Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
nasa ya amince yasa ya hakura shima Yanzu babban damuwasa shine inda zaici abin buda baki Dan jiya ma da mom tayi tafiyar nan yasha wahala sosai Daddyn sane yamishi coffee yasha da cake Danshi bayacin abincin hajiya zabbau bare na nakannanshi wato yaranta kenan Shiyasa daddy ya je da kanshi yadafa mishi coffee da cake da dambun naman da momy tabar wa daddy yadinga bawa al'amin Sai kace wani karamin yaro shifa al'amin inabanda wanka da zuwa office da kuma business dinshi bai iya yiwa kanshi komai ba shiyasa da mom dinsa tayi tafiya yakeshan wahala daddy ma yasha Dan zaice sai daddy yadafa mishi abinci da kanshi tun dady be iya dafa indomie da coffee ba har koya yazama gwani Dan ko ayanzu mummy tayi tafiya daddy ne yake hidimar al'amin na abinci In bahakaba bazaici ba Shiyasa yaji duk hankalinsa yatashi to ga daddyn ma yayi tafiya shima sai gobe zai dawo yazai kenan yau Zayyad ne yasa al'amin a gaba shida Faisal suna ta dariya Ya bata rai yace wai Ku Dan uwarku wakuke was dariya haka abin kutausaya min shine zaku min dariya Sai da mummy tace zata tafi dani naki saboda naga da wadan nan yaran zasu Dayanzu duk banshiga matsala hakaba aikuwa wanann maganar ma dayayi dariya suka sake yi Faisal yace yanzu Dan Allah dagash Dan mummy tayi tafiya saitace zata tafi dakai kai Kuma yanzu harda wani Dana sanin rashin binta dakayi Faisal yace gaskiya shagwaba tamaka yawa dagash ai gwamma da za a daura ma aure da biyu at the same time Guda daya ai tamaka kadan Dan bazata iya daukan tension dinkaba guy Zayyd dariya yayi yace wallahi kam tun bayauba na nulura da Dagash ya na da mugun shagwaba Shagwaba ce tamishi yawa ba wani abuba amma badamuwa kayi lokacin Kane kana ajiye yara ai dole ka hakura ko Dagash shidai ko kallonsu beba duk damuwarshi yadda za a yi yaci abinci ne in ansha ruwa Karfe biyar da rabi su Faisal sukace dagash yatashi suje daya daga cikin restaurant dinshi zuci abinci Dagash yace Sai kundawo zayyad yace to tashi muje gida gurin mum dina musha ruwa acan Yace kuje kawai fa niba inda zanje kubarni kawai naji da damuwata Faisal yace wa zayyad mutafi kaji guy rabudashi yunwa ai kanin Dad bane bakuma kanin mom bace ai dole zai nemi abinci dai zaiyi azumi ne yazauna haka Dagash yaraka su da harara dariya sukayi sutafi abinsu Bayan anyi sallaar magriba ne dagash yadawo daga masallaci direct falon hajiya zabbau ya wuce abinda bai taba yiba Suna shan ruwa ita da yan mataan ta suka ga AL'amin kaman daga sama Rai a hade yace ke nazeeefa zonan baijira amsarta ba yayi waje abinta Nazeefa ta tashi tabi bayansa Hajiya zabbau ta kebe baki tace mutum Sai isa saikace shiya haifar min yaran Sai kace wani ubansu sha sha kawai dan giya Afanan da kanwarta suka kalli junaa sunsan ummyn tasu akwai cika baki bazata taba cemishi Dan giya agabanshi ko agaban mom dinshiba Nazeefa tace gani yaya yanuna mata fridge Basai tafada ba tasan meyake nufi zuwa tayi ta hado mishi fruit su ta kawo ta ajiye mishi Ta dauko ruwan faro ta ajiye mishi Tace shekenan hanu ya nuna mata alamun taje Zamayayi yasha kankana yaci ayaba yaci apple Amma jiyayi ba inda yake zuwa mishi Tashi yayi yaje kitchen din mom dinsa Yafara kalle kalle nan yaga gwan gwan min coffee yadauko ya ajiye yadauko shuga ya ajiye Ya instruction din yadda ake kunna gas cooker din ya kunna danshi bai taba zuwa kusa da kitchen ba Bai kiba dai lokacin yana karami amma da wayonsa kam baishigo ba Ya zuba ruwa cup daya a tukunya yadauko shugar yazuba yafi cokali biyar haka ma coffee din yazuba yafi Rabin gwan gwamin shifa duk adole saisha coffee ya baki sosai ya tafasa yajuye a cup yadauko snacks da danbun nama yafita abinshi yaje dakin shi wanka yafara shiga tukun yagabar da isha kafin yazauna ya nutsu zai sha ruwa aikuwa kurba daya ya zuka da kyau kuwa aikuwa da sauri ya zubar da nabakin nashi saboda wani azaban daci dayaji yace o my God what's this Yayi saurin shiga bathroom yayi ta brush kaman zai cire bakin Yadawo ya zauna yana maida numfashi fresh milk ya dauko yaci da danbun naman Waya ya dauka yayi try din number din dad dinsa not available Yayi na mom ringin biyu yayi mom tadauka haba nan yafara zuba mata shagwabarshi Akan yaushe zata dawo ne yagaji fa **** Fitan su daddy suka dau hanyar abuja suna Bayan mota shida aminin sa driver kuma na gaban mota shi kadai Sun kusa kaiwa Abuja dai dai wani kauye da akekira da mararraban abuja motar ta lalace abin yabasu mamaki lalle karfen nasara bashida tabbas Duk irin duba motar nan da akayi amma saida ya lalace musu Dad din Al'amin yace kagani Dan asabe shiyasa nace maka mubi jirgi amma ka insisting Sai dai mota kaga sharrin mota ko Alhaji Dan asabe yace aiba wannan bane ma damuwar hadarin da hadu gan ga gashi ba network bare mikira his Excellency ya turo mana helicopter ya karasa damu Dad din al'amin yace kuma kosun nememu bazasu samu ba tunda gabadaya ma network ya tatsya Komawa gefen titi sukayi suka tsaya ga wani ga garumin hadari da iska dayake hade gari Driver ne yace alhaji kuzo muje tacan ga runfa can kufake saboda wannan iskar Kallon juna sukayi su alhajin Basu da zabi haka sukabi driver sukayi wajen runfar nan suna zuwa driver yaje yasamu matar dayake tunanin itace mai runfar nan yace mata Dan tayi hakuri su uban gidansa zasu Dan fake Tace Bakomai bari a dauko musu benci ta kwala wa yarinyar ta kira *MARYAM MARYAM MARYAM* Ta amsa na'am anty tace dauko wa baki bencin nan su zauna tace to anty Nan yarinyar da akakira da maryam ta dauko takawo runfar nan tasa tsumma ta goge sannan tace sannunku da zuwa Abin mamaki daddyn DAGASH shiyafara amsawa cikin saukin kai yace Yauwa yarinya sannu ko Allah yayi albarka ko tace ameen antynta tasake kiranta akaro na biyu Tace maza kifara bada kunun nikuma insa hankali na nagama tuyar kosan nan kafin ruwa tsinki MARYAM tace to anty, ankira magriba Dan haka masu zuwa siyan kunu da kosai suna ta zuwa Dad din al'amin ya kalli abokainsa yace yanzu yazamuyi ne ansha ruwafa Alhaji Dan asabe yayi murmushi yace kai su'ad baka wasa da cikinka fa driver yace bissimilla ga ruwan awala Ganin ruwa sukayi a gwangwamin madara wai a matsayin buta Bayadda zasuyi haka sukayi alwala sukayi sallah Bayan sun dawo ne dad din al'amin yakalli driver yace za asamu mota da saika hau mubaka sako kawai zuwa Villa kasanar dashi hallin da muke ciki Driver yace ai ba mota saidai kozuwa anjima idan ruwan yayi sauki wataki nasamu Daddy yace OK alhaji Dan asabe yace abokina gaskiya zansha kunun matar nan Dan na lura suna da tsafta sosai Daddy yace toya zamuyi ba network ba restaurant me kyau ai dole musha haka Nan driver yawa matashiyar matar nan wacce bazata wuce shekaru talatin da Biyar ba aduniya Yace suna bukatar kunu da kosai Anty tace to ta aika maryam tadauko mata kwanan sha masu murfi acikin Dan dakinsu dake jikin rumfar da alama anan suke rayuwarsu biyun Tadauko takawo wa antyn tata Akazubawa su dady cike da tatsafta tabawa driver din yakai musu Kai mai zafi ta kwashe musu aka kai musu Daddyn Al'amin da Alhaji Dan asabe sunci sunsha sosai Mamaki yagama Yakama driver dan baitaba tu nanin wadan nan mutane zasu ci abincin sayarwar talakawa ba Lalle agaida yunwa yayita dariya a ranshi sosai Anty tace Maryam kije kish ruwa mana maryam tayi murmushi tace ai kema kinsan bazan iya shan ruwa alhalin kebakishaba Sai dai kitashi muje musha tare tunda kingama soya kosan Murmushi anty tayi tace maryam kenan Allah miki albarka Allah yarabaki da sharrin duniya Takarasa tana megoge hawayen da ya zubo mata maryam tace wai anty kullum saikin zubar da hawaye akaina kokina tuna mutuwar nane Dan Allah kidaina zan ga kaman akwai wani Abu da kike boye min ne Ta share mata hawayen tace ina alfahari dake mahaifiyata Bani da kamarki a aduniya mamana kinsadau kar da komai saboda ni insha Allah zaki yi dariya wataran anty na Murmushi anty tayi tace kinga maryam tashi muje kisha ruwa karmutane su fuskanci wani Abu maryam tace to mamana Anty tayi murmishi tace bakisaba da fadin maman ba ma shiyasa ba dadi nafison kirani da sunan da kikasamin antyn MARYAM tayi dariya tace wallahi kam nima bazance maman ba saboda uwata ba tsohuwa bace takarasa maganar tana dauka musu kunu da kosan zasu Shiga cikin dakin langalangar dage jikin rumfar Jiyo war uwar suka hada ido da daddy gabbanshi yabada dammmmmm Kyakkyawar mace mace duk tana cikin wahala hakan baihanaka aga zahirin kyau da Allah yamata ba Ashe ba banzaba kanwarta kyakkyawar yarinya Ashe ma gadonsu ce kyau din anty takau da kallonta daga kallon daddyn al'amin suka wuce cikin dakin nan Dan shan ruwa Daddy dai yarasa nutsuwarsa tunda ga ganin anty maman MARYAM MARYAM yarinyace kyakkyawar gaske Dan kyanta yana bawa antynta tsoro Dan antynta ita tasan sharrin kyau aduniya kafin ta haifi maryam batawa kanta adduar samun kyakykyaqar yarinya ba saboda ta hadu da sharri kalala a rayuwarta asakamakon kyan datake dashi Saikuma Allah bai karbi adduartaba Yabata maryam wacce harta tama fita kyau sosai Shiyasa kullum acikin addua da kuka take Allah yakare mata yar'ta Maryam shekararta shabiyar aduniya yarince mai tausayi dasanin yakamata Bata taba zama ba hijabi Yarinya nutsatsiyya Can dai kusan karfe goma na dare network yadawo aikuwa su daddy sukaji kira yana dubawa kuwa yaga his Excellency ne nan yafada mishi komai Hi Excellency yace subhanallah Yanzu zansa azo akaraso daku Nan daddy kashe wayarshi Daddy ya kalli driver yace ga matar nan kaman sun kawanta ya za ayi mubasu kudinsu driver yace a haba alhaji ai nabiyata Daddy yace duk da haka Dan kwankwasa musu kofar dai Bai musaba ya kwankwasa musu daman idon anty biyu Dan bazata iya bacci ba idan bata ji tafiyar mutanen nan ba karsu cutar da su Tabude tace sannu bawan Allah Yace Yauwa daman megida ne yake miki magana tace lafiya aika Riga kabiyani kudina Jin abinda tace yasa daddyn al'amin yataso yace mungode baiwar bana yawo kudi amma ban account number dinki Anty tace accounts kuma alhaji ai yariga yabiya karka damu Ya kalli driver yace jeka cikin brief cake dina kawaso kudin dayake ciki Haka kuwa akayi yadauko jakar ma gaba daya Daddy yace Ciro gabasu zatayi magana daddy ya daga mata hanu alamun bayason musu Tayi shiru kawai tana kallon ikon Allah Nan gefe kuma wasu hadaddun motocine harda me jiniya Suka karaso su daddy suka shiga aka wuce dasu sukabar anty da sakin baki tana kallon kudin da suka ajiye musu akasa Kawashewa tayi takoma ta rufe musu dakin Tofa WAI SHIN MEYE LABARIN MARYAM DA MAHAIFIYARTA Next page fans your comment is needed Love u much 😘😘 *SIGNED BY UMMU AFAN* πŸ’» [26/06, 11:52 AM] SIS UMMY: πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€ 🎑🎑🎑🎑🎑🎑 πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€ 🎑🎑🎑🎑 πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€ 🎑🎑 πŸŽ€ *BISSIMILLAHIR_RAHAMANIR_RAHIM* *Ummu Afan the Gorgeous writer of the year ,Author of 'YAN BIYAU NE &AKWAI LOKACI* 🌟GORGEOUSE WRITERS FORUM🌟 🌟 G.W.F🌟 *Home of gorgeous, intelligent and expert writers we are the best among the rest* I DEDICATE THIS PAGE TO YOU UMMU FARHAN INA ALFAHARI DAKE OVER WALLAHI ALLAH YABAR ZUMUNCI ❀❀❀ πŸŽ€ *AL'AMIN DAGASH* *PAGE* 4⃣ Antyn maryam tajuyo dan takoma cikin dakin da kudin a hanunta jiki asanyaye Sai taga Maryam zaune akan katifarsu Anty tace maryam bakiyi bacci ba Maryam tayi murmushi tace anty ai kina tashi na tashi Anty tayi murmushi tace to barin zauna muyi magana Anty ta ajiye kudin akan cinyar maryam zatayi magana maryam tace ai naji komai anty Mungode allah yasaka musu da alkairi yasa Dan Allah sukayi badan sucutar da muba Anty tace amin maryam Kirga kudin mugani Maryam ta kirga kudin nan cas suka ga dubu dari da hamsin Maryam da anty saida zufa ya jikasu Dan maganar gaskiya dai ko dubo goma basu taba rikewa ba Anty tace anya kuwa maryam muatanen nan ba da wani manufa suka bada kudin nan ba Maryam tace insha Allah allah bazai bari su cutar damuba Anty tace amin maryam amma duk da haka gobe zamu bar gurim nan mukoma can cikin kyauyen nan musamu wani gida mushiga haya mubiya kudin wata shida Kinga ko sundawo sutar damu allah bazai basu ikoba kuma bazasu ganmu agun ba Maryam tace kuma fa hakane anty Anty tace kinga zaki koma makaranta insha Allah gobe saikije kibiya ko Kisamu kizana jenior waec dinko Maryam tace kai anty wallahi naji dadi Allah yacika min burina anty namiki gatan da aduniya zakiyi alfahari dani a matsayin 'Ya Anty ta janyo ta jikinta ta kwantar da kanta akan cinyar ta tace amin maryam Allah yakareki da sharrin mutane da aljanu Maryam tace amin anty Tace anty yaushe zakibani labarin babana Anty tace zan baki maryam insha lokaci ya kusa kisan koke wacece Maryam tace to anty allah ya nuna mana ***** Daddy dai dasu anty ya kawana a ranshi yakasa bacci saboda tunanin su Yana mamakin kanshi wai meya damu da matar nan ne Duk da yasan bawai kyau ne ya rudeshi ba Dan bazai iya tantance wacce tafi kyau tsakaninta da mom din AL'AMIN ba Sai anty zata nuna wa mom yarinta Haka yakwana baiyi bacci ba har washagasuka shiga meeting suka fito Dagash air line suka tafi **** *Dubai* Mom da surakanta ne a wani shagon siyar da kayan mata Ta nemi guri ta zauna su suke ta zazzaban kayansu Kaman hauka haka suke daukar kaya Sai da suka gama mom din AL'AMIN na kallonsu Akaje gurin biyan kudi akayi lissfa mom din AL'AMIN ta biya suka fita dama yau shine zuwan karshe sungama sayayyar kaf Dan dama kullum sai sunfito siyan kaya Sun koma masaukinsu mom din Al'amin tashiga bathroom ta Dan watsa ruwa Aymana kuwa da suhaila a fall suka zube kowacce tana shan kamshi tana ganin tafi yar uwarta Mummyn Aymana tadawo itama daga nata sayayyar Dan batare suka fita ba Aymana tace oyoyo mummy tace a Ku harkundawo kenan kunrigani dawowa yau Suhaila kota daga ido ta kalli mom din Aymana itama bata damu da rashin gaishetan da suhailabatayiba Taja haunun Aymana sukayi ciki Suhaila tabisu da harara Wayarta ta dauka takira mummynta Tace yau sungama sayyaya zuwa jibi zasu taso Mummyn suhaila tace masha Allah kindai zabu kaya masu kyau da tsada ko Suhaila tayi murmushi tace ai mummy nera tayi kuka wallahi kinga tsadaddun kayan da mukazaba amma haka mummyn Al'amin take biya batare da taji komaiba Mummyn suhaila tayi dariyan jin dadi tace ai nafada miki su fa tawajen kudi basu da matsala zamu kwashi rabonmu gaskiya Suhaila tayi murmushi tace aike dai bari mummy ai wani abumma sai anyi auran tukun zamu warke Dan wallahi duk sati sai na tambayeshi kudi Mummy tayi wani shewa daga wayar tace saiki yar gidana nasan zaki iya allah dai yamiki albarka kuma nasan Al'amin sai yafi sonki Dan irinku ake yayi siraran mata ba irin wanann fan kamar yar'uwartashi ba Suhaila tayi dariya kanta yasake kato tace se mom dina kina fasamin kai dayawa Haka sukayita hirarsu saida mom din Al'amin tafito kafin takashe wayar tace sannu da fitowa mummy Mom din al'amin tace yauwa suhaila tana zama tadauki wayarta takira Dagash Itakuwa suhaila mom tazuba wa ido gaskiya mom akwai kyau ga tsafta bata yarda kazanta Sam Ba banza al'amin yabiyo tsaftarta ***** DAGASH yana cikin ruwa sweemingful na gidansu la'asar ce sakaliya yafito daga wajen training kenan yafada ruwa Dan yayi wanka Yau ne su mom din shi zasu dawo Yana cikin wankanshi a ruwa security dinsa ya matso yace sir ana kiran phone naka Dagash yace sunan Security din yace lovely yace bani yafito daga ruwan ya karbi wayar yace mom ko kunyi landing ne Mom tace a a amma nan 15 minutes we will be there insha allah Yace OK on my zanzo na daukoki tace that's my son sai nazo to i miss u son Yace me too mom shiyasa nagaji da gidan babu ke tace Don't worry son yanzu zakaga mummy Nan suka kashe wayar baikoma ruwan kawai part dinsa yawuce yaje yashirya cikin wasu balain kaya Jim's ne dark blue sai kuma T shirt dinsa light blue sai ya dauki farin glass yasaka Ba abinda ketashi ajikinsa sai kamshin turarruka masu tsada yadauki wayoyinsa da wallet dinshi yayi waje Direct wurin motocinsa ya wuce yakai kallonsa ga gabadaya motocin dasuke wajen Yazabi wata hadaddiyar homer jeeep mai matukar kyau da daukar ido Shima jeep dark blue ne gaskiya duk wanda yakalli dagash cikin motar nan yasan Sundance da juna Yana isa DAGASH AIRPORT girgin su mummy na sauka ma'aikatan wurin suka taso sukazo suka bude mishi kofa Suka Sara mishi dayan yace sir ai dabaka zo dakanka ba munta nadi motar da za akai su hajiya har gida Dagash yace akwai wadan zaku tafi dasu ai Ku kawo matar nan Suka bi umarnin ubangidan nasu shikuma jirgin nagama sauka motanen ciki suka fara fitowa Idonshi akai ya hango suhaila a gaba mom abaya Suhaila tayi shiga cikin Riga da wondo kamar yadda tasaba sai Dan karamin mayafin data yafa akanta ga uban dogon takalmi itakuwa Aymana dogowar Riga tasa tayi rolling dashi saboda gimbiya ce Dagash cikin missing din mom dinsa yakara ya rumgume mom dinsa yana mata welcome itama taji dadin ganin shi Sai dai tace meyasameka son ka rame yace badole na rame ba mom kin San dad ba abinda ya iya dafawa sai indomie shinayi ta ci kinga kuwa ai dole na rame nasaba abincin mom na Yakarasa maganar yana murmushi mom ta shafa kumatunsa tace kuma ga azumi ko Yace wallahi tace ai balefina bane sayyayar matanka najeyi Sai alokacin yakai kallonsa ga mom din Aymana yace oh mom harda ke akatafi Abin yaba mom din Aymana mamaki tace au dama bakasan tare mukaje ba Yace naman ta yakk irin gaisuwarsa kenan yawanci Cike da mamaki mom din Aymana tace lafiya kunya yakamata da irin gaisuwar da al'amin yamata Suhaila kuwa dady abin yamata Mom dinsa kuwa dama ita yar baruwankace Aymana tace yaya ina wuni Ya kalleta ya watsa mata wani kallon rainin hankali Ganin haka yasa suhaila kama bakinta Can kuma ya kalli suhaila ya ce kekuma kinfi karfin gaisuwar ne Jiki na bari tace am sorry doctor munsame Ku lafiya wani wawan kallo yamata baice komai ba Yakama hanun mummynsa data keta faman waya da daddy yace less go mummy Ya kira security yace yakarbi jakan mom din Aymana sutafi Dagash ya kalleta yace to mummy sai anjima kigaida da dady king sai na shigo Yaja hanun mummy sukatafi mummy tace to hajiya sai munyi waya ko Mummyn Aymana tace OK by Takaici Yakama suhaila saida tafaki idon su Aymana ta goge guntun hawayen wulakancin da dagash yayi musu wai damma ba ita kadai ya wulakantaba bare sumata dariya Dagash suna isa gida ana kiran magriba mummy tace zanyi sallah kafin kadawo daga mosque zan dafa mana abinci maisauki Yace that's my mom yabata fek a kumatu yayi waje Tayi sallahi kafin tafito zuwa kitchen duk da gajiyar datake tare dashi hakan baihanata son faranta wa danta raiba Couscous tayi da miya shaf shaf miyar amma za aiya cewa ta kazace Dan naman yafi yawa nan takwashe komai tafito dashi falon alokacin Al'amin yana shan kankana yana ganin mummy yace kai mummy tunkafin naci kamshin ya kosar dani mom tace aikuwa baka isaba Sai kacinye komai Dana maka yayi dariya yace ai wasa manake miki Ba abinda zanbari a abincin nan Mom tayi dariya tace kaman gaske Dagash na cikin cin abinci kona ce mummy na feeding nashi dad yashigo yace a a son rigima ya kareko mom tadawo Murmushi mom tayi tace ai son badama Al'amin yace dad wallahi harnaji nadawo mutum haba ai nasha wahala kwana biyu Yadda al'amin yake zuba wa iyayenshi shagwaba kai zaka dauka Dan shekara biyar ne *** Bayan kwana biyu da dawowar su mummy da daddare mummy tayi shirin kwanciya ranar kwanantane taga daddy yazuba wa guri daya ido yana kallo Tace Alhaji wai mekefaruwa da Kaine tunda nadawo na lura akwai wani Abu akasa wanda yake damunka kakasa fada min Shere your problems with me mana haba sweet heart Murmushi dad yayi yace matata kema kinsan da akwai wani Abu bazan boye miki ba zo ki kwanta dare yayi yajanyo ta suka kwanta Mom dai taji shine amma bata amince bakomaiba Dan bata taba ganin shi cikin damuwa hakaba amma zatayi kokari tasan komenene **** Alhaji su'ad zaune shida alhaji Dan asabe suna tattaunawa kan matsalar data damu alhajin Alhaji Dan asabe yace anya kuwa abokina ba gamo kayiba kayi sanyi lokaci daya akan talakawa da basu da wani gata a rayuwarsu duk kabi kadamu kanka akansu Wai tsaya ma meyaja hankalinka har kafada son yarinyar nan Dan yarinya zankirata Dan munhaifi wadan da sukafita Alhaji su'ad yace wallahi nima bansaniba kawai nasan nakamu da matar nan sosai kuwa Alhaji Dan asabe yace to sonawa muna komawa taki sauraronmu itafa gani take ma zamu cutar da ita da yarinyar tane Dan Allah kabar maganan matar nan idan auran kakebukata wayayyo gasunan kanema mana Dad din al'amin yayi murmushi yace kodaya banida ra'ayi wasu matan Bayan wannan baiwar Allahn Kawai bani wani shawarar amma banda na inrabuda ita bazai yiwuba I can't please Alhaji Dan asabe yace ok nafahimceka abokina yanzu dai kagani munje kauyen nan yafi sau biyar Taki bamu hadin kai ganitake cutar dasu zamuyi Saboda haka mubi komai a sannu mubari ayi auran yaran nan sai musake komawa muje mata da kokon barar mu Alhaji su'ad yayi murmushi yace yauwa abokina yanzu naji magana amma zakace narabu da ita Wallahi ko bacci bana iyawa yakai ma har matana sunfara gane ina da matsala Alhaji Dan asabe yayi murmushi yace gaskiya ka kamu dayawa abokina amma dai kasan waje zaka kaita a polishing dinta ko yafada da tsokana Dad din yace babban burina ma dai ta amince da bukatuna sunfi min komai Alhaji Dan asabe yace to wai yazakayi da matanka Alhaji su'ad yayi murmushi yace duk bazamana sukeyi ba dole sukarbi abinda nazo musu dashi Alhaji Dan asabe yace se namijin duniya wallahi ina son nakoyi jarumta irin taka abokina kwata kwata baka shakkan mata Nima fa wallahi ina da bukatar karin auran nan amma bana son fitina shiyasa kawai nabar komai Dad din Al'amin yace lafinkane tunfarko abokina Alhaji Dan asabe yace hakane kam ***** Yau take sallah Doctor al'amin dagash na hango cikin wata shadda ash colour dark tunda daga kan shaddar zuwa dinkin bakina da hanuna bazai iya fayyacewaba amma komai na Al'amin daban ne kawai Ya kalli kanshi a madubi yaga shikanshi yasan kayan sunkarbi jikinshi sosai amma shidai bazai iya cigaba da amfanida manyan kayaba shi aganinsa takurace kawai bawani abuba Faisal da zayyad sukashigo suma cikin shaddodi na alfarma duk sunyi kyau Zayyda da Faisal kusan atare suka hada baki wajen ihun ganin dagash Harda babbar Riga sosai sukayi mamaki zayyad anya mutumina Kaine kuwa ai yau kafito a Prince din naka sosai Al'amin ya watsa musu harara yace muna fukai wallahi wannan ma da kuke gani aikin dadine Shiya bata kudinsa aka yi amma sanin kankune bazan sake amfani dasuba Faisal yaceaikuwa dakaga yadda suka maka kyau da kacigaba amsawa Zayyad yace kana bata bakinka ne fa Dan tunda yace basawar zaiba bazai

Chapter 3 of 18