ta katseshi jin yana cewa
“Auwal ba komai mutum yake sa rai kuma ya samu ba!
Kar ka ga ka mallaki Sakina ka yi tunanin duk wani abu idan ka sa rai nan gaba zaka samu.
Ubangiji shi ya baka ita ba wai saboda nacin ka da rashin lafiyarkaba.
An d’aura muku aure jiya kai da ita sakamokon matsalar da ta b’ullo a alamarin
Aurenta da Ashraff.
Amana ce Yarinyar nan
Mahaifinta yayi mana kawaici da mutunci
Dan Allah kar ka bamu kunya.”
Tunda ya fara magana Auwal ya k’ame! Ya kasa motsi sam!
Ji yake yi ma kamar iskar oxygen d’in bata isarsa………
A hankali Daddy ya yi wani sassanyan murmushi ya ce
“Dota idan kuna buk’atar wani abun ga waya chan….idan Likita kuke so za ki ga digits d’in a gefe
idan kuma abinci ne
shima digits d’in suna gefe.
Mu bara mu wuce ko?
Yana da number mu
duk abunda kuke buk’ata ku kira.
Allah ya yi muku albarka.”
A hankali Sakina ta ce “ameen” tana mai sunkuyar da kai.
Da kyar ya iya bud’e idanuwanshi ya ce
“Thankyou Daddy”
A hankali dan shi kad’ai ya san luguden da zuciyarsa take yi masa.
Murmushi ya yi daga haka suka juya shi da Mom suka fice
tare da alk’awarin ‘zuwa anjima za su dawo’
Bayan Itama Mom d’in ta yi musu addua sun amsa......
A hankali ta ga ya mik’o mata hannunsa yana kallonta.
Cikin nutsuwa ta k’arasa ta sa hannunta a cikin nashi.
Still yana kallon fuskarta ya zaunar da ita a gefenshi.
Da kulawa ta ce
“Ina wuni”
Tana kallon bakinshi ya amsa da “Alhamdulillah”
a hankali.
Daga nan ya ja hannun nata ya d’aura a gefen fuskarsa saman kumatunshi ya had’a da nashi hannun ya runtse
kafin ya maida idanunsa ya rufe…
Ko minti uku ba a yi ba ta ji
yanayin rik’o da ya yiwa hannun nata ya sauya
alamun ya yi bacci, bata san lokacin da murmushi ya sub’uce mata ba..
Kallon shi kawai take yi tana sakewa..ya d’an tara k’asumba har da gemu, tabbas ta so
ta tarwatsa rayuwarta da hannunta dan bata jin akwai wanda zata iya so ta zauna ta rayu ta yi farinciki da shi idan ba Ya Auwal ba. Bata tashi sanin zazzafar soyayyar da take yi mishi ba sai da ya kwanta ciwo….
Sun fi 40 minutes a haka
gaba d’aya hannunta ya k’age amman bata so ta motsa gudun kar ya farka dan
ta lura baccin nashi mai dad’i ne yake yi cikin nutsuwa da kwanciyar hankali
kamar ma murmushi taga yana yi.
Sai da ya yi 1 hour yana baccin tukunna ya farka. Yana bud’e ido da fuskarta ya fara tozali
Itanma shi take kallo dan haka ya sakar mata wani tsadadden murmushi. Sai kuma ya d’an gyara ganin kamar a takure take kafin ya ce mata “call the Doctor” a hankali.
Ta fahimci me ya ce
shiyasa ta mik’e ta je ta danna kiran Doctor d’in. Bayan sun gama magana ta koma ta zauna.
Tana zama ya sake kamo hannunta yana kallonta sam murmushi ya ki barin fuskarsa.
Ba ta jima da zama ba Likitan ta shigo.
Yanayin yadda ta ganshi kwance yana kallon kowa tar hakan ba k’aramin dad’i ya yi mata ba. Jininsa ta fara aunawa cike da mamaki ta shiga dudduba shi…
Ganin no nid of oxygen d’in ne
ya sa ta cire ta yi mishi y’an allurai
daga nan ta cewa Sakina “ta k’ok’arta a samu ya ci abinci
jikinshi is weak kuma ta cire mishi drip d’in da yake d’an rik’e shi
tunda ba abincin yake iya ci ba.....”
Tana gama fad’in haka ta juya ta fita tana murmushi…Irin wannan soyayyar haka
tabbas saboda wannan Yarinyar ne zuciyarshi ta d’an tab’u dan gashi daga zuwanta
komai ya fara yin normal a hankali..Ashe dama Nigerians ma suna irin wannan zazzafar soyayya haka?
Dukda ba bak’ak’en fata bane amman ta fahimci Hausa suke yi..........
Sakina na shirin mik’ewa
ya sa dukkannin d’an ragowar k’arfinsa ya jawota, bata ankara ba shiyasa yayi nasarar janyotan, ta tafi ta fad’a jikinshi.
A zabure ta yunk’ura zata tashi ya ce
“Don’t move please”
A hankali dede kunnenta.
Shiruu ta yi kawai
tana jin yanda bugun zuciyarshi yake yi da k’arfin gaske....
Ganin lamarin na shirin sauya masa ya sanya ya d’an cikata.
Da sauri ta tashi ta koma gefe ta zauna dan tabbas ba zata iya had’a ido da shiba kuma.
Ya fahimci ta gano shi
shiyasa kawai ya yi murmushi ya girgiza kai
kafin cikin kasala da rashin k’arfin jiki ya ce
“D’an duba chan locker
ki fitar min brush da maclean da body lotion
sai jallabiya da k’aramin wando. Please.”
Ya fad’i hakan a hankali.
Jinjina kai kawai ta yi ta mik’e ta isa inda locker take, ta
d’auko duk abubuwan da ya lissaafa mata ta dawo
ta ajjiye a gefen gadon kafin ta ce
“Gashi”
tana kauda kanta
sannan ta d’an turo baki..kallon nashi ya fara isarta
kwatakwata ko kifta idon ma fa baya son yi!
Aranta ta ce
“Har sai ya hango muni na”
“Um”
Ta ji ya ce
wanda hakan yasa ta juya ta kalleshi.
Gani tayi ya d’an d’aga hannuwanshi biyu irin yanda Yara suke yi idan suna so a d’auke su.
Bata san lokacin da dariya ta sub’uce mata ba, da sauri ta sa hannu ta toshe bakinta sannan cikin dariyar k’asa k’asa ta ce
“In d’auke ka?”
Ta yi maganar tana nuna kanta.
D’aga mata kai yayi kawai
Idanuwanshi a kanta
kafin a hankali ya ce
“Allah na kasa tashi!
Jikina ba kwari ko mostin kirki fa ba iyawa nake yi ba
so kike in mik’e in zube?”
Cikin yin kalar tausayi ta ce
“Ya Auwal dan Allah ta yaya zan iya d’aukar ka?”
Tana maganar tana kawar da kai dan bataso su had’a ido.
Murmushi ya yi yad’an ciji lower lip d’inshi kafin ya ce
“To shikenan naji ba zaki iyaba
Zo to ki taimaka min In tashi.”
Da sauri cikin tarar numfashinsa
ta ce
“A’a gaskiya”
This time around sai da ya d’anyi dariya wadda ta taho mishi da d’an tari, sai da
tarin ya tsagaita tukunna ya ce
“Mai yasa ba za ki rik’e ni in tashi ba?
Ko bakya so in sake.....”
Da mugun sauri ta k’arasa ta sa hannunta ta toshe mishi baki, cikin muryar kamar wadda zata fashe da kuka ta ce “Wallahi idan ka k’arasa sai na tafi yanzunnan zan koma wajen su Mom”
Da kyar dan jikinshi sam ba k’arfi ya iya zare hannun nata ya ce
“Ni kuma wallahi idan baki taimakamin na tashi ba
sai na k’arasa kuma In rufe k’ofar in hanaki fita sannan In yi ta maimaitawa.”
Kamar zata yi kuka haka ta sunkuya kansa yadda za ta iya taimaka masa.
Sai da ya gama d’aga mata gira yana kashe mata ido tukunna ya sak’ala hunnunshi a kafad’arta
yana dariyar yadda ta chuno baki ta kauda kai gefe.
Sai da ta yi bismillah tukunna ta d’an motsa da niyyar taimaka mishi, d’an yunk’urawa shi kuma ya yi hakan ya bashi damar mik’ewa
ya zauna, da taimkon Ubangiji da na Sakina da kyar ya samu ya mik’e! K’afafuwansa har d’an karkarwa suke yi……
Ita ta d’an fara motsawa yana rik’e da ita ya ce “ta d’auka kayan da ta d’auko mishi”
Hannu kawai tasa ta d’auka
daga nan suka d’an fara takawa……..
Har Cikin bathroom d’in ta kaishi.
A bakin tangamemen bathtub d’in ya zauna, sai da
jirin yad’an sakeshi tukunna ya cikata ta had’a mishi ruwan wankan tab bathtub d’in
sanann ta matsa mishi Maclean ta mik’a masa..
Sai da ta taimaka masa ya isa wajen sink d’in yayi tukunna
ta fara k’ok’arin fita domin ya samu ya yi wanka.
Cikin ruk’o hannunta ya ce
“Saurin me kike yi?
Jikina fa babu kwari!
Idan kika fita na fad’i baya fa za ki dawo damu.”
A hankali ta d’an matso suka nufi bathtub d’in tare……….
Sanabe! Kala Kala
awajen Auwal dan
hatta shirt d’in ma ita ta b’alle mishi mab’allin ta cire, da kyar ya yarda ya sa hannu ya cire singlet d’in!
Tun daga nan ta sunkuyar da kanta sosai ta fara k’ok’arin tafiya amman ya rik’e mata hannu….
Drama sosai suka yi
dan ya kafe akan wandon ma ita zata cire masa gashi ya tare hanya ya rik’eta for support ya hanata tafiya.
Ganin da ya yi ta tubure sannan tama k’i kallonshi tana shirin fashewa da kuka yasa kawai ya kama wandon ya fara ja yana dariya k’asa k’asa
a hankali ta ji ya ce
“FYI! Babu boxers a ciki.”
Ta mugun k’arfi ta saka kuka ta durk’usa a wajen dede nan kuwa ta ga ya saki wando ya fad’o k’asa dan
haka ta ci gaba da kuka ta k’i dagowa sam! Ta runtse idonta.
Kukan da take yi ne yasa ya cika mata hannu, ai kuwa
bata yarda ta kalli direction d’insa ba ta juya
ta mik’e ta fice da mugun gudu.
Banda dariya ba abunda yake yi…
A hankali ya zare boxers d’in jikinsa ya shiga cikin ruwan da kyar. Ya kwanta a ciki ya lumshe idanuwanshi yana jero wa Ubangiji kirari da godiya….
Ya dad’e a haka tukun ya ja sponge da soap ya fara wankan....
Banda dukan uku uku ba abunda k’irjinta yake yi!
Da kyar ta samu ta tsaida kukan nata…
Kana ganinta ka san a mugun tsorace take
ba abunda yafi d’aga mata hankali irin kar ya zo fitowa ya fito mata a haka! Tunda ta lura sam babu d’igon kunya a tattare da shi…..
Da wannan tunanin ta juya gaba d’ayanta tana me kallon bango. Ta jima a haka ta ji k’arar bud’e k’ofar, sake
matsawa jikin bangon ta yi
wanda hakan ba k’aramin dariya ya bashi ba.
Tana jinshi yana yi mata dariya ta yi banza da shi.
A hankali ta ji ya ce
“Relax! Har da jallabiyata da towel a kaina na fito,
Okay?!”
Bata yarda ba sai da ya matso kusa da ita ya kamo hannunta ya d’aura akan jallabiyar jikinshi tukunna
t sauk’e ajiyar zuciya ta juyo
amman still dukda haka bata kallonsa.
A gefen ta ya zauna da kyar yana jin tsananin jiri da rashin kuzari ya ce
“Anya ba a sauya mini ke ba kuwa? Ina tawan ta tafi ne?”
B’ata rai ta yi ta turo baki.
A hankali ya sauk’e ajiyar zuciya ya d’an matsa ya yi peckn kumatunta ya ce
“Matata!”
Yana kallonta yana murmushi.
Bata san lokacin da murmushi ya sub’uce mata ba
Itama.
A hanakali ta mik’e ta yo musu order abinci sannann ta dawo ta zauna a kusa da shi.
Yana nan rik’e da hannunta tana bashi labarin Ashraff aka kawo abincin....
Auwal,
ya ma manta rabon da ya ci abinci irin wannan sai dai drip most a times, da kanta take bashi!
Wani nishad’i farinciki da jin dad’i yake ji wanda ba zai misaltu ba.
Haka nan ta ciyar da shi suka yi baccin su tare suka farka
suka yi sallah tare!
Kafin washe gari kam Auwal ya warke ba laifi
sai dai yawan baccin da yake yi da kuma rashin k’arfin jiki da y’an abubuwan da ba za a rasa ba..
Dan ko da Daddy ma ya je da daddare yana bacci.
Ba k’aramin dad’i Daddy ya ji ba da ganin shi har yayi wanka kuma babu oxygen.
Bai wani jima ba gudun kar motsin shi ya tada shi yasa ya yiwa Sakina sallama bayan ya bata abubuwan da ya tsaya ya siya musu.
.....……………..
Suna gama video call d’in Daddy ya mik’e idanunshi sharkaf da hawaye zai wuce!
Da sauri Mom ta ruk’o hannunsa ta durk’usa a gabansa.
Ta lura tun d’azu da ta fara bada labarin ta’asarsu ita da Mammy Daddyn yak’i kallon direction d’inta,
yanzu ma haka.
Tana kuka ta ce
“Dan Allah Daddy kar ka yi min wannan shirun naka……Ka hukuntani! Ka yi min duk hukuncin da kaga ya dace dani amman dan Allah kar ka rik’eni a zuciya ka banxatar da ni.”
A hankali cikin share hawaye Daddy ya ce
“Adama I love you
morethan you can ever imagine! Amman ba zan iya zama ince wai na yafe miki duk abubuwan da kikayi min lokaci guda kuma naci gaba da sonki ba!
Tbh, wallahi k’aunarki da k’imarki tayi mugun raguwa a zuciyata…
How could you?!
Haba Adama!
Saboda son zuciya?
Adama Mommy fa kusan a kwance ta yi rayuwarta
kin sani kin san matsalar
amman kika yi shiru!.
Sannan kika taimakawa Mammy dan ku kwantar da Aslam yayi jinya shima?
Doguwar jinya!!!
saboda kawai kwad’ayin MT??”.
Cikin kuka ta ce
“I was wrong!
I have been wrong for so long Daddy dan Allah ka yafe min.
Ban san ta Ina zan fara baka hak’uri ba, ka yi hak’uri tabbas na yi kuskure kuma kuskuren ya dawo mini
tunda gashi na rasa y’ar uwa ta d’aya tilo a duniya.”
Numfashi Daddy ya furzar kafin ya ce
“Duk son da nake yi miki
dole ne in kin tab’a min family zan ji haushi Adama!
Ba zan iya kallon ki ban tuna abubuwan da kika yi ba.
Ki je wajen Inna!
Ni ban ce na sakeki ba
amman kawai ki tafi wajenta
zan nemeki
idan na huce.”
A hankali ya zaro atm ya bata ya ce
“Akwai driver da Aslam ya turo ya taho
wai Auwal ya ce a kawo mishi wasu abubuwa..
Idan ya zo zan turo miki shi ku je ke da shi ku yi visa da komai
Direct ki wuce wajen Innaa.
Dan Allah ko kira na kar ki yi.
Idan na neme ki to..Idan kuma ban neme ki ba shikenan,
zan aika miki da takardarki!
Allah ya raya mana Auwal.....”
Yana gama fad’in haka ya juya ya fita da sauri.
A wajen ta durk’ushe tana wani irin mugun kuka.......
..BAYAN KWANA BIYU..
Haka kurum tunda Mama ta tashi yau jikinta a mace
Ummu na lura da ita dan tun jiya a wajen saloon taga kamar ma kuka take yi.
A hankali ta matso kusanta tace “Maama”
A karo na biyu.
D’agowa ta yi ta kalle ta.
A hankali ta ce
“Ki tashi ki cire lallen nan mana a yi miki black mai k’unshi ke take jira”.
Ajiyar zuciya Mama ta sauk’e kafin a hankali ta janyo abun sakace Ummu ta hau b’alle ledar…
Atake suka cire ita da Ummu ta shafa mata Mahallabiya.
Mik’ewa Ummu tayi da zummar zuwa ta kira me lallen tayi mata bakin
ta ji Mama ta rik’eta
a hankali ta ce
“Abba ya fi son jan lalle”
Murmushi Ummu tayi ta koma ta zauna ta kamo hannuwanta biyu kafin ta ce
“Kina tunawa kenan har yanzu
alamun yana nan rad’au a zuciyarki har abada amman kuma kiketa faman k’unci tun jiya Me yasa baki da walwala?
Ko kema kukan za ki yi mana kamar y’ay’anki
Huda da Sakina?”
Ajiyar zuciya Mama ta sauk’e kafin ta ce
“Bawai walwala ne bani da shi ba, dana sani nake yi.”
Da sauri Ummu ta gyara zama kafin ta ce
“Dana sani kuma?
Name?”
Wani d’an guntun murmushi Mama ta yi
kafin ta ce
“Dana sanin kuka da sab’on dana dinga yi ina cewa ‘mai yasa rayuwarmu ni da y’ata ta zo a haka?!’.
Ummu na cire rai da Abba
na cire rai da soyayya
amma gashi yanzu
Ubangijin da nake ganin ya d’aura mana kaddara mai tauri
zai sake mallakamin Abba
sannan Huda ma ta auri wanda yake tsananin k’aunarta shi da iyayensa
What more could I ever ask for?.
Godiya da tasbihi nake ga Ubangijin talikai amman gani nake yi kamar is not enough!
Bansan ta yaya zan fara yiwa Ubangijina godiya ba.
Ki duba fa kiga yadda rayuwa ta chanja mana
daga k’unci tashin hankali da bak’in ciki
zuwa
Farin ciki cikar buri
a lokaci daya!.
Ba abunda yake bani mamaki nake kuma gasgata Ubangiji mai kun fayakun ne
Irin yadda komai yake tafiya smooth..
Hatta Granpa ya sauk’o sosai
jiya fa kira na yayi a waya wai ya kira mu gaisa
sannan ya sake bani hak’uri!…
Ashe dama za mu ji dad’i ni da Huda? Ashe za mu yi farin ciki?
Ashe zan sake d’and’anar soyayya?”.
Ajiyar zuciya Ummu ta sauk’e a hankali ta matsa kusa da ita tasa hannu ta rungumeta, a
take kuka ya taho musu a tare su biyun.
Suna a haka Shuwa ta shigo.
Murmushi kawai ta yi cikin dakiya ta k’arasa inda suke ta d’an b’ata rai
kafin ta ce
“Yanzu dan Allah Maryam kema sai kin saka mu kuka?
Su Huda sunayi kema kina yi?”
Sannan cikin d’an fad’a ta cewa Ummu “tashi ki fita,
yi maza ki fita kije kin bar Zainab da had’a abinci ke kin zo nan.
Oya Maryam kema tashi ki shirya yanzunnan za ki ga an fara zuwa”.
Bata Ida rufe bakinta ba
Hudan ta shigo ita da Mommy.
Da d’an sauri ta k’arasa ta fad’a kansu Ummu
tana murna.
Jujjuya kai kawai Shuwa tayi ta ce “Nikam wannan alada taku ta turai ban santa ba!
Dan tsabar rashin man kai Huda yanzu keda za akai miki Maman naki inda kike shine kika fito? Kalleki ko nuna baki gama yi daga jinin amarcinba
amman dan fitina har kin fito?”
Murmushi Mommy ta yi suka gaisa ita da Shuwa kafin ta ce
“Hajiya ayi mana uzuri, nima
naso in hana amman ita da Mijin suka kafe!
Wai zata yi mishi kuka idan na tafi.”
Cikin d’an fad’a Shuwan ta k’arasa ta sakar mata rankwashi a kai tace “ja’ira!!
Sannnan kin zo kin wani wuce ni kin fad’a jikin iyayenki..”
Murmushi Huda ta yi ta mik’e ta yi hugging Shuwa kafin cikin dariya da zolaya ta ce
“Hajiya kawai ki fito ki ce daman kishi kike yi ban kula ki ba ba wai kiyi ta kame kame ba .”
Dariya duk akayi.
A hankali Shuwa itama tana d’an murmushi tasa hannu ta yi hugging Huda tukunna ta cika ta ta juya ta fita da sauri tana cewa “su tabbata sun sa Mama ta shirya yanzu”.
Already Maman ta yi wanka tun sassafe dan haka
kayanta kawai ta shiga bathroom ta saka
Sky blue lace
da white jaka takalmi da jewelry’s
Ummu ce tayi mata d’auri
nan take ta fito rass Amarya…
Anyi hotuna sosai
Allah sarki sakina
a video call Huda ta kirata
ta saka fuskarta akan screen din full aka d’auki hoton da ita su Ummu suna ta yiwa shirmen nasu dariya gashi Sakina ta dage sai an yi da ita.
A masallacin unguwar kusa da gidan Madu anan za a d’aura aure dan tun kafin lokaci ya cika manyan motoci suka cika layin tap! Har layin baya
saboda Abba gayya yayi kamar wannan ne na farko.
Lokaci yana cika dubban mutane suka shaida
D’aurin Auren
Yakubu Umar Farouk Mt (Abba)
Da Amaryarsa
Maryam Muhammad Madu (Mama)
Akan sadaki naira dubu d’ari uku.
Ana shirin watsewa Kaka ya cewa Limamin ya sanar za a sake wani d’aurin auren
…..……Tun lokacin da Kaka ya bada sanarwar Jalila
wani mai d’an kantin
ana ce mishi
Abdullahi
ya ce yaji ya gani!
Shi da Mahaifiyarshi basu wani dad’e sosai da tarewa a anguwar ba
kasancewar Mahaifinsa ya rasu kuma anata rigima tsakaninsu da dangi da iyayen uban a kan gado yasa suka baro Katsina suka dawo Kano da shi da Mahaifiyarshi da k’anwarsa Aminatu tsarar Jalila.
Da farko Hudan ya so
sai da mazan layin suka zaunar da shi suka yi mishi lecture
a kan ‘indai ba gudumar late comer da heartbreak yake son yasha ba tou ya hak’ura’ Tukunna ya hak’ura
ya koma kan Jalila
wadda sai da ya fara sonta ne ma ya lura yama fi k’aunarta akan Hudan, dan haka ya je ya sameta ya gaya mata..
K’iri k’iri ta fito mishi ta k’i amincewa da shi sannan ta wankeshi tass!! Ta yi gaba abunta.
Babu yanda bai yi ba amman ya kasa cire ta aranshi
har rashin lafiya yake yi saboda Jalila
tun ba ma lokacin da Auwal ya fara kwasarta ba
sai da ya yi k’aramin hauka.
Har gida Mahaifiyarsa ta je ta samu Sadiya
amman tijarar da Sadiya ta yi mata har yamafi wadda Jalilan ta yiwa Abdullahin kumafa idan ka ga Abdullahi bashi da laifi sam! Bak’in saurayi dogon gaske mai fad’in k’ashi
bashi da wani muni a fuska sam
ya kammala degree d’inshi
bai samu aiki ba
shiyasa ya bud’e shago saboda d’awainiyar Mahaifiyarsa da k’anwarsa dole shi ne zai yi.
Yana jin labari ya tafi wajen Kaka..
Ba abunda Kaka ya b’oye masa
gameda cikin da Jalila tayi amman wannan Yaro ya ce yaji ya gani.
Kaka ba k’aramin farin ciki yayi ba dan bai tab’a tunanin Jalila zata samu Miji saurayi kamar Abdullahin ba amman still sai da ya sake tura Baaba Talatu wajen Mahaifiyarsa da bayani
Itama ta amince
Dan haka aka bashi Jalila ba tare da an gayawa ita kanta Jalilan ko Sadiya ba
Baba ne kawai ya sani……
Su Sadiya suna gidan Baaba Laraba sai uban hayak’i suke yi dan Malamin nasu yace in dai sun yi wannan hayak’in a anguwar in da Maryam (Mama) take tou ba za a d’aura auren Maryam da Yakubu ba.
Suna hayakin suna ta uban tari kawunan su na ciwo suka jiyo an d’aura auren Maryam da Yakubu!……
Fatali Umma ta yi da kaskon
kafin ta fashe da wani matsanancin kuka!.
Jalila kanta sai da ta yi kwallar tashin hankali.
Ba a yi minti talatin ba suna cikin jimami da tashin hankali suka ji ana sanarwa
“An D’aura Auren Abdullahi Muhammad
Da Amaryarsa
Jalila Usman Bashir”.
BULAMA ✍️
So da Buri
Free book
73
Mikiya Writers Association.
A hankali Mama ta lumshe idanuwanta wasu hawaye suna zuba. Dai dai nan Ummu
ta shigo, ta na Isa gareta ta sa hannu ta yi hugging d’inta ta ce “congratulations”.
Ajiyar zuciya kawai Mama ta sauk’e daga nan d’akin ya fara cika da jamaa..
Banda hayaniyar mata babu abunda ke tashi.
Suna cikin hira
suka ji d’aurin auren Jalila itama, nan take kowa ta hau tofa albarkacin bakinta
wasu su ce “Allah shi k’ara” wasu kuma su ce “Ai ta ma yi sa a data auri Abdullahin,
Mutum mai kirki da hankali da zuciyar nema
wallahi ta tsinci dami a kala...”.
Kowa idan ya ga Abba a wajen d’aurin auren nan tashi d’aya zai san yau d’in fa yana cikin farin ciki. Ba shi kad’ai ba hatta su Granpa idan ka gansu fuskokinsu tap! Cike da annuri.
Ba a jima ba suka shiga parlourn Madu aka yi musu hotuna suka wuce bayan sun ce “nan da anjima in an d’an watse Abba zai dawo ya d’auki Amaryar shi da kanshi.”
Madu ya ji dad’in hakan dan dama shima ya gama deciding
akan ‘ba sai an yi wani reton kai Amarya kamar wata Yarinya ba’.
Hakan kuwa aka yi,
Hudan ta so tsayawa amman awa uku kawai Aslam ya bata daga nann ya dawo ya d’auketa a cewarshi ‘gidan yayi mishi girma ya kasa shan ko ruwa tunda ya koma’…
Tunda ta ji haka dama ta b’aro jirginsa! Dan haka ta yi murmushi kawai ta girgiza kai tana mamakinsa.
Tunda aka idar da sallar Magrib Abba ya shirya tsaf!
Ana idar da sallar isha ya kama hanyar gandun albasa bayan ya samu Dad ya cika shi dakyar dan da farko rik’esa ya yi ya ce “akwai wani important aiki da zai tayashi
dan Allah”
Kamar Abba zai yi kuka haka ya yi mishi sai kuma ya ga Dad d’in yana dariya k’asa k’asa
dan haka ya gano tsokanace!
Amman dukda haka sai da ya yi da gaske tukunna Dad d’in ya cika mishi riga ya wuce mota Dad d’in kuma ya nufi gidanshi yana dariya……….
Yana zuwa ya tadda Madu zai shiga gida ya fito kenan daga masallaci dan haka suka shiga tare har parlourn Shuwa.
Nan Madu ya d’au waya ya kira Kaka da Baaba Talatu
suka zo suka had’u suka yi musu Nasiha!
Daganan suka sanya musu albarka….
Sai da suka zo tafiya ne Mama ta ji kuka ya taho mata.
Murmushi kawai Baaba Talatu da Shuwa suka yi
daga nan Baaba Talatu ta mik’e ta k’arasa ta mik’ar da ita suka yi gaba
Abba shima ya yi musu godiya da fatan alkhairi ya bi bayansu…..
Da shi da mai aikin ne suka ja akwatunan Mama guda biyu da ta had kayanta a ciki
suka kai mota suka sanya mata a booth...
Har k’ofar mota Baaba Talatu ta raka Mama ta bud’e ta saka ta a ciiki tukunna ta ce “Allah ya miki albarka”
Tana mai rufe mata motar ta koma ciki.
Dede nan Abba ya shigo ya rufe motar ya kunna ta,
a hankali ya sauk’e ajiyar zuciya sannan ya juyo ya sa hannu ya jawota ya yi hugging d’inta wasu hawaye suna zubowa daga idanunshi..
Da sauri ta ce
“Abba mutane fa suna wucewa”
Tana mai d’an k’ok’arin janyewa.
Bai cikata ba sai da ya yi niyya tukunna ya matsa amman still yana rik’e da hannunta yana kallonta ta cikin mayafin da ta d’an ja.
Murmushi kawai ya yi yana sauk’e wata nannauyar ajiyar zuciya kafin ya koma ya zauna
All Chapters
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 22 Chapter of 26