Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
ne in ka mutu ka sadu d rahamar Allah,ita kuwa Rahama bata samuwa g wanda bai bi Allah d manzo ba. Bn Allah kuwa shine kada ka bata masa,kabi dukkan abn d Manzonsa ya yi umurni,Sannan ka hanu daga abn d ya yi hani. Aure bautar Allah ne Kum sai kayi hkr sannan za ka yi bauta d kyau. hk dai umma tayi ta wa Abba nasiha hr zcyrsa t sauka, sannan sukayi Sallama. Washe gari misalin karfe 2,Abba ya dawo gida dg mkrnt d yake koyarwa, dn suna ta shirye-shiryn jarabawa (J.S.C.E.) Su ummi ne za su zana,wnk y fito sai ga wayr Alhj ta shigo.Y daga cikin girmamawa. Bayn sun gaisa Alhj ya ce Abbana kana ina ne? Ya ce ina nan gida.Alhj ya ce kaje gidanmu ka amshi mukallin dakina ka shiga kasa mukallika bude dirowar nan tawa,zaka g wadansu ta kardu irin littafin nan na rubutu. kabi a hnkl za ka g wani a samnshi an rubuta Alhj Sale Jigawa,d ajami ne rubutun,maza ka kawo min. Abba ya ce to.,Yana cikin duba littattafan sai ya ga wani an rubuta wasiyya,dk littattafan d ajami Alhj yake rubutu, Abba ya dauki littafi ya bude shafin farko an rubuta........ Babi Na Daya "Ni Alhj Sulaiman, nayi kudirin ko bayan raina 'yata Habiba (ummi) zan aurar d ita ga dan Idrisu(Abba). Da sauri Abba ya rufe littafin gabnshi yana wata muguwar faduwa,ya sake budewa ya kalli kwanan wata. Alhj yayi rubutun ne ranar d a ka haifi ummi,Ya yi sauri ya maida komai ya dauki wnd aka aiko shu yana zufa ya kalle dakin ya maida wa umma makullin ya fita da sauri Ya buga mashin can ya hango ummi suna dambe da wani yaro an raba su ta tirje kafafunta ba ko takalmi, mayafinta taci damara da shi. Ya ce "Ke! tn dg nesa ta jiyo muryar Abba,ya yi mata dakuwa ta kwashi takalmanta a hannu ta yanka d gudu. Yabi ta da kallo hr ta shige gida ya lumshe ido tare d fadin "Innalillahi wa'inna ilaihin raji'un."Me ma ya kai shi bude littafin wasiyyar Alhj Babba, Duk garin kano akwai mutumin d ya tsana irin Ummi?? To fa! ku biyomu a littafi na biyu rk ****ZURFIN CIKI :-2**** ta dafa kafadata tana cewa kayi haquri mubarak na sani kana son nabeelah sannan itama tana sonka,sai dai kuma kayi kuskuren rashin bayyana soyayyarka gareta a sanda ta bukaci hakan,nayi kokarin dai- daita tsakaninku amma naji tsoron kada mutane suyi tunanin na aurar da nabeelah ga d'ana ba bisa son ranta ba sai dai bisa dole kasancewar ta girma a hannuna.......haka kuma yanzu bazan saka kaina cikin wannan matsalar taku ba amma zan goya muku baya bisa dukkan shawarar da kuka yanke,idan kuna nemana ku sameni a fallow*** na kalli nabeelah idona cike da hawaye na fara magana kamar haka'nabeelah ina sonki,kuma ina kaunarki, sai dai na kasance cikin irin mutane da sukan boye sirrin zuciyarsu,kiyi haquri ki gafarceni,nasan nayi miki laifi...nagode ki tashi ki tafi allah ya bada zaman lafia sannan allah yasa shine mafi alkhairi gareki........na miqe zan fita daga motar,ta kamo hannuna ta zaunar dani tana magana hade da wani kuka mai tsuma zuciya gami da sa tausayi kamar haka'yamubarak da farko na yarda kana sona amma yanzu na gane cewar soyayyar batayi tasiri a zuciyarka ba tunda har ka yarda zaka haqura dani kan wani ya aura,lallai na yarda baka kishina baka tausayina irin zaman da zanyi tare da wani namiji wanda ba kaiba,ka sani cewar zuciya ba zata aminci rabuwa da kaiba,jikina na haramtashi ga dukkan wani d'a namiji idan ba kaiba dan haka na qudiri niyyar mallakarka ka ta wane hali,yamubarak kayi kokari ka soni kamar yanda nake sonka,yamubarak kada ka bani kunya'*** na share hawayen dake zuba kan kuncinta,na kama hannayenta na kwantar da ita bisa kirjina,nabeela h ki amince da soyayyata gareki kada ki zargeni da komi sai alkhairi,nabeelah ina sonki kuma nine mijinki da yardar allah,da sauri ta tashi daga kan kirjina ta dafa kafaduna tana kallon fuskata,ta sumbaci goshina sannan ta rungumeni kan kirjinta tana cewa hakika farincikina ya karu,burina ya cika sannan alheri ya tabbata gareni.....amma *menene mafita? *da wane zance zamu tunkari abba? *sannan kuma lokaci yana da karanci garemu.... Na kalli nabeelah dake kan kirjina nace zaifi sauki muje wurin kawu aminu mu shaida masa halinda muke ciki...ni nasan me zan fada masa kuma zai yarda. *kai tsaye na tuka motar zuwa gidan kawu na tarar ya gama cin abinci yana gindin bishiya yana hutawa..bayan mun gaisa ya cigaba da magana kamar haka'lallai daga ganinku akwai matsala dan naga alamun damuwa gareku, shin ko baki son auren ne? Ya tambaya' na fara da cewa gaskiya kawu ita nabeelah ba wanda take son za'a bata ba,kawu yace wannan zancen banza ne dama shi yasa suke boye min to wallahi wannan maganar babu ita,ku tashi mu tafi gidan.... Na tuka mota har kofar gidan muka shiga shi kuwa kawu tun daga kofar gida yake ta fada..yana shiga su mama suka fito suna gaisuwa amma ko amsawa bayyiba ya cigaba da cewar'maganar auren nabeelah babu na soketa yanzu zata fada mana wanda take so kuma goben zan daura mata aure dashi...nabeelah ta kada baki tace'ya mubarak nake so' kawu yayi dariya yace au to ai shikenan ta kwana gidan sauki kuda dan iskanci abin na gidane ma kuke bata lokaci,to ai ni yanxu xan daura auren idan yaso kuje chan kuyi ta bikinku,sannan baba ya shigo yaji meke faruwa amma ba yanda zaiyi da kawu dan yasan halins doe qura ya zama waliyina shi kuma waliyin yamubarak aka daura auren*** take yamubarak ya daukeni muka tafi gidan kunshi daga nan ya kaini nayi kitso muka wuce gidan aunty nafeesat nayi wanka na saka rigar atamfa kaina ba dankwali na fito gareshi,wow nabeelah amma kinyi kyau,ya kamo hannu daga inda yake zaune gefen gadon,ya sumbaceni har saida numfashina ya dauke,ya kwantar dani kan gadon ya fara cire kayan dake.......hakika ban taba sanin haka yamubarak ya iya soyayyaba sai yau,lallai da tuni nayi asar miji,haka muka kasance cikin nuna kaunar juna har zuwaN CIKI book 2 part 1 ZURFIN CIKI book 2 part 1 Posted by Bashir Sani Fesan on 14 Dec 2016 - 22:05 Abba kwance kan gado,dare yayi nisa amma shi ya kasa bacci sam.saboda matsalar da yake ciki yanzun. domin kuwa matar shi in yaga bazai iya ba sai ya sawwake mata,amma maganar auran ummi koda Alhaji bai goya mishi ba bazai iya guje mata ba. "yanzun menene mafita?"ya tambayi kansa,wata zuciyar ta ce, "kayi shiru tamkar baka ga wannan takarda ba,tunda ba wanda yasan ka gani." a fili ya ce,"haka ne." ya ci gaba da tunanin kila ma yanxun ya janye kudirinshi,tunda yaga ummin bata da kan gado. don yaga rubutun yayi shi ne tun ranar da aka haifi ummi,ko kuma ranar sunanta. tunda gashi har da sunan ummi a jiki.mafita kenan yayi shiru.wata zuciyar ta ce,"in ko kayi haka kayiwa Alhaji da ummanka adalci? koda yar su ba yar adam ba ce bai kamata ka gujeta ba.ko don albarkacin son da suka nuna maka. shin da ummi ta kasance mai jin magana da nutsuwa,kuma mai tsananin kyau zaka gujeta? Kada kayi zaton Alhaji yayi kudurin aura maka yarsa ne don yasan zata zama mara ji,kayi nazari. haka Abba yayi ta tunani har asubah tayi,amma hukuncin da ya yanke shine yayi shiru. sai dai ya janye batun rabuwa da matar shi,don yasan yana sakinta zai zama mijin ummi,kai batun nan hadiye ma cikinshi shine mafi dacewa. dunkuna masu kyau yayi wa matarshi saboda cin suna.haka yayi wa dan siyayya daidai karfinshi,ya kawo ma umma. Taji dadi sosai nan ahj ya iske su, shima ya shiga dakin umman ya xauna ya ce a dauko masa abinci nan xai ci yau.ya dubi abba, babana nayi sautun raguna xuwa qauye nace xa a siyo nmanya.abba ya ce biyu?umma tace hakan yayi.abba ai tuwan girma miyarsa nama, aja rago daya xiqal a shiga wannan gida da shi? abba yace,me xai hana tunda ban musu qaryar arxiki ba sun san mu talakawa ne.ahj yace xancanka dutse bacna,amma maganar ummanka ita xa a bi, sannan xa a sai buhun shinkafa da cefane a kai musu.ana gobe suna abba da abokansa suka dira gidan da ragunan da kayan mai jego da na yaro sannan ga kayan abinci. sun samu anty a gidan,ta musu tarbar mutunci.da yake abba xana waya da ita,ya fada mata komai ta sani.hjy zainu da taji kukan raguna ta fito,anty tace dan Allah momy kada ki musu magana,kin ga shi da abokansa ne.da qar ta samu ta turata sashin ahj,shi kuma murna yayi yace aje a daure su.zainu tace ahj menene na numa farin ciki sai kace ba ma cin nama?can ba xa a ka kada ba dan kawai shagalin sunan, sannan tace harda shinkafa suka kawo sai kace muna yunwa? nana take ya hade rai tare da cewa,zainu kada dai ki ce min kin sa an dawo da yarinyar nan gidan ne dan ki kashe mata aure?tace haba dai. ya ce to hir dinki dan bansan in kuma jin irin xantukan nan yayi ma matarsa daidai arxikinsa. mu kuma mu ma yarmu da jikanmu gwargwadan arxikinmu,in ya fito daga gun mai jegon ki turo min shi,sbd mu ji in da xa a yi sa sunan.tace ina xa ayi in ba nan ba?ya dube ta an taba haka?ki dai turo minshi.ta taba baki sannan ta wuce.lkcn da ta leqa dakin abba da abokansa suna xaune,abba yana ta fama da danne dannen waya,domin tun da suka shiga ya qi ko kallan inda bishira take bare danta.tace bishira ki eada musu in sun fito ahj na san magana da su.ta wuce ba tare da jiran jin amsa ba,ko amsa gaisuwan da abokan abba suke mata bata yiba.bishira ta kalli abba wanda tana hankalce da shariyan da yayi mata,tace kaji abin da momy tace?sai lkcn ya dubeta me tace? yayi maganar ne cikin tsare gida.dadynmu yana san ganin ku. bai amsa ba,sai kurun ya tura mata jakar kayanta,ki duba,ta xaxxage dinkuna ne na gani na fada masu kyau,duk da xannuwan ba masu tsada ba ne kala uku atamfa daya shaea daya sai kuma leshi.sai ko kayan yaron.ta dube shh an riga an sai mana kayan fitar sunanmu.ahmad ya dube ta wannan din baki so? tace ni bance ba.abba yace ku tashi muje.tace ina san magana da kai.ya ce kiyi maganarki.muktar yace kuxo mu fita ta dauki yaran tare da miqa mashi ta ce ina lura da kai rabon da ka dauke shi tun randa aka haifeshi,alhalin mu kuma yana nan yana hana mu baccin dare.kai kana can kana baccin ka.ta fadi haka ne cikin sanyin murya.ya amshi dan tare da cewa ai gara ya hanaku bacci tunda kunqi ku kaishi gurin babanshi.ya tsura ma yaran ido,wata qaunan dan ce take shigarsa.ta matso jikinshi.abba ya kalli furkarta,ita ma kallansa take,ta ce yanxu ko dan murmushin ka bana gani.yace,in da kina san gani da baki dawo ghda ba.yaci gaba da cewa na sha mamakinki bishira,da har xa ki yarda ki dawo gidanku ba da ixinina ba. kuma tun kafin ki haihu sai da na fada miki ba za ki zo gida ba.Ta ce To Abba mony ce ta ce sai an zo. Ya ce shi kenan ku zauna. ya mike mata yaron ta amshe shi ta kwantar ta kama mishi hannu. Abba wane suna ka sa masa? ya ce Sunan Alhj babba. Da sauri ta saki Hannushi . Sunan 'yan da? ya kalle ta Na zaci zaki ce suna mara ma'ana,tund da ne da sauki. ya fice. Haushin hali irin na Bishira ya ke ji.dn son shi yasan tana matukar sonshi,amma bata son yin biyayya ga abn d yake so. Ya samu su Mktr sannan suka shiga gurin Alhj ya tambaye su in d za a sa sunan,Abba ya ce a masallaci kusa d gidn babnshi ne za a yi addu a. Amma tuni an sa wa yaro suna Sulaiman.sunan babana. Alhj ya ce Madalla Allah ya raya mana shi, ba sai mun zo ba dn yanayin sanyi ne. Nan dai Abba d abokansa suka tafi suna yabn Alhjn. An ci sunan shima Abba shi d abokansa sun yi walima da Azahar. matar abokinshi Bala ita ce suka bai wa girkin ta yi masu. Mai jego taci gaba d wnk. Abba kan leka su lkc zuwa lkc,kusan dk lkcn d yaje ba su cika rabuwa d dadi ba sbd mgnr d hjy zainu kn datsa mishi. Umma shi ma bata yi fushi ba tana leka su dk d rashin sakar mata fuska d mai jegon tare d mahaifiyar keyi. Ummi tana tafe tana 'yan tsince-tsincenta,kmr yadda ta saba,sai ko taga sim,take ta yarda dk wani abu d t samu t dauki Sim din. Gefen zaninta t samu ta kulle,sannan ta tafi,cikin jakr mkrntrta t saka.wata rana ta dauki wayar umma ta shige daki,ta bude wayar ta cire sim din ta saka wanda ta tsinto a cikin zani ta soke wayar ta fito soro.Jikin dakin yaya Abba a bakin kofar ta dauki lamar Abba da ya rbt sbd masu zuwa nemanshi tana kira taji wayr tana ringing. Ta kashe tana ta dry,hk tayi ta yi wa Abba Flashing dg nan tayi gidn du Amina kawarta,tana ba wa Amina lbrn abn d ta ke wa Abba. Ta ce Amina nsn yanzun hk yana cn yana jin haushi,shi yasa ki ka ga ina murna.Ta ce in ya gane fa?Ummi ta ce Ai tsintar sim din nayi,Umma kuwa ba za ta san na dauki wayarta ba,domin yaya Abba da Alhjnmu kawai suke kiranta. Amina ta ce Yadda za a yi ki kira shi ne in ya dauka sai ki make murya ki canza suna. Ummi ta ce Tab,dn in ci duka. Amina ta ce Dalla cn gane ki zai yi? suka kira ya daga ummi ta sirantr d muryarta tana fadin "Hello! Abba ya ce Ke wace ce ki ke kiran layina? Ta ce Sunana '"Suhaila. ya ce Menene ki ke kirana?Ina ma ki ka samu lambata? Ta ce Gani nayi ni ma a cikin wayr. Tsaki yaja Sannan ya kashe.Suka dinga tsuntsira dry. Amina ta ce Sake kiranshi ki ce ma ke a kaduna ki ke. Ummi ta ce Kai yin waya akwai dadi ni ina son buga waya. Ta sake kira cikin Zafin rai ya ce Ke lfy??kin dame ni fa!Ummi ta ce To tsaya mana kaji ina son mu gaisa ne ni ina kaduna ne. Ya ce To na gode. Sai ma ya kashe wayar gaba daya suka yi ta kira a kashe. Tun daga ranar Ummi ta samu in umma tana aiki ko tana bacci sai ta sace wayar ta cire sim tasa nata ta kira Abba. Tun yana kyararta hr ya daina ya koma rokon ta daina kiranshi,dk a banza. Daga baya sai Abba ya soma sauraronta, ranar kuma ta kira shi ne misalin dayan dare,ranar taki zuwa dakin Tsohuwa ta kwanta a dakin umma. umma kuma dama dakin Alhj take kwana. A dai-dai lkcn ya kwanta kadaici ya dame shi,ga garin yanayin sanyi. wayar ta katse tunaninshi d yake yi na matarshi zuwa yanzu ya haddace lambar Suhaila. Ya daga ya ce "Hello ya ce Ke wai me ya hana ki bacci?Ta ce Ni ba sunana ke ba,Ni sunana Suhaila,kai fada min sunanka. Ya ce Abba Ta danne dryr d taso kwace mata ta ce Abba ba suna bane,Fada mn sunanka n gsky. Ya ce "Idris Yadda ya fadi sunan sai da ta dage kwarai sannan ta maida dryrta. Ya katseta d cewa Ina ku ke a kaduna?tayi dim,dn dai bata san ko ina ba a garin kaduna ba,ba ta ma ta6a zuwa ba. Take ta tuno Amina sun ta6a zuwa unguwar Sarki,dn hk ta ce "Unguwar Sarki. Ya ce, wai shekaranki nawa? Ta ce Sha takwas. Ta sheka masa karya.Ya ce Amma shi ne a ka ba kiwaya? ta ce ta ka san wanene Babana? Ya ce A"a ta ce, To shi ne mai bawa Gwamna shawara a jihar kaduna. Abba ya ce Lallai, ki ce in nazo kawo miki ziyara ba zan samun ganinki ba? Ta ce za ka ganni mana. Ya ce To zan zo. Ta ce To, Ya ce,Amma fa ina d mata ta haihu ne ta tafi wankan gida. . Ummi ta ce Lallai to sai da safe. Ya ce, Wa ke zuba miki kudi ne cikin waya?Ta ce Babana mana. ita sai lkcn ne ma ta tuna cewa ana saka kudi tunda ta ke kira bai taba kin zuwa ba,aranta ta ce kila wannan ba a sa kudi. Sunyi Sallama babu dadewa,wayar ta sake daukar tsuwwa. Ga zaton Ummi Abba ne sai da ta daga sannan taji muryar wani. Ya ce Da wa nake waya? ta ce wa ka ke nema?Ya ce Me wayr. ta ce Ummata ce kuma tayi bacci. Ya ce Yallabai nake nema. Ta ce Ban san wani yallabai ba,kada ka dame ni Ta kashe wayar tare da jan tsaki. Sannan ta cire layin ta maida na umma Wasa- wasa cikin kwanakin Abba ya soma damuwa da lamarin Suhaila kaduna, lokuta da dama ya kan kira layinta amma sai ya ji shi a kashe. Sam ba ya samunta sai lkcn d ta kira shi,ko da ya yi mata korafin hk,sai ta ce "Eh ita ce ke kashe layin sbd ana damunta. Sun yi jarabawar (J. S. C.E.)sakamako suke jira. dn hk yanzu tana gida ko yaushe tsokana kuwa bata fasa ba. Kullum ita d Amina cikin shirya yadda za su yi wa Abba waya suke, kudin cikin layin ya kare,Abba shi ke tura kati yanzun. Duk lkcn d Abba yazo gidansu d ya ga ummi ya hade rannan yana muzurai,ita km sai ta yi ta sheka dry,dmn tana tuno yadda yake kwantat d murya a waya. Wata rana hr duka ya yi mata sbd dryr d ta dinga yi daga sallamrshi a gdn. Tsohuwa kam ranar yini tayi fada,wai ita za ta bar gidan.Cin kashin d ake yi wa ummi ya yi yawa. A ce rashin 'yancin yakai ko dry ba a son tayi. Da kyar umma ta sha kanta t hkr. Wannan ta kaicin dukn yasa ummi tace ita kam sa tasa shi wahala. dn hk ranar gdn su Amina taje. suka shirya yadda in ta kira shi zata ce yaxo Kd ta ganshi, ummi ta ce mugu dama in yaje ya 6ace in huta. Hakn kuwa ta fada mishi, a ranar d suna waya. Ta ce '"Idris.dn Allah yaushe za ka zo ne? Ya ce Tun yaushe Suhaila nake cewa zan zo amma kin ki,to yanzun yaushe zanzo? ta ce kazo Juma'a ya ce A"a zan dai zo Asabar,Juma'a rabin rana ce. Ta ce,To sai kazo.Nan d kwana 4 kenan?ya ce Insha Allah,sannan ina son ki toro min da adireshin dn gdnk,sannan ranar d zan zo ki bar wayarki a kunne. Ta ce To." Ranar Asabar misalin goma na safe Abba ya shigo cikin sabbin kaya,ya yi matukar kyau tamkar sabon Ango. Umma ta ce za ka je gurin su Maigida ne?Ya ce A"a umma koda yake zan bi ta can.Kd zan je. Umma ta rike baki "Kd,? Me a ke yi?ya ce sai na dawo za ki ji.Ummi d ke wanke-wanke ta kwashe da dry. Umma ta dirma mata dundu tare d cewa,Ke wai ciwon dry ne y kama ki?Abba ya dubeta cike da tsana. Ummi ba za ki shiga hnklnki da ni ba?ta sunkuyar da kai tare d maida dryrta ciki. Sannan ta ce Yaya Abba dn Allah ka siyo min biredi,wlh biredin Kd dadi ne da shi. Lkcn d Amina suka dawo ta sammin. Ya galla mata harara,tare d fadin an ce miki nima bakauye ne irinki?In ma ki ka sake min mgn sai na gabje ki. . Ya kalli Umma Kada ki ce ma Alhj nayi tafiya amma in na dawo zan fada masa. ta ce ,To" Allah ya tsare. Abba ya fita. Ummi tana gama wanke- wanke ta shige daki dn yin gyaran gado. Umma na shiga kicin itama ta fito falo ta ciri wayr a caji taje ta saka sim. Take kuwa kiranshi ya shigo, ta daga ta matse murya kamar yadda ta saba, ka taso ne? ya ce Ina mota mun kusa tasowa. Ki turo mn adireshin. Ta ce Ba fa wahala,d kun sauka tasha sai ka ce a kawo ka unguwar sarki gidn mai ba Gwamna shawara. Ya ce Suhaila ma su ba Gwamna shawara d yawa Ta ce Um to ai a nan unguwar Sarki shi daya ne. Ya ce Ya sunan layin?ta ra sa me zata ce,gabnta y shiga faduwa.Ta samu kanta da cewa, Abuja Ya ce Abuja kuma Suhaila?ko dai Abuja road? Ta ce Eh gida mai lamba 6. ya ce To zan ci gaba da kiran layin. ummi ta ce To," Ta zauna tana sauke numfashi. Tab da ya dogata d ta bani,Sannan ta saka dry murna take yau yaya Abba zai sha wahala. Jefi-jefi ya kan kira ya ce sun zo gari,dk lkcn d ya kira in ta ji ringing sai tayi bayi da gudu, har Tsohuwa da suke zaune tare ta ce, ke takwara gudawa ki ke ko atini ne? Ta yamutsa fuska, sannan ta ce Bacin ciki ne. Tsohuwa ta ce, To taso uwarki ta baki magani. Ummi ta ce ya yi min sauki ma. Can kuma masu kiran layin suka kara kira. Ummi tayi kofar gida ta daga wayar a ka ce ke ina ki ka samu wannan wayar? Ta ce Oho 'yan rainin wayau kada ku sake kirana. Ta kashe wayar ta koma gida. Lokacin da Abba ya ce sun shiga KD har ma sun kusa sauka, sai ta cire layin ta ci gaba da harkokin gabanta ta manta ma da labarin wani yaya Abba. KADUNA Abba suna sauka a tashar kawo, ya sauka ya shiga raba ido yana kallon garin kaduna. Yau ce rana ta 2 d ya ta6a zuwa KD, daman sun zo daurin auran wani abokin su bara waccan. Ya kalli wani dan aca6a sannan ya yafito shi da hannu. Ya iso yana cewa Ina za ka? ya ce Unguwar Sarki. Dan aca6a ya ce Wane layi? Abba ya ce Abuja Road. Ya dubi Abba Rigasa kenan, unguwar Sarki babu layi mai wannan sunan. Abba ya ce, Ina zuwa, bari dai in kirata. Koda ya kira layin Ummi sai ya ji shi a kashe, yana ta kira a kashe. Ya dubi dan aca6a ya ce, Kasan gidn Mai ba Gwamna shawara? Dan aca6a ya ce, Hau dai muje sai mu tambaya. Abba ya hau mashin yana mai ci gaba da nemn layin Suhaila. Sun zagaye unguwar Sarki layi-layi suna tambayar masu gadi da 'yan dai-daikun mutanen da ke giftawa kasancewar unguwa ce ta manyan mutane, daga karshe dan aca6a yaba Abba shawar ya tafi gida kawai. Don haka sun gama zagayen unguwar Sarki har da makotanta, amma ba su samu ba. Gida daya ne aka ce musu da akwai Suhaila, amma yarinya ce ta goye. Kusan karfe 3 sannan suka koma tasha,ya biya dan aca6a, sannan yaje ya yi sallah. Zuciyarsa cike da takaici sai yanzu yake Sallah. gashi ya kasa samun layin Suhaila. kila ma tana sane ta kashe wayr dn kawai ta tazarta shi. Ya tuna d zagin d wani mu2m ya masa lkcn d suka tambaye shi ko ya san ina ne gidan mai ba wa Gwamna shawara? Mutuminya ce,mai ba Gwamna shawara a kan me? Ma su ba da shawara suna da yawa, ya sunan layin da ka zo? ya sunan mai gidan? kama ina lambarsu? Abba ya ce, Lambr kadai gare ni,km taki shiga.Mutumn ya ce,"Amma kai soko ne,gashi kmar wayayye.Ya ja tsaki ya wuce. Shi kanshi sai yanzu yaga wautarshi. ko me ya kawo shi gurin yarniyar?Shida dai ba za ya ce sonta ya keba,km ba ya ce ba sonta yake ba. Wani ma ya zaci dn kudi ubanta yazo,shi kam in ya koma shiru zai yi ko abokanshi zai ce musu bai gane ba kawai,dn yabi ya fada musu lbrn Suhaila,sun km san d batun zuwanshi gurinta sarai,km yasan hlinsu za su maida abn na tsokanarshi. Cikin matukar takaici suke tafe cikin motar kaduna zuwa kani,sun zo kwanar Dangora tsautsayi ya akfa musu. in da tayar motarsu guda ta fashe. . Nan take motar ta bar hannunta ta mulmula da su suna ta salati,nan aka kwashe su xuwa asibiti.wasu sun mutu take,wasu sun yi dogon suma.masu waya ta cikin wayarsu aka yi ta kiran yan uwansu,shi ma abba a cikin wayarsa aka kira lambar ummanshi da alhj da sauran su aka shaida musu cewa mai wannan layin sun samu hadari,kuma an kawo su asibitin mlm aminu kano yanxu.iyakan rudewa su umma sun rude,tsohuwa kam take cikinta ya kada ta soma xagawa bandaki tana kuka tana face majina.ummi bata gidan tana can gidan su amina suna ta hira suna cin dariya ,tace bari in je in qara sa layin in ya kira sai ince wayata chaji ne sai yanxu nayi.sadaf sadaf ta shige daki,kan kujera taga wayar,ta dauka ta saka sim din ta cire wancan. tana kunnawa sakuna suka soma shigowa. kafin ta bude ta duba sai ta jiyo muryar tsohuwa cikin kuka tana cewa wannan yaro ashe ajalh ne ya kira shi,ko me xashi yi kaduna?ni ban sani ba.ummi ta fito da sauri tana cewa,tsohuwa me ya faru?tace ba kina can gun yawanki na tsiya ba.Mai sunan mlm da ya tafi kd sun tafka hadari, yanxun haka suna asibitin mlm. ana xatan shi ma ya mutu.ummi ta saki ihu,sam bata san ta damu da dan uwan ta abba ba sai yau,ko tana kukan ita ce sila?oho.kafin kice haka,lbr ya watsu a unguwa abba ya mutu.cikin kuka ummi ta tambayi tsohuwa ina ummata? tace tare suka nufi asibitin da ummarku.taqi yarda ta jira su.ummi tana jiyo ihun kukan umman bashir ta xaga gidan.gidan ya rincabe da kuka,ummi fa hankalinta ya qara tashi.matarsa ta iso da kuka da yan uwanta a motoci.yayyantamaza suka nufa asibitin.can kusan qarfe takwas su alhj suka shigo.alhj ya ba mutane haquri,ya ce bai mutu ba dogm suma yayi.kuma Allah yayi taimako ba karaya.likitocin sunce xast duba shi xuwa gobe su gani.nan ko jama'a suka dinga fadin alhamdulillah.ummi ma tadan ji dadi a ranta,sanna fa kowa ya tafi dama wasu sunce xa stje yin sallah su dawo.saida suka koma sannan suka taho da umma,ummi cikin kuka tace umma da gaske bai mutu ba, umma tace eh bai mutu ba,muyi magana dashi. . Umma tace in sha Allah gobennan xai dawo gida. ummi tace to,umma tace kinga wayata? gaban ummi ya fadi ta tashi da sauri ta shiga neman waya,taci sa'ar ganin wayar,sai

Chapter 7 of 24