Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
sannan Umma,Tsohuwa kam ai tana manne jikinta hr suka zo tafiya.Shi ko Ya Abba yanzun kunyarshi take ji,dn haka tunda suka gaisa mgn bata kara hada su ba. Sai dai jife-jife suna satar kallon juna,in sun hada ido sai ya dan daure fuska.Safiyya da khadija sun gaisa da su sannan sun yaba da yadda a ke ji da Ummi. Da za su tafi kuwa Ummi kuka Tsohuwa kuka,sai da Abba ya ce ba za a sake zuwa da su ba,Sannan Ummi tayi shiru.Sun tafi sun barta d kewarsu,Kamar yadda suma suka tafi suna kewarta. ********** . Bishira da kanta ta dauki Walid ta kai ma Umman Bashir,domin ta san zai kai ma Ummanshi ne. Abba ya rufe ta da fada lkcn d y tambayi dan ta ce ta yaye shi ta kai ma Umman Bashir. Ya ce To je ki dauko mn yarona,dn ba can nayi niyyar kai shi ba,Ta rike kugu,kaje mana da kanka,tunda ba ka son zamn danka hannun mahaifiyarka to ni ba zan yi saken da Mahaifiyarka tayi ba a ka raba ta da danta ina fata ka fahimci karatuna? Kallo kurum ya bita da shi,sannan yaja tsaki tare da cewa,Dube ki kmr wata Bauna,jiki sai tsami yake. Ta ce,Eh dk abn da zaka ce kace. Ya juya ya fita rai 6ace. Umma ya Samu ya fada mata, ta ce, To menene na bata rai Abba? Can din da nan ba dk daya ba ne? ai ba za su cutar da shi ba. Ya ce, ki fahimce ni Umma,ba ina nufin zai cutu ba ne,amma can da yara kanana,nan kuma babu. Sannan......... ...... Sai kuma ya yi shiru tare d cewa,Shi kenan. Umma ta ce,Yauwa bana son kana daga murya kan abn da bai kai ya kawo ba. Allah ya raya mana shi ya kuma sauketa lfy. Abba Ya ce Ameen. Gidan (T.V)sun kira Abba sun masa (intervier)da kusan wata 2,dmn ya cire ran samun akin, ko da yaje suka ce sun dauke shi aiki. Abn d yasa suka yi jinkiri daukarshi,suna canza tsarukan aikin ne sannan sun sake tantance ma'aikatansu. Litinin Abba ya soma zuwa aiki kmr yadda a ka bukata,dakin watsa labarai a ka kai Abba. Sam bai samu matsala ba,dk d shi na mai yawan surutu ba ne,amma a cikin sati 1 ya goge da aikin,km an yaba da yadda yake watso labarai. Yana yi da Hausa minti sha biyar da turanci minti sha biyar,ana sakawa karfe 7 na yamma. Abba ya kama aiki cikin sa'a nan da nam sai farin jini cikin abn d bai fi wata ba ya nemi izinin a bashi fili koda mint 15 ne don gabatar da wani fili da ya yi masu don matasa. filin yana kiran shugabannin matasa na unguwanni suna hira da su akan halin da matasa suke ciki na shaye- shaye da sace-sace da kuma rashin sana'a. Da turanci a ke shirin,sannan a kan baiwa sauran matasa na gida su bugo waya su fadi nasu ra'ayin,game da abin da ya kawo hakan,da kuma hanyoyin da za a bi don magance su. Haka nan ya kan samu lkc ya shiga cikin matasan musamman ma su shaye-shayen da marasa sana'a dn jin ra"ayoyinsu,da dalilan fadawarsu cikin harkar. Kafin wani lkc filin ya yi suna kuma kullum yakan tallata filin kan cewa ya kamata Gwamnati ta dauki nauyi filin don yana taimakawa mata wurin inganta rayuwar matasa. Cikin ikon Allah sai gashi Gwamnati ta yaba da filin,ta dauki nauyin shirin kuma an sa shi hr fannin Radiyo. Lallai Abba ya shigo da kafar dama,Sannan hukumar gidan Radiyo tayi Matukar farin ciki da zuwan Idris Aminu Idris,wannan Ma'aikata. Sannan sai Abba ya zama wani sabon tauraro wurin Al'umma,dk in da a ka ganshi ya zama abn kallo. Matsalar shi daya gidanshi,in ka ganshi a waje Sam ba za a kayi tsammanin haka zaka samu gidanshi ba,Dattin ya karu,musamman da ya kasance yanzun ba shi da lkcn kanshi ballatana ya yi sammakon share gidan. Wankinshi mai kaiwa yake yi,haka nan nasu ya ce ta dinga kaiwa makota gidan wanki. Amma kafin ta hada ta kai aiki ne ita dai tayi kallo ko a shiga makota hira. Sam Abba ko adreshin Zai bada ya gwammace ya bada na gidansu Ummanshi dn ba ya so aje gidanshi ************* . Kwanci tashi Ummi suna ta fana da jarabawa zuwa (SS2) cikin ikon Allah suka gama. ranar da aka yi musu hutu kamar ta sani bata tsaya jiran Abba ba,Ta nufo gida. Shi kuwa lkcn suna kici-kicin kai Bishira asibiti zata haihu,amma yana sane da cewa yay Ummi zata dawo kuma hnklinshi na can. Motar wani Salis Abokin aikinsa ya aro ya kai su asibitin ita d Ummanashi. Bayan ya ba d dk wani abu da suke bukata ya ce Umma za shi dauko ummi. Umma ta ce,Ka barta tukunna in matarka ta sauka lfy gobe sai kaje tunda tana mkrnt ne. Ya yi-ya yi Umma ta ki,dole ya hkr. sai bayan la'asar sannan ta haihu,Nurse ce ta zo tayi musu albishiri an samu 'ya mace. Bayan an kintsa uwar,sannan a ka kaita dakin hutu,su kuma a ka kawo musu 'yar.Nurse din da ta kawo 'yar ta ce d Umma ke ce Mamanta? Umma ta ce,'Eh."Nursr din ta ce "kazantar yarinyar tayi yawa,kafin ta haihu sai da likita ya korata ta yi wanka,muka yi mata aski ko'ina jinkinta datti. Gsky Mama mijinta yana kokari,yanzun kuje ku dafa ruwan dumi ku kawo mata tayi wanka. Abba ya yi tsaki ya ce, kin ji ko Umma,Allah ya kara.Umma ta ce,Yanzun kaje gida ka dauki babban filas dina ka shiga wurin Umman Bashir ka ce Mata ta dafo ruwan Zafi,daga nan ma sa ji haihuwar. Yana shiga gidan tun daga zaure ya jiyo Muryar Tsohuwa tana cewa,Naji shiru-shiru kin ga dai hr yanzu. Yana saka kafa a tsakar gidan muryar Ummi ta daki dodon kunnanshi.in da ta ce,Kila kuma ta haihu yanzun. jinin jikinshi ya tsinke dn jin Muryae. Ya nufi dakin.Tana zaune tana shan rake. Ya dubeta, ita ma shi take kallo dn tunda ta diro ba wanda take muradin Gani irin shi,cikin sanyi murya ya ce,Ummi ke da wa ki ka taho? Ta sunkuyar da kai,Ni da wasu 'yan mkrntrmu ne muka dawo. Ya ce '"Good,tashi ki dafa ruwan zafi ki zuba a babban flask. ya dubi Tsohuwa da take ta tambayarshi ko mai dakin nashi ta sauka? Ya ce, Eh ta haifi 'ya mace. Tsohuwa cikin takaici ta ce,Sai yanzu kaga damar bani amsa?Dan walakanci kawai? Kai mai sunan Malam ka gyara halinka. Abba ya ce,Yi hkr Tsohuwa dk na gaji ne,Nan kuma ina yi wa Ummi mgn. Ta ce kana mata fadan ka dai. Ya ce,Tsohuwa wai ni hr yanzun ba zan wanku a wurink ba game da Ummi? ta ce, Ina fa zaka wanku?Har abada mai sunan Malam kai ba me kaunar takwara bane. . Yace to naji a bar maganar yanzu dai kishiyarki ta haihu.an samu ya mace.tace Allah ya raya mana. Yana jingine da bango yana kallon ummi tana ta shige da ficen daura ruwan zafi.komai cikin tsafta da natsuwa take yi. Sai da tasa ruwan zafi ta wanke flask din kasancewar anjima ba'ayi amfani dashi ba.ta tafasa ruwan tazo ta bashi,ya ciro wayarshi ya mika mata. "sa min a caji naga nepa sun kawo wuta" ummi ta jona waya sannan ta ci gaba da girkin dare don tasan Alhaji bai cika son wani abu da dare ba sabanin tuwo. Ta gama wanka sannan tayi sallar magariba tana kwance gadon tsohuwa tana tunanin abba. Tsohuwa nata lazimi in tayi magariba bata tashi sai tayi isha sannan taci abinci.ummi ta tuna wayar da yaya abba ya bata ajiya. Da sauri ta tashi tare da cewa "ke tsohuwar nan anzo tayaki hira kin share mutane" ta mike ta nufi daki ta dauko wayar ta kunna HEHE KIN MANTA YAYA ABBA KENAN?" Sakwanni ne sukai ta go slown shigowa sannan sai kira tashin farko data daga wayar muryar mace taji, ta ce "dawa nake magana" wadda ta kira ta ce "ina mai wayar?" ummi tace "dq matarshi kike magana,ke din wacece?" waccac n ta ce "in yazo ki tambayeshi? yasan me lambar." nan da nan sai ummi ta samu kanta yana juyawa,tayi tsakita kashe.ta shiga duba sakonnin da yawansu na mata ne masu sonshi,daidaikune na maza masu nuna yabawar aikinsa.hankalin ummi ya tashi ganin yadda mata suke farautar abinda take tsananin so.ta kashe wayar cike da nadamar kunnata Hankalin Ummi ta samu kanta yana juyawa,tayi tsaki ta kashe.Ta shiga duba sakonnin da yawansu na mata ne ma su sonshi,dai-daiku ne na maza ma su nuna yabawar aikinsu. Hankalin Ummi ya tashi,ganin yadda mata suke farauta abnda take tsananin So. Ta kashe wayar cike fa nadamar kunnata. Sintiri ta dinga yi a tsakar dakin,Sallamarshi ce ta, katse ta.Ta amsa ciki,sannan ta zauna ba tare da ta kalle shi ba. Ya ce,Bani wayata da abinci 'yan asibiti. Ta mike ta dauko masa abncin,sannan ta bashi wayar.sai dai tana yin komai ne fuskarta daure. Ya ce,Lafiya na ganki wani iri?ta dago ido ta kalle shi,ta sake tsuke fuska. lfy lau.Ya ce,shi kenan na tafi Sam bata tanka ba. Yana fita ta mike a kujera,so takeyi a lkcn ta samu makanta mafita,shin ko dai ta tare shi ne ta fada masa? wata zuciyar ta ce,In ko ya dinga kwallo da ke sai kin rasa mai cetonki. Ta tashi tare da cewa,Bari kawai in fada ma Tsohuwa.Zuciyarta ta sake rayawa.Tsohuwa fa ba zata yarda ba, domin kullum tana bada shaidar tsanar da Ya Abba ya mata,ta koma ta zauna. Sai ta samu kanta da fashewa d kuka,tana fadin wannan wace irin fitina ce ta same ni?me yasa zcyt ke son tozarta ni? Me yasa zata so wanda ya tsane ta?Ta mike ta shige uwar daka. Gado ta hau tana son ta lallashi zcyrta,dn ta daina son Ya Abba. Shi kuma yana tafe a mashin zcyrshi na mitar bata gaji da ganin Ummi ba,yadda take ta kai kawo ya ke gani a idonshi. Lkcn da ya kai musu abnci me jego ta gyare,dama ta zubar d jini ne shi yasa suka ki sallamarta,sukace sai da Safe. Ya samu kannanta sun zo da wata 'yar Babnsu.Sun gaisa an yi 'yar hira sannan suka ta fi lkcn ya dauki 'yar ya yi mata kallon sosai. Ya dubi Umma kin san yarinyar nan da wa take min kama?Ta ce,A'a. Bishira ta tsare shi da ido,ya ce lkcn d Ummi na karamarta sak wannan. Umma ta ce,Kana nufun d Ummi take kama?ya ce,"Eh,Bishira ba kunya ta ce,Allah ya kyauta ni 'yata bata kama da wata can wai ummi. Umma tayi saurin cewa,Dama zolayarki yake ba suyi kama ba.Shi kuma ya kalleta.Ko ki so ko kada ki so yarinyar nan sak take kama d Ummi. Ya mika ma Umma ita,yana ci gaba da fadin Maman Walid kina bani mmki,kina zaton zan ki raba 'ya'yanku d Ummi? Ya girgiza kai"Sun hadu hr abada ,domin in kin tsaga jikin 'ya'yanki dole za ki ga jinin Ummi. to ya ya ma ki ke tsammanin zan so wanda ba ya son Ummi? Ta ce, "Oho! Ni ba ka sona kenan?To in da na gode ma Allah dk dyniya ta san cewa Ummi bata kaunarka.dk da kana wanta.Ba ita ba ce silar kariyarka?ko an kashe ka ma bata da asara. Umma ta ce,'Abba jeka ban son in kuma jin bakinka in na isa. / ZURFIN CIKI book 2 part 7 ZURFIN CIKI book 2 part 7 Posted by Bashir Sani Fesan on 15 Dec 2016 - 00:16 Ta samu an saka ranar auren fati da saurayinta Fahat,nan fa Alhj ya ce dama ke ni ke jira uwata ki dawo. A masu sonki ki fito da daya a hada auranku da 'yar uwarki Fati. Hankalin Ummi ya yi matukar tashi,ranar kasacin abnci tayi. Da suka zauna da Umma a daran ta ce Umma baki fada ma Alhj bani da tsayayyen saurayi ba?Umma ta kalleta,ba shi yasa na ce Kitsada ba,amma ba kya son fita. Duk kin bi kin kori masu sonki Abba na daure miki gindi,kin san dai Alhj ba yarda zai yi ki wani ci gaba ba,gara ma kin yi kokarin fidda miji kafin lkcn da ya dibar miki,in ki ba haka ba ya daki da mai rabo. Ummi tasa kuka ranar,kwana tayi tunani hr ta yanke shawarar zata fada ma Alhj Ya Abba take so. Da safen taje hr dakin Alhjn ta gaishe shi,ya ce uwata naga kamar bakinki da magana ko?Ta dube shi "Eh,a'a ba komai.Ta mike,dakin Tsohuwa ta shiga ta haye gado ta soma kuka. Tsohuwa ta dubeta a rude,Takwara ke da waye,? Nasan ba zai wuce me sunan Malam ba,dn shi ne kadai ke hana ki sukuni. A ran Ummi ta ce,shi ne kam,amma ba irin wanda ki ka sani ba. Amma a fili sai ta ce,Tsohuwa Alhj ne wai in fito da miji,kuma abn da ke damuna ni ba wanda na ke so. Tsohuwa ta ce, "Au, shi ne abn kuka?To bari kiji bana ba zan goyi bayabki ba,dn da ubanki ya ji ta tawa da yanzyn kina da diya 2 in da rabo. Amma mai sunan Malam ya ce za ki ci gaba da krt,yamzun ko tun da Allah ya kawu mu angama wannan kaddararriyar mkrnt ba sai aure ba? Ga Bunta nan hr an yi baiko, to rana guda za a yi shi in muna cikin masu rai. FUU Ummi ta fice,ta shiga dakin Umma tana tunanin wa zata fada ma matsalarta?kamar an tsikareta ta dauki mayafi zata fice. Umma ta ce, "Zo nan, ina za ki? ta ce "Wurin Fati. Tana shiga Bashir zai fito . Ya ce Yauwa Ummi ina son magana da ke. Ta dawo baya ya fita kofar gida ita ma ta fito,suka tsaya ya ce "Ummi gaskiya dama ba wani abu ba ne, ni dai na tsinci kaina da sonki. Ummi ta dafe kirji da sauri."Sona?" ya ce kwarai kuwa, dn haka za ya ki ka gani?ta dube shi,sam babu wata alama da ke nuna cewa dan uwan Ya Abba ne. Ta girgiza kai "kayi hakuri kawai Ya Bashir,wlhy zuciyata ta jima da kamuwa da son waninka." ya ce, Me ki ke nufi?Kin fi son bare da ni jininku? Ummi ta ce,"Ni dai na fada maka." Ya ce, "To kin fada min,ni kuma zan fada wa su Alhj." Gabanta ya fadi. Shi kuma ya yi tafiyarsa, . Sabon tashin hankali kenan. Sai damuwa ta lunku,bata ta6a marmarin zamn mkrntr kwana ba sai ranar. Ta rasa me zata yi taji dadi,gida ta koma cike da nadamar fitowa,ta zauna a falon Umma ta soma kuka. Umman tana dakin mijinta ya yi karin kummali. Sai da ya fita sannan Umma ta maido hankalnta ga lamuran gidan, kan kujera ta samu Ummi ta nata rera kuka. Umma ta ce "Ke Ummi lafiyanki? Abun ya soma zama iya shege,daga cewa ki fito da miji sai ki tsira kuka? To ina ganin kwadantaki zamu yi muci. Ummi ta ce, "Ni fa ba kukan da nike yi ba kenan,ni fa Ya Bashir ne fa. Umma ta ce Bashir me,? kiranki aka yi? Gara daya da ke ki. ta ce ba fa dukana ya yi ba wai cewa yai wai fa yana sona. Tab,Allah ya tsare ni. Umma dn Allah bana sonshi,gaban Umma jikinta a mace ta ce "Tabdi,ai ko in Alhj ya ji wannan zancan ta zauna. Ummi ta sake firgicewa, cikin kuka ta ce Da na shiga 3 Umma, ya ya zan yi ne don Allah?Umma ta ce,"Mafita daya ce ki fidda wani kafin zancan yaje wurin Alhj. Yinin ranar Ummi ta rasa mafita Addu'arta daya,Allah ya turo mata ko ma waye a daran yau ta ce ya turo iyayenshi. Wayar Umma tana hannunta,ta rubuta text ta goge yafi sau 20 da niyyar ta tura ma Ya Abba cewa tana sonshi,amma da ta tuno da irin dukan da zai zo gidan ya yi mata in ya karanta sai ta share. Ita dai ta san shi kadai take so. Tayi Sallar Istihara kusan sau 3,amma hr yau zcyrta na nan makale da son Ya Abba. Don bayan Isha'i kuwa a ka aiki kiranta, ai tare da dan aike suka fita. Wani saurayi ne wai shi Sahabi,dan unguwar ne Kuma sana'ar aca6a yake yi. Na dai manta. Suka gaisa ya gabatar da kanshi sannan ya fada mata dalilin zuwanshi ba tare da wani nazari ba,ta ce ta amnice. suka yi sallama ta dawo gida,umma ta tambaye ta wanene?Ta fada mata,sai dai Umma bata gane shi ba. Can jimawa Bashir ya aiko Kamal kaninsa wai Ummi tazo,ta ce kaje ka ce masa ba zan zo ba,ya sake aiko shi cewa in bata zo ba shi zai shigo. Umma ta ce mata tashi kije. Ummi hr d kuka ta fita,dn a rayuwarta ta tsani Bashir,sbd yanda ya raina Umma. Kuma ba ya ganin kowa da gashi sannan tana ganin in hr ta auri Bashir zai mata tsakani da auren Abba. Tana zuwa ta same shi zaune a dakalin kaofar gida,ta isa gurishin. Ya Bashir kiran me ka ke min? Ya ce,kin sani kema. Ta ce Ya Bashir dn girmn Allah ka bar ni ba,Usaina gidan kurma ce buduwarka ba? Ya ce Da ba, ya ci gaba da cewa,Ummi ina sonki so na hakika nayi mamakin yadda lkc daya zcyta ta kamu da sonki,to wai dn Allah ni me yasa ba ki sona? ta ce Ya Bashir ina da wanda nake so tun farko..........kamar daga sama suka ji muryar Abba yana cewa,Kai Bashir me ka ke fada? ya ce sonta nake. Abba sai da wayarshi da ke hannunshi ta kwace ta fadi don figici,bai bi takan wayar ba ya isa gabn Bashir ya ce, In ka kuma furta kalmar so ga Ummi sai na maka matsiyacin duka,ke kuma hr da fitowa kin zo tadi ko? kafin tayi magana ya ce,Bace min daga nan. Bashir ya ce,Amma ai ba laifi ba ne don nace ina sonta? Abba ya bige mishi baki tare da cewa In ji wa ya ce maka ba laifi ba ne?Bashir ya ce,An haramta aure tsakaninmu ne? Abba ya cakumo wuyan rigarsa Ni ne nan na haramta haka,kuma kar in kara jin wannan mgnr. Bashir ya fige ya nufi gida yana fadin cewa Yau zan samu Alhj da mgnr. Ina ruwanaka da zaka ce ka haramta min sonta? . Abba jikinshi hr 6ari yake dn tashin hankali, yasan in mgnr taje teburin Alhj to ta kullu yanda yake mishi mgnr hada auran Ummi da Fat. Har ya saka kafa a zauran gidan su Umma,sai kuma ya fasa ya dawo ya nufi gidan su Bashir din,yana saka kafa a zauren gidn Alhj Krm na fitowa. Don haka sai yaja baya,Alhj ya fito ya ce,A'a Abba ne? Abba ya ce "Eh ni ne. Ya gaida Mahaifin nasa,sannan Alhj ya tambaye shi cewa Babn naka yana gida? Gaban Abba ya yi mummunan faduwa,ko dai Bashir ya fada wa mahaifinsu ne? Alhjn ya ce ko ba ka ji ba?Abba ya ce "Eh a'a ban riga na shiga gidan ba. Alhjn ya ce To bari in ganshi. Nan jikin Abba ya jike da zufa. Da azama ya shiga gidan. Mahaifiyarsu tana alwala ya ce Umma ina Bashir? ta dube shi Lafiya ba ko sallama? ya ce Nayi ba ki ji ba ne? ta amsa sannan ta ce lfy ka ke nemanshi? ya ce lfy lau. ta ce Yana daki,shima na ganshi ya shigo a fusace. Abba ya nufi dakin. Bashir na zaune kan katifar idonshi na kasa yana girgiza kafarshi ta dama,Abba ya shiga ya ce,Bashir nazo ne in sake gargadinka a kan Ummi,sai dai naga hr kayi kuskuren fada ma Alhj krm ko,? Bashir ya mike ya daga sauti Ban fada mishi ba,amma ina da niyya. Ina sonta babu wanda kuma ya isa ya hana ni sonta. Abba ya kashe masa fuska da mari. Sai suka ji muryar Mahaifiyar tana cewa, Kara mishi Abba,ka cika dana. Ta shigo dakin hr gabn Bashir ta ce, Ni za ka tozarta? kayi kuskure. Ai da in ga ranar aurenka da Ummi gara naga gawarka kwance yafi min sauki. Abba da Bashir suka dubeta a rude. Ta ci gaba da cewa Bashir kai ma kasan ba zai ta6a sa6uwa ba ne in hada jini da Suwaiba,kafi kowa sanin kin da nike mata,zan iya daukar ranta ba don tsoron hukuma ba. Kuma hr dny ta nade ba zan ta6a kaunarta ba,kai ko fatan alheri ba zan ta6a mata ba. Ta kalli Abba, Baka ta6a faranta min rai ba irin yau,dama nasan cewa dole wata rana ka bayyana dana in dai kai jinina ne,na gode Allah da yasa ka zama mai kishina Kuma ka wanke dukkan laifukan da ka min a baya da ka nusar da ni Bashir na shirin jefa rayuwata a cikin garari,da ba ka mishi mgn ba yaushe zan san yana shirin jefa ni cikin bala'i. . Abn da Umma bata sani ba shi ne,tuni Abba ya yi mutuwar tsaye,hnklshi ya ninka na Bashir tashi,dn haka Bashir ya riga shi fita daga dakin. Da kyar Abba ya dago ido ya kalli Umma,ta ce Daina damun kanka shi ma din ko ba don Allah ba zai dawo hanya,duku-dukayau sati guda fa kenan da naje kauye na saida 'yar Akuyata guda daya sannan na bada kaji 2 ga Bokan kuka sbd a min akin da Ummi ba zata samu miji ba. Sai kuma a ce ko satin bai rufe ba dana na cikina ya zo ya ce yana sonta? Da sauri Abba ya dafa kirji Umma Boka! Boka ki ka ce Umma? Inna lillahi wa'inna ilaihin raji'un,Umma kin san cewa zuwa gurin Boka shirka ne ga Allah? kin san duk wanda ya mutu a shirka Allah ya yi alkawarin kona shi a wuta?Umma kina cikin hadari............ta kaste shi. Kai Abba!Ni ce nake cikin hadari?Ni ce Allah zai kona a wuta? ya ce, umma bana nufin haka, ina fada miki ne ki kiyaye da zuwa gurin Bokaye makaryata,macuta 6arayin Imanin Jama'a. Na ranste miki da girmn Allah umma Bokaye 'yan wuta ne,matsawar ba su tuba ba. Ta ce, Kai ni rufe min baki,da za ka ce karya ne sau nawa suna min asirn kuma yana ci. Ba gashi nan da ya min na kada Ummi ta riga Fati samun miji baga Fatin ta riga samun ba? ummi kuma ba ta d masoya. Abba ya ce, Umma kin ga karya ko? wa ya fada miki Ummi bata d masoya? ta ce, To me yasa ba wanda ya tsaya? Ya ce, Ni dai Umma ki bar zancan nan a wurina, Bashie zai bar Ummi ko yana so ko baya so,dn haka na hada ki d girmn Allah kada ki koma gidan mishieikin Bokan nan. Ta ce, Ba zan koma ba in hr zaka raba Bashir da alakakai din yarnyar nan. Ya ce Na miki Alkawari. ta ce, Shikenan. Ya fice jiki babu karfi.URFIN CIKI book 2 part 8 ZURFIN CIKI book 2 part 8 Posted by Bashir Sani Fesan on 15 Dec 2016 - 00:18 Kasa shiga gidan su Umma ya yi,haka nan ya manta sam da batun motar da yazo da ita a kofar gidan Umma. Ko Bishira bata san cewa ya shigo gidan ba,tana can jarabar kallonta na tsiya,ya rufe gidan ya nufi dakinshi. Ranar mu2m 5 bacci sai dai 6arawo,Umman Bashir kwana tayi saka da mugun zare. Umman Abban ma juyi kurum take yi hr Alhj ya gaji ya ce,Yau dai sai juyi ki ke yi. ta ce Na kasa bacci Alhj. Ya ce, Tashi to kiyo alwala kizo ki kama sallah,in kina da damuwa ne sai ki fada ma Allah. Umma bata tsaya ba,ta tashi. shi ko Abba wani matsanancin ciwon kai ne ya hana shi sallah. Ya dai yi nasarar yin alwala da ya shiga daki sai jiri. Dole ya kwanta rigingine tare da dafe kanshi da hannuwa guda 2,sunan Allah yake ta kira dan neman dauki. Ita ko Ummi dirshan ta zauna tana kuka,hr sai da hawayenta suka kafe,idanunta suka shiga zafi,kanta ya soma sarawa gefe daya. Ita ma ringingine ta kwanta tare da lumshe ido,Istigfari kurum take yi tare da hailala,shi ko Bashir mafarkai ne suka hana shi bacci,dk mafarkan na Ummi ne. Da safe da matsannancin zazzabi ya farka,dn haka bai iya zuwa Masallaci ba,da kyar ya yi alwala.yana idar da sallah ya kundundune cikin bargo. Matsanancin ciwon kan da Ummi ta tashi dashi ya firgita 'yan gidan,Musamman Umma wadda ta same ta kwance a tsakar daki da safe. Ganin fuskarta a kumbure ya tsorata Umma,hr sai da ta kira Alhj.Nan fa Alhj ya dauko wayarshi ya shiga kiran Abba,kan cewa yazo ya kaita asibiti. Sai dai tayi ringing ya kai sau 10 amma ba a daga ba. Alhj ya ce Ina yaron nan ya shiga ne?kuma ga motarshu a kofar gidan nan,na ganta da asubahi da na fita Masallaci. Umma ta ce,Tao Allah yasa dai lfy. Har karfe 8 Alhj na neman layin Abba shiru ba a dauka ba,ga Ummi rike da kai tana ta salati Umma ta ce,Alhj ko Bashir za ka sa ya duba shi? Alhj ya koma daki ya dauki hula ya nufi gidan Abba. Gidan a kulle ya same shi,dn haka ya dinga bugawa.Abba na jiyowa amma ba zai iya tashi ba,haka dk ringing din da wayarshi ke yi yana ji ya kasa tashi ne. cikin bacci Bishira taji bugun gida ya yi yawa,ta tashi ta bude. Da Alhj suka yi ido 2,ya ce lfy ba ku tashi ba? Ta ce Mun tashi. ya ce Ina maigidan naki? ta ce Ina ga ya fita,bari in duba. Ta juya ta nufi ciki. Alhj ya cika da mmk,ya za a ce wai mace bata san fitar mijinta ba? Anya wannan matar tasan darajan mijin? Tunaninshi ya katse lkcn da ta dawo tana cewa Alhj yana kwance ba shi da lfy. Alhj ya bita yana cewa Ba shi da lfy,amma ke ba ki sani ba?Wanna wane irin zama ku ke yi ace kina matarsa amma ba ki san cewa ya tashi ba lfy ba? Bishira ta ce To ai shi ne bai kira ni ya fada min ba. Alhj ya ce, Allah ya kyauta. ya nufi dakin. Abba na kwance ya kundundune cikin bargo sai rawar sanyi yake yi. Alhj ya yi Sallama ya shiga dakin ya rusuna ya daga daidai fuskarshi ya janye bargon ya ce, Abbana ba ka ji dadi ba? Abba ya bude ido,idanunshi jajir,ya ce Abba kaina ne tamkar zai 6alle. Sai zazza6i tun daren jiya. Alhj ya ce,Ikon Allah Yau kuma abn da na wayi gari da shi kenan? Ummi ma na can kwance da ciwon kan,to tashi. Shi yasa nake ta kiranka don ka kaita asibiti amma da ka daga ba. Yanzu tashi in za ka iya ka kira Ahmada abokinka sai ya kai ku asibitin. Abba ya ce To Wayar Ahmada din a kashe don haka sai Alhj ya ce "Af, na tuno da Bashir,kintsa bari in je muzo naga mator can kofar gidanmu ko?Abba ya lulubo makullin motar yaba Alhj., Zani kawai Umma ta daura ma Ummi,sai ta zura mata hijabi,suka shiga bayan mota su 3 da Umma da Alhj,sukaje gidan Abba suka dauko shi. Bishira

Chapter 10 of 24