Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
ayi haka ba haquri dai xa ka ci gaba da yi.xuwan su alhj biyu gidan amma ba suyi dace ba ance musu mahaifinta baya nan. antynta kuwa ta kira shi a waya ya ce yana nan xuwa gidanta.da dare suka je da ahmad sun same ta ita da mijnta,anty ta tare su cikin fara'a aka kawo musu kayan shaye shaye.nan dai abba ya fada mata komai.ya qara da cewa ban sani ba ko dan ni talaka ne shi yasa bishira bata ji maganata? anty tace dame ka gaxa mata? iskancintane kawai, wai bishira har da rashin sallah,xa ko taci qaniyarta gun alhj.mijin anty yace,tabdi lalle kana haquri nan dai suka ci gaba da hira har mijin antyn yayi mishi alqawarin cewa ya kawo takardunshi.MD din gidan rediyon tarayya na jihar kd, amininshi ne. Amininshi ne tun da abn da ya karanta kenan za a sama mishi aiki.Abba ya yi ta godiya. Bai san da wane baki zai gode ma mijin anty ba,tun daga nemna auran Bishira yake taimakoshi, darajar su shi da Anty da Alhjn su Bishiran yake hkr da halayanta. Ya zo ya sanar da su Umman,Sun yi murna hr Alhj ya ce dole ne in in masa godiya. Umma ta ce To Abba ka gani fa,ta dailin matarka gashi zaka samu aiki,ka yi ta hkr fa. Abba ya ce Umma ba fa ta dalilinta ba,in Allah ya rubuto zan samu ta hanyarshi sai ki gani,ko ban santa ba Allah ya kawo sila.Ta ce To yanzun dai ita ce Silar,Allah yasa albarka.Sai dai ba zan ji dadin tafiyarka garin Kd ka barni nan ba. Ya ce Umma ko ni tunda ya ce kd ke kurum ni ke tunan.Umma tayi Murmushi,Allah ya maka za6i na alkairi,dk in da za ka je.Amin Ummata. Mahaifin Bishira ya dawo kuma Alhj ya tasa Abba sun je in da aka kirata gata ga shi ga kuma iyayensu. Abba ya jero duk laifunkanta bai rage ko daya ba. Sannan ya ce,shi ma yana son ta fadi tsakani ga Allah me yake mata wanda ba ta So?Nan fa a ka ce ta fadan, sai ta shiga Kame-kame, Wai in ya shigo gida sai ya yi ta fadace-fadace sannan ba ya zama a gida sai tayi bacci,km ga abnci ta dafa amma sai ya amso na Ummarshi ya c. Alhjnta ya daka mata tsawa."Yi min shiru,yaushe ki ka bar musulunci? Ba kya sallah ko?sannan ki bude baki kina zagar masa da a gabansa?Ya bige miki baki kin kwaso kin taho gida,to a miki uban me?ya dubi Abba "Idiris me yasa ma ka mata duka ba?Ai ke babu abn da ya dace da ke irin duka. Maza ki kakkabe mayafinki ki koma gidanki,bana son in sake ganinki da sunan yaji a gidana, . Zan wulakanta ki. Kuma game da batun sallah dk lkcn da bata yi ba ka dakar min ita ni na saka,batun tsafta kuwa kada tayi,ka nemi mata ka aura ka barta da tsiyarta. kai dk lkcn da ka samu matar ma zan biya maka sadakinta ko 'yar wanene.Sai a lkcn Alhjn Su Abba ya yi magana. Hakuri za ka yi ranka ya dade,Allah ya saka da Alkairi bisa karamcin da a ka yi mana,kuma insha Allah ba za su sake ba. Abba ma ya yi godiya,sannan suka masa sallama.Ita ko Bishira mayafi ta dauko tana kuka suka tafi. Hjy Zainu ranta ya 6aci,taso a kashe auran don dama bata son Abba sam,kafin zuwan iyayen Abba da shi kansa Abban ta fadawa mijinta karairayi,kamu ransa ya 6aci. Ya kuma daukar wa kansa alkawari in ya bincika ya tarar haka ne dukanta da zaginta yake ba tare da ta masa laifin komai ba?sai yasa an raba auran. Amma da yaji batun Abba gata a gurin bata musu ba,sai ranshi ya baci da ita, har dai batun sallar nan.dn haka ya bincike yana da kyau ayi shi,kada ka yanke hukunci da maganar gefe daya,wannan shi ne adalci. Bayan sun dawo Abba ya rakata gida ya zo gurin Alhj da ya ce ya dawo yana jiranshi. Alhaji ya masa fada cewa dk in da tara tayi to ya kansace a gida. Sannan fadan da ta ce yana yi in ya shiga shi ma ya daina,haka ya dinga zama yana cin abncin.Abba ya ce to.Umma ma da ya shiga suyi Sallama nan dai ta kara masa fada tare da nuna mishi hanyoyin da zai bi ta ce kuma cikin satin nan yayo mata rijistar Islamiya tunda da ita a kusa. Ya shiga ya same ta zaune bakin gado tana ta fushi,ya zo ya zauna kusa da ita.Yasa hannunshi ya kamo nata,sannan ya kira sunanta bata amsa ba bata kalle shi ba ya ci gaba da mgn. Kin san dai ina sonki ko??ta dube shi Da ba kafin a zuga ka.Ya ce wa zai zuga ni? ta ce Wa kuwa in ba Ummar taka ba. Ya yi tsam ya ji haushin maganarta sosai,amma sai ya danne kada ki zargi Ummata tana sonki kin ki fahimta ne kawai.amma mu bar zancan kiyi hkr akan abubuwa da nike miki. ki yafe min nima na yafe miki. . Ya jawota zuwa jikinshi,hr gobe ina sonki sosai.Ranta ya yi sanyi don mata na son wannan kalma daga mazajensu. Ya kira sunanta ta dube shi cikin ido suke kallon juna,ya ce kin ya fe min?ta daga gira,kina sona hr yanzun?Ta kara mannewa a jikinshi "Ina sonka sosai ma.Ranar dakin shi suka kwana,kuma ranar ce rana ta farko da suka soma kwana a dakin nasa. Washe gari tunda ya dawo Masallaci ya soma akin share gida,lungu-lungu ya gama ya wanke bayi kan su sannan ya yako ta da kyar ta tashi ya ce tayi sallah ta yiwa yaro wanka. Tayi Sallar,wankan ta kuke wai akwai sanyu,sai ranar ta daga. Ya ce,To t dafa musu ruwan zafi su karya.Shi kuma ya fitar da wankinshi yana yi ya gama ya ce ta fito da duk wankinsu ita da yaron.Tsawaya ya yi yana kallon tilin kayan,amma gudun kada suyi rigima sai ya yi shiru ya ci gaba da wanki. . Ya cire kayan yaron da zannuwanta hr ma zanin gado wadanda yaron ya yi kashi ta aje su suka bushe,,wasu kayan hr da tsutsotsi. Ya kira ta ya ce "To kalli kayanki hr da tsutsotsi,wanna n ya dac fisabilillah?samo leda ki kwashe su,ba zan iya wanke su ba,in kuma za ki wanke to. Nan ta samo bako ta kwashe takai gurin bola,ya ce Bishira tsafta cikin addini ce,Annabi (S.A.W)ya ce Babu mai shiga Aljanna sai mai tsafta. Don Allah ki dinga kula,ke kanki za ki ji dadi in har ki ka tsaftace ko'ina na gidanki.Ta tura baki ta wuce. Ranar haka ya yini wanki kayan yaron dk sun dafe kaya masu tsada da kyau irin wadanda a ka sai masa daga gidan iyayenta,ranar dai ko shago bai je ba. Cikin satin dai babu laifi suna ta shiri,kuma tana daurewa tana yin tsaftar jikinta,haka nan yasa ta wanke kai tayo kitso. sai dai ita gani take dk an takura mata,amma tana jin dadin yadda ya sakar mata fuska kamar farkonauresu. Mitar da take masa kullum ya daina dadewa a waje,ita don Allah ya zauna a gida suyi hira. Ranar dai saiya gwada zama tun da ya dawo sallar Isha'i ya shigo gida. Tana zaune ba riga ya ce,Wai Bishira kayan kwalliyarki sun kara ne? ta ce,Me ka gani?ya ce,Rabon da in ga kwalli a idonki tun kina amarya bare dan jan baki. . Taja dan tsaki "kwalliyar me zan yi sai kace wata budurwa?Da dai nayi.Ya ce kin ji wani shirme kuma,ban da ke ai matar aure me miji a hannu ita ce da yin kwalliya. Ta ce, To ko ma nayi ba zama ka ke ba.Ya ce "To yau dai gani na zauna,kuma ina son a sheka min kwalliya. Ta dube shi Gsky sanyi ba zan iya yin wanka yanzun ba.Shiru ya yi yana kallonta,can sai ta zame ta kwanta,sai kuma bacci. Ya yi murmushi.Dubi matar da ta ce wai ba na zama a gida. to yau na zauna amma kalli yadda ta bingire tana shirgar bacci. Ya mike ya fice.cikin takaici korafin banza kenan take yi tunda ba ta san yadda za ta yi fira da mijin ta ba. haka dai abba yayi ta hakuri don baxai yiwu ya ce shi kadai zai dauke mata duk aikin gidanta ba. sai dai yayi wanda zai iya,amma duk wanda ya shigo gidan shi ko ba a fada ba yasan matar gidan kazama ce ta bugawa a jarida. ummi tana zaune gaban umma,fuska shabe- shabe da hawaye.ta rikewa ummar hannu."kinji don Allah umma kice wa ya Abba ya dawo dani garin nan.wallahi bana son makarantar kwana,ni dai bazan koma ba."umma ta ce "haba ummi xuwa yanzu ya ci ace kin saba da makarantar" ta ce,"umma bazan saba da rashinku ba....."karaf a kunnen Abba. ya ce,"to sai ko ki shirya sabawa,don wata rana ma aure zaki yi." umma ta ce sosai kuwa. tsohuwa dake zaune a kofarta,tana jinsu ta sako baki da cewa,"ku dai lallasheta,karatun nan fa da ake ta matsanta mata bana ganin manzo bane." Abba ya ce mata,"in ji wa? kin ji ki,to ana neman aljanna da karatun boko kuma ana neman wuta." ta ce,"kai ni raba ni da shegiyar karya tunda bata so a barta." Abba ya dubi ummi,"kada ma kiyi za ton maganar tsohuwa za tayi wani tasiri,gara ma ki shirya komai gobe da wuri zamu wuce." ta dube shi,"don Allah ya abba." ya mike ki shirya da yamma zanzo muje (sahad store). ya dubi umma na tafi. . Ta ce,"abba bamu ko gaisa ba,ya mutan gidan?" ya ce,"suna lafiya,sauri nake in karasa wasu dinkuna,saboda gobe bana nan jibi litinin zanje interview da gidan radiyo da talabijin na (c.t.v) ta ce,"a'a ka samu anan din ne?" ya ce,"eh bana fada miki ba da aka tura takarduna can sai suka ce gurin da zasu saka ni akwai wani wanda suke jin dadin aikinshi a gurin? don haka zasu turo ni kano,suna ganin ana bukatar irina.to shine mijin anty ya fada min to yanzu sun kirani ranar litinin zasu min (interview).ummi dai na jinsu bata ba kukanta ba.abba na ficewa umma ta ce tashi kije kiyo kitso ummina,kin ji? dakyar taje ta dawo.umma tana yankan kubewa wayarta ta shiga ruri,ta dauka Abba ne.ya gaisheta ta amsa,ya ce ummana ummi fa ta shirya? umma takai duba cikin daki inda ta hango unmi nade kan kujera tunda ta fito wanka. Tace can cikin kujera,wai sanyi take ji.yace sanyin lfy kuma? ta shirya ta sameshi gida,umma tace to gatanan xuwa sukayi sallama.umma tace ke ummi fito man in kin gama shirin.ummi tace umma nifa sanyi nake ji,ina ganin xaxxabi ne xai kamani.tace to ku biya ta kyamis kusai magani.tsohuwa tace ke yi kwanci yanki, dole ne fitan? umma ta miqe tana cewa, yanxu in ban je ba da yaxo xai fara min masifan shi ne. ta shirya ta fuce rai a bace.a nutse ta ke tafiya har daf da qofan gidan ya abba. sallama taji anyi mata.wani matashi ne suka gaisa, ya tambaye ta nanne gidansu? tace a,a lafiya?ba tare da bata lkc ba ya fara xayyane mata manu fanta,santa yake kuma da aure,tace kaga mlm sai anjima.ta shige gidan abba shiko ya kafe yaqi tafiya.da sallama ta shiga gidan,qaran inji baisa aji sallaman ba,dan haka ta jingina da rijiya tana kallan tsakar gidan.mamakin daya yadda mace daya a gidan ta kasa gyara gidan.sai kace gidan namiji, namijin ma qaxami. . abba ne ya fita wanka sanye da jallabiya fara.ya aje bokitin ya dube ta. yace ki siga ciki mana, ai tana falo.tayi sallama,bishiratana xaune da baso tana kalan tv, ganin umma ta daga labule sai ta hada rai tare da cewa lfy? ummi tace ina wuni. bishira tace lau, nace lfy? ta fada hadi da xare ido. ummi tace ya abba ne ya ce na xauna anan na jira shi. tace baxa a xo nan adame ni ba, ehe dan kallo nakeyi. ummi ta ja tsaki tare da sakin labulan, ta koma ta jin gina da rijiya.bishira ta fito.ke sarkin rashin kunya wa kike ma tsaki? ummi ko kallanta batayi ba.sannan tace baki isa kixo min har gidana ba,kice xakimin rashin kunyan da kika saba.abba ya jiyo hargowanta ya fito, yana qoqarin saka t- shirt baqa akan faran singiletin shi,wandan jeans ne mai laushi blue.yace,menene? tace, wannan mara kunyan yarinyan nanne xata sameni har dakina tamin tsaki.oa dubi ummi dake kallan qasa tamkar bata san me akeyi ba. yace ke ummi, ta dube shi da sauri,xan bata maki rai kinsan bana san raini ko? tace nifa ya abba banfa yi mata komai ba kawai fa.ya daga mata hannu,yace banasan ji. yace na fada maki dai bana san raini. takaicin duniya ya isheta,ta sunkuyad da kai cikin qunan rai.wanna shine gaba kura baya damisa.bishiqa kam sai ci gaba da mita take, shiko abba tuni ya koma dakinsa da qarasa shiri. ya fito fes, sam baxaka ce mijin bishira bane.qamshin turaransa ya karade gidan ya daga labule.ni na fita. tace sai ina? xan kai ummi ta sai duk abinda xata nema dan gobe xata koma mkrt. ta tabe baki. ya dubi ummi wadda ke cika tana batsewa,sannan ga sanyi alamun xaxxabi yana damunta.yace muje ko? ta dube shi sannan ta bishi.a qofar gida ya iske wannan saurayin,yace lfy, ko kana jiran wanine? saurayin ya ce wata yarin....sai ya hango ummi,dan haka ya katse batun da cewa yauwa gatanan. . abba ya kalleta ke uwar rore rore wannan ke yake jira ko? ummi tace oho mashi, bina yake tayi.abba ya ce, kayi haquri dan samari,ba aure xa a mata ba, krt takeyi. yace nima din bawai ina nufin yanxu bane.ya ce na fahince ka.to ka bari sai nan gaba,ina nufin in auran yayi sai kaxo ko???? Ya dubeta ranshi bace,ke kuma wuce muje.suka bar shi nan tsaye yana kallansu.yaga kishi qarara a idon abba.yace wannan ba wanta bane shima santa yake.ya raya aransa shima yayi gaba abin shi.shi kam abba suna tafe yana yi mata fada,wai tabi ta sakar ma maxa fuska kowane gaja sai ya xo yace yana santa.maimakon ta tsaya tayi krtnt,xamani na ilimi,ita dai ta qi kula shi,har yanxu takaicinta abin da matarshi ta mata,kuma ya nuna ya goyi bayanta.wayarshi tayi ringing,ya kalli ummi muje shago na mashin din nacan.sannan ya daga wayar,ita tana tafe ne amma sam bata jin dadi.da yake tafiyanta yanxu tamkar tana jin tausayin qasa take yinta,sabanin da da sai dai tayi gudu,shi da ke tafe yana waya ya riga ta isa.gefe ta tsaya ya shiga shago bayan ya gama amsa wayar.ahmad abokinsa yaxo xai shiga shagon ya ganta tsaye.tace ina yini ya ahmad? yace lfy lau yar daru.daman haka ya kan ce mata.ya shiga shagon yana waiwayanta,abbana barma yan shagon sallahu wasu kayan da xa a xo dauka,ahmad ya shigo. suka tafa,sannan suka gaisa.ahmad yace naxo ne in fada maka anjima xamu shiga gidan su hafsa dan gaida iyayenta,sai dai kuma ganin ummi ya sani jin wani abu.anya ba xan dawo gida da neman aurena ba?a rude abba ya ce wace ummi kenan? ahmad ya ce qawarka mana.abba ya ce dan Allah saki xancen nan kada ma ta jiyo ta raina mu,me ka gani naso a gun ummi? dan Allah kada ka cta min rai. . ahmad yace, allah in xai yiwu, nutsuwan ta birge ni .abba ya ce to ba da ni xa aci amanar hafsa ba.ummi kuwa dan Allah ka bar xancenta.yaea ahmad yaga abba ya sha mur ya tsare gida,dole ya saki batun.suka yi sallama ya tafi,abba na cewa sai yaxo da dare.yasa yaron shagon ya goge mashi mashin din sannan ya tada,ya kalli ummi fuskarshi daure xo ki hau.itama tata fuskar a daure take.tahau suka tafi,iskar dake kadata tasa xaxxabin dake san kamata ta qaru.ya kafe mashin dhn ya kalleta,muje mana.ta bishi suka shiga cikin sahad store din.tsaye tayi tana kallanshi yana diba kaya.da alama na iyalanshi yake diba,dan taga ya soma da pampas. Hannuwanta harde a qirjinta tana kallan shi,kome nashi yana birgeta.ya waiwayo ya dubeta, tsayuwarme kike yi a nan da ba xaki dauki abinda ya kawo kiba? ta rasa me xata dauka,sai kurun ta dauki makilin ta riqe a hannu,ya gama diban abin da yake so,sannan ya aje gaban masu amsar kudi.ya dubeta,bakya buqatar komai kenan? ta nuna mishi makilin din hannunta,tana murxa shi.ya harareta baxa ki dauki komai ba,kina da kayan tea dasu complex? tace a,a.y2e to ki tsaya kada ki dauka.ya soma dibo mata saitin sabulan nan daya taba sai mata na aloe vera,dan yaga duk kananan qurajen sun mutu.sannan ya hada mata da audugar mata guda biyu.ya kai table.lkcn ta dauki madara da milo ta kawo.yace wawiya,dalla matsa ki bani gu.yaje ya qara tsinto mata ,sanna akayi musu total ya biya.suka fita.kafin sukai gida haqoranta sun s6a haduwa,gashi tana ta takurewa,yace lfy,wani irim xama kika yi haka?tace,sanyinake ji.tana magana muryarta na makyarkyata.wani dan asibiti ya nufa da ita nan kusa da unguwansu aka dubata. Wurin allura,nan fa a ka soma daga.Ta ce,ita kam bata san allura.Abba ya daka mata tsawa da cewa,Allurar ce abn tsoro?Na gane sam ba ki son ki koma mkrnt,a gobe ne kuma sai kin koma duk abnki. Ta ce, Naji zan koma amma yanzun kam dn Allah Ya Abba kada amin allura.Nurse dai sai kallonsu take yi tana dariya. kwai Ummi sai ta soma hawaye ita fa har ga Allah bata son allura.Nurse ta ce,To ka rike ta mana ko ba Amarya ba ce?Naga shagwabar tayi yawa. Abba ya ce,Me? cikin tsawa ya yi maganar,hr sai da Nurse din ta tsorata,ya ce kanwata ce fa,kin ga wannan kucakar tayi kama tayi kama da Amare? Nan take Ummi taji ta muzanta,sannan km ta tsorata da irin tsawar da ya yi,ba ta san lkcn da ta shige a ka yi mata allurar ba. Ta fito tana sharar kwalla suka koma gida. Sai dai tana hada kayanta a Jaka,Sannan ta ga wadannan sabulun da kuma audugar,kenan shi ne dama ya sai mata wancan?ko me yasa ya sai mata kuma hr da augugar mata? . wata zuciyar ta ce,kila dn yaga Umma bata san kan abubuwan zamani ba sosai.A fili ta ce,kai umma tasan audugar mana. Haka dai ta ci gaba da tufka tana warwarewa,hr ta gama shirya kayanta. Yau kuma a bayan Tsohuwa ta za6i kwanciya,da dn komai ba sai dn suyi hirar yaushe gamo. Sai dai Maimakon hira sai ta tsunduma a tunani,ta bar Tsohuwa tana ta zance ita daya. Fitarsu da Ya Abba ta tsaya mata a rai,ita tayi ta tunowa tana murmushi.Sai dai bata Son tuna lkcn da ya yi wa Nurse din nan tsawa dn ta ce ko ba amarya ba ce kom me yasa zai mata Tsawa? ita kam kalamn Nurse din nan sun birgeta,shi kuma daga ganin yadda ya yi tsawar nan kalamn ba su masa dadi ba.......... wai takwara bacci ki ka yi ne?Muryar Tsohuwa ta katseta,ta ce,Idona biyu Tsohuwa.Ta ce, Tunanin me ki ke yi ne haka?Ummi ta ce "Um" ina tuna gobe yanzun ina can.Tsohuwa taja tsaki,Ai mai sunan Malam ya san takan mugunta. UMMI dai ta ce "Um.Tsohuwa kuwa sai yi take da mai sunan Malam.Tun Ummi naji tana "Um", hr zcyrta ta soma tsanar kalaman Tsohuwa. Sai dai bata da damar ta katse Tsohuwa tunda dn ita take yi,bata da mafita da ta wuce ta bar dakin,don haka ta suri butar Tsohuwa,wai zata je kewaye(bandaki). Shi ma Abban da ke kwance a tsakar dakinshi kan kafet ya tada kai da katifarshi,ban da tunanin fitarsu ta dazun ba abn da ya keyi. Sai dai damuwarshi daya,me yasa samari da dama suke kawowa Ummi hari?Me yasa ya ke jin zafin haka?Zuciyarshita amsa da cewa,ka so ko ka ki kana Son UMMI."a fili ya furta "Haba dai so,Allah ya tsare ni." Tun misalin tara Ummi ta gama shirinta tsaf,cikin kayan mkrnt mai ruwan hoda,mai gida-gida.Da kuka ta bar gidan yau ma. Haka nan kuka take hr suka isa mkrnt,ta samu Khadija hr tazo,dn haka tare suka kwashe kaya.Kafin Abba ya tafi sai da ya yi mata fada kwantankwacn wnda Umma tayi mata.Waton ta kula d kanta,kuma tayi abn da ya kawo ta,waton krt.Sannan ba ya son tayi kawance d yaketa shari'a.irin wanda wasu watsatstsun yaran ke yi.(Allah ya shiryesu). Sannan ya jadadda mata batun ibada,sannan ya kawo kudi ya bata,ta ce Umma fa ta riga ta bani. Ya ce,"Ki kara."ZURFIN CIKI book 2 part 5 ZURFIN CIKI book 2 part 5 Posted by Bashir Sani Fesan on 14 Dec 2016 - 22:12 Umma fa ta riga ta bani. Ya ce,"Ki kara." Rayuwarta a mkrnta wannan karon ba laifi,sai dai fa hr yanzun ta tunu da gida sai tayi kuka. Su Safiyya suna mmkn yadda Habiba take da matsanancin nacin gida. ******** Abba ya shigo gidanshi dauke da ledajin kayan miya,da sauri ya dire su kofar kicin ya nufi Bishira da ke kofar bandaki tana shara amai. Ya kama ta,"lafiya?Me ki ka ce? Sai da ta gama aman sannan ya karasa da ita ta wanke baki da fuska a cikin bayin. Ya ce,Ba ki d lfy ne?Ta soma Hawaye, Ka gani ko Babn Walid,kila fa ciki ne da ni.Tun wancan Satin ya kamata in ga al'aldata amma shiru. Ya ce, To menene na kuka? Yi shiru,Allah ya inganta.Ta harare shi Dana fa bai shekara ba.Ya ce,To dole ne sai danki ya shekara sannan Allah zai baki wata kyautar? Ta soma kuka,Ni dai zan je a ciremin ne. ya hade fuska,Ban yarda da haka ba. Ganin ta tada hnklnta tana cewa "Dama Hjyrsu ta ce mata tabi a hankalu ta ki ji gashi nan yanzun tana da wani ciki. Ya ce To kada ki damu kin ji? Zamu je asibtin dn a tabbatar da cikin kafin a san abnyi. Da za suje asibiti shi ne ya dage sai da tayi wanka,dn d farko kaca-kaca ta dauko mayafi, ya ce sai tayi wanka ta canza tufafi. Gwajin farko ya tabbata tana da ciki,nan ta shiga kuka. shi kanshi ya damu domin bai so ciki yanzun ba.A son ranahi sai an yaye yaron kafin wani cikin. Amma ba shi da ra'ayin zubarwa,nashi ganin kyautar Allah ce,dn haka ya amsa ya kuma gode. Ya lallashe ta da cewa,ta yi hkr su amshi kyautar Allah dn haka wani na nema da kudi bai samu ba. likita ya ce,Kada ta damu,taci gaba da bai wa danta abnci tana hada mishi da nonon,a hnkli zata yaye shi bana farat daya ba. Bayan ya kaita gida ya kuma lallashenta,saiya nufi gurin Umma. Bayan sun gaisa,ta tambayi iyalanshi ya ce "Daga asibiti ma muke da Bishira." Umma ta dube shi da sauri,Waye ba lfy? ya ce, Ita ce.Sai kuka ma take yi wai dn an ce tana da ciki. Umma ta ce, Ikon Allah, to Allah ya inganta.Sai dai kuma kada Walid ya sha ciki. Abba ya ce,likiya ma ya yi mata bayanin yadda za ta yi masa,hr ta janye shi daga nono cikin hikima.Umma ta ce, Da za ta yarda ma an kawo mana shi nan. ya ce,Ai dama nan zan kawo shi da zarar an yaye shi Umma. Sam bai fada ma Bishira nufinshi na baiwa Umma Walid ba,dn yasan ba zata ta6a laminta ba.Sai dai itama tasan dole hakan zai yi. Don haka ta garzaya gurin Umman Bashir ta shaida mata cewa sunje asibiti,dk ta fada mata komai,sannan ta ce ita danta take tunani kada ya dauka ya kawo wa Ummarshi ita ma a mallake mata yaro. Umman Bashir Ta ce Wannan a zaune take,sai dai in ko ba a kai shi ba.Amma ki bari daga kin kula ya daina damuwa da nonon ki janye shi,zan zo in taho da shi wurina. Bishira taji dadi tare da cewa, Hakan dai yafi. Sabuwar kazanta ta samu,Bishira dk abn bi bangon daki an tofe da yawu.Rashin wanka sabo,kai abn nata sai addu'a. Ibada kuwa ba a mgn,domin dai tuni ta aje Sallah a gefe,Azumi dai tana yi amma in ta sha bata ramawa.Allah ya shirye wanda ya 6ata. Abba ya dai yanzun tuni ya yafe abincin gidansa,matsawar ba shi da kanshi ya girka ba,don kuwa dama can shi mutum ne mai kyankyani. In zata fita takan wanke kafafunta ta dauki kaya ta saka,sai ka rantse tayi wanka.Amma da zata matso kusa da kai,nan za ka ji kauri na tashu da karni da kuma wari. Dole ya hkr da laluranshi ta aure a gurinta,domin in yaje shimfidarta ba zata ki ba,amma wari da zarni suna hana shi yin komai cikin nutsuwa. In kuma dakinshi ya kirata ko bata kwana ciki ba har gari ya waye yana jin warin jikinta a shimfidarshi don haka lokuta da yawa yake hakura da ita. *********** . Ummi tana kwance kan gadonta,yayin da Khadija da Safiyya suke zaune bakin gadon Safiyyan wadda ke kallon Ummi. Hirar masoyinta take basu,Safiyya bata ko gajiya da zancensshi. Khadija ta ce,ita ma da zata taho har kuka nata Saurayin ya yi. Sai lkcn Ummi ta dube su,"kuka Khadija?Khadijata ce,"Riris Kuwa. Ummi ta ce, Hu'um ba namijin shi yasa nike da za6i a kan irin mijin da zan aura. Safiyya ta ce,"ke banza,dk cikin so ne. Ummi ta ce Ban damu da sai namiji yaso ni ba,in dai ya tara abubuwan da nake so ga namiji to zan yi amfani da kasantuwata 'ya mace in koya mishi Sona. Khadija ta tashi ta dawo kusa da Ummi,Kin san me ki ke fada?Koda yake sanar damu yadda ki ke son mijinki ya kasance? Ummi ta ce "Na farko mai son Addini,Mai Ilimi duka 2,mai hakuru ,sannan yana da saurin fushi,mai kuzari da kwarjini. Ma"abocin tsafta da tsantseni,wandadk tufafin da yasa sai sun kar6e shi,mai biyayya ga iyayensa,sannanmai kula da gidansa,baki mai tsare gida,ga yawan Ibada, Safiyya da khadija suka kwashe d dry,Khadija ta ce, Ina za ki samu dk mai wadannan lissafin da ki ka yi??? Safiyya ta ce, Kuma fa bata gama lissafin ba ke ba ki ji ana cewa dan Adam tara yake bai cika goma ba? Ummi ta ce,Akwai shi,Ya Abbanmu haka Halayansa suke. Yanzu ma da ni ke lissafin shi na ke kallo a idona.Khadija ta ce,To ba dan uwanki ba ne da shi kenan kin samu a gida.Ummi ta ce,Wuu fitina Road,wannan ya mugun tsanata, ina son dai me irin halayarshi ds dabi'unsa.Khadija ta ce,Har da kamaninsa? Ummi ta ce,sosai ma. Saitaga sun sa dry.Safiyya ta ce, Malma shi ki ke so,kuma dk yanda a ka yi ba shakikin ki ba ne,da aure a tsananinku. Umma tayi Shiru tana kallonsu,Khadija ta ce,Habiba kenan,wai har saurin fushinshi tana so. Ummi ta 6ata rai tare da cewa,Tunda kun kasa fahimtata shi kenan.Ya zan yi in ce ina son Ya Abba yana da matarsa? SAfiyya ta ce,ke dai in da aure Tsakaninku kada ki tsaya "ZURFIN CIKI, kizo a karshe kina da kin sani. Ummi ta ce,A bar zancen. 32... Sai dai kuma a daran ranar ta tsinduma duniyar tunani.Tabbas zuciyarta da shisshiga take,tunda ta rasa wanda zata so sai Ya Abba. Wanda ya yi mata muguwar tsana.Afili ta ce,Duk kauce-kauce da kewaye-kewaye ba za su kai ni ba,Ya Abba nake so. Hawaye Suka soma sintiri daga idanunta. Wannan lkcn ziyarar da yazo Abba da Umma d Tsohuwa da Alhj Karami dk suka zo. Dadi ya kashe Ummi,ta rasa jikin wanda zata fara fadawa don dadi. Alhj karami ta soma kamkamewa

Chapter 9 of 24