Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
na fahimci K’arya Yaudara Da tsoro a lamarin Ashraff. Inaso ka zo mu je mu samu Mahaifinsa a nan na tabbatar in dai mutumin kirki ne to gaskiya za ta fito k’arara! But first sai na fara kulle asibitin nan da mai asibitin tunda karb’ar cin hanci ya maida sana’a” Bai gama rufe bakinshi ba Likitan ya shigo! Sai da ya kallesu one by one tukunna ya k’arasa inda Ummu take ya shiga yi mata bayani akan wasu takardu da ya shigo da su yanzu…. “Case d’in Sakina fa is severe! In ba a fitar da ita a yau ko gobe ba tou tabbas za a samu babbar matsala! Shima sai yanzu ya ke ganin wannan result d’in bayan ya tsananta bincike…..” Kasa magana Abba yayi tsabar mamaki da takaici dan haka kawai ya turawa commisioner of police message tare da adress d’in asibitin daga nan ya cewa Baban Sakina “ya zo su je..” Suna fita ya ce mishi su wuce gidansu Ashraff. A motar Abba ya yiwa Baban Sakina k’arin haske akan abunda ya fahimta game da Ashraff d’in kuma aka ci sa a Baban Sakinan ya fahimceshi. Ba Baban Sakina ba hatta Abba sai da ya cika da mamaki da suka k’arasa k’ofar gidan suka tarar da tafkeken masallacin juma’an dake a jikin gidan cike da jama’a anata shige da fice. A hankali da kamala suka kutsa kai suka shige ciki, sakamokon hango Mahaifin Ashraff ya gilma ciki sanye cikin shiga ta alfarma. Ba su gama tunanain meke faruwa ba suka ji a loudspeaker ana “An d’aura auren Ashraff Muhammad Bashir Da Suhailat Yusuf Tanko a kan sadaki naira dubu d’ari uku lakadan ba ajalan ba.” Kallon kallo suka hau yi kafin su hau kallon jamaar one by one… Chaan! Suka hango Baban Ashraff d’in da suka biyo cikin masalllacin, yana ta fara a yana gaisa wa da wasu Abokanayen sa na jiki jiki waenda suka samu damar halartar d’aurin auren gaggawan da aka gaiyyacesu. Yana ganin Baban Sakina hankalinshi ya d’an tashi! Dan a iya saninshi bai gaiyyaceshi besides auren ma ai secret aka yishi to me kuma ya faru?! Bai gama dawowa dede ba suka k’arasa wajen shi da Abba suka zauna a kusa da shi. Abba ne ya iya bashi hannu suka yi musabaha Baban Sakina kuwa da kyar ya iya ce mishi “Barkanmu.. Dan Allah d’an yi min elaborating abunda na ji an fad’a yanzu.” Sai da Baban Ashraff d’in ya d’an kalli gefe da gefen shi tukunna ya mik’e ya ja su gefe ya fara magana k’asa k’asa “Kasan me ya faru ne? Yaron yanzu sai a hankali wallahi….” Sai kuma ya d’an yi shiru kafin ya fesar da numfashi ya ci gaba da cewa “Shi Ashraff an d’an samu matsala ya je ya yaudari wata Yarinyar oga na wanda shi ya siya min takardar kujerar sanatan da nake mulka a yanzu! Hatta campaign shi yake taimaka min da komai. Kaga ni d’an siyasa ne In na yi mishi butulci ban kyauta ba kuma siyasata za ta samu matsala tunda party d’inmu d’aya. Jiya Yayar Yarinyar ta kira Mahaifiyarshi direct… To kasan mata abun nasu sai a hankali, a take sai ta yi mata fata fata kuma ta ce ‘ba dai Ashraff d’inta ba’. Tofa shine Yaran su kuma suka je suka samu Mahaifinsu da Mahaifiyarsu suka fad’i komai. Adress da sunana kawai ya karb’a ya gano Ashraff d’ana ne! Yau da safe sai ganin shi na yi. Baban sakina ko kaine a situation d’in da nake na san dole ka yi abunda nayi. Amman ka kwantar da hankalinka Aure tsakanin Ashraff da Sakina babu fashi! In sha Allah lokacin da muka d’iba yana cika za a d’aura musu aure. Jiya sai cikin dare Ashraff ya dawo gidan nan a hargitse wallahi ya bani tsoro kuma hakan ya sanya na sake fahimtar yana tsananin k’aunar y’arka dan na san tabbas labarin ta ji suka d’an samu matsala shiyasa ya damu har haka.. Kar ka ce za ka yi interfering dan Allah kar kace za ka yi komai ka barsu, dan Ashraff jiya har d’an k’aramin hauka ya yi! Idan ka ce za ka hanashi Sakina ban san ya za ai ba”. Cikin tsananin b’acin rai Baban Sakina ya ce “A jiyan da ya dawo muku a haukace ka san me ya je ya yi?” Bai jira jin amsarshi ba ya ce “K’wamushe mini y’a ya je ya yi! Ya kaita wani asibiti suka had’a baki da mai asibitin aka manna mata ciwon hauka! Yanzu haka da ka ganmu da farko shirin d’aura musu aure shi da ita muke yi saboda ya ce ya san wani k’warerren Likita A New York Inkuma aka barta ba a kaita wajen Likitan da wuri ba to zata iya mutuwa.” A firgice Baban Ashraff d’in ya ce “Innalillahi wa inna ilaihirrajiun” Sai kuma ya dafe kanshi kafin ya d’ago ya ce “Kayi hak’uri Alhaji Muhammad Ashraff yayi laifi amman wannan yana yi maka nuni da abunda hanashi ita ka iya jawowa! Na tabbatar tsorata yayi shiyasa yayi hakan! Yanzu ka kwantar da hankalinka zan yi mishi magana ba zai k’araba In sha Allah Lokaci yana yi za a d’aura musu aure a samu a zauna lafiya”. Shi kam Abba dariya ma Mutumin ya so ya bashi… Yana shirin yin magana ya ji Baban Sakina ya ce “Unfortunately, Alhaji ka yi hak’uri amman itama Sakina akwai wanda na ga ya fi dacewa ta aura! Za mu dawo muku da duk wasu kud’ad’en ku da kaya dan na janye maganar aurenta da Ashraff gaskiya! Bawai saboda Ashraff ya yi aure ba..not at all. Zan yi hakan ne saboda yadda na ga kana shakkar Mahaifin Yarinyar da ka aurawa d’anka a yau na tabbar idan ya ce kar a yiwa y’arsa kishiya to ba za ka bari ba. Cikin b’acin rai mutumin ya ce “Wai Alhaji Muhammad ya mutum kamar ni da girma na ina yi maka magana har da magiya amma kana yi min musu???” Ciki sauk’e ajiyar zuciya Baban Sakina ya ce “Shiyasa zan barka In bar maka d’anka dan ba zan iya musun rashin gaskiya da kai ba” Yana gama fad’in haka ya wuce inda ya ga limama, ya same shi ya gaya mishi wata magana kafin ya dawo inda Abba yake tsaye shi da Baban Ashraff ya ce masa “Kana da sadakin da zaka bayar na Auwal ko sai ka je banki?” Kallonshi Abba ya yi a d’an rikice sai kuma ya sauk’e ajiyar zuciya yana murmushi kafin ya ce “akwai a mota, bara in je in d’auko”. Ko minti biyar bai yi ba ya dawo…. Alokacin limamin har ya d’an tara jama’a an zazzauna. Yana zuwa bayan an shirya komai ya mik’a sadaki ya yiwa Auwal wakili…a take aka d’aura auren Auwal Yusuf Umar Farouk MT Da Amaryarsa Sakinat Muhammad a kan sadaki naira dubu d’ari biyu lakadan ba ajalan ba. Ana gamawa Baban Ashraff ya juya ya fita fuuuuu! Daman tun d’azu ko zama kasa yi yayi yana mamakin tsaurin ido da taurin kai Irin na wannan talakan mutumin............ Ana shafa Fatiha Abba ya bayar aka siyo alawowi a shagon gefen su aka zo aka rarraba aka watse.. A take ya kira su Dad ya sanar da su good news. Kasa hak’ura suka yi suka ce ya bawa Baban Sakina wayar Shi kam har d’an kunyar irin godiyar da suka dinga yi mishi ya ji, daga nan suka yi sallama suka nufi wajen Granpa domin sanar da shi. Su Abba kuma suka koma asibiti wajen Sakina. Suna shiga dede suka tarar ta farfad’o amman Mama da Ummu sun danneta Likitan yana k’ok’arin sake sank’ama mata wata allurar yana cewa “Ai dama na gaya muku! Ku duba fa kugani irin abubuwan da take yi if possible a wuce da ita kawai Yau! Tunda na ji Yaron ya san garin da Likitan, shi zai yi komai dan haka komai zai zo da sauk’i.” Da sauri Baban Sakina ya je ya kwab’e allurar daga hannunshi! Yana shirin yin magana y’an sanda suka shigo. Babban su ne ya k’araso ya karanto mishi laifinshi.... Tabbas Likitan ya san Ashraff zai fito da shi tunda ba ayau suka fara harka da shi ba! Yasha kawo mishi mata ya cire musu ciki amman duk da haka sai da ya ji gabanshi ya fad’i! Da kyar ya dake ya bi bayansu salin alin bayan ya turawa Ashraff d’in message…. Suna fita Sakina ta ce “wallahi Abba k’alau nake, Ashraff munafuki ne! Shi ne ya shak’a min hanky d’insa wanda Allah kad’ai ya san girman kwayar da ya saka a jiki shiyasa nake jin k’aik’ayi a kaina kuma yanzu na daina. Dan Allah ku fahimceni Munafuki ne! Baba dan Allah kar ku kaini wajen Likitan mahaukata……” Matsawa inda take Baban nata yayi a hankali ya dafa kanta ya ce “ba komai komai ya wuce ki kwantar da hankalinki kin ji? Mun yarda da ke Aaima ta fad’a mana komai ai” Kallonshi kawai Ummu da Mama suke yi….: A hankali cikin nutsuwa ya karanto musu yadda suka je suka tarar ana d’aurawa Ashraff aure da komai da kuma yadda suma suka d’aura auren Sakina da Auwal a yau….. Wani sassanyan murmushi ne ya sub’ucewa Mama a hankali ta ce “Alhamdulillah” Abba da yake kallonta ne ya ce “Ma sha Allah.” Yana sakin nashi murmushin. Sakina kuwa wani irin kuka ta saki....... Direct parlourn Granpa Dad da Daddy suka nufa. a nan suka iskeshi shi da Gramma yana jik’a towel yana d’aura mata a ajiki. Ba yadda suka iya haka suka sanar da y’ay’an nasu rashin lafiyar Gramma d’in wanda hawan jinine yake neman yi mata illa tun rasuwar Ummi…. Ba k’aramin tashin hankali su Dad suka shiga ba kuwa. Da kyar! Granpa da Gramma d’in suka lallab’asu suka d’an nutsu bayan sun gama shiryawa akan za a fitar da Gramma d’in waje ta d’an huta ta samu change of environment ko da na wata d’aya ne ta yarda. Sai da Granpa ya tambayesu tukunna suka tuno da zancen Auwal da Sakina dan haka suka zaiyyano musu labari tiryan tiryan….. Mik’ewa Gramma ta yi ta zauna tana murmushi ta ce “Alhamdulillah na samu another grand in-law Allah ya sanya albarka dama inata addua wallahi saboda Yarinyar ta shiga raina tun a ranar da suka zo za a kai Huda. Barka Alhamdulillah. Auwal sai ya warke ai yanzu Ja’iri mai ciwon so.” Dariya duk suka yi har da Granpa kafin Granpa d’in ya ce “Yanzu abunda zai faru shine.. Ku fara shirye shiryen visar har da na ita matar Auwal d’in, Yahaya ka kirawo Kakan ta ka sanar da shi cewa Duba da yanayin halin da Mijinta yake ciki muna so mu tura mishi ita da wurwuri! At least a samu ya warke da wuri ja’irin.” Dariya duk suka yi nan ma kafin Granpa ya ce “Sai ta wuce as soon as possible mu kuma idan mun yi welcomin Maryam sai mu wuce da washe gari ko?” Ya fad’i maganar yana dafa kafad’un Gramma. Murmushi kawai ta yi ta sunkuyar da kanta dan duk sai ta ji ya bata kunya. Daddy ne ya ce “Inyeee.. Grand honeymoon za.....” Bai k’arasa ba Gramma ta d’auko throw pillow ta buga mishi! Da sauri suka mik’e suka fita shi da Dad suna dariya. A hankali Gramma ta kwanta a jikinsa tana sauk’e ajiyar zuciya kafin ta ce “Thank you Daddie” Murmushi kawai yayi yana me shafa kanta a chan k’asan zuciyarsa kuma yana regretting abubuwan da ya yiyyi.. ashe haka happines d’in frank family life yake amman ya dinga depriving kanshi da zuri’arsa ba tare da ya sani ba? Tabbas miskilanci da mugun hali bashi da rana.................... BULAMA ✍️ Bismillahirrahmanirrahim So da Buri Free Book 71 Barkanmu da sallah Al’ummar Musulmi🥰 Allah ya maimaita mana, Ameen. Abba Madu yana gama waya da Dad Motar su Baban Sakina tana yin parking. Sai da Baban Sakina ya raka su har ciki tukunna ya ce “Bari ya je ya samu d’an uwanshi ya sanar da shi halin da ake ciki.” Yana fita su kuma suka fara korawa Shuwa bayani…. Har ga Allah Shuwa ta ji dad’in hakan..at least su duka ukun za su zauna a family d’aya. Basu damu da gyangyad’i da jirin da take yi ba (dan allurai da abun da Ashraff ya shak’a mata masu k’arfi ne sosai) Haka suka duk’ufa wajen gyarata Ita kam anayi ma tanata baccin ta. Sai dare tukunna Huda ta samu ta kira Mama Gramma Ummu da Abba ta gaidasu. Suna gama waya da Abba ta fara jiyo motsi dan haka tayi sauri ta runtse idanuwanta kamar mai bacci. Dama ya bata dinner ta ci ta yi sallah tukunna ya fita bayan ya ce mata “bara ya je ya d’an yi aiki” Dan in dai yana gabanta to ya san ba abunda zai iya tab’ukawa. Yana ganin yadda ta lumshe idanun nata ya fahimci ba bacci take yi ba! Murmushi kawai ya yi ya k’arasa y’an abubuwan da zai yi ya hayo kan gadon. Tashi d’aya ya lura da yadda jikinta ya hau b’ari dukda kuwa baccin k’aryar da take shararawa amman he cant help it! Ba k’aramin k’ok’ari ma ya yi aka kawo yanzun ba. Addua ya yi ya tofa ya shafa mata shima ya shafa. Jin an shafa mata addua ya sanya hankalinta yad’an kwanta a tunaninta kyaleta za ayi amman inaa nan take ta ji sabon labari… Babu daman kwacewa dan yau ma Aslam d’in da gaskensa ya zo mata kamar jiya. Babu kalar magiyar da bata yi amman yayi mata kunnen uwar shegu!…… Ga rad’ad’i ga azaba ga ciwon kai ga rashin bacci shiyasa kafin asuba zazzab’i ya rufeta, ruf!. Shi ya kira family Doctor ta zo da sassafe ta yi mata allurai harda k’arin ruwa tukunna ta d’an ji dama dama… Ba abunda yafi bata tsoro irin yadda ya sake zuwan mata yauma kamar jiya da shekaran jiya. Ita kam har mamaki da tsoro ya fara bata dan idan yana wani abun kamar wani mai aljanu..yanzun zaka ganshi garau amman yana d’aukar hanya zai birkice sam baya ji baya gani. Bashi da aiki sai dai ya bata abinci ya yi ta lallab’ata yana faman lallashinta yana kula da ita, ya yi ta gaya mata kalaman soyayya yana lallashinta Idan dare yayi kuma a koma ruwa...... Tun a washegarin ranar aka shirya musu komai na tafiya. Basu wani sha wahalar yiwa Sakina komai ba saboda Dad ne akan komai. Auwal, bai san da labarin ba dan ko da aka gayawa Mom da ta ga jikin nasa yad’an nutsu kamar ya sani sannan nan da kwana biyu Sakinar zata zo sai kawai ta barshi akan sai ta zo d’in ya ganta kawai a surprise Another thing kuma tana tunanin in dai Auwal ya ji an aura masa Sakina kuma tana Nigeria tou tabbas zai iya tsige oxygen d’in ya dawo gida ko bai gama warkewa ba..... Tun lokacin da aka ce ‘visar su ta fito gobe zata wuce’ Take kuka! Har yau da safe..Shuwa da su Baaba Talatu da Ummu ne sai kuma matar wan Mijin Ummu sai wata distant cousin d’insa, suka shirya za su kaita MT. Suna cikin shiri Anty Zainab ta shigo ita da su Khadija waenda zuwansu kenan. Da mamaki Mama take kallon Anty Zainab d’in wadda duk ta rame ta lalace jikinta yayi mugun sanyi kamar ba itaba ko dan ta jima bata ganta ba dan ko ranar da Kaka ya kirata ta je bata ganta ba tana d’aki wai tana bacci. Inda Mama take Anty Zainab ta nufa tana zuwa ta rungume ta sai kuma ta fashe da kuka!. Duk tsayawa suka yi suna kallonta da mamaki. A hankali Mama ta zaro ta daga jikinta kafin ta ce “Haba Zainab kuka kuma?” Cikin share hawayenta ta ce “Dole in yi kuka Maryam! Dole in yi takaici da bak’in cikin abubuwan da na aikata.. Na yi miki laifi na yi kuskure wanda a yanzu nake matuk’ar danasani, sam! Na kasa nutsuwa na kasa yafewa kaina.” Sai da ta share hawayenta wasu suna sake zubowa tukunna ta d’aura da cewa “Yanzu haka daga gidan me unguwa nake..na je na fad’a masa gaskiyar laifin da na yi miki sharrin da na yi miki wanda yayi sanadiyyar har aka koroki a makaranta.. Na gayawa Kaka shima gaskiya. Ki tayani neman yafiyar Abba dan Allah Maryam kema ki yafe min na yi kuskure Sadiya ta cuceni! Wallahi duk hud’ubarta ce ta sanya na juyawa aminiyata baya” Ta k’arashe maganar tana fashewa da wani sabon kukan. A hankali Mama ta yi hugging d’inta tana murmushi kafin ta ce “Zainab! Har ga Allah ba zan ce miki zan iya mantawa da abunda kika yi mini ba a lokaci guda ba, dan zan iya cewa ke ce ummulabaisin fad’a na da su Abba. Amman maganar yafiya kam wannan na yafe miki Allah ya yafe mana gaba d’aya. Sanna ki yi k’ok’ari ki yafewa Sadiya itama ko ba komai kar abun ya yi mata yawa saboda ko da bakin y’an layi aka barta ya isheta! Dan kowa idan ya tashi magana ita, kowa matsalarsa Sadiya… Idan mu bamu yafe mata mun yi mata fatan alkhairi ba wa zai yi?”. Wani sabon kukan Anty Zainab ta fashe dashi tana mamakin kyakkyawar zuciya irinta Mama. Da kyar su Shuwa da Ummu har Maman suka samu suka lallasheta ta nemi waje ta zauna tana gunjin kuka. Basu kai ga fara magana ba Madu ya shigo ya ce “Su fito da Sakina ga motocin MT sun k’araso” Sai a lokacin ta saki kukanta mai sauti…. Haka nan tana kuka tana komai Mommy da Mammy suna shigowa aka d’auketa aka fita da ita. Tana shiga motar motocin suka d’auki hanyar MT. A b’angaren Gramma aka ajjiyeta. Hudan, daman ta san da zuwan nasu dan basu ma dad’e da gama waya da Sakinar ba, shiyasa tana jin shigowar motoci ta lek’a ta sama da yake gidantane a farko farko yasa ta hango su. Tama manta da ciwon kafa da na jikin da take yi…Haka nan tana takawa tana d’an d’ingishi ta nufi hanya.. Da kyar ta iya sauk’a daga benen farko kawai sai ta durk’usa a wajen ta saki kuka… A haka Aslam ya shigo ya sameta. A rikice ya k’arasa ya hau tambayar ta ‘me ya sauk’o da ita?’. Ko kallon sa bata yi ba ta mik’e kawai ta fara k’ok’arin wucewa wanda sai a lokacin ne ya gane matsalarta… Dariya da tausayinta ne suka rufeshi amman ya dake ya b’ata rai ya ciccib’eta. Duk kalar rigima da yakushin da take yi mishi da kuka bai diretaba sai da ya kaita kan gadon tukunna. A hankali ya zauna ya kamo hannunta tana shirin mik’ewa ya ce “Ki nutsu. Kin san dai Sakina ba zata tab’a wucewa ba tare da ta zo ta yi miki sallama ba ko? Ki kwantar da hankalinki yanzu ma da na ajjiye su na ji suna cewa duk za su shigo miki kafin su wuce” Shiru ya yi yana kallonta still kafin ya ce “Yanzu ke idan aka barki a haka a wannan yanayin naki za ki je gaban su Ummun?”. Sai a lokacin kanta ya d’an d’au chaji. A hankali ta sunkuyar da kanta kafin ta ce “Ya Aslam tou dan Allah ka je ka taho da su, kar su k’i zuwa.” Sai da ya d’an yi shiruu tukunna ya kamo hannunta ya rik’e ya d’anyi kisssing sannan ya ce “Okay love, amman ki nutsu kin ji” D’an d’aga masa kai ta yi alamun ‘okay’. Ya d’an jima yana kallonta yana murmushi kafin ya sauk’e ajiyar zuciya a hankali ya ce “Alhamdulillah”tukunna ya mik’e ya fice a ranshi yana tunanin ta yadda Hudan take so ya je ya sake fuskantar su Ummu! Shi fa da kyar ma ya iya tsayawa suka gaisa especially ma Mama lokacin da ta rako Sakina har k’ofa, wata irriyar kunyarsu yake ji gaba d’ayansu. Shi kam gaskiya idan Mama ta k’araso estate d’inma bai san taya za su kaya ba. Cikin ikon Allah yana sauk’a parlourn chan k’asa Khadija da Yayarta suka shigo tare da Gramma da Sakina, dan Sakinar tunda taga su Ummu za su tafi ta sake d’aga hankalinta shine Gramma ta ce ‘bara ta yi bribing d’inta ta kaita wajen y’ar uwarta’. A parlourn sama Gramma ta ajjiyeta bata k’arasa chan sama ba ta juya ta fice dan tashi d’aya ta fahimci Aslam d’in baya so ta had’u da Hudan. Ba kunya haka ya kinkimeta bayan ya koma sama wajenta wai zai kaita wajensu. Da kyar sai da ta saka mishi kuka tukunna ya sauk’e ta ta yi practicing tafiyar da zata yi a gabanshi ta d’an dedeta yanayinta dan duk tayi kalar da duk mai hankalin da ya ganta sai ta tona masa asiri ne, ga kuma ciwon k’afa da na jikin da suka taru suka sauk’ar mata da d’ingishi. Sannan ya kama mata hannu ya d’an karata a jikinsa suka sauk’a tare. Suna tahowa Khadija ta fara yi mata dariyar tsokana k’asa k’asa Sarai Hudan ta fahimceta amman ta basar dan bata shirya biye mata ba Ita a ganinta wannan lamarin da take ciki jaje ya kamata ayi mata ba tsokana ba dan ita komai ya wuce tunaninta. A kusa da Sakina ya ajjiyeta kafin ya ce “Su zama ready nan da 2 hours su Sakinar za su wuce In sha Allah” Yana gama fad’in haka ya juya ya fita. Yana fita Huda ta fad’a jikin Sakina ta yi hugging d’inta. A hankali ta ji Sakinar ta sa kuka, d’agowa ta yi ta d’an b’ata rai itama idonta yana kawo kwalla ta ce “Haba mana dan Allah ki daina kar ki saka ni kuka nima” Ta fad’i haka ragowar hawayenta yana zubowa. Murmushi su Khadija ita da yayarta suka yi kafin Yayartata ta ce “to yanzu wa zai lallashi wani?” A hankali Huda wadda taga d’an rashin kyautawarta ta juya ta yi hugging Khadijar sannan ta kamo hannun Yayar khadijah daga inda take zaune ta ce “ina wuni” A hankali tana murmushi dan itama yanzu duk ta sauk’o ta ce “Alhamdulillah, gida yayi kyau Huda Allah ya sanya alkhairi ya baku zaman lafiya” A hankali ta juya cikin d’an tsokana da dauriya ta yayewa Sakina fuskarta, dan har yanzu fuskar tata a rufe take cikin mayafin laffayar da aka nad’a mata. Da kyar ta iya daurewa batayi kuka ba, fuskar nan tayi dagaje dagaje ta yi jajawur kana gani ka san ta ci uban kuka bana wasa ba, daman tun shekaran jiya da suke waya take jin yanayin muryarta a dashe. Cikin son sakata nishad’i ta ce “Haba mana Sakina, ki daina kuka, kinga fuskarki kuwa? Gashi duk kin yi wani laushi kamar ba ke ba. Ai ba wai zama za ku yi achan d’in ba har abada, yana warkewa fa za ku dawo in sha Allah…Ni kumafaa daa? da zan tafi chan wani gari ba ke kika yi ta bani kwarin guiwa ba?” Ta k’arashe a hankali daga nan ta yi shiru ta kasa ci gaba da magana. Su Khadija ne suka saka baki, suka taru suka yi ta lallab’ata har sai da ta d’an sake ta bar hawayen ta d’an kwantar da hankalinta tukunna suka d’an shiga hira a hankali. Khadijah ce ta ce “Gaskiya Huda gidan ki ya had’u over! Kalla kuma kaya koina duk girman gidan. Bara mu lek’a mu kashe kwarkwatar idonmu” Ta fad’i haka tana ajjiye mayafinta ta mik’e. Itama yayartata mik’ewa ta yi. Hudan har ta mik’e ta d’an fara takawa za ta bisu Khadija ta kamo hannunta ta zaunar da ita ta ce “zauna mai tafiyar ta’ta’taaa mun san hanya” Duka Huda ta kai mata ta yi saurin gocewa tana dariya suka nufi k’asa ita da yayar tata. Banda dukan uku uku ba abunda k’irjin Sakina yake yi daman tun d’azu ta d’an tsorata da yanayin tafiyar tata da ta gani. Maganar da Huda ta fara yi mata ne ya dawo da ita daga duniyar tunani da tsoron data tafi. A hankali ta juyo tana kallonta jin tana cewa “Ya Arshaad ya sake guduwa.. Ba a san inda yake ba! D’azu inaji Ya Aslam suna maganar shi da Dad a waya da na tambayeshi kuma sai ya k’i gaya min komi, kamar ma haushi ya ji.” Ta k’arashe maganar cikin karyewar zuciya. A hankali Sakina ta sauk’e wata nannauyar ajiyar zuciya kafin ta ce “Hudan I can’t even begin to imagine what Ya Arshaad is goin through! Dauriya ce kawai yake yi dan haka idan ya ga ba zai iya zama ba ya nuna yanaso zai tafi ya kamata ku bashi space ku barshi ya tafin. Kuma dan Allah ki daina nuna damuwarki over a kan Ya Arshaad a gaban Ya Aslam…Yes! Na san dole abun is somehow amman ki d’an dunga daurewa har Allah ya yaye miki son shi a zuciyarki ki manta da shi ki rungumi Mijin da Allah ya zab’a miki ku zauna lafiya dan na san Ya Aslam yana sonki wallahi tun a mansion d’in chan naso In fahimci wani abun shiru kawai na yi miki.” Shiruuu, Hudan ta yi kamar tana tunanin wani abu kafin chan ta ce “Yauwa Sakina, kin san wani abun

Chapter 19 of 26