanta kusa da mijinki ba turare amfada miki kazami ne irinku Aymana ita abin yabata mamaki dan ammata gyaran amare haryanzu jikinta kamshi yake fitarwa Amma dai gudun karyasake narka mata wani zagin yasa taje kan gurin ajiyar turarnsa ta dauko ta feffesa itakanta tasan turaren dagash akwai dadi sosai Tazo ta hau gadon takwanta a bayanshi tashiga shafashi Ganin abinda take so kenan yasa dagash yatashi yagito mata a namijin gaske Ummu Aymana kam tasha wahala tun tana jin dadin abin hartadawo tafara fita a hayyacinta dakyar yabarta shi a hakama bai gamsar da kanshiba dan kar ya sumar musu da yarinyace yasa yabarta Shiyasa Vicky take burgeshi sosai bata taba gajiya dashi dan itama jarumace Tsaki yayi yatashi yashiga Wanda Aymana kuwa kukan farinciki take dama babban burinta tafara mallakan Al'amin amatsayin miji koba komai Tayi wa suhaila zarra kenan Yana fitowa daga wanka yafesa turare kafin yarage karfin ac ya kwanta abinshi Nan da nan kuwa bacci ya daukeshi Suhaila kuwa ta farka tsakar dare taganta kan kijerar falo Takalli inda Aymana take taga batanan sai wayarta kawai ai kuwa hankalinta yatashi tace nashiga uku Allah yasa dai yarinyar nan bata rigani shiga doctor ba Tayi part din Aymana tajishi a bude ba inda bata duba ba amma bataciki Suhaila tace shikenan nashiga ukuna tarigani wallahi haka taje part dinta tana kuka Takasa bacci can da asuba dataji fitar Al'amin salah tayi saurin zuwa part dinsa harsaman tahau ai kuwa tana zuwa tanaga Aymana tana ta bacci aciki blanket Kishi yasake turniketa kaman takashe kanta ta huta takoma part dinta tarasa abinda zatayi saita kira mom dinta tafashe da kuka tace nashiga uku mom wallahi yafisonta mom. Wallahi adakin sa takwana mummy yazanyi Mum dintace kekuma kina inakibari hakan tafaru Suhaila tafada mata yadda akayi Mom tace Yauwa wayo tafiki taki tayi bacci saiyazo kekuma kika hangame baki kina bacci ko Suhaila tace wallahi mom bada gangan nayi baccin ba Tace to yau dai karkibari tarigaki shiga dakin mijinki gwamma kuringa kwana daddaya yafi Nan dai mom din tashiga fada mata yadda zatayi Dagash yana dawowa daga sallah ya daka wa Aymana duka acinya yace oya tashi kikoma dakin ki bacci zanyi ta bude baki zatayi magana Yasa hanunshi akan lebensa yace shiiiiiii get out of my room inason nayi bacci Tunda kinsamu abinda kikeso Cike da haushin maganar dayafada Ta tashi jiki asanyaye zata fita yace heeeeee wakika barwa wadan nan tsunmo karan yakwashe miki tace tadawo takwashe kayanta tafita Tana zuwa falon ganin suhaila a zaune a falon tayi murmushi Dan yanzu zata kular da ita Waya tadauka takira sauda tace ke akwai labarifa kinga yadda mutuminki ya rikece jiya kuwa Wallahi wannan girman kan da izza nan duk na sauke mishi su jiya Wallahi yaban wahala jiya yanzu gudowa nayi kayana a ahanu Tayi shewa tace kedai bari Barinshiga daga ciki kisha labari takarsa kofar part dinta kafin tajuyo ta jalli suhaila da tunda tafara maganar hankalinta Yakoma kanta Suhaila kishin Aymana yakamata sosai amma tayi alkawarin yau itama agun mijinta zata kwana Aymana tashirya tafito itama falon da su fruit tana sha Takira mummynta a waya tace mummy aturo kuyangu guda biyu Suhaila ma tayi waya gidansu a turo mata yan aiki biyu Dukansu kafin yamma yan aikinsu sun iso Dagash kuwa bashi yatashiba sai da ake kiran sallar azahar Ya tashi yayi wanka yayi sallah kafin yashira cikin kananun kaya yafita abinshi zuwa gidan mummyn shi Yana fitowa falon ya kallesu a wilankance Yakira bitrus a waya mai akinsane ko agidan mummy shiyasa yataho dashi gidanshi Bitrus yazo dasauri yace gani sir yace Jeka gyara min part bitrus OK sir Yana fadar haka yawuce suhaila tace adawo lafiya Abin mamaki sai yadaga mata hanu daya batare da ya kalletaba Dadi yakashe suhaila Aymana kuwa kishi sai ta shi tayi hanyar waje waizata rakashi ai kafin ma takarasa haryaba motarsa wuta yayi gaba Tadawo tazauna tana hararar suhaila itama tamayar mata da hararar Da daddare kusan karfe goma na dare suhaila tafito daga sashinta cikin wasu arnar kayan bacci masu matukyau da tsari yana da naciki yana kuma da nawaje Aymana cikin doguwar Riga Arabian gown Suhaila tazauna tana taunar chewing gum saiga dagash yashigo suhaila da sauri ta tashi tana mishi sannu dazuwa Bai kulataba dan daman abin zuwa zuwa ne Ya wuce part dinsa yasa key yabude dan daman bitrus kawai yabarwa spire key din part dinsa saboda gyarawa Yana shiga suhaila na binsa Itama dai adakin nashi ta kwana kuma itama ba irin wulakancin da bai mataba Haka rayuwar gidan dagash yakasance suda Kansu suka raba kwana ba aikin daaukeyi acikin gidan saboda kowacce da mai aikinta Bayan sati biyu da auran dagash Daddyn dagash yana zaune a falonshi hajiya Aisha tashigo tace daddyn Al'amin yanzu

Chapter 4 of 18