Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
uku Lokacin da muke tafiya tare? Tambaya ta biyu itace, menene dlilin da yasa naga hawaye na zuba a idanunka bayan munyi sallama ka tafi saadda ka waigo muka hada idanu? Tambaya ta uku wacce itace ta karshe menene dalilin da yasa ka yanke tafiya tare da dani bayan na ceci rayuwarka a cikin kogin kadoji? Lokacin da aljani huraisul marwas yaji wadannan tambayoyi guda uku sai yayi ajiyar zuciya sannan yace, dangane da tambayarka ta farko ba wani abune yasa na kafa maka wannan dokoki ba sai domin na jarraba iyakar bajintar ka na ga abinda zaka iya yi wanda ni bazan iya ba a matsayina na sadaukin jarumin da babu kamarsa a can kasarmu. Ina mai sanar da kai cewa fiye da shekaru arbain baya na sha jarraba zuwa nan birnin domin na yada addinin Allah amman sai na kasa shigowa duk da cewa ina neman taimakon Allah. Al'amarin daya mutukar bani mamaki kenan na tambayi mahaifinmu abinda yasa na kasa shiga birnin shumbul. Amsar da yabani itace, ba zan taba sun damar shiga birnin ba har sai na jira izuwa wani lokaci nan gaba da wani jarumin bil adama dan uwana musulmi da zaije birnin dan ceto rayuwar dakarun kasarsu da kuma wata kyakkyawar budurwa da aka tsareta tun tana yarinya karama a birnin. Mahaifin nawa ya bani labarinka kuma ya tabbatar min da cewa ka fini jarumta juriya da hakuri. Al'amarin da ya matukar bani mamaki kenan na ce ni kuwa duk saadda muka hadu sai na jarraba jarumtarka juriyarka da hakurinka. Dokokin da na kafa maka guda uku su suka bami amsar abinda nake mamaki akansa. Ina mai sanar da kai cewa mahaifinmu shine sarkin musulmi aljanu na birnin hairil salas kuma mu hudune yayansa kuma duk ya rabamu izuwa nahiyoyi hudu na duniya domin mu yada addinin musulunci. Har yanzu babu wanda ya gama samun nasara a cikinmu kuma Mahaifin namu yace damu kada mu kuskura mu koma gida face da biyan bukata koda kuwa rayuwarmu zata salwanta. Yanzu haka na sami nasarar kafa addinin Allah a kasashe dari da arbain dake wanann nahiya taku a cikin kasashen har da birninku na darul Husuf. Ka sani cewa a halin yanzu saura kasashe dari bakwai da sittin a wanann nahiya taku, damuwata shine abune mawuyaci na sami nasarar kafa addinin Allah a sauran wadannan birane kafin zuwan ajalina. Game da tambayarka ta biyu itace, dalilin da ya sa na fuskanci cewa biladama Allah yayi muku baiwa irin wacce mu aljanu bamu da ita kuna har abada bazamu sameta ba. Wannan baiwa ba ta komai bace face ta ikon sarrafa mu kanmu aljanu. Kaifin basira da kuma matsayi a wajen Allah. Sanin cewa har abada bazan zama mutum ba kamarka shi yasa na ji ina shaawar baiwar da kake da ita kuma rashin samunta yasa hawaye ya zubo daga idanuna domin nasan cewa bazan taba taka matsayi da ka taka ba. Dan gane da tambayarka ta uku kuwa, dalilin da yasa na yanke tafiya tare da Kai bayan ka ceci rayuwata shine, inda ban rigaka shiga cikin wannan birnin ba na zo gidan wannan mutum na daureshi ba kuma na juye izuwa kamanninsa da sai asirinka ya tonu a fadar sarki sha'aran kuma karfinka bazai kwaceka ba awajen. Kaga ke nan sai da hikima da basira sannan za ka sami nasarar gabatar sa abinda kazo yi anan birnin. Sai bayan ka sami taka nasarar sannan nima zan sami nasarar yada addini Allah a kasar gaba daya. Wanann yana nufin kenan saimun hada karfi da karfe sannan kowanne zai sami nasarar abinda yasa a gabansa. Lokaci da huraisul marwas yazo nan a zancensa sai kawai suka ji tsoho humzalu ya bushe da dariyar mugunta. Al'amarin d ya matukar basu mamaki kenan duka su biyunsuka zuba masa idanu. Humzalu yace, yanzu ku a tunaninku din kun kamani kun tsare ni anan asirinku zai rufu kuma zaku sami nasarar yin abinda ya kawoku kasarmu? Tabbas kunyi babban kuskure kuma kun yaudari kanku domin bazaku taba samun wannan nasarar ba koda a mafarki kuwa. Ina mai yi muku bushara da cewa irin tsananin tsaron da sarki sha'aran ya shirya a cikin wannan birni namu ya wuce gaban tunanin ku musamman a can krkuku da kuma gidan gonarsa dake can bayan gari inda ya boye sarauniyar kyawawn matan duniya kuma tauraruwar taurari wacce yake shirin aurenta bayan ya gama cin kasaku da yaki, wato Luhaira. Kafin tsohon humzalu ya gama rufe bakinsa tuni huraisul marwas ya shafeshi da gefen fuka fukinsa guda sai ya kife kasa sumamme. Koda ganin haka sai uzaifa ya dakawa huraisul marwas tsawa yace, shin baka yi tunani bane har da zaka yi gaggawar sumar dashi ? Ai inda da tsautsayi da tuni ka mallakashi, idan ya mutu waye zai sanar damu inda kurkukun garin yake da inda gidan gonar yake kuma ta yaya zamu iya zuwa wurare biyu kai tsaye har mu shiga ciki a kwanciyar hankali ba tare da mun fuskanci matsala ba? Koda jin wannan bati sai jikin aljani huraisul marwas yayi sanyi kuna ya sunkui da kansa kas yana tunani da nazari. Daga can sai ya dubi uzaifa yace, kayi min afwa hakuna nayi kuskure amma ka zuba idi ka gani yanzunan zan gyaran kuskurena. Gama fadin hakan ke da wuya sai huraisul marwas yaje ya debo ruwa ya matsawa tsoho humzalu. Nan take humzalu ya farfado a firgice. Dama a cikin wata katuwar kwatanniya huraisul marwas ya debo ruwan. Koda humzalu ya dawo cikin haiyacinsa kuma yayi arba da su uzaifa sai idanunsa suka zazzaro ya dubesu cikin razana yace, me kuke yi mini ne menene ya faru gareni? Huraisul marwas yace babu abinda mukayi maka face mun dandana maka dacin mutuwa. Kafin kuma mu turaka inda ba'a dawowa muna so yanzu ka amsa mana tambayar da zamuyi maka, idan ka yi mana gardama sai na cikin Kabari ya fika kwamciyar hankali. Koda jin wannan batu sai tsoho humzalu ya takarkare ya bushe da dariya a karo na biyu yace ai ni zuciyata a ke kashe take bata jin tsaron abokin gaba... Mu hadu a DAKARUN MUSULUNCI NA 4 Part E don Jin cigaban wannan Kasaitacce Kuma Kayataccen labari Mai dadi ✍️✍️👌👌**DAKARUN MUSULUNCI** LITTAFI NA HUDU 4 PART E ♥️♥️ MARUBUCI: ABDUL AZIZ SANI MADAKIN GINI Typing: UMAR FAROUQ ZANGO Posting: Najibullah Muhammad 🥷🥷🥰 Idan zaku rinka yankar naman jikina da guntu guntu ba zan sanar daku komai ba sai dai ku kasheni. Ina so ku sani cewa na tsani musulunci da musulmi don haka zan iya bayar da raina fansa domin ruga asirin sarkin mu da jama'ar mu. Kafin humzalu ya gama rufe bakinsa tuni aljani huraisul marwas ya shaki wuyansa da yan yatsu biyu ya tsoma kansa a cikin wannan kwatanniya wacce ke cike da ruwa sai gashi humzalu yana ta wutsil wutsil da hannayensa da kafafunsa sakamakon daukewar numfashin sa, har sai da ya kusa suma sannan ya dago da kansa sama, sai gashi idanun humzalu sun kada sunyi jauwr tamkar an gasa dan buda a wuta. Huraisul marwas ya dubeshi yace, muna son kayi mana jagora izuwa inda kurkukun garin nan yake domin ka shigar damu har ciki domin mu ga luhaira. Koda jin haka sai tsoho humzalu ya sake bushewa da dariya a karo na uku sannan ya murtuke fuska yace, ai ko me zaku yi mini bazan bi wannan umarnin naku ba. Abu mafi sauki a gareku shineni ku kama gaban ku tunda ba zaku taba samun hadin kaina ba. Kafin humzalu ya gama rufe bakinsa tuni aljani huraisul marwas ya sake danna kansa cikin wannan kwatanniya ruwa. Sai da ya sumar da shi sai bakwai har ya zamana cewa shi kansa uzaifa yaji tausayin humzalu kamar ya hana huraisul marwas yi masa azabar amma sai ya dake. Bayan humzalu ya suma sau bakwai sai huraisul marwas ya sake maimaita maa wadannan tambayoyi guda uku. Bisa mamaki sai suka ni humzalu ya sake bushewa da dariya sannan yace, ai na gama magana azabarku bazata sa na sanar daku komai ba gwara kawai ku kashe ni ku hutawa da takaicin. Dajin haka sai huraisul marwas yayi masa murmushin mugunta yace, ni da kai yau zan ga wanda yafi wani taurin kai da dakakkiyar zuciya. Ba tare da bata lokaciba huraisul marwas yaci gaba da yiwa tsoho humzalu azaba iri iri har kala dari ba daya, saboda tausayin sa ma sai da uzaifa ya zubar masa da hawaye domin tun humzalu na iya yin ihu da kuka ma har ya zamana cewa ya kasa. Koda uzaifa yaga cewa huraisul marwas bashi da niyar daina yi masa azabar kuna a ki da yaushe azabar zata iya zama sanadin ajalinsa sai ya dakawa huraisul marwas tsawa yace, ya kyaleshi. Huraisul marwas yai jifa da humzalu tamkar ya yar da mushe domin ko motsi baya iya yi face numfashi sama sama da kyar sannan ya dubi uzaifa a fusace yace, to yanzu ka ce a kyaleshi ta yaya kenan bukatar mu zata biya? Uzaifa yaja dogon numfashi yace, ai aikin gaggawa yana daga shaidan. Mu bi a sannu da yardar Allah zamu sami nasara, yanzu dai ka bani lokaci daga nan zuwa ko wayewar gari zamu sami mafita. Koda gama fadin haka sai uzaifa yaje ya sake watsawa tsoho humzalu ruwa ya dawo cikin haiyacinsa kadan sannan ya tasheshi zaune ya bashi ruwan ya dinga kwankwada har sai da ya shanye tulu guda sannan hankalinsa ya dawo jikinsa sosai kawai sai ya kurawa uzaifa idanu yana yi masa wani irin kallo mai dauke da alamar tambaya. Nan take idanunsa suka ciko da kwallah ya kama zubar da hawaye. Al'amarin da ya matukar baiwa uzaifa da huraisul marwas mamaki ke nan domin duk tsananin azabar da ya sha a dazu yayi ta ihu da kuka nasu sashi zubar da hawaye ba sai a yanzu a karon banza. Koda ganin haka sai uzaifa ya gano wank abun amma sai yai shiru baice komai ba, kuma bai iya komai ba. Uzaifa ya mike tsaye ya shiga cikin dakinsa dafa abinci ya shiga dube dube bai ga abinci ba sai yayan itatuwa kala uku, lemon bawo ayaba da baure. Nan take ya debosu a cikin farantai guda biyu ya ajiye faranti guda a gaban tsoho humzalu sannan shima ya zauna daf da humzalu suna fuskantar juna ya fara cin yayan itatuwan shi kuwa aljani huraisul marwas sai ya fice daga cikin dakin gaba daya saboda fushi domin gani yake kawai uzaifa ya bata musu aiki babu yadda za'ayi su san inda kurkukun yake in da aka tsare yan uwansu da kuma gidan gonar sarki inda aka boye luhaira. Uzaifa yaco gaba da cin yayan itatuwan yana satar kallon humzalu sai ya ga har yanzu kansa a sunkuye yake yana ta zubar da hawaye ko kallon faranti dake gabansa baiyi ba. Uzaifa ya gyaran murya yace na sani cewa hawaye da kake zubarwa bana wahala bane hawayene na takaicin abinda ka rasa wanda ko shakka banyi yanzu baka tar da shi. Koda jin wannan batu sai tsoho humzalu ya dago kai da sauri ya dubi uzaifa cikin tsananin mamaki sannan ya budi baki da kyar yace, yaya akayi ka san abinda ke damuna? Uzaifa yai murmushi yace ai sau tari a idi mutum yakan karanta zuciyar bil adama. Irin kallon da ka yi mini dazu da kuma hawayen da na ga ya zubo maka shine ya tabbatar mini da cewa ka rasa masoyi walau mata ko da ko mahaifi. Gaya mini gaskiya wa ka rasa, shin yana nan a raye ko kuwa ya bar duniya? Humzalu yai ajiyar zuciya kuma yayi shiru kamar bazai ce komai ba, sannan yace, ya kai wannan jarumi kuma dan sarki nasani cewa kaine uzaifa dan uwan uzaifa kuna a yau na yi mamakin wani al'amari dangane da halayyarka a matsayinka na maabocin addinin musulunci wanda muje kallonku da marasa tausayi da adalci amma sai gashi na ga ka zubar da hawaye a dalilin jin tausayina da zaka ji zan gaya maka komai. Yau shekarata goma sha daya ke nan dana guda daya tilo a duniya yayiwa sarki shaaran laifin kuna ba wani babban laifin yayi ba amma sai aka zo aka tafi dashi a wata safiya. Har abada bazan manta da wannan rana ba domin muna tare da shine muna buda baki kawai sai naga dakarun sarki sun banko mana sun Ka mashi suka rufeshi da duka na mike da sauri na rukunkumeshi ina tambayar su ko lafiya. Ko saurarena basuyi ba suka banbareshi ta karfin siya daga cikin jikina suka tafi dashi yana ihu yana cewa na ceceshi ni kuma ina kuka ina rokonsu su kyaleshi. A haka suka rabamu suka tafi da shi suka barni a tsaye cikin tsananin bakin ciki da kuka da takaici. Bayan tafiyar dakaru da dana khushairu sai na shirya cikin hanzari na tafi izuwa fadarsarki a gigice. Da isata cikin fadana fadi gaban sarki shaaran ina kuka gani da nemawa dana afuwa bisa laifin da ya aikata duk da bansan irin laifin da ya aikata ba. Nan take sarki sha'aran ya daka min tsawa sannan yace yakai humzalu babban hadimin mu kayi sani cewa Sanna khushairu yayi mana laifi wanda bazamu iya yafe masa ba doke ne mu yi masa hukuncin horo mai tsanani. Laifin da yayi mana shine ajiya da yammaci yaga fuska matata ta ghobe wato luhaira sarauniyar mata ta wannan zamana. Ka sani cewa tun da na kawo luhaira saadda take yarinya karama na boye ta a cikin gidan gonata ya zamana cewa babu wanda ya sake ganin fuskarta har ta girma ta zama budurwa. Danka khushairu shi ne kadai mutumin da yasami damar ganawa da ita a kullum da yamma sau daya. A kullum din kuwa idanunta kadai yake gani kuma basu taba yiwa juna magana ba domin na kafa doka mai tsanani akan hakan. Tsawon shekara goma sha hudu suna tare khushairu bai karya wannan doka ba amma sai gashi ajiya luhaira tayi tuntube a gabansa ta fadi kawai sai ya manta da dokar sa muka sanya a tsakanin su ya ruga da gudu ya kama kafadunta da nufin ya tasheta tsaye, a dalilin haka ne mayafin da ta rufe fuskarta ya cire suka yi arba da fuskokin juna. A dai dai wannan lokacine dakarun da ke tsaron gidan gonar suka rugo izuwa cikin lambun suka ga abinda ke faruwa a tsakanin su. Ka ga ke nan danka khushairu ya rigani taba jikin amaryata da zan aura sannan ya rigani ganin kyakkyawan fuska fuskarta a Lokacin da ta cika mace domin nima tabon da na ga fuskarta ta tun tana da shekarun bakwai a duniya. Yanzu haka tuni na sa a yanke hannun khushairu kuma an tsiyayar da ruwan idanunsa biyu yadda har abada bazai iya taba komai ba kuna ba zai sake ganin komai ba. Wannan shine hukuncin da yayi dai dai da laifin da ya aikata. Koda sarki shaafa yazo nan a zancensa sai na kwarara uban ihu kuma na fashe da matsanaicin kuka na bakin ciki na dinga rokon sarki ina mai cewa nima ya sa akasheni kawai na huta da takaicin abinda ya sami dana. Koda jin haka sai sarki sha'aran ya bushe da dariyar mugunta yace, bazan sa akasheka ba kuma ba zaka sake ganin danka ba sai ranar da na auri luhaira. Dole ne ka ci gaba sa yi mana hidima Kamar yadda ka saba idan kuma ba haka ba to lallai ni da kaina zan kawo maka kan danka a cikin buhu. Daga wannan rana kawo I yanzu sa nake baka wannan Kabari ban sake ganin dana khushairu ba kuma ban san inda aka tsareshi ba, abinda na sani kawai shine an daukeshi daga gidan gonar sarki inda yake kula da lambun shakatawar luhaira. Duk saadda na ga saurayi kyakkyawa sai na tuno da da shi har hawaye ya zubomin. Yanzu tayaya kake tsammani zan baku hadin kaibisa abinda kika zo yi alhalin na san cewa idan sarki yasan cewa nine na taimake ku sai ya sare kan dana? Saadda tsoho humzalu yazo nan a zancensa sai uzaifa ya kamu da tsananin tausayinsa har hawaye ya sake subuto masa ya dubi humzalu a cikin nutsuwa yace, hakika wanna sarki naku ya cika azzalumi mara tausayi. Yanzu ina son ka tsaya kayi tunani ka fahimci halin da kuke ciki kai da danka. Da farko dai kaga kai ka tsufa domin shekarun ka a kalla sun haura tamanin ba lallai bane duniya. Gashi baka da kowa a dangi da ya rage maka face danka khushairu. Yanzu khushairu bashi da idanu kuma bashi da bannaye wanne sauran jin dadi duniya ne a gareshi? Hakika sarki sha'aran ya gama tauye rayuwar danka data taka kuma a cikin bautarsa zaku mutu tare da bakin cikin abinda ya muku. Shin sarki masoyi ne gareka ko kuwa makiyine? Koda jin wadannan tambayoyi sai tsoho humzalu ya fashe da kuka yana cewa hakika bani da wani maiyi a duniya wanda yafi sarki shaaran. uzaifa yace Yauwa madallah da ka fahimci haka. Yanzu tunda kai da kanka ka san cewa sarki sha'aran makiyinka ne to me yasa bazan taimakawa makiyansa basu sami nasarar kawar da shi ba? Me yasa baka tunanin samun tsira daga mulkinsa na zalunci? Me yasa baka Aina addinin mu da naku ka fahimci cewa addinin mu shine na gaskiya tunda bai yarda da zalunci ba kuma komai matsayin mutum idan ya aikata barna ko rashin gaskiya sai an hukuntashi? Ina mai baka misali cewar a dokar addini mu koda sarki sha'aran ne aka Ka mashi sa laifin yin sara Tofa sai anyanke masa hannu kuma a gaban talakawansa. Koda jin haka sai tsoho humzalu ya cika da tsananin mamaki yace, yanzu dama haka wannan addini naku yake? Uzaifa ya gyada kai cikin murmushi yace ai mu addini mu addinine na salama wanda baya bambanta mai mulki da talaka attajiri sa fakiri malami sa almajiri bawa da maigidansa dukkanin su dayane babu wanda yafi wani sai wanda yafi tsoron Allah. Ya kai humzalu ka bami hadin kai mu kawar da wannan bakin mulki na zalunci da kafirci wanda aka dade ana shukawa a wannan babban birnin naku mu kawo muku sauti na amini da adalci domin rayuwarku bayani ta inganta. Lokacin da uzaifa yazo nan a zancensa sai jikin tsoho humzalu yayi sanyi ya sunkui da kansa kas ya fada kogin tunani. Jim kadan sai yaga hawaye na ta kwarara bisa kan kumatunsa. Cikin tsananin nadamar ya dubi uzaifa yace hakika ban taba jin kaunar wannan addini naku ba arayuwata sai yanzu. Tabbas na gamsu cewa addinin musulunci shine addini gaskiya kuna ko yanzu taje a shirye nake na karbeshi. Dajin wannan batu sai uzaifa ya kamu da tsananin farin ciki. Ba tare da bata lokaci ba uzaifa ya biyawa humzalu Kalmar shahada ya maimaita, kawai sai suka rungumi juna cikin tsananin farin ciki. Humzalu ya janye jikinsa daga cikin na uzaifat ya fuskanceshi a Lokacin da idanunsa suka ciki da kwalla yace, ya kai uzaifa kayi sani cewa yanzu da na karbi wannan addini mai daraja sai naji tamkar an janye mini dukkan bakin cikin rayuwata, haka nan naji an yaye mini kadaicin na rashin ganin dana khushairu, tabbas na ji a jikin cewa ina da sauran yan uwa a duniya ban kasance maraya ba wanda bashi da kowa. Koda jin wannan batu sai uzaifa ya sake rungumeshi cikin murna yace, tabbas zancenka dutse ne domin kowanne musulmi dan uwan musulmi ne, babu bambancin yare ko kalar fata a ko ina cikin duniya. Dole ne musulmi ya kaunaci dan uwansa musulmi kuma dole ne ya taimakeshi a duk irin halin daya ganshi na wuya ko kakani kayi. Da sannu zan kofar da kai yadda ake bautar ubangijn musulunci tun daga yau din nan. Yanzu yaya kake ganin zamu tunkari kurkukun garinnan don ceto rayuwar yan uwan mu da aka tsare da kuma yadda zamu je gidan gonar sarki sha'aran mu dauko luhaira? Saadda tsoho humzalu yaji wadannan tambayoyi guda biyu sai yayi ajiyar zuciya, ya kawo gwauron numfashi ya ajiye sannan yace, ya kai wannan dan sarki kayi sani cewa shiga cikin kurkukun kasar nan dai dai yake da mutum Ya sayi ajalinsa da kudinsa domin matakan tsaron dake cikinsa sun wuce dukkan t tunanin ka da hangenka. Ina mai sanar da kai cewa musamman sarki sha'aran yaje ya gaiyato dakarun haya daga manyan kasashe dake wanann nahiya gamu kimanin su dunu dari uku ya zuba su a cikin kurkukun ko ina da ina suna gadi. Su dai wadannan dakaru an basu horon yaki na musamman irin wanda sauran mayakan duniya basu da shi domin suna iya shafe sa'a ashirin da hudu suna yaki ba tare da sun gaji ba kuma suna da tsananin zafin nama, juriya da jarumtaka a ban alajabi. Baya ga wadannan mazajen dakaru, akwai wadansu masifaffun karnuka guda dari uku wadanda girmansu ya kai ja bijimin sa. Suna da azababben gudu kuma kuna suna da karfin tsiya ko da kirji suka bangaji mutum sai dai kaga ya baje a kasa ya kasa tashi. Idan kuwa suka sa fikar bakinsu suka gatsa jikin mutum barta kashinsa sai ya ragargaje. Banda wadannan karnuka kuma akwai wadansu zakwakuran mayakan aljanu suma su dari uku ne. Su dai wadannan aljanu basa jin sara ko suka, kuma idan zasu shekara suna yaki bazasu gaji ba, kuma ba zasu bukaci abinci ko ruwa ba. Dole sai mutum ya ratsa ta cikin wadannan halittu rukuni uku sannan zai isa inda aka ajiye yan wanku. A can bangaren gidan gonar sarki kuwa, a iya rayuwata ban taba wuce farfajiyar farko ba inda lambun shakatawar luhaira yake wato inda dana khushairu yake aiki. Ni dai a sanina akwai katon gida a cikin gidan gonar wanda girmansa ya kai na gidan sarautar sarki sha'aran kuna yana da waje waje dakuma barkatai ban san adadi ba, kuma kowacce kusurwa dake cikin gidan akwai dakarun tsaro a tsaitsaye. Ita kanta luhaira duk saadda zata fito daga cikin gindata sai kuyangi arbain sun take mata baya gami da dakaru dari don tabbatar da tsaron lafiyarta. Saadda humzalu yazo nan a zancensa sai uzaifa yayi ajiyar zuciya sannan yace, yakai dan uwana kayi sani cewa mu bamu dogara da karfinmu ko iyawar mu ba da Allah muka dogara domin mun san cewa shi kadai ne zai iya bamu saa da nasara bisa wanann gagarumin aiki da muka zo aiwatarwa. Lallai ai gobe da safe nake son kayi mana rakiya izuwa can kurkukun, idan har muka sami nasarar ceto rayuwar yan uwanmu kashe gari kuma sai ka rakamu izuwa can gidan gonar sarki. Yanzu zan koya maka yadda ake yin tsarki, alwala da sallah don haka sai ka nutsu da kyau ka saurareni, bayan kayi wadannan domin na GHA lokacinta ya gabato. Nan take kuwa uzaifa ya koyawa tsoho humzalu abubuwan da ya lissafa sannan suka yi alwala suka tayar da sallah. A dai

Chapter 19 of 21