biyu itace, wannan karon adadin mayakan da muka fito da su rundunar ka data ukashat gaba daya basu fi rabin rundunar da muka saba fitowa da su ba a duk sa'adda zamu yi yaki da birnin shumbul.
Mu hadu a DAKARUN MUSULUNCI NA 1 PART F don Jin CIGABAN WANNAN KASAITACCEN KUMA GAGARUMIN LABARI 🩷🩷🩷**DAKARUN MUSULUNCI**
LITTAFI NA DAYA 1
PART F 💯❤️
NA: ABDUL AZIZ SANI MADAKIN GINI✍️
TYPING:- UMAR FAROUQ ZANGO
POSTING NAJIBULLAH MUHAMMAD 💪 🥷🥷
MARUBUCIN YACI GABA DA CEWA..
Uzaifat ya dubi Abul shaja'a yace, wai shin wace irin sadaukantaka sarki ke da ita ne? Kasan cewa ban taba ganin yakinsa ba.
Abul shaja'a ya jinjina kai yace, ai ni a rayuwata ban taba ganin sadauki mai zafin nama da jarumataka ba kamar Mahaifinku face mai bakaken kaya na birnin shumbul, wanda a ko yaushe suke RAGAS!
Cikin mamaki uzaifat yace, to wai shin shi Wannna mai bakaken kaya wane ne shi, menene matsayinsa a birnin shumbul?
Abul shaja'a yace, yau shekara takwas kenan da fara fitowar mai bakaken kaya filin yaki, babu wanda ya taba ganin fuskar sa kuma baya daya daga cikin manyan mayakan kasar. Ina tabbatar maka da cewa koda kai da ukashat zaku taru akan mai bakaken kaya bazaku iya hallakashiba, saboda yana da mutukar karfin damtse na gaban kwatance.
Uzaifat ya sunkui da kansa kasa yace, ai kuwa ko zan hallaka zai natari wannan mai bakaken kaya koda zan halaka.
Haka dai uzaifat d Abul shaja'a suka ci gaba da hira har lokacin sallar isha yayi, suka fito daga tantin suka iske tuni su ukashat sunyi alwala.
Koda aka zo za a tayar da sallah sai ukashat yayi sauri ya shige gaba da nufin yayi limanci alhalin ko a gida uzaifat ne yaci gaba da limanci a lokacin da sarki ya sami lalurar rashin lafiya.
Koda salahuddeen yaga ukashat ya wuce gaba zai yi limanci sai ya matsa daf dashi yace, ya shugabana sarki fa ya nada uzaifat a matsayin limaminmu na sallah a cikin wannan tafiya.
Koda jin wannan batu sai ukashat ya dakaw salahuddeen harara yace, nan ba gida bane, don haka da ni da uzaifat anan kowa sarki ne.
Koda gama fadin haka sai ukashat ya juyo ya dubi mai tayar da ikama yace da shi Bismillah, nan take kuwa aka tada sallah.
Ko kadan uzaifat bai nuna wata damuwa ba. Bayan an idar da sallar sai uzaifat yaje ga ukashat yace, ya kai dan uwana ka sani cewa yana da kyau mu zauna ni da kai mu tattauna akan yadda zamu bullowa mai bakaken kaya na birnin shumbul, domin na sami labarin cewa ni da kaima bazamu iya da shiba.
Haka kuma yana da kyau mu tattauna akan yadda zamu bullowa tsarin yakin, domin adadin da abokan gaba ya ninka mu sau biyu ko ma fiye da haka.
Yayin da ukashat yaji wannan batu sai ya yi irin murmushin mugunta da ya saba yi, sannan yace.
Ya kai dan uwana shin ka manta ne cewa wannan yaki da muka fito gasane a tsakanina ni da kai? Ya za'ayi mu hada kai wajen neman nasara? Ai sai dai kowa tasa ta fishsheshi!
Ka sank cewa a halin yanzu duk sa'adda na dubi fuskarka sai naga kamar bakin kumurci nake kallo.
Nifa ban daukeka a matsayin dan uwa ba face makiyi wanda ke kokarin dakusar min da burin rayuwa.
Ni yanzu abin da nake so da kai shine, ka manta da cewa akwai wata nasaba ta jini tsakanina da kai, idan ma kana ganin zaka iya Kawar da ni ka jarraba, domin rayuwata hadarice ga taka.
Koda ukashat yazo nan a zancensa sai uzaifat yace, subahanallahi! Yanzu matsayin da ka daukeni kenan?
To in dk saboda ka mallaki karagar mahaifinmu ne ka tsaneni har kake son Kawar da ni daga yau na janye wannan gasa na bar maka.
Na yarda ka zamo sarki Darul Husuf!
Koda jin haka sai ukashat yayi tsaki yace, ai bakin alkalami ya bushe tunda ka Riga ma amsa cewa zaka yi wannan gasa a gaban sarki. Inda bakason muyi gaba da tun sa sannan zaka janye ka bar min.
Daga yau ina mai shawartarka da ka fita daga harkata, idan da hali ma ka daina yi min magana.
Bazai ga Uzaifat yace, wa'iyazubillahi! Ai a matsayina na musulmi haramun ne na daina maka magana. Ya ya kake zance kamar wNj jahili?
Ukashat yace, ai ni akan wannan sarautar na makance, kuma na kurmance. Gaba daya tinanina ya gushe, babu komai a gabana face nasara ta kowanne hali.
Koda jin wannan batu sai uzaifat ya gyada kai yace, ai kuwa sai dai nace Allah ya shirye ka.
Ukashat yayi tsaki a karo na biyu ya tafi ya bar uzaifat a tsaye yana binsa da kallo kawai cikin mamaki, domin bai taba zaton zai ji kalaman da yayi ba daga bakinsa.
Lokacin da uzaifat ya koma cikin tantinsa ya kwanta don yayi bacci sai ya kasa saboda tunani da mamakin kalmonin da dan uwansa ukashat ya gaya masa a yau.
Yana cikin wannan haline Abul shaja'a ya shigo cikin tantin. Koda yaga uzaifat a cikin wannan hali sai ya zauna kusa da shi yayi gyaran murya, hankalin uzaifat ya dawo jikinsa.
Abul shaja'a ya sake dubansa cikin mamaki yace dashi.
Ya shugabana me kuka tattauna ne da dan uwanka ukashat? Ga dukkan alamu abin da ya hanaka bacci kenan.
Koda jin wannan batu sai uzaifat ya kurawa Abul shaja'a idanu na dan wani lokaci, daga bisani ya kau da kai gefe yace.
Tsakanin dan uwa sirrine, bazan iya gayawa kowa ba.
Koda jin haka sai Abul shaja'a yayi shiru bai kara cewa komai ba. Kawai sai ya koma kan shimfidarsa ya kwanta.
Uzaifat ya juyo ya dubeshi yace, yaya ka tsara harkar tsaro anan?
Abul shaja'a yace, rabin dakarunmu ne zasu yi bacci, rabi suyi gadi.
Muzaira Uzaifat yace, da kyau, kayi tsari mai kyau.
Daga nan duk su biyun suka yi shiru basu kara cewa komai ba har bacci ya kwashesu basu sani ba.
Asuba na yi dai dai lokacin sallah sai Abul shaja'a ya farka.
Koda ya bude idanunsa yaga uzaiu bai farka ba sai ya mike da hanzari ya fita wajen tantin.
Koda fitowa sai yaga babu dakarun ukashat ko mutum daya daga cikin masu aikin tsaro.
Nan take hankalin Abul shaja'a ya dugunzuma, yakoma cikin tantin nasu da gudu a dimauce ya taso uzaifat.
Koda suka fito daga cikin tantin sai suka shiga duba cikin tantuna.
Bisa mamaki sai suka ga babu kowa a cikin tantunan. Hatta tantin yarima kuwa.
A dimauce suka duba sawu lo zasu ga sawun 'yan uwansu ko wani wuri suka tafi amma ko alamar sawunsu basu gani ba.
Al'amarin daya jefasu cikin tsananin mamaki kenan, hankalinsu ya kara dugunzuma ainun, suka tsaya suna tunanin mafita.
Daga can sai uzaifat ya dubi Abul shaja'a yace, mu fara gabatar neman 'yan uwanmu.
Ba tare da bata lokaci ba kuwa suka yi alwala sukayi sallah, sannan suka roki Allah akan ya baiyanar musu da 'yan uwasu.
Nan take suka nufi inda aka daure dawakai bisa mamaki kuwa sai suka iske dawakan rututu a daure kamar yadda aka barsu jiya, Ma'ana ko guda daya ba a daukaba.
Cikin hanzari suka kama dawakansu suka zaburesu izuwa cikin dajin suna tafiya a hankali suna waige waige ko zasu ga alamar inda 'yan uwansu suke.
Abu kamar wasa sai da suka shafe sa'a uku suna yawo a cikin dajin basu ga duriyar abokan tafiyar su ba.
Babban abin da yafi tayar musu da hankali shine, yayin sa suka kara nutsawa a cikin dajin suna shiga cikin muguwar sarkakiya don ratsawa, kwatsam! Sai suka ji sun fada cikin wani irin mugun tabo. Kafin suyi wani yunkuri tuni tabon yarike dawakansu suka kasa gaba ko baya, sannan kuma dawakan na nutsawa kasa.
Uzaifat da Abul shaja'a suka daga kai sama suka yi nazarin wajen gaba daya, suka ga ba zasu iya yin tsalle ba daga kan dawakan nasu subar harabar da tabon yake, domin tabon ya mamaye ko ina, gabas da yamma, kudu da arewa.
Koda suka fuskanci hakan sai hankalinsu ya kara dugunzuma ainun, domin sun tabbatar da cewa in ba wani ikon Allah ba babu yadda za suyi su tsira da rayuwarsu.
Babban tashin hankalin shine , tuni tabon ya shanye gangar jikin dawakan nasu, yazo musu iya wuya.
Cikin karayar zuciya Abul shaja'a ya dubi uzaifat yace, ya shugabana bamu da abinyi face mu fara shahada, domin tabbas mutuwa za muyi a cikin wannan tabon, domin ban ga yadda zamu iya kubutar da kanmu ba.
Koda jin wannan batu sai uzaifat ya dakawa Abul shaja'a tsawa yace, akul ka kara irin wannan furuci, domin dukkan mai rai baya cire tsammanin rahamar Allah a irin yanayin da ya tsinci kansa.
Koda gama wannan jawabi sai uzaifat ya fada karanto wata addu'a bisa neman taimakon ubangiji.
Haja dai wannan tabo ya ci gaba da shanye jikin su uzaifat har ya zamana cewa gangar jikinsu ta nutse a ciki, ya kawo musu iya habarsu.
Har a sannan uzaifat bai cire tsammanin samun taimakon Allah ba, kuma bai fasa yin addu'a ba.
Shi kuwa Abul shaja'a ban da Kalmar shahada babu abinda yake yi.
Ba zato ba tsammani sai suka hango wani mutum daga can saman wani tsauni mai tsawon gaske bisa dole ya taho izuwa karshen tsaunin.
Mutumin na sanye da bakaken kaya, fuskar sa ma a rufe take ruf cikin hanzari mutumin ya sauko daga kan dokinsa ya debo wasu dogayen igiyoyi guda biyu yayi musu zarge, sannan ya jeho su kasa daga saman tsaunin.
A lokaci guda igiyoyin suka fada kawunan su uzaifat da Abul shaja'a, sukayi musu kawanya a wuyansu.
Kawai sai mutumin yaja igiyoyin. Sai gashi yana janyosu daga cikin tabon, amma saboda igiyoyin sun shake wuyan su nan da nan suka fita haiyacinsu. Kafin ya gama fito da su daga cikin tabon duk su biyun sun suma.
Koda mutumin yaga ya samu nasarar janyosu izuwa gareshi jikin tsaunin da yake kai saiya dauko battar ruwa ya budeta ya sako ruwan daga sama ya zuba a kansu.
Faruwar Hakan ke da wuya sai uzaifat da Abul shaja'a suka farfado suna taron wahala a matukar galabaice.
****** ****** *******
Najibullah Muhammad 🥷🥷🥷
==================
Koda suka daga kai sukayi arba da Wannan mutum wanda ya ceci rayuwar su sai ya bude baki yace dasu, ku cire igiyoyin daga wuyanku ku rikesu, ni kuma zan taimaka muku na hawo da ku izuwa saman wannan tsauni inda nake.
Yayin da uzaifat da Abul shaja'a suka ji muryar wannan mutumi sai suka cika da tsananin mamaki, suka daga kai suna kallonsa a cikin rashin yarda.
Ba komaine ya janyo hakan ba face sunji muryar tasa ce irin ta mata mai zakk tamkar sarewa.
Uzaifat ya dubi Abul shaja'a yace, anya kuwa wannan mutumin da ya cecemu ba shibane mai bakaken kaya na birnin shumbul wanda aka bamu labari? Wata kila wata muguntar ya ke son ya shirya mana shine ya ke son ya yaudaremu.
Sa'adda Abul shaja'a yaji wannan batu sai yace, anya kuwa hakane? Ai inda shine ba zai cecemu ba. Ai kawai mubi umarnin sa mu ga abinda zai faru tunda dai bamu da wani zabi, babu yadda zamu iya fita daga nan face mun hau kan wannan tsauni.
Cikin gaggawa uzaifat da Abul shaja'a suka cire igiyoyin daga wuyansu sannan suka kama igiyoyin suna hawa izuwa saman tsaunin. Babu abinda ya basu mamaki face ganin irin tsabar karfin wannan mutum mai bakaken kaya, domin shine ya rike igiyoyin da hannayensa har suna lilo a kai ba tare da nauyinsu ya rinjayeshi ba.
Shi dai wannan tsauni ya kai zira'i dari da arba'in.
Amma mutumin nan mai bakaken kaya bai gajiya ba har su uzaifat suka gama hawa saman tsaunin suka riskeshi.
A sannane yayi haki guda daya yayi watsi da igiyoyin kawai sai ya kwaye rawanin da ya rufe fuskar sa.
Take uzaifat da Abul shaja'a suka dimauce, bisa yin arba da fuskar. Ba komai suka gani ba face wata tsaleliyar budurwa mai tsananin kyawun na gaban kwatance.
Gashin kanta ya zubo har kasan kwankwasonta. A bayanta tana goye da wata jibgegiyar takobi.
Budurwar ta dubesu tayi musu murmushi tace, lale marhabun da yarima uzaifat dan sarki uwaisul karni.
Kayi sani cewa akwai labari mai yawa a bakina, domin na san komai akanku. Hatta abokan tafiyar ku da suka bace na san da inda suke.
Koda jin wannan batu sai uzaifat da Abul shaja'a suka sake cika da tsananin mamaki.
Uzaifat ya dubeta cikin mamaki yace, ya akayi duk kika san wannan al'amari? Kuma wacece ke ? Sannan saboda me kika ceci rayuwar mu?
Koda jin wadannan tambayoyi sai budurwar ta sake yin murmushi tace, duk za kuji amsar tambayoyina, amma sai kun nutsu tukunna. Abin da nake so daku shine, ku kwantar da hankalinsu ku bani yarda, na rantse da girman uwata ba zan cutar daku ba, domin kuna da mutukar amfani a gareni.
Ku biyoni izuwa cikin gidana domin mu zauna mu tattauna a cikin nutsuwa.
Koda gama fadin hakan sai budurwar ta kama dokita ta hau tayi gaba tana mai tafiya a hankalin, su kuwa sai suka bita da sauri don kada tayi musu nisa ta bace.
Sannu a hankali suka gangara kasa tsaunin, sannan suka iso bakin wani katon mulmulallen dutse fari fat, irin wanda basu taba gani ba a rayuwarsu.
Koda isowar wannan budurwa gaban farin dutsen sai ta sauka daga kan dokinta ta shafi dutsen da hannunta na hagu, kawai sai suka ga wata kofa ta zinare ta baiyana akan dutsen, ta bude kanta suka hango kayataccen gida a cikin dutsen.
Budurwar ta waiga ta dubi uzaifat da Abul shaja'a cikin murmushi irin wanda ke ruda dukkanin da namiji tace, ku biyoni izuwa ciki.
Nan take ta kunna kai cikin gidan, shi kuwa wannan doki na ta sai ya raba jikinsa da wannan farin dutse, take ya shige cikin dutsen ya bace bat! Tamkar bai taba wanzuwa ba a wajen.
Abul shaja'a da uzaifat suka dubi juna. Abul shaja'a yace, ya shugabana anya kuwa ma shiga cikin gidan nan? Na fuskanci cewa wannan budurwa ma'abociyar tsafi ce, bai kamata muyi Hulda da. ita ba.
Uzaifat yayi ajiyar zuciya yace, ai akwai hulda ta lalura, don haka ba laifi bane. Mu shiga cikin wannan gida, amma dole ne mu kiyaye ga barin duk abinda zayasa mu sabi Allah.
Koda gama fadin haka sai uzaifat ya bi bayan wannan budurwa, shima Abul shaja'a sai ya bi bayan sa yana tafiya a cikien dari dari.
Gaba daya kasan gidan an malaleshi da lu'ulu'u ne, kuma komai na amfanin gidan da zinare aka yi shi. Babu abinda ya baiwa su uzaifat mamaki face yadda gidan ke da girman gaske, sannan an tsarashi wuri wuri, kuna ko ina an zuba kayan alatu na gaban kwatance. A takaice dai wannan gida aljannar duniya ce a cikin sa.
Nan dai suka yi ta wuce barori da kuyangi suna ta hidima, har suka isa wata kasaitacciyar fada mai dauke da shimfidu da kujeru na alfarma iri iri.
Da Isar su wannan fada sai budurwar ta hau kan wata karagar mulki ta zamu, sannan ta yiwa su uzaifat nuni da wasu kujeru tace su zauna. Zamansu ke da wuya sai aka kawo musu abinci iri iri da ababan shaye shaye kala kala da kuma 'ya 'yan itatuwa.
Kyakkyawar budurwar ta dubi uzaifat da Abul shaja'a tayi musu tayi. Kawai sai uzaifat ya dauki tuffa guda daya ya soma ci.
Ganin hakan ne shima Abul shaja'a ya dauki tuffa ne sai uzaifat ya dauki tambulan na kayan shaye shaye yana shinshinasu har sai da yaji wanda ke kanshin ruwan inibi sannan ya dan dana kadan ya tabbatar da cewa babu giya a cikina, ya sha.
Shima Abul shaja'a sai yayi koyi dashi. Sai da suka sha ruwan inibin suka koshi sannan suka yi hamdala suka zubawa Wannna kyakkyawar budurwa idanu.
Budurwar ta bushe da dariya tace, hakika ku dai ma'abota addinin musulunci kuna da tsantseni akan alamuran duniya. To ku sani cewa na san duk irin dokokin cin abinicinku, don haka na zan taba cigar da ku abin da addininku ya haramta ba. Ina mai sanar daku cewa na zauna da ma'abota addinin addininku har tsawon shekaru shida, babu abinda ban iya ba na dangane da yadda ake bautar ubangijin ku.
Nayi ilimi dai dai gwargwado, kuma nayi nazarin addinin naku da kyau, na gano shine addinin gaskiya, amma na ki karbarsa saboda in na karbeshi ba zan taba cika burina ba na duniya. Wannan wank darasine Daban a cikin tarihin rayuwata.
Yanzu dai ina mai sanar daku cewa sunana Lafirat, kuma na kasance 'ya ga sarki sha'aran ibn Nukaib mai mulkin birnin shumbul, wato birnin abokan gabarku.
Ina son ku sani cewa ba nice kadai 'yar sarki shaaran ba, akwai 'yar uwata mai suna sazirat, wacce aka haifemu tare.
Ma'ana Hassana da Hussain's muke, wato uwa daya uba daya. Ni da ita kamarmu daya tamkar an tsaga kara, komai Kular mutum ba zai iya bambancemu ba , to amma akwai bambancin, kuma duk duniya babu mai iya tantancemu face mahaifinmu. Tun da aka haifemu muka taso da tsagwaron sadaukantaka, wato karfin damtse na tsiya tsiya, sannan kuma sai mahaifinmu ya rinka tsumamu da tsumin tsafi har izuwa sa'adda muka zama cikakkun mata.
A sannane na fara samun sabani da 'yar uwata sazirat, bisa burinta na son ta gaji mahaifinmu, watota zamo sarauniyar birnin shumbul kamar yadda a yanzu kaima ka sami sabani da dan uwanka ukashat.
Kafin wannan lokaci daga kuruciyarmu zuwa gairmanmu ni da sazirat bamu taba yin koda sa inda ba, amma sai gashi a ta kaimu ga zagin juna, harma da yin kazamkn fada. Idan muka fara kwamarzuwa sai mu kwana uku muna yaki bamu saurara ba har mu rushe wurare da dama a gidan sarautar mu, mutuwa junanmu mugayen raunika.
Babu wanda ya isa ya rabamu wannan fada face Mahaifinmu, amma kuma sai yaki rabamun sai dai ta kaimu ga sumar da juna.
Bisa wannan halaiya ne watarana sarki shaaran ya taramu a gabansa yace, a cikin ku duk wadda take son ta gajeni dolene tayi abu uku.
Abu na farko dole ne ta bani kanta na kwanta da ita.
Abu na biyu dolene ta yanka jariri a gabana ta shanye jikinsa. Abu na uku kuwa dole ne ta hakura dayin aure har abada.
Koda naji wannan batu sai na kwalla ihu mai firgitarwa na rushe da kuka, sannan na dubi mahaifinmu nace.
Tur da wannan bakar al'ada taka. In dai sai nayi wannan abubuwan uku sannan zan gajeka na hakura da mulkin kasar nan har abada. Ni kan da na aikata wadannan abubuwa uku gwara ma na rasa rayuwata.
Na dubi 'yar uwata sazirat nace, yake 'yar uwata kada kwadayin mulki ya rudeki ki bata rayuwar ki. Lallai kema ki hakura da wannan bukata.
Yayin da sazirat taji wannan shawara tawa, sai ta bushe da dariya, daga can kuma sai ta murtuke fuska tace,
Ni kan na sami hanyar da zan cika burin a cikin ruwan sanyi. Don haka dole na aikata wadannan abubuwa uku.
Koda jin wannan batu sai hankalina ya dugunzuma ainun, na sake fashewa da kuka na shiga rokon sazirat, ina maicewa da ita.
Kada ta yarda ta aikata wadannan mummunan aiki.
Koda na ga ta nufi inda mahaifinmu ke tsaye, sai na duga da gudu da nufin na riketa na hanata zuwa gareshi.
Kawai sai mahaifinmu ya nunani da hannunsa na hagu, taje wata irin murtukekiyar sarkar tsafi ta nannade jikina gaba daya tayi min mugun dauri ya zamana cewa na kasa koda motsa hannayena.
Nan fa ma shiga amfani da karfin sihirna don na kwance kaina, amma sai tsafina yaki yin tasiri.
Mahaifinmu ya sake dubana ya kyalkyale da dariya yace, yake 'yata ki hakura kawai, domin baki isa ki iya hanamu aikata wannan aiki ba. Yin wannan aiki ne kadai zai sa ki samu cikakken tsafin sihirin tsafi dai dai da nawa.
Nan take sarki shaaran ya farwa 'yar uwata sazirat ya santa 'ya mace a gaban idanuna, a lokacin da na ke ta faman rusa ihu da kuka saboda tsananin takaici.
Bayan sun gama aikata lalatarsu sai sarki yasa aka je aka nemo jariri sabon haihuwa aka kawo. Nan take sazirat ta yanka jaririn da wuka akan makogwaronsa, ta kafa bakina ta sha jinin jaririn.
Mu hadu a DAKARUN MUSULUNCI NA 1 PART G don Jin CIGABAN WANNAN KASAITACCEN KUMA GAGARUMIN LABARI 🩷🥰🥰**DAKARUN MUSULUNCI**
LITTAFI NA DAYA 1
PART G
NA- ABDUL AZIZ SANI MADAKIN GINI
TYPING:- UMAR FAROUQ ZANGO
POSTING NAJIBULLAH MUHAMMAD 🥷🥷
LAFIRAT ta ci gaba da cewa.
Koda na gama ganin wannan mugun aiki na rashin imani da batanci, sai nan take naji na tsani mahaifina da 'yar uwata sazirat kamar yadda na tsani mutuwa ta.
A sannane sarki ya sake nuna ni da hannunsa na hagu, wannan sarka data daure ni ta bace bat. Kawai sai na dubi sarki da sazirat a lokacin da hawaye ke zuba a idanuna nace, Hakika daga yau bani baku! Wannan gidan ya haramta a gareni, zamana daku ya kare har abada, tsakanina da ku sai yaki! Kiyayya ta a gareku ba zata gushe ba face na ga na zare muku ruhin numfashi saboda mugun aikin da kuka aikata.
Ya kai Abbana hakika ka cika kazami wanda yayi amai ya lashe abinda. Wannna abu da ka aikata ya shafe matsayinka na uba a gareni. Kuma ka cusa mini bakin ciki wanda har abada ba zai kankaru ba a cikin zuciyata face ajali ya riskeni. Ina nadama da na zamo tsatsonka.... Gwara ace na kasance ba 'yar kowa ba sai 'yar talakan da babu kamarsa a talauci a fadin duniya.
Da wannan furuci nake yi muku bankwana na karshe... Duk ranar da kuka fa na dawo gidan nan, to ku tabbata cewa wannan rana itace ranar mutuwarku.
Koda gama wannan jawabi sai na juya na fice daga cikin fadar.
Sarki sha'arn da 'yar uwata sazirat kuwa, suka yi ta kyalkyala dariya kamar bazasu taba dainawa ba har abada."
Lokacin da Lafirat tazo dai dai nan a labarinta, sai ga hawaye na sartu akan kumatunta. Al'amarin da ya sa uzaifat da Abul shaja'a suka kamu da mutukar tausayinta kenan.
Uzaifat
All Chapters
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 4 Chapter of 21