daita sannan ya fuskanci abokansa "zan dan fita amman bazan dade ba zan dawo ya karasa maganar ya nufi kofar fita .."Tabi bayansa tana adduar Allah yasa gidansu zai kaita ta huta ..
suka bisu da kallo kowannensu na maganar zuci .yana gaba tana biye dashi abaya har suka ƙaraso inda motarsa ke fake eku na ganinsa ya taso da hannu jaguwa ya dakatar dashi ya buɗe murfin motar ya shiga itama ta shiga yayiwa motar key ya tada motar mai gadi na ganinsa yayi hanzarin tashi ya bud'e masa yana daga masa hannu ya fice ya hau kan titi tafiya kad'an yayi ya waigo gefen da take zaune cike da takaici"sai nace kisa seatbelt zaki sa kome ?" ya tambayeta cikin yanayi na ɗan jin haushi. Janyo belt tayi ta saka batare da tace umm ba bare Uhmmm sai qirjinta dake bugawa kamar zai fito waje.Sunyi tafiya me d'an nisa akan titi bata waigo ta kallesa ba, sai faman wasa take da yatsun hanunta tana addua acikin ranta ."
Kai tsaye 1829 plaza ya shiga har ya gama daidaita parking ɗin motar bata d'ago ba ya ciro wayarsa ya lalu'bo number aliyu yayi dealing ya manna a kunnensa maganar minti biyu yayi ya katse ya kira sadiq shima bai dade ba yayi disconnect din Kiran ya fito ya barta ya kulle motar gbdy, taja tsaki aranta ,shiru tayi tana zance zuci da dube dube da idanunta sai lokacin ta fahimci inda ya kawota, kallo d'aya tayiwa gurin ta fahimci gurin sun ta'ba zuwa da ib ta cigaba da zance zuci kmr ance ta Kalli kan kujerar daya tashi idanunta suka sauka akan wayarsa ta d'auka da sauri ta shiga daddana code din data ga ya danna jiya tana addaur Allah yasa haka ne 2020 ta danna sai ga wayar ta bud'e jikinta na rawa tashiga dealing number dad dinta kira biyu ya d'auka bakinta na rawa tace "dad ..."!daga can bangarensa a zaune yake amman sai daya mike tsaye cikin firgice yace"tan !!! where are you ? dad ka zo 1829 plaza ...." ai bata Kai karshen maganrta ba taga yana tahowa da sauri ta sauke wayar a kunnenta tana kokarin goge number ta kashe waya gby da sauri ta ajiye wayar zuciyarta na bugawa da karfin gaske ta sunkuyar da kanta tana danne kukan dake kokarin fito mata ".
ya bude murfin bayan motar ya jefa ledar hannunsa sannan ya bude banagaren mazaunin direba ya shiga yaja Kai tsaye fmc hospital ya nufa a hankali ta d'ago idanunta nan ta fahimci asibiti ya kawota yayi parking Yana kokarin fitowa yace "fito muje" ya faɗa yana ciccin magani .jiki a sanyaye ta fito daga cikin motar ya rike tsintsiyar hannunta gam cikin nashi suka jera koina hasken fitilu ne kowa ya gansu sai ya sake kallonsu dan bakaramin dacewa sukayi da juna ba zaka d'auka su din mata da miji ne ,yayinda gabanta ya dinga faɗuwa aranta tace "Allah Ka bani iKon tserewa yau daga hannunsa ".
Tafiya kad'an sukayi taga sun tsaya a bakin wani ƙofa ya Kai hannu yana knocking din kofar daga ciki aka bashi izinin shigowa." shiga muje "babu yadda ta iya ta shiga kmr zatayi kuka Sadiq na ganinsu ya miƙe yana fad'ad'a fuskarsa da murmushin jin dadi Dan bai taba ganin yayansa da wata mace ba sai yau shiyasa murnarsa a fili take da hannu ya nuna mata gurin zama ita Kuwa kallonsa take saboda tsananin kamaninsu zaka rantse tagwaye ne , babu shakka wannan mutumin dake gabanta dan'uwansa ne km na jini dan kamar ta baci a natse muryarsa ta fito tmkr ta dan'uwansa "father ya sunanta ne ?"ga tan a gabanka ta fad'a maka sunanta tunda shishigi kake son yi ".
sadiq yayi murmushi yana kallon tan wacce ta dago ta kalli jaguwa sannan ta d'auke kanta ita dai addua take har lokacin ,shi kuwa sadiq ya kasa hakuri hakan ya tsinci kanshi da cewa "aunty nah ya jikin naki?" ya sake tambayeta cike da kulawa." da sauƙi!" ta basa amsa murya a sanyaye a natse sadiq ya soma haɗa kayan aikin da zai mata amfani dashi yana gama had'awa yace "miko hnnunki shiru tayi Taki mika masa sadiq ya
kalli yayansa, jaguwa ya wani haɗe fuska yace "kiyi abinda yace mana karki batawa mutane lokaci "
Hawayen dake makale a kwarnin idanunta suka zubo duk da kasancewarta likita amman Allah yayita da tsananin tsoron allura muryarta na rawa tace "ni...ni banason allura a bani magani ".
"dole kiso allura ko mutuwa zakiyi sai an Miki " cikin sanyin jiki sadiq yace ", father ka bita a hankali kasan mata akwai su da mugun tsoron allura "rabu daita munafurcin ne kawai ita kanta likita ce mutane nawa tayiwa allura? murmushi sadiq ya sake yi yana cewa " aha ai likitocin nan sun fi kowa shegen tsoron allura ganin tana ta bata musu lokaci yasa jaguwa kamo hannunta tare da matseta gam ajikinsa "bismillah sadiq kayi mata allura " sadiq ya soma k'okarin tsira mata ta makale ajikin jaguwa sosai tare da sakin K'ara mara sauti ,wani irin harbawa jijiyar jaguwa tayi da karfi take yanayinsa ya sauya bayan hk wani sanyi yaji yana taso masa tarayyarsu ta shekaranjiya ce ta dawo masa a hankali tsigar jikinsa suka dinga mkewa gbdy ya nemi natsuwarsa ya rasa ana gama mata allurar ya saketa dan idan suka cigaba da kasancewa haka komai zai iya faruwa dan zai iya danneta a office din.
sadiq ya had'a mata maganunguna har dana zazzabi ya mika mata yana sake mata Sannu jaguwa yayi masa sallama suka fito kmr farkon da zasu shiga yanzu ma hakan ce ta kasance taji kmr ta fixge daga hannunta ta kwasa da gudu ."
suka karaso Inda sukayi parking suka tsaya abakin mota kamar ya sani ya bude mata sai data shiga ta zauna ya kulle sannan ya zagaya ya shiga bai zauna ba sai daya d'auke wayarsa
ya zauna yana danna gefenta yayi mamakin ganin wayar a kashe ya kunna ya ajiye a ma'ajinta tare da yiwa motar key ko cikakken minti biyar bayi da kunna wayar ba kira shigo da sauri zuciyar tanweer ya shiga bugawa da karfi .
ta kame guri d'aya ya d'auki wayar da hannun d'aya yana dubawa yayinda hannunsa ke kan stearing yana tuki sunan Abubakar Hamid ya gani yana yawo akan screen din wayar da yake yana da truculler a wayarsa ,bai gane ko waye ba ya dai d'auki wayar yana dauka yaji saitin muryar hade da Kiran sunan tanweer ...!wani wawon burki yaja a tsakiyar titi ya waigo yana kallonta "tanweer !!! are you okay ? shiru cikin tsananin tashin hankali minister yace "Talk to dady tan where are you ? "Inna lillahi ta furta a fili tare da juyowa da sauri Jin sautin muryar mahaifinta dake fita cikin tsananin tashin hankali .
Kit jaguwa ya katse Kiran tare da ɗauketa da barin makauniyar take hancinta ya balle da jini ,wani kuka ta saki mai ban tausayi ta bud'e baki zata yi mgn ya sake yarfa mata wani mari wannan karon gilmawar duhu ta gani acikin kwayar idanunta ta sake fashewa da wani sabon kuka tana neman d'auki tana kallonsa ya bud'e bayan wayar ya cire sim din ciki ya karya ya watsa a bakinsa ...."
Mmn sudai
💗💗💗💗💗💗
KUSKUREN BAYA
💖💖💖💖
💗💗💗💗💗💗
PAID BOOK
FREE PAGE
WRITING BY
AYSHA .A BAGUDO
WATTPAD @HAUESH
bismillahirrahmanirrahim
Wannan littafin na kudi ne mai bukata karanta shi ya tura 500 ta wannan account number din 1438775094 Aishat Abdullahi Access bank ,Idan a tura sai a turawa wannan number+234 703 534 8686 alert domin tabbatar da an tura ko wannan number 08059623096 Idan Kuma vtu za'ayi sai a tura ta wannan number 08059623096 kada ayi vtu a number MTN ,domin sauraran littafaina a tuntubi Channel dina ta Hausa bakwai.
🅿️17
A matukar fusace ya bawa motar wuta gabansa banda fad'uwa babu abinda yake , ita Kuwa kuka take sosai kamar ranta zai fita .
zuciyarsa ke wani irin ciwo da zafi dan idan akwai abinda ya tsani gani shine zubar hawayenta sai dai a halin yanzu baya jin zai iya rarrasheta ,zai jure Jin zafin saukar hawayenta .hannunta ta Kai kan hannunsa ta rike gam hawaye shabe shabe kwance a fuskarta ,
da sauri ya waigo fuskarsa ya kalleta yana zabga mata katuwar harara ,gashi fuskarsa gbdy babu annuri , cikin muryar kuka ta kira sunansa "Adnan '!
Yana jin ta yayi mata banza tare da d'auke kanshi ya maida kan tukin da yake yana jan dogon tsaki "me yasa Adnan ? " me yasa bazaka maidani gidanmu ba ?"
Shiru yayi yaki ce mata Komai dan ko yace zai yi magana muryarsa bazata fito ba saboda 'bacin rai dake daskare a zuciyarsa ,zubewa tayi ajikinsa ta saki wani sabon kuka me tsuma zuciya tana cewa "kayiwa Allah da manzonsa ka maidani gidanmu nagaji ! nagaji !! " .
bai ce ta daina kukan ba haka zalika bai ce ta bar jikinsa ba ya barta tayi kukanta , shi Kuma ya cigaba da falfala gudu akan titi ."
Bangaren minister kuwa cikin lokacin da bai wuce minti biyu
da yaji wayar farko da sukayi da tanweer ta mutu ba ya soma neman number din commissioner batare da bata lokaci ba ya d'auka nan minister ya shiga zayyano masa abinda ke faruwa . cikin sauri commissioner ya katse Kiran ya kira dcp dake rike da halakin kula da binciken tanweer kafin kace me jimi'an tsaro sun hallara a gabansa ,cike da natsuwa ya soma magana "please ku maida hankali sosai yanzu nan minster yace sun gama waya da diyarsa tana 1829 amman ga number data kirasa dashi ya turo mana ku tafi kuna tracking din number ku samu location Inda gurin yake .
Nan take dcp ya amshi number suka fito cikin sauri suka shiga motocinsu suna tracking din number sai dai yaki nuna musu location saboda number bata shiga gbdy bare su samu location din da akayi amfani da wayar har suka hau babban titi .
dcp ya kira commissioner yana d'auka yace "sir layin nan bai shiga ba bare mu samu locacin din Inda suke amman zamu k'arasa 1829 plaza dake igando ko zamu dace a nan akayi amfani da layin yanzu dai zamu cigaba da Kiran layin har mu Isa ."Allah yasa ba fahimta yayi ya kashe wayar ba ? "Dan Allah kuyi aiki yadda ya kamata dan yarinyar ta kira cikin mawuyacin hali da alamun tana cikin tsaka me wuya, wannan wata dama ce me kyau da muka samu kada ku bari ta subuce mana "okay sir inshallahu zamuyi iyakacin k'ok'arinmu ".
Commissioner ya katse Kiran yana juyi akan kujera gashi dai shirin tafiya gida yake Kiran minister ya same shi Amman a yanzu ya zama dole ya fasa tafiya gida ya zauna zaman jiransu idan ta kama ya kwana ma a office zai yi ".
gudu motocinsu suke sosai akan titi tare da jiniya ,kowacce mota ta gansu sai ta kauce ta basu hanya ,irin gudun da sukayi yasa cikin kankanin lokaci suka k'araso 1829 suka faka motocinsu suka firfito cikin sauri wasu suka nufi babban get din plaza din , yayinda wasu suka tsaya abakin kofar motocinsu rike da bindugu suna mazurai kamar wasu zakuna ,mutane kuwa tuni suka fara bawa kafarsu iska kar tsautsayi ya rutsa dasu .
a hankali police suka kusa cikin plaza din ,bincike suka fara yi kafin daga baya suka bukaci ganawa da manager gurin , Kai tsaye aka Kai su Inda yake , tun kafin su fito da Id card dinsu ya fahimce su din su waye , nan take ya rikice yana kallonsu .Jimi'an tsaro ne suka nuna masa I'd card "akwai wani mai laifi daya shigo plaza dina a mintunan da suka gabanta ko zamu iya ganin cctv camera dinku ?muryarsa na rawa yace babu matsala yalla'bai ya juya ya soma lalu'bo daukar yau dan Daman a qunne yake , a hankali suke kallo har ya kawo zuwa sanda suka shigo babu wanda ya shigo me irin fuskar da suke nema tare da yarinyar dan haka suka juya cikin sauri suka shishiga motocinsu suka nufi wani branch din dake ikotun ."
Jaguwa na isowa gida yayi parking yana ƙoƙarin bud'e mota domin ya fito da sauri tanweer ta rike shi gam ajikinta "dan Allah kada ka sake shigar dani cikin gidan nan "ya waigo a natse sai dai a fusace yake kallota sai daya d'auki second biyar yana kallon sannan yace "wai meke damun tunaninki ne ?"me ya samu gidan nan da kike son barinsa bayan rayuwarki ake k'okarin karewa ?
Tayi shiru tana kallonsa da nazarin maganarsa kullum maganarsa kenan rayuwarta yake son karewa "ka fad'a min waye wanda yake son d'aukar rayuwata da har kake k'okarin karewa ? tayi masa tambayar jikinta na rawa tare da sheshekan kuka."ganin yadda ta rikice yasa ya kamo hannunta ya rike cikin nashi gam suna jin dumin juna "ki natsu zan fad'a miki amman ba yanzu ba "ni dai ka fad'a min ko waye shine samun kwanciyar hankalina da samun natsuwar zuciyata, Idan ma
ta kama zan hakura da gidanmu na cigaba da zama da Kai ,"ko Kuma ka siyo min sabon layi ka had'a min waya sannan ka fad'a min ko waye sai na fad'awa mahaifina a d'auki mataki akansa , wallahi nayi maka alkwarin bazan fad'awa kowa ba ."
Yayi d'an murmushin gefen baki wanda ya bayyana ainihin sirrin kyawun da Allah yayi masa "Ina ce kince zaki tona min asiri byn kin bar gidan nan ? "tayi saurin girgiza masa Kai alamun a'a "bazan yi ba na maka wannan alkwarin duk runtsi duk wuya bazan aikata hakan gareka ba muddin ka fad'a min ".
"kada ki damu idan kin shirya fad'awa duniya kiyi karki fasa , idan kin koma gida ki tara gbdy 'yan jaridan garin nan ki sheida musu cewar Adnan dan fashi ne abinda nayi Imani dashi Allah bazai basu nasara akaina ba , mahaifiyata tana tsaye a kaina da adduointa haka mutane da dama suna min addua , duk da Ina aikata zunubai Allah zai tsareni daga sharrin duk wani jami'n tsaron albarkancin adduar mahaifiya data mutanen kirki ."
shiru tayi tana kallonsa hawaye na gangaro mata cike da sanyin jiki ta zare hannuwanta dake cikin nasa ta soma k'okarin zare jikinta daga garesa ,yana kallonta tayi baya da kujeran da take zaune ta maida jikinta ta kwanta tana mai runtse idanunta , yatsun hannunta ya kamo bai san yadda akayi ba ya tura cikin bakinsa ya fara tsotsa , wani iri ta dinga ji a sansar jikinta kmr ana zarar ranta , tayi k'okari cirewa ya rike yatsun da karfi yana cigaba da tsotsa kamar ya samu sweet sai daya tsotsa son ranshi sannan ya cire bakinsa ya ciro hanky ya goge mata hancinta dake digar jini yana cewa "ki kwantar da hankalinki zan fad'a miki ko waye amman ba yau ba ". yana gama fad'ar haka ya sakar mata hannu ya bud'e murfin motar ya fito ya zagayo bangarenta da take ya bud'e mata ta fito jiki a sanyaye, ya d'auki ledar maganin da aka basu ta dubeshi fuska da hawaye .
bai tsaya bi ta kanta ba ya riko hannunta ta turje alamun bazata ba ya juyo ya watsa mata idanunshi fuskarsa a d'aure "karki min taurin kai " ya fada tare da sake juyawa suka shiga cikin gidan bakinsa d'auke da addua (bismillahi walajna
wa bismillahi kharajna wa'allahi rabana tawakkalna ) tana jinjinawa girman iliminsa, gashi tantiri gashi malami ta fad'a acikin ranta .
Kai tsaye d'akinta ya shiga daita ya kamota ya zaunar daita abakin gado ya janyo kujerar madubi ya zauna yana bin d'akin da Kallo duk ta hargitsa d'akin ko d'azu daya shigo yaso yayi magana yanayinta yasa ya share ya girgiza Kansa sannan ya fuskanceta ,baya jin dadin yadda take d'aga hankalinta akan gida ,
shi bashi da niyyar cutar daita , ko abinda ya faru daren shekaranjiya ma ba yin Kansa bane itace sila , tillastawarta ce ta janyo hakan ta faru ban cin haka babu abinda zai kai shi aikata zina daita.
"tan ...!
Ya kira sunanta cikin kasalalliyar muryarsa yana sake kamo hannunta tare da kafeta da tsumammun idanunshi masu kashe mata sansar jiki , d'ago idanunta tayi ta zuba masa tana sauraronsa tare da jin wani iri a sansar jikinta duk sanda zata kalleshi sai taji wannan yanayi wanda babu tantama na qunar da take masa ne . "wanda ya tura mu fashi gidanku bashi da hannun cikin zamanki tare damu , rikeki da nayi Kuma nayi amfani da maganar da mukayi dashi a karshen maganarmu cewa "yayi yana da wasu target akanki a dawo dake ya aiwatar da nufinsa wannan shine dalilin da yasa na rikeki ba dan raina na so ba ".
"Dan ranka na so dai ka rikeni idan ba haka ba meye aciki ? tayi maganar a matukar fusace " ka mayar dani Inda ka d'auko ko ka fad'i wanda ya turaku gidanmu kawai a wuce gurin , ya runtse idanunshi yana nazari wasu abubuwa akanta .
ta dubeshi idanunta cike da ruwan hawaye "adnan ka d'auke ni a daren nan ka mayardani gidanmu dukkanin alamun sun nuna min iyayena na cikin tsananin damuwar rashina da.... ...."
"na sani Kuma zan mayar dake amman ba yau ba ki bani lokaci wallahi zan mayar dake akwai binciken da nake da zarar na gama zamammu tare zai zama tarihi ".
ta matso kusa dashi sosai har gwiwowinsu na gogan juna "naji amman dan Allah ka sanar dani Wanda ya tura ku gidanmu fashi ?ya girgiza mata Kai sannan yace "idan ma kika ji ko waye ba lallai ki yarda ba, Killa Kuma ma kiji kin tsanani kanki sannan tabbas wasu rigingimu zasu faru saboda kusancin dake tsakanin mahaifinki da wanda ya bamu aikin ." ta kamo hannunsa ta rike gam cikin wani yanayi "cikin dangin dad dina ne ko na mum dina ke son ganin bayan iyayena da ni kaina ? ya girgiza mata Kai alamun "a'a"to sanar dani dan Allah zan barwa cikina bazan ta'ba fad'awa kowa ba ".
Shiru yayi yana nazari akan lamarin ya fad'a mata ne ko ya shareta "abinda yasani tabbas idan batun
ya fito ya sa'bawa dokarsu domin a aikinsu babu wannan tsarin ,duk runtsi duk wuya ba'a tonawa juna asiri tunda tun farko da wajewa ake tsara komai ba'a juyawa juna baya.
ta katse masa tunani ta hanyar cewa "kana ganin zan iya tona maka asiri ne ?" Allah na dai fad'a ne amman bazan iya aikata hakan ba. "na sani dan fad'awa soyayya ba abu ne me sauki ba da har zaki tona asirin masoyinki I know you can't do that to me tanweer bazaki iya fad'ar komai akaina ba saboda qaunar da kike min."
ta lumshe tsumammun idanunta na second biyu tare da jan tsaki acikin zuciyarta dan muddin tayi a fili balai zai mata a hankali ta bud'e idanunta akan kyakkyawar fuskarsa "ba wannan story din na tambayeka ba ,ka ajiye batun wani soyayya dan a yanzu babu ita acikin raina buqatata ka min bayani wanda yasakaka aikin bana son jan aji da salo tayi mgnr tana murgud'a masa k'aramin bakinta .yayi murmushin gefen baki yace "to da gaske zaki rufa min asiri agurin iyayenki ? da sauri tace "me zai hana in bukatar hakan ya taso ?"
"sannan Ina fatan zaki fahimceni ?" ta gyada masa alamun zata fahimcesa, shiru tayi tana jiran ya faiyace mata Komai kawai taga ya zare hannunsa ya mike tsaye tare da zura hannuwansa duka cikin aljihunsa , a hankali ya juya mata baya yayi taku zuwa daf da kofar bayinta ya tsaya tare da waigowa yace "ni zaki yaudara ko ? ta girgiza masa Kai alamun "a'a "karya kike tanweer yaudarata zakiyi dan zuciyata bata yarda dake ba duk da d'arurar soyayyata dake cikin kwayar idanunki da zuciyarki kina son na fad'a miki wanda ya tura mu fashi gidanku sai ku taru ke da jami'an tsaro ku cutar damu ko ?
yana rufe baki yaji ta rungumesa tsam ta bayansa tana cewa "wallahi kaji na rantse maka bazan sheidawa kowa ba ,bazan zamo me Saka hannu gurin cutar da kai ba ,ya juyo daita gabansa suka fuskanci juna "dame zaki gamsar dani bayan tun farko kice da bakinki kika fad'a min zaki tona min asiri ?" ta tsugunna gwiwowinta biyu a kasa ",ka yarda dani Adnan na rantse maka bazan aikata hakan ba ". ya tako a hankali ya tsugunna a gabanta "na sani bazaki fad'a ba amman ni ba mahaukaci bane da zan fad'a miki wanda ya tura mu a aiki gidanku , babu wannan ajandar acikin aikinmu ko gaban alqali za'a Kai d'aya daga cikinmu da wahala ya fad'a ,kada ki damu ki bar son jin komai gida ne dai zan kaiki a duk sanda wa'adi ya kai ya fad'a yana janyota jikinsa ya makaleta tare da Kai bakinsa daidai kunnenta "ki K'ara natsuwa da jin dumin jikina ."
Tayi shiru zuciyarta na quna da tuttukin bakinciki ,duk abinda take tana yi ne dan ya fad'a mata wanda ya bashi aikin amman shine zai rainawa kansa hankali yace ita ya rainawa ?" cike da matsanacin bakinciki fixge jikinta tace " kar Allah yasa ka fad'a kuma Allah ya Isa da rungumata da kayi ban yafe maka ba mugu kawai me zuciyar dutse duk irin rantsuwar dana yi maka bai sa ka yarda dani ba saboda muguwar zuciya irin taka ." cikin dariya ya sake janyota jikinsa sosai ya rungumeta tsam yana busa mata numfashinsa tare da cewa "kada ki damu da irin zuciyata dan babu abinda zai qareki dashi Allah ya Isa Kuma daman allah isashe ne ko baki ce ba , wayonki yayi matukar burgeni I love it keep it up yayi mata kiss a goshi sannan yace "zaki cigaba da zama da Adnan har zuwa sanda yaga damar maidake gidanku sannan kiyi k'okari ki rage wannan soyayyar da kike masa idan ma da hali ki cireta gbdy ya saketa ya koma jikin window ya tsaya yana kallon farfajiyar gidan kusan minti biyar yana tsaye sannan ya juyo "me zaki ce akawo miki kici ki sha magani ? babu abinda zanci ta fad'a a fusace tana dubansa hawaye na tsiyayowa akan quncinta "daman Kin saba kwana da yunwa idan shi kike ra'ayi fine ,I don't care ya nufi kofar fita daga d'akin ya barta cikin tsananin damuwa da sake shiga tashin hankali ."
Yana fita number minister ya fara nema kira uku yayi kafin a d'auka ,hajiya zainab ce ta dauka cikin sanyayyiyar murya tace" hello yana jin sautin muryar ya fahimci mahaifiyar tanweer ce dan bazai manta da muryar ba da irin kuka da kururuwan da tayi a daren da zai taho da tanweer muryarsa a dikile ya soma magana cikin Isa " Ina minister ?ta waiga a sukune ta Kalli Inda minister yake zaune aqasan tayis yayi tagumi da hannunsa d'aya cikin tsananin tashin hankali "wake magana ?ta tmby cike da faduwar gaba "babu buqatar sanin haka sai dai dalilin Kiran shine ki fad'awa mijinki idan yana kusa " cewar ya dakatar da kawalayen daya tura haushi gari dan nemammamu wato jami'an tsaro idan ba haka ba zai zama sanadin rasa rayuwar diyarsa tanweer ".
nan take jikin hjy zainab ya kama rawa hawayen dake makale a kwarnin idanunta suka sauka akan quncinta , a hankali ta soma karanta hasbinallahu wa ni'imal wakil tana cigaba da sauraransa "ki fad'a masa ya janye if not you'll lose your daughter ko Kuma musa ayi reping dinta mu yada a social media yana gama fad'ar haka yayi disconnecting din kira yana fesar da iska.
wani kuka hjy zainab ta fashe dashi ta zube kasa tana furta kalmar " inna lillahi wa inna ilaihi rajiun da sauri minister ya matso kusa daita dan tunda ta d'auki wayar tana kallonsa shima ya tattara hankalinsa da natsuwarsa gurinta a rud'e yake tambayarta "menene zainab me akace miki a wayar da'aka kira ?" dan girman Allah ka kira office din commissioner yanzu yanzu ka sheida masa a tsaida jami'an tsaron nan bana son na rasa tanweer ,bana son wani mummunar abu ya faru daita iya abinda ta fad'a kenan ta zube jikinsa tana sake fashewa da wani sabon kuka numfashinta na sama
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Chapter 36
Chapter 37
Chapter 38
Chapter 39
Chapter 40
Chapter 41
Chapter 42
Chapter 43
Chapter 44
Chapter 45
Chapter 46
Chapter 47
Chapter 48
Chapter 49
Chapter 50
Chapter 51
Chapter 52
Chapter 53
Chapter 54
Chapter 55
Chapter 56
Chapter 57
Chapter 58
Chapter 59
Chapter 60
Chapter 61
Chapter 62
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 19 Chapter of 62