suka yi makaranta secondary
ajinsu d’aya!
To irin sun d’an shak’u d’innan kamar besties haka suke.
Wata rana Ina tunawa muna level 1 lokacin ya zo kawo mata ziyara (shi bestyn nata) sai suka zo shi da wani Abokinsa mai suna ‘Sageer’
Tun da Sageer ya kyalla ido ya ga Suhailat tashi d’aya ya ji yana sonta!
Kasa ma hak’ura yayi mu koma a lokacin dayake ni na rakata,
a take yake cewa Abokin nasa shifa ya ga mahad’in shi!
Bai bar wajen ba sai da number da address d’in gidansu Suhaila na nan Kano.
To ashe itama Suhailan duk kanwar ja ce
dan muna komawa d’aki itama ta haukace mun haka nan
ta dinga yabon kyawun Sageer d’in da had’uwar shi
sanann ta sanar da ni yanda ya samu kyakkyawan gurbi a cikin zuciyarta.
Kafin wata d’aya
Soyayya da shak’uwa mai zafi ta shiga tsakanin Suhaila da Sageer...
A Dawowar da nayi kafin exams lokacin bikinku da Ya Arshaad, kafin In koma wani mumunnan alamari ya afku ata dalilin rashin wayon Suhaila!
Ta biyewa soyayya
ta mallakawa Sageer kanta
gaba d’aya bayan ya
d’auketa sun je sun yi court marriage sai kace wasu marasa mafad’i!
A cewar sa hakan zai sanya ta yarda da shi ta aminta ita zai rayu da har abada tunda ita a tsarin gidansu
Mace sai tayi phd tukunna take yin aure!
Haka nan Babansu yake da wannan muguwar ak’idar,
shi kuma Sageer ya ce ‘in dai ita kad’ai zai so kuma ita kad’ai zai aura zai kula
to ya kamata ta fahimci a yanayin tsarin halittarshi ta d’a Namiji ba zai iya yi mata wanann dogon jiran ba’.
In tak’aice muku labari dai
ciki yana yin wata d’aya ya baiyyana kanshi a jikin Suhaila!
Dan tsananin laulayin da take yi ya sanya hatta
matan dake gefen d’akin mu sai da suka
soma fahimtar wani abu
game da wannan
k’addarerren cikin!
Dan ta ce babu kalar protection d’in da ba suyi using ba.
Ba yadda muka iya haka muka rufa mata asiri mu uku
muka nufi asibiti da ita
dan tace idan Baban ta ya san labarin wallahi na lahira sai ya fita jin dad’i!
Yadda kika ga Granpa to haka itama Babanta yake da mugun tsauri! Kuma ita abun nata ma duka biyu za a iya cewa
dan Mahaifiyarta itama hakan take da tsauri.
Muna zuwa muka zubewa Likitan kud’i muka gaya mishi flushing muke so a yi mata duk da tanata ce mana ance ‘tana da matsala cikin ba zai fita ba’ Amman still muka zab’i mu gwada sa’ar mu..
Bayan y’an gwaje gwaje
unfortunately
Likitan ya zaunar da mu yayi mana cikakken bayani akan cikin nan ba zai fita ba!
Saboda tanada matsala
kuma in dai ance za a cire d’in tou it’s either ta mutu
ko kuma ta samu uterus failure.
Bamu da wani zab’in da ya wuce mu nemi Sageer duk da kuwa ta ce mana ‘tun last zuwanshi da ta ce mishi tana da ciki
ya d’auke ta ya kaita asibiti aka gaya mishi abunda aka gaya mana!
Kwana d’aya kawai yayi mata a gidan da suke had’uwa
daga nan ya k’ara gaba
kuma tun daga ranar ko wayarshi ta kira a kashe take jin ta. Although bai nuna mata komai ba
dan faram faram ma suka rabu
ko amai idan ta yi shi yake kwashewa ya gyara gurin
yanata faman jera mata sannu’.
Wani babban tashin hankali da abun al’ajabin da muka fuskanta shine
Hatta gidansu Sageer da address d’insu da ya bayar a garin Gombe gaba d’aya fake ne!
Hatta sunan Babanshi
Alhaji Bashir mai galon da ya fad’a mana gaba d’aya k’arya ne. Har Gombe
d’aya a cikinmu ta rok’i saurayinta ya je
ya bincika mana
amman babu abu d’aya da yake gaskiya a cikin labarin Sageer!
Komai fabricating kawai yayi.
Da muka fahimci haka
sai muka koma wajen Bestien ta, to shima dai ta wajen na sa duk sammakal dan ce mana ya yi
shima Iyakar wannan information d’in da muka sani akan Sageer shima shi kad’ai ya sani, ya ce
a wajen ball suka had’u suka fara shiri
suka d’anyi business tare
ranar kuma suna tare ya ce masa zai je wajen k’awar shi shine yace zai rakashi.
Shi bestyn nata ma
cewa yayi
wai ‘mu yi ta addua gaba d’ayan mu
maybe aljani ko maye muka had’u da
Allah ya tak’aita’.”
Ajiyar zuciya Aaima ta sauk’e sannan ta ci gaba da cewa
“To yau dai Allah ya had’ani da Sageer!”
Bata gama rufe bakinta ba ta mik’a musu hoton data nemo a wayar tata tun d’azu………
Sakina ce ta fara karb’ar wayar
tana kallonta kafin ta sauk’e idonta a kan wayar.
A hankali Huda ta ce
“Innalillahi wa innailaihirrajiun”
Bayan itama ta l’eka ta gani.
Sakina kuwa lumshe idonta kawai ta yi ta bud’e
ta kalli Aaima idonta jazir tap kwalla ta ce
“Aaima are you sure??”
“Very sure Sakina!
Ki yi ta sliding za ki ga pictures da videos d’insu kala kala irin wannnan shi da Suhaila.
Daga nan ki gaya min Idan wannan bawan Allahn ba Ashraff bane ba.”
BULAMA ✍️
So da Buri
Free Book
69
Mikiya Writers Association.
Kai kana ganin fuskokinsu ka san suna cikin tashin hankali ba na wasa ba.
Kallo suke suna sake kallan pictures d’in amman ba ta inda za su ce ba Ashraff bane ba.
A hankali Sakina ta mik’a mata wayarta sannan ta ce “yana Ina?”
Ta yi mata tambayar tana k’ok’arin mik’ewa tsaye.
Cikin ruk’o hannunta Aaima ta ce
“Ya tafi”
Sannan ta d’aura da cewa
“Mai aiki nasa taje har chan waje ta shigo da shi parlourn Mammy.
Abunda ya bani mamaki ya kuma d’aure min kai
shine
yadda ya nuna kamar irin kwata kwata babu alamun yama tab’a ganina d’in nan
sannan kuma he looks calm and innocent!
Kasa hak’ura na yi bayan mun gaisa na ce mishi
“Sageer”
Amman sai na ga yana kallona da mamaki!
Ganin da nayi ban ma san abunyi next ba yasa kawai na ce masa ‘ya tafi, dan Allah yayi hak’uri wani abun ya taso min urgent!’
Cikin fahimta ya nuna min ba damuwa ya mik’e ya tafi.
Sakina kaina ya d’aure saboda a ganina inda ace Sageer d’in ne to da ko a idanunsa zan fahimci firgici! Da d’an alamun wani abun dole zai nuna amman kuma
ko twins banajin za su iya zama super identical haka kamar shi da sageer..
Hatta fa yanayin magana kallo tafiya komai nasu iri d’aya ne..”
Cikin katseta Sakina ta ce
“Kar ki damu Aaima, ba wani
Sageer
sunanshi Ashraff!
Shine!
Raina miki hankali kawai yayi.
Ga Abokin sa nan ma Abbakar a wanann hoton.”
Da sauri Aaima ta karb’i wayar ta kalla sai kuma ta ce
“Ai shine Saddik d’in”
“Hmm”
Kawai Sakina ta ce tana
mai dialing numbershi a wayarta.
Ajiyar zuciya Aaima ta sauk’e kafin tace
“Kuma kin san abunda zai sa ma mu sake gasgata shi d’in ne…
Ranar farko da suka fara zuwa
a ranar da ya had’u da Suhaila
da ya ce mata
‘I’m Sageer by name’
Sai da Abokin nashi ya juya a zabure yana kallonshi
sai kuma na ga ya fara murmushi yana girgiza kai.”
Dede nan Ashraff ya amsa call d’in Sakina…
Daman a handsfree ta saka
“Hello baby”
Suka ji ya fad’a.
Sai da Sakina ta sauk’e wata nannauyar ajiyar zuciya tukunna ta ce
“Ashraff ko Sageer?”
“My god!!
Waye ne Sageer d’innan ne?
Kin san i was just about to call you sai kika kira…
That cousin of yours
she looks confuse!
Tana ganina ta ce min Sageer itama.
Ask her ta yi miki bayani please dan i d.........”
Cikin katseshi ta ce
“Dakata Ashraff!
Ba ita bace confused, ni ce!
Bayani kuma ba ita za ta yi min ba kaine!.
So I’m all ears
Ina so inji
ta yadda ka chanja sunan ka
da kuma yanda kake planing zaka yi da mu
Ni da Suhaila da kuma d’an cikinta”
“Oh Noooo!
Innalillahi wa innailaihirrajiun
Sakina haba mana.
Tana ina ita cousin d’in taku?
Bata wayar please…
Wallahi daman yadda na ga tayi na san akwai matsala,
waye Sageer? Wacece Suhaila? Ciki kuma a Ina?.
Sakina na riga na gaya miki y’an mata biyu kawai na yi dating b4 you
and duk na nuna miki pictures d’insu, please Sakina
kar ki biye mata
i think akwai confusion a lamarinta
amman wallahi ni ban san wani Sageer ba,
bata wayar please”.
Fashewa kawai ya ji Sakinar ta yi da kuka, cikin kukan ta ce
“Haba Ashraff!
Despite abunda ka yi da k’aryar da ka yi
still kana so ka ci gaba da b’oye b’oye?
Wat have i ever done to you to deserve this?”
“Innalillahi wa inna ilaihirrajiun” kawai ta ji yanata maimaitawa kafin ya ce
“Shikenan Sakina,
na gane! Yanzu na fahimci komai…
Kina neman hanyar da za ki zillemun ki auri Auwal d’in da kike ta tunani kullum ko?
Ko kina tunanin ban saniba ne?
Idan ba kya sona ki fito fili kawai ki gaya min ki daina yi min kwana kwana!
Bawai ku had’a baki ba
ku k’ulla min sharrin abu mai muni haka ba.
Wallahi tallahi kin ji de na rantse miki
ni ban san wani Sageer ba
ban san wacece Suhaila ba
sanann wallahi Sakina da gaske nake sonki ba yaudara a ciki! Ke kad’ai ce a cikin zuciyata”
Ya fad’i haka yana me fashewa da kuka kamar k’aramin Yaro
sai kuma ta ji ya kashe wayar, kiit!.
Ashraff, yana kashe wayar ya kira Saddik yana d’auka bai jira jin me zai ce ba
ya ce
“Saddik, I’m doomed….”
Sanann ya hau koro mishi bayani hankalinshi a mugun tashe.
Shiruu Saddik d’in yayi
bayan ya gama ji
kafin ya ce
“Listen closely Ashraff..................”
Gaba d’ayansu hankalinsu a tashe yake, bama su san ta Ina za su fara ba.
Aaima ce ta yanke shawarar kiran Suhailar dan haka ta d’au waya ta shiga sunanta ta danna call……
An fi thirty minutes tukunna aka samu layinta ya fita daga busy ta amsa kiran Aaiman.
Ajiyar zuciya Aaima ta sauk’e kafin ta ce
“Da wa kike waya haka?”
Sai da ta d’anyi jimm! Tukunna ta ce
“Wata friend d’ita ce”
Shiruu, Aaiman ta yi tana tunanin wacece k’awar Suhaila haka da bata san ta ba…
Sanin ba wannan ne a gabansu ba
ya sa kawai ta kawar da zancen ta hanyar bata labarin Sageer Ashraff from A -Z kafin ta ce
“Yanzu ko gidan su idan kinaso zamu iya zuwa dan Sakina ta ce ta san gidan
kuma zata bamu adress har number Mamansa.”
Cikin katseta Suhailan ta ce
“Mun gama case d’in Sageer fa!
Ki manta kawai please, kar ki
sake yi min maganarsa”
A rikice Aaiman ta ce
“Kin gama case d’insa da cikinsa a jikinki??”
“Please Aaima”
Shine kawai abunda Suhaila ta ce.
Aaima za ta yi magana kawai ta ji ta katse kiran.
Kasa cire wayar daga kunnenta Aaiman ta yi,
da kyar ta d’ago tana kallonsu still da wayar kare a kunnenta.
Kirane ya shigo wayartata
dan haka ta d’an zabura saboda a kunnenta wayar take har yanzu…
Tana ganin mai kiran nata ta d’auka da sauri ta ce “yauwa Khadija kin san me yake faruwa?
Yanzun nan....”
Cikin katseta Khadijar ta ce
“Sageer, yanzun nan ya kira Suhaila….
Suna fara magana ta tashi ta shiga bathroom, haka
kawai na ji inaso in yi mata lab’e saboda na san kusan wata nawa ana neman shi
sai yau kawai muga ya kirata.
A yadda na fahimta
Its like akwai wadda zai aura a yanzu! Wai family d’insu
sun zab’a masa
shiyasa ma ya d’auke k’afa
amman yayi mata alk’awarin aure nan da wata biyar
muddin ta yi shiru.
Ban gama dawowa daga mamaki ba
na ji conversation d’in ku a waya yanzu.
Meyene yake faruwa?”.
Ajiyar zuciya Aaima ta sauk’e rai a b’ace ta ce
“Wato shine Ashraff d’in ta tabbata kenan!…”
Nan ta d’an yi briefing Khadija a kan case d’in sannan ta ce
“Khadija Suhaila tana son
Ashraff
ba zata tab’a iya k’etare umarninshi ba!
Dan haka yanzu aiki yana a hannunki..
Ki taimaki y’ar uwar ki
tunda ni dai kinji yadda muka yi da ita.
Zan turo miki number Mamansa yanzu
daga nan ki kirata ki yi mata bayanin komai!
Lokacin b’oye b’oye ya wuce
dole iyaye su shiga case d’innan.
Mugun tantiri ne Ashraff d’innan wallahi! Kin san yadda ya nuna kuwa kamar bai sanni ba amman kalli har ya kirawota munafuki d’an iska!
Kuma wallahi k’arya yake yi
shi ya ga Sakina ya ce yana sonta ba wani had’asu da akayi
Infact
Families d’insu ma basu san juna ba sai ata dalilin ita Sakinar da shi Ashraff d’in.
Wanne irin rashin wayone haka Suhaila take yi!
Dan bayan soyayya tabbas akwai dak’ik’anci a cikin lamarinta, saboda Allah ace wai Mutumin da yayi maka wannan abun
tashi d’aya ya dawo ya kalallame ka kuma ka yarda?
Duk da ban san me ya ce mata ba amman ai ya kamata ta tambayeshi dalilin da ya sa ya bamu fake adress ko?”
A hankali Khadija ta ce
“Tabbas”
Sannan ta ce
‘Ta tura mata number Maman ashraff d’in ta kirata yanzu ba sai anjima ba
kafin Suhaila ta dawo d’akin.”
Da “to” ta amsa sannan ta katse kiran
kafin ta kallesu ta ce
“Yayar Suhailan ce,
Itama ta san da zancen.
Ina number Maman nashi?”
Kamar yadda Sakina ta fad’a haka ta bada number Maman Ashraff bayan sun kwantar mata da hankali da kyar! Dan da cewa ta yi sai ta je ta sameshi a duk inda yake!
Hudan ma harda y’ar kwallarta ganin yadda Sakinar duk ta firgice ta fita haiyyacinta tana ta kuka wiwi.
Gaba d’aya sun gigita da lamarin Ashraff. ..........
Suna zaune a d’akin wata maid ta shigo musu da abinci kala kala..
Aaima da Huda ne suka d’an ci
Sakina kam har yanzu hankalinta a tashe yake,
ashe ita ta yi gudun gara ne ta tadda zago
ba tare da ta sani ba…
Sai bayan sallar Magrib tukunna Junaidu ya kirata ya ce “taje yana waje, su wuce.”
Aaima ce ta rakata har bakin mota bayan sun sha kukan su ita da Huda
sannan sun d’an yi mata y’ar guntuwar Nasiha suma, dan itama Aaiman ba komawa za ta yi ba sunyi sallama kenan
saboda
ta san Huda tsaf sai ta rik’eta kamar yadda ta kanainaye Sakina.
Duk da halinda Sakina take ciki
sai da ta fahimci kallon da Aaima da Junaidu suke yiwa juna!
Tun d’azu dama da za a kawo Huda ta d’an lura
yanzu kuma ta sake tabbatarwa
dan har tana yiwa Junaidun magana ma bai sani ba.
Kasa hak’ura tayi bayan sun d’au hanya ta ce
“Ya Junaidu ko dai In had’aku ne?”
Wani lallausan murmushi ta ga ya yi kafin ya ce
“A’a fa Sakina,
tuwon girma ai miyarsa nama!
Idan na d’auko wannan ina da wajen ajjiyeta ne?”
Da sauri Sakina ta ce
“Ya Junaidu
ranar nan fa na ji Kaka yana cewa Gidajen ka wajen biyar a Kano kawai ga motoci
ga filaye.”
Dariya ya yi this time around
sanann ya ce
“Ki bar maganar nan..
Although har ga Allah i felt something
towards her
very strong
amman tunda na rasa Huda
i don’t think zan yi aure
idan ma zan yi d’in to
gaskiya ba nan kusa ba.”
Ajiyar zuciya ta sauk’e
tana kallon yadda fuskarsa ta chanja
lokaci guda.
Daga haka motar ta d’auki shiruuu
kowa da abunda yake sak’awa a ranshi, har ya kaita k’ofar gidan nasu ya ajjiyeta.
Tana sauk’a yayi reverse ya juya dan akwai ayyuka da dama akanshi.
Tana shirin tura gate d’in gidan ta ji ya ce
“Sakina”
Da sauri ta juyo!
Daman taga kamar motarshi a parke d’an gaba kad’an.
Ganin sa d’in ne kuwa yasa ta had’e fuska tamau! Kafin ta ce
“Naam, Sageer.”
A hankali ya k’araso inda take, sai da hasken globe d’in k’ofar gidan nasu ya haska fuskarshi da kyau tukunna ta lura da abun mamaki..
Gani tayi yana
kuka wiwi
fuskarshi har ta kumbure da alamun ya dad’e yana yi.
Tana shirin yin magana shi ya rigata ta hanyar cewa
“Sakina komai Aaima ta fad’a muku gaskiyane
nine Sageer!
Amman asalin sunana Ashraff.
Ba zan b’oye miki ba…
Har ga Allah tun farkon had’uwata da Yarinyar na ji ina sonta
amman ba so na aure ba
sha’awace kawai irin wadda shed’an kan saka a zuk’atan waenda ya yi nasara.
Na san Abbakar Abokina ne tun Yarinta. Muna barin gurin ya tambayeni ‘dalilin b’oye mata asalin sunana da na yi’
Ban b’oye mishi ba
na fad’a mishi k’udurina a kanta!
Ya ji ba dad’i kuma yaso nusar da ni amman da yake
shed’an ya riga yayi galaba a kaina yasa sam ban ji ba.”
Matsowa ya sake yi kusa da ita
wanda hakan yasa ta d’an ja baya.
Cikin kuka kamar Yaro ya ce
“Sakina na yi laifi, na san
na yi laifi!
Amman dan Allah ki fahimceni
ki fahimci k’aunar da nake yi miki ta tsakani da Allah ce.
Ki duba kiga yadda ita na fad’a mata fake adress fake suna and everything
Ke kuma na fad’a miki komai nawa! Har waya kuke yi da Mamana.
Dan Allah kar ki bari a rabamu,
ki toshe kunnuwanki, fight for our love! Ko wanne d’an Adam ajizi ne
ni ga nawa mistake d’in
dan Allah ki fahimceni
kin ga gashi
na fad’a miki komai ban b’oye miki ba,
ki yi min adalci Sakina.”
Girgiza kai kawai Sakina ta yi sannan ta share hawayenta ta ce
“Meyasa ka zab’i ka gaya min yanzu?
Saboda an kira Maman ku ko?
Kuma ka san dole case zai taso…
Bara ka ji Ashraff
magana d’aya kawai zan iya gaya maka
saboda at this stage ba zan ma iya tolerating ganinka ba! Saboda abubuwan da ka yi sunada yawa ban san ta Ina zan iya farawaba…
Abunda nake so ince kuma nake so ka fahimceni da kyau
tunda naga kana da sharp brain
shiine
Ba zan aureka ba!”
A gigice ya d’ago yana kallonta.
“Kwarai!!
Babu wannan maganar.
Ga responsibility d’inka chan ‘Suhailat’
Ka koma gareta
ka nemi yafiya
ku haifi d’anku
ku zauna lafiya
ku reneshi a tare!”
Tana gama fad’in haka ta juya zata shige gidan ya yi saurin ruk’o hannunta.
A mugun fusace
ta juyo bata yi wata wata ba ta d’auke shi da wani irin mahaukacin mari
jikinta har karkarwa yake yi ta ce
“Na rantse maka da Allah idan baka bar nan ba
zan iya yi maka illa!
Dan duk abunda na raruma sai na maka ma
saboda raina ya kai k’ololuwa wajen b’aci!
Audacity d’inka shi yafi komai d’aga min hankali Ashraff!
Ka ma raina min hankali wallahi!
How kake tunanin.....”
Shiruu ta yi ta kasa ci gaba da magana chan kuma ta ce
“Kaga! Just go, kama
gabanka. Like i said
Idan na ce zan yi maganar abubuwan da ka yi da renin wayon da ka zo da shi yanzu to
ba zan iya jurar ganinka k’alau akan k’afafuwanka ba!
So just leave!!!!”
Ta k’arashe maganar cikin tsawa sannan ta juya ta tura zata shige cikin gidan
ta ji ya ruk’ota!
Za ta yi magana ta ji ya toshe mata baki da hanci da wani handkerchief....
Sai dare tukunna Granpa ya tara su Dad da Gramma ya fad’a musu d’aurin auren Maryam da Abba
next week in sha Allah.
A ranar Abba kasa bacci yayi
yadda ya ga rana haka ya ga dare!
Daga k’arshema ma ji yayi cheecks d’inshi sun fara ciwo tsabar murmushi. Tun ba ma da ya kira Mama ta kula shi sosai ba.
Kaka ma ya samu Madu,
babu alamun wasa a fuskarshi yace
“In dai har yanzu
yana yi mishi kallon Mahaifi a wajen Maryam
to ya sani ya saka ranarta!
Rana ita yau su Granpa za su zo a d’aura aure. Kuma dan girman Allah kar ya tambayeshi dalili ko ya yi mishi musu indai yana buk’atar Abotar su ta d’aure har k’arshen rayuwarsu.”
Murmushi kawai Madu yayi
kafin ya ce
“Kaka ai Abotar mu har aljannah in sha Allah
ba abunda zan bari ya shiga tsakani
dan haka duk abunda ka yanke na goyi bayanka
blindfolded….duk da ban san dalilinka ba
amman i trust you kuma zan yi sopporting d’inka d’ari bisa d’ari!
So dan Allah kar ma ka sako
maganar lalacewar Abotar mu
Allah ya kaimu ranar asabar d’in da rai da lafiya.”
Ya k’arashe maganar yana murmushi.
Duk fushin da Kaka ya kwaso daga gida sai ya ji gaba d’aya ya kau. Dan haka yad’an sake suka shiga tattauna abunda ya shafi alamuransu
mostly a kan Jalila. Kafin daga baya ya nemi ganin Mama itama….
Same yada ya yiwa Madu itama haka yayi mata
kafin ya d’aura da cewa
“Indai ta d’auke shi a matsayin uba har yanzu tou kar ta yi mishi jayayya
kawai yanaso ta amince da abunda ya zo da shi”
Daga anan ya d’aura mata da Nasiha akan ‘kar ta rik’e Abba a ranta komai ya wuce
su zauna su yi rayuwarsu kamar farko
Allah yayi musu albarka.’
A hankali ta ce “ameen” sannnan ta yi mishi godiya
daga nan ta mik’e ta fita.
Wata nannauyar ajiyar zuciya Kaka ya sauk’e yana jin wani nauyi yana sauk’ar mishi
tun kafin ya kai ga sauk’ewa gaba d’aya…….
Tana zaune a kan darduma ta idar da sallar isha kenan
Gwaggo Asabe ta shigo
da akwati sai kuma Mommy da ragowar masu aiki mata
duk da akwatuna…
Tun tana iya irga su har ta hak’ura ta tsaya kawai a tsaye
bayan ta mik’e ta gaidasu cikin girmamawa.
Sai da aka jere akwatunan tukunna suka yi mata sai da safe suka juya suka fita suka barta nan a daskare.
Ta fi minti uku
kafin ta samu ta k’arasa bakin gadon ta zauna still idanunta a kan akwatunan.
Da sallama ya turo k’ofar ya shigo! Da leda a hannunshi.
Da sauri ta sunkuyar da kanta ta ja hular alkyabbar ta rufe fuskartata.
Murmushi yayi kafin ya k’araso inda take nan bakin gadon ya zauna ya kamo hannunta cikin nashi ya rik’e ya d’an murza kafin ya ce
“Sai na yi siyan fuska shima?”
Dariya Hausar tashi ta bata dan haka ta d’an saki murmushi wanda har sai da ya jiyo sautin shi.
A hankali ya ajjiye ledojin dake nan rik’e a hannunshi
kafin ya sauk’o gabanta yad’an durk’usa tukunna ya sa hannu ya janye hular alkyabbar.
Wata nannauyar ajiyar zuciya ya sauk’e kafin yace
“Ma sha Allah”
Sai kuma ya sake cewa
“Kukan me kika yi?”
A hankali ta girgiza kanta alamun ‘ba komai’
Tana jin bugun zuciyarta yana kara tsananta!.
Cikin son ya tashi a gaban ta ta ce
“Akwatunan menenen wannan?”
Murmushi yayi yad’an sunkuyar da kanshi k’asa ya ciji lips d’inshi kafin ya d’ago da kanshi yana kallonta tukun ya fara magana
“Ai dama sai da na cewa Mommy ta yafe min a barni ba sai na yi ba
amman ta saka ni kashe uban miliyoyi akan lefe!
Yau kusan wata biyu kenan tana ta tatsemin aljihu.
Ga shi ke kanki bama ki so ba ko?
Mu mayar mu karb’o kud’in mu?”
Sai yanzu ta d’ago ta kalleshi
“Ma sha Allah” ta fad’a a ranta..
Tunda ya shigo dama ta lura da fararen kaya ne a jikinshi kaftan, sai yanzu taga ashe har hular kansa itama fara ce tas! A ranta ta ce
“Manyan kaya sun fi yi maka kyau”
Cikin katseta ta ji ya ce
“Kwalliya ya biya kud’in sabulu kenan!
Tunda gashi har an saki baki ana kallona”
Ya fad’a yana murmushi gefen baki da d’age mata gira.
Da sauri ta d’auke idonta da kyar.
Cikin son kawar da zance
ta ce
“Ya Aslam wasa wasa fa kanada rowa, tun ba
yau ba na fuskanci haka”
Dariya sosai yayi kafin ya ce
“Ai kin fini rowa!
Tunda gashi ana ta yi
mini rowar zuciya.”
Ya fad’i maganar yana k’ok’arin yin zaman dirshen akan kafet d’in gaban gadon ( a gabanta)
Yana zama, bata san lokacin da ta yi sauri itama ta sauk’o ta zauna a gabansa ba
har guiwowinsu suna gogar juna.
Sai kuma ta fara k’ok’arin janyewa…
Hannuwanshi ya saka ya rik’e cinyar tata ta yadda ba zata iya motsawa ba!
Yana jin wani yanayi na daban ya na shigar shi…
A hankali yana d’an murmushi ya ce
“I love this respect
da kike min Hudatie,
Thank you.”
Sunkuyar da kanta ta yi kawai ta kasa cewa komai.
A hankali yana kallonta ya ce
“Baki ce komai ba.
Akan maganar mu da muka fara a d’akin Gramma”.
Da sauri ta ce
“Ya Aslam dan Allah ka daina bana son maganar.
Kuma ni dai ka d’auke hannunka.”
Gefe ya kalla yayi wani murmushin gefen baki..
Bata gama fahimtar murmushi da jinjina kan me yake yi ba
ta ga ya mik’e tana shirin yin magana ya sunkuya ya d’auketa!
Sai da ya k’arasa wajen sofa tukunna ya zauna ya d’aura ta a kan cinyarshi kafin ya ce “Bud’e idon sannan ki ja numfashi
Matsoraciya kawai…
In kika sake yi min musu ko kika ce kar In tab’aki Allah sai na nuna miki matsayina a wajenki.”
A hankali ta bud’e idonta tana kallon k’asa.. Hankalinta In yayi dubu tou ya tashi!
Tanajin yadda jikinsa yake d’an rawa kad’an kad’an
ga zuciyarshi tana iya feeling bugunta!
A hankali ta ji ya ce
“Unhm ina jinki.
Say something anything…
i told you how I feel.
Let’s
All Chapters
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 17 Chapter of 26