ka san inane jail kuwa?”
Sai yanzu Gramma wadda tunda aka fara case d’in ta sunkuyar da kanta tana salati
ta samu ta fashe da kuka…
A hankali ta d’ago kanta ta taso ta iso inda suke
ta kama Arshaad ta mik’ar da shi tana kuka ta ce
“Aslam ka manta waye Arshaad ne?
Tun kuna Yara
Idan ya yiwa mutum laifi b’uya fa yake yi ko da ace mutumin ya yafe masa sai yayi kusan wata yana wasan y’ar b’uya da shi. Ka san Arshaad yana da kunya yana da kawaici kuma yana k’aunarka!
Na tabbatar laifin da ya aikata ne ya saka shi yake jin ba lalle a yafe mishi ba sanann shi kanshi ba zai iya fuskantar kowa ba shiyasa ya gwammaci zaman jail a kan zama da mu
sannan kuma ka tuna Arshaad
yana iya sacrificing komai saboda Mahaifiyarsa
unlike her! I’m pretty sure ita yake ta k’ok’arin rufawaa asiri
wanda hakan ya had’u da
Guilt shiyasa yake k’ok’arin tura kanshi jail!
Haka ne ko ba haka ba! Arshaad?”
Gramma ta k’arashe maganar tana sake fashewa da wani sabon kukan.
Gaba d’aya kuka suka saka
Aiima Huda Dad Sudais Shuraim Mammy Daddy Mommy hatta Granpa da Abba wanda yake chan a zaune ya kasa motsi
kowa kawai hawaye yake yi.
Hannuwan Gramma ya rik’e gamm! A cikin nasa ya ce
“Gramma dole Ina da laifi one way or the other..
Ga Junaidu sannan ga successful company d’in da na tarwatsa na lalatawa Aslam…
Na biyewa son zuciya Gramma!
Na biyewa
So da buri, ki kyaleni dan Allah ki rabu da ni
I need time alone away from all of you!
Besides Ina jin tsoron kaina
a duk lokacin da na ga Huda da Aslam na kan ji tsananin kishi!
Ba zan iya ba!
This is torture!
Ni kad’ai na san abunda nake going through”
Ya k’arashe maganar yana fashewa da kuka.
Wanann karon hatta Abba kuka ya saka.
Da sauri Huda ta mik’e ta fita da sauri
Aaima kuma ta bi bayanta.
Bata tashi sanin Aaiima na bayan nata ba sai da suka shiga cikin parlourn gidanta.
Jin mutum a bayanta yasa ta juyo suna had’a ido kawai sai suka fashe da kuka a tare gaba d’ayansu….
Da kyar Huda ta iya d’akko wayarta ta kira Junaidu yana d’auka ta ce
“Dan girman Allah ya zo tana son ganinshi
a kan case d’in Ya Arshaad!
Ya dubi girman Allah
ya taimaketa
idan wannan ce alfarma d’aya tak da zai yi mata a duniya ya zo ya yi withdrawing complaints d’inshi dan ya rasulillahi...........”
“Za mu yi arresting Rukayya Yusuf za mu tafi da ita! Za a sake bincikar ta sannan
a kotu za ta ji hukuncinta”
Daya a cikin y’an sandan ya fad’a…….....
Anfi 20 minutes ana fama da Mammy dan hauka tayi musu tuburan da kyar sai da aka nuna mata bindiga tukunna ta tsaya aka datsa mata ankwa.
Kukan da Arshaad yake yi sai da ya saka kowa kuka.
A hankali ya durk’ushe a wajen.
Mommy ma ta so hanawa amman Dad ya rik’eta
haka aka fita da Mammmy tanata kuka tana tonawa kanta asiri dan sai faman jerowa Dad Granpa da Mommy Allah ya isa take yi
a cewarta su ne suka tunzurata ta yi komai
sannan in da Granpa bai bawa Aslam gida
sannan ya bashi Mt a b’oye a munafurceba to da bata yi abunda ta yi ranar birthday d’in su Shuraim ba.
Ana fita da Mammy bayan d’akin ya d’auki shiru
na kusan 7 minutes.
Babban y’an sandan ya yi gyaran murya ya sake cewa
“Unfortunately za mu tafi da Arshaad shima..
Bashi da laifi a case d’in Ummi
amman yana a case d’in Junaidu!
Kuma Junaidu a sama shima ya kai k’arar shi
dan direct case d’in daman hannuna ya fad’o.
Sannan Aslam ma idan yanaso zai iya filing complaint ya yi shara’a da shi
akan tarwatsa mishi company da ya yi.”
Cikin tsananin b’acin rai Asalm ya k’arasa inda mutumin yake tsaye ya ce
“Who the hell do you think you are?
Ni zaka gayawa abunda zan yi da brother d’ina!?
Idan na sake ji kace zan yi shari’a da shi I ‘ll make sure ka yi regretting kasancewarka d’an sanda!
Off you go..
Just leave!
Za mu k’arasa issue d’in mu mun gode.”
A hankali cikin d’an b’acin rai mutumin ya ce
“Mr Aslam watch you words!
Kuma let me assure you
Idan ba Junaidu ne yazo nan ya ce ya yi withdrawing complaints d’inshi a Arshaad ba to dole za mu tafi da shi!
And idan ka yi interfering to
za mu had’a da kai”
A hankali Arshaad ya mik’e ya k’arasa ya dafa kafad’un Aslam ya ce
“Let it go..
It’s fine i’m fine.”
Yana shirin yin magana
Junaidu ya shigo shi da Aaima…………………
Tabbas!
Ya so ya hukunta Arshaad,
yaso ya hukuntashi akan irin abunda ya yi masa amma
ta dalilin Hudan sannan tsakanin shi da Aaima tabbas ya san watak’il wani abun ya k’ullu dan tunda ya ganta ya rasa sukuni sam!
Waennan dalilai biyu suka sanya kawai
ya k’arasa inda mutumin yake tsaye ya ce
“Na yi withdrawing complaint d’ina! Arshaad can go free.
Allah ya sa mu fi k’arfin zuciyoyinmu.”
Wata nannauyar ajiyar zuciya Aslam ya sauk’e
kafin ya juya inda Junaidun ya ke ya yi hugging d’inshi sannan ya d’ago yad’an yi tapping shoulder d’inshi ya ce
“Thank you Junaidu,
thank you so much.”
Murmushi kawai ya yi
Arshaad yana shirin yi mishi magana ya juya ya fita.
Da sauri Aaima ta bi bayansa dan yi mishi godiya.
Bata samu ta cimmasa ba
sai a compound d’in Granpa dan sauri yake yi sosai.
Da d’an k’arfi ta ce
“Hey”
Ajiyar zuciya ya sauk’e ya lumshe manyan idanuwanshi tukunna ya juyo.
Gaba d’aya jikinta a sanyaye yake a haka ma bata ga sanda aka tafi da Mammy ba.
Tana zuwa ta ce
“Thank you. Mun gode kwarai!
Allah Ubangiji ya taimakeka kaima a lokacin da kake buk’atar taimakon gaggawa”
A hankali ya d’an sunkuyar da kanshi, har ya d’ago zai yi magana sai kuma ya lura da yanayinta..
Ganin da yayi bai kamata su yi wannan maganar yanzu ba yasa ya ce
“Ba komai.
Amman akwai alfarmar da nake nema a wajenki!
Naga yanzu
you are not in a good shape idan ba damuwa
zan iya zuwa nan da 1 week
da laasar
around 5 haka!
I need to talk to you.”
A hankali ta ce
“Allah ya kaimu”
Daga nan suka yi sallama ta sake yi mishi godiya
ta koma ciki. Tana tafe tana matsar hawaye.
Abakin kofar shiga taga mutumin ya fito da ragowar mutane biyu
Haka kawai jikinta ya bata
an tafi da Mammy dan daman bata ganta ba d’azu da ta dawo parlourn...
Anan wajen kawai ta durk’ushe ta sa kuka.
Aslam yana ganin mutumin ya fita ya sauk’e ajiyar zuciya ya kalli Gramma ya ce
“Gramma Ina takardun dana baki d’azu da safe?”
A hankali Gramma tana matsar hawaye
ta juya ta nufi hanyar d’akinta.
Bata yi 4 minutes ba ta fito rik’e da wasu takardu masu yawa file file wajen uku.
Bai bari ta k’araso ba ya k’arasa ya karb’a sannan ya zaunar da ita a kan kujera ya ce “thank you”
A hankali ya k’arasa ya d’an rissina ya mik’awa Granpa ya ce
‘ya duba,
yana zuwa
bara ya d’anyi magana da Arshaad.’
A hankali ya k’arasa inda Arshaad yake ya ce
“Arshaad you are my brother and best friend.
Bani da d’an uwa kuma Aboki kamar ka
amman ka yi hak’uri ba
laifina bane
Allah ne ya d’aura mana son mace d’aya!
Ba zan iya b’oye maka ba
I loved Huda tun kafin ka kaini wajen ta mu gaisa
i knew her tun ina Uk....”
Nan ya bashi brief labarin da ya gayawa Huda. A hankali ya ce “Da na dawo naga yadda kake k’aunarta
shiyasa kawai na yi deciding
In bar maka ita! Which almost kill me shiyasa yanzu nake mai baka hak’uri..
Da ace inada iko da zuciyata
to da na hak’ura na bar maka ita amman ba zan iya ba!
I’m sorry to say this to your face wallahi ban san irin k’aunar da nake yi mata ba
ban san ma kalar wannan son nake yi mata ba sai da na mallaketa a matsayin matata!
Dan Allah ka yi hak’uri ka fahimceni......”
Hugging d’inshi kawai Arshaad ya yi yana hawaye.
Dakyar suka cika juna
Arshaad d’in ya ce
“You have sacrificed a lot for me ka gaya min dalilin da zai sa ba zan hak’ura In cire matarka a raina ba?
Kar ka damu
you have tried
Aslam
for my happines
kanaji kana gani ka danne farin cikin ka saboda ni in yi farin ciki.
You are the best brother and the best friend in the world..
Komai ya wuce
Ina so ka saka a ranka kamar ban tab’a had’uwa da Huda ba
amma dan Allah please inaso zan bar k’asar nan!
For some years
Ina son in yi healing daga Mammy da kuma everythin..
Don’t stop me please......”
Murmushi Aslam ya yi kafin ya ce “ba zan barka ka tafi haka ba”
Ya fad’i haka yana mai juyawa ya isa inda Granpa ya ke yad’an rusuna tukunna ya karb’a takardun da Granpa ya gama dubawa
ya fara magana..
“Granpa ya mallaka min Mt
duk da na san kowa ya sani a nan a yanzu, wanda maganar ta fito ne ta wajen Mammy da ta ga copies d’in takardun a d’akin Arshaad, shi kuma na san a mota ta ya ga takardun
ranar da ya d’auka ya fita ya ce tasa ta lalace.
A ranar da ya bani gida a UK a ranar ya bani had’e da MT.
Ba yadda ban yi da shi ba
amman ya ce
‘yana so yayi komai ya gama
ya gaji da cases
kuma daman shi ni ya shirya bawa.’
Na yi godiya tabbas na kuma yi farin ciki amma a ranar na fara working akan nima nawa decision d’in………
Arshaad, mun yi magana da kai a kan kana so ka bar k’asar nan shiyasa na baka na Uk!
Hope you are happy.”
Da sauri kowa ya zuba mishi ido.
Murmushi ya yi
ya d’aga musu kai alamun tabbatarwa
Sanann ya ci gaba da magana
“Auwal kuma na bashi na Abuja, ni kuma na d’auki na Kano”
A hankali ya juya inda Granpa yake ya ce
“Granpa ba wa ban ji dad’i akan kyautar da ka yi mini ba
No
I really appreciate it
but this has been my wish since..
It was your wish ka mallaka min MT ni kuma wish d’ina shine mu rabashi a tsakaninmu brothers uku.
I hope ban b’ata maka rai ba
sannan kayi farin ciki da decision d’ina.
Ban yi tempering da wish d’inka na passing MT from generation to generation ba
Instead na sake fad’ad’a wish d’in naka ne
Na tabbatar duk mu uku zamu zage kwazo wajen kular maka da MT in sha Allah
kowa zai kula da nashi
sannan za mu yi passing d’in shi each to our capable child just like you wanted
sannan zamu rubuta mu ajjiye
y’ay’an mu suma su
bawa capable jikan mu each suma kuma jikokin namu
su bawa capable d’ansu…
A haka dai har illa masha Allah.
I hope ban sab’a maka ba.”
Ya k’arashe maganar yana sunkuyar da kanshi
ganin yadda Granpa ya kafeshi da idanuwa.
A hankali Granpa ya mik’e ya sauk’o daga kan kujerar tashi
ya dogara sandarshi ya k’arasa inda Aslam yake tsaye ya shafa fuskarshi a hankali
yana jin tsantsar k’aunar jikan nashi tana sake shiga cikin zuciyarshi, a hankali ya ce
“I wonder why
mutane suke jin haushi
Idan nace kaine favorite jikana.”
Yana gama fad’in haka
ya ce “Allah ya yi muku albarka
I’m very happy with your decision, thank you.”
Daganan yasa kai ya wuce side d’inshi yana dogara y’ar sandarshi Gramma itama ta mik’e ta mara mishi baya.
A hankali Dad ya k’arasa ya yi hugging Aslam sai kuma
ya jawo Arshaad shima ya had’asu duk su biyun ya rungume.
Murmushi Abba yayi
shinda su Shuraim waenda suka koma kusa dashi tun d’azu da za a tafi da Mammy suka mak’ale masa.
Haka shima Daddy
yana d’an murmushi idanunshi tap kwallah ya ce
“Inama ace inada super powern da zan yi using in ganni a tsakiyanku”
Dariya duk suka yi har Mommy.
A hankali ya ke kallonsu
kafin ya ce
“Sai mun dawo in shaa Allah..
May this smile never fade away a fuskokinmu”
Duk had’a baki suka yi wajen cewa “Ameen”
Daga nan su Daddy suka yanke kiran.
BULAMA ✍️
So da Buri
Free Book
72.
A parlourn k’asa Aslam ya tadda Huda tanata faman safa da marwa…
Duk yadda taso kasa rik’e kukanta tayi dan haka kawai sai ta sakeshi ta taho tana zuwa ta fad’a jikinsa.
A hankali yana sauk’e ajiyar zuciya ya shiga lallashin ta
yana rad’a mata wasu maganganu a kunne.
Cikin d’an murmushi da kuka at the same time ta kai mishi duka a k’irji.
A hankali ya ce “auch!!”
Yana shafa kanta.......
Washe gari da sassafe
Arshaad ya zo. Aslam bai tashi ma akan sallayar da ya gama karatu ba ya ga call d’insa..tunaninsa kuwa yake yi dama
yana rayawa a ranshi dalilin da ya sanya bai ganshi a masallaci ba.
Yana d’auka ya ji ya ce masa
‘yana k’asa gidansa,
ya zo ya bud’e masa.’
“To” kawai ya ce daga nan ya mik’e ya cewa Hudan
“Ina zuwa”
ya fita.
A hankali ta bishi da kallo har ya wuce ya fice tana jin yanayin da takan tsinci kanta a gameda shi yana sake nunkuwa.
Masu aikin su duk ba anan suke kwana ba shiyasa sai da Arshaad ya jira Aslam ya bud’e mishi tukunna ya shigo.
Da murmushi suka yiwa juna sallama kafin Arshaad d’in ya ce “sorry, na tada ku da sassafen nan ko?”
Ajiyar zuciya kawai Aslam ya sauk’e sanann ya ce
“Bismillah”
Yana me bashi hanya.
Suna zama ba tare da b’ata lokaci ba Arshaad ya ce
“Sallama na zo yi muku”
Yana d’an murmushi.
Da mamaki Aslam d’in yake kallonshi kafin ya ce
“Tun yanzu?”
Sai da ya sauk’e ajiyar zuciya tukunna ya ce
“I have to, sanann inaso in fara aiki da wuri..you promised Granpa ba za mu yi letting nashi down ba
so bana son in baku kunya
da kai da shi.
Sannan tun a jiya bayan mun rabu da na kira Daddy
yake cemin akwai aiki gaskiya
a company d’in.”
A hankali Aslam ya ce
“So this is it?”
“It’s just a good bye na d’an wani lokaci, zan dinga zuwa in sha Allah kar ka damu.”
Arshaad d’in ya fad’i hakan cikin tarar numfashin shi.
Ajiyar zuciya Aslam ya sauk’e ya sunkuyar da kanshi yana kallon k’asa sai kuma ya fara wani kalar murmushi tukunna ya fara magana
“This Life is very funny!
Difficult! Harsh! And way too upside down
A ko da yaushe it’s very hard ka ga mutum ya samu all that he ever wished for
ko da ace kuma zai samu d’in to sai kaga ya samu late
ko kuma ya samu opposite
ko dai ma ya rasa gaba d’aya….
Tun tasowarmu
ba ni da burin da ya wuce
Inga mun rayu cikin farin ciki gaba d’ayanmu a inuwa d’aya
Ni Kai Aaima Dad Mommy Mammy
har da su Auwal
this has been my wish since childhood
amma
It turns out
ba wai ga ni kad’ai ba ga yawancin mutane za ka ga dukkannin abunda kake so shi yake zame maka jarrabawa.
Hak’ik’a Ubangiji yana jarabtarmu ne domin ya gwada imaninmu, yana jarabtar mafi soyuwa a cikin bayinsa da abunda ya san sun fi tsananin so da kwad’ayin samu….i have accept my destiny, i have accepted the fact that
rayuwar da na so in yi da ku baki d’aya a inuwa d’aya ba zata tab’a yiwuwa ba.
Although i was and I’m broken amma
I’ll heal and embrace it with time.”
Wata nannauyar ajiyar zuciya ya sauk’e kafin ya d’ago ya kalli Arshaad wanda tunda ya fara magana ya kafeshi da idanuwa, a hankali ya ce
“Ina yi maka fatan alkhairi
Allah ya sanya albarka a cikin dukkannin alamuranka
Allah ya baka sa’a ya kare ka a duk inda kake.
Arshaad inaso ka sani
you will forever be my best friend, bani da da d’an uwa who stood by me through my worst times irinka
shiyasa nake ji a raina inama ace Ina da dama to da ba zamu so mace d’aya ba.”
Murmushi Arshaad ya yi ya had’iye wani yawu mai tauri kafin ya ce
“Na gode Aslam,
Allah ya k’addara saduwarmu.
Kar ka damu ko da ace bama kusa I’ll make sure ban baka chance d’in da za ka yi missing d’ina ba daga kai har su Mommy zamu dinga waya video call sannan zan dinga zuwa time to time
In sha Allah”
Cikin sanyin murya ya ce
“Ubangiji ya azurta ni da family masu matuk’ar sona dole in dinga lek’o su”
A hankali yana murmushi yana kallonsa ya ce
“Especially ma you Aslam..
Ina takaicin yadda na bari soyayya da takaicin ganin an mallaka maka MT suka kaini
na kusa in halaka ka!
A tunani na
ina ganin maybe if I have the company zan iya mallakarta ta hanyar power!
Hak’ik’a
So da Buri ya kusan kaini ga matakin da za a iya saka ni a mazaunin the most ungrateful and selfish being a duniya!”
Numfashi mai matuk’ar zafi ya fesar sannan ya ce
“Babban darasin da na fahimta na d’auka shine
‘Wayo! Dabara da kuma k’arfin iko ba su Isa su baka abunda Allah ya riga ya k’addara ba naka bane ba!
Shi ne kad’ai mai bayarwa kuma mai hanawa a duk lokacin da ya so ya kuma ga dama, bawa bai Isa ya kwatar wa kanshi abu ba Allah kad’ai ne yake wannan, shine kad’ai yake kwata ya bawa wanda ya so ya ga dama a duk lokacin da ya so ya kuma ga dama’.”
Shiruu ya yi kafin ya sauk’e numfashi yana mai kallon k’asa a hankali ya ce
“Na yi wayo, na so kaina, na kawar da duk wani negative Abu da nake gani a kan hanyata da ka iya kawo min tangard’a wajen mallakarta, na take gaskiya, na cutar da Junaidu kaima na so in kawar da kai amma duk da haka….”
Shiruu yayi ya kasa ci gaba da magana sai kuma ya d’ago ya kallesa sosai ya ce “Aslam dan Allah please forgive m…”
Da sauri Aslam ya ce
“Arshaad mun wuce wannan wajen..
Idan akwai abunda zan rok’eka ka yi min a zaman ka na Uk shine
ka goge komai..
Duk abunda ka ga yafaru it was already written tun kafin a haife mu dan haka ya faru ya wuce na manta kaima ka manta kar ka bari ya dameka…
Bana duba abunda ka yi min dan bana ganinshi ma
Iyaka abunda na sani nake gani
shine
‘You are my best Man Arshaad’
Shine kuma abunda zan rik’e har abada.
Ina rok’on Allah ya bar mana zumunci mu.”
A hankali Arshaad ya ce “Ameen”
Sannan ya mik’e ya ce “bisssalam”
“Bara in kirata ku yi sallama”
Aslam ya ce yana k’ok’arin juyawa.
Da sauri Arshaad ya ce
“A’a barta.
Kawai ka ce mata na wuce”
Da “to” Aslam ya bishi,
daga nan ya yi mishi rakiya har bakin mota.
Already sun yi sallama da su Dad da Granpa da kowa
dan haka ya shiga..
Driver na k’ok’arin ja a hankali Arshaad d’in ya kalleshi ya ce masa
“Ka kula mana da Aaima,
tana wajen Mommy.”
A hankali Aslam ya ce
“I’ll.”
Sai kuma kamar wanda baya son yin maganar ya ce
“G’bye Arshaad”.
Yana kallo driver ya yi reverse daga nan ya ja suka fice….
Yafi minti biyar a tsaye ya zubawa inda motar ta bi ta fice ido kafin a hankali ya sauk’e wata nannauyar ajiyar zuciya
ya juya ya shige ciki
idanuwansa jazur!. ..................
….24 HOURS AGO!….
Jirginsu yana Landing
Daddy ya na shirin d’aukar drop ya ji Mom ta dafa shi
ta ce “Daddy”.
A hankali ya juyo suna had’a ido ya d’an b’ata fuska ya ce
“Ke da ba y’ar gari ba Adama Ina ke ina zuwa d’aukar mu??”
Murmushi kawai ta yi ta ce
“Sorry” sannan ta wuce ta isa inda Sakina take tsaye
tanata kame kame dan tun tasowarsu
take fargabar ya zata kasance mata ita da Mom d’in.
Ga mamakin Sakina Mom tana zuwa kawai sai taga ta yi hugging d’inta
a hankali ta ce
“Welcome dota”
Sannan ta ja hannunta da d’an k’aramin trolley d’inta suka yi gaba.
Murmushi Daddy ya yi
dan ba k’aramin dad’i ya ji ba.
Cikin sigar zolaya shima ya nufi motar da suka nufa yana jan nashi trolley d’in yana cewa
“Wato ni ko In taho ko In zauna a nan ba damuwarki bane ba ko?
Tunda kin samu y’arki”.
Murmushi kawai Mom d’in ta yi
a haka suka isa bakin motar.
Suna zuwa drivern ya fito ya karb’i akwatunan ya saka a booth, suka shiga
driver ya jasu suka wuce.
Ga mamakin Sakina sai ta ga an kaisu hotel!
So take tayi tambayar ‘Ina Auwal d’in’ dan in akwai wanda tafi buk’atar gani ta ga lafiyar shi a halin yanzu tou Auwal ne..so take ta yi magana amman kuma kunyar su sai ta hanata dan haka kawai ta bi bayan Mom wadda take ta wani lallab’ata har suka isa k’ofar wani d’aki.
Wanda ya d’aukar mata akwati yana ajjiyewa
Mom ta bud’e d’akin ta ja suka shige bayan ta mik’awa Daddy makulli.
Suna shiga Mom ta rufe k’ofar kafin ta kamo hannun Sakina duk biyun ta rik’e, a hankali ta ce “Dota ki huta ki ci abinci
daga nan sai ki je asibiti wajen Auwal ko?”
Sai kuma ta d’an yi shiru
chan ta ce
“Ki yi hak’uri akan abunda na yi miki ranar birthday d’in su Shuraim, ki yafe min”.
A hankali Sakina ta ce
“Ba komai Mom ya wuce,
ki daina bani hak’uri dan
Allah”
A hankali Mom ta saka hannu ta yi hugging d’inta.
Sun d’an jima a haka kafin ta cikata ta juya ta fita tana cewa
“Yanzu za a kawo miki abinci,
ki ci ki yi wanka
sai mu zo mu wuce gaba d’ayanmu.”
Da “to” kawai ta iya binta dan ita har ga Allah so take kawai ta ji ance ta zo su wuce wajensa.
Ba yadda ta iya haka ta daddannna abincin ta yi wanka duk ranta a jagule.
Allah yaso su Mom basu wani d’auki time ba ta ji ana knocking..
Ta san sune
dan ta gansu ta jikin d’an TVn dake jone da cctv camera d’in gaban k’ofar, dan haka gudun ma kar a sake yin wani jinkirin
ta d’auko har handbag d’inta ta sak’ala akan bak’ar abayar da ta chanja dama ta yi rolling
ta nufi k’ofar ta bud’e ta fita.
Suna ganin ta a shirye chap suka ce “su wuce kawai”
Mom na y’ar dariya k’asa k’asa
tana yaba tsantsar k’aunar da Sakina take yiwa d’anta
tana jin k’aunarta na shiga zuciyarta. Tun d’azu ta lura da yadda Sakinar take ta rawar k’afar son zuwa ta ga Auwal d’in……
Da wannan tunanin
suka k’arasa mota
Drivern jiya shi ya ja su ya kaisu har cikin tafkeken asibitin.
Tunda suka fara takawa cikin asibitin gabanta yake mugun fad’uwa! Had’e da wani sanyin farin ciki da ya lullub’eta.
Suna shiga dakin ta fashe da kuka, duk da kuwa Aaima dama ta gaya mata halin da yake ciki amman bata yi tunannin samun shi da oxygen har yanzu ba.
Ajiyar zuciya Daddy ya sauk’e kafin ya k’arasa wajen ya tsaya a dede kanshi yana kallon shi..
Ya rame ba kad’an ba
ya yi haske sosai.
A hankali ya shafa kanshi ya ce “Son”
Tun lokacin da suka shigo yake d’an jinsu sama sama. So yake ya bud’e idanuwan nashi amman ya kasa
dan haka kurum suna shigowa gabansa ya yanke ya fad’i.
A hankali ya samu ya bud’e idanuwan nashi
da suka k’ank’ance..
Suna had’a idanu da Daddy ya sakar masa d’an murmushi.
Murmushi Daddyn shima ya yi masa kafin ya ce
“I’ve a surprise for you”
Ya yi maganan yana mai juyawa ya yafito Sakina.
A hankali ta k’arasa inda suke.
Tunda ta taho jikinshi ya bashi,
yana cikin tunani
kawai ya ganta a tsaye a kanshi!
Mutumin da ko iya motsin kirki baya yi kawai su Daddy suka ga ya yunk’ura da sauri
zai tashi sai kuma ya ce “auch!!”
Yana dogarar da guiwar hannunsa a kan gadon for sopport
dan da mugun ciwo
k’irjinsa wuyansa kafad’unsa da kansa suka sara!
Sai kuma ya fara juwwa.
Da sauri Daddy ya tareshi yana mai zama a bakin gadon ya maida shi kwance
ya ce
“careful mana”
Sai kuma yasa dariya ya ce
“har ka warke kenan?”
Sai a lokacin kunya ta rufe Auwal….A hankali ya d’auke idanuwansa a kan fuskar Sakina ya mayar ya lumshe…..
Tsananin farin ciki ya ji da ya ganta by surprise
dan ji yayi kamar an tsundumashi a aljannah!
Sai kuma a take batun
Aurenta da Ashraff ya fad’o masa dan haka take lokaci guda ya ji wani tsananin tashin hankali
sanann k’irjinsa ya hau zafi.
Muryar Daddy ce
All Chapters
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 21 Chapter of 26