babbar rabo.
Yanzu dai sai muyi shawara bisa abinda ke gabanmu, wato dangane da yakin da za'ayi gobe na mutum dari biyar.
Koda jin haka sai uzaifat yayi murmushi yace, to yanzu sai ku fadi taku shawarar naji domin nima ina da tawa shawarar a zuciyata.
Uwar mayu tayi gyaran murya tace, ni dai a ganina babu abin da ya kamata muyi face muje mu sami mahaiimu sanar da shi cewa ya dakatar da wannan salon yakin da ake yi yanzu.
Gwara kawai ayi fito na fito gaba daya a karar da yakin kowa yasan makomarsa a huta da fargaba.
Koda jin haka sai uzaifat yayi murmushi yace, ai wannan shawarar taki ba abar karba bace, ina tabbatar miki da cewa shi kansa sarki bazai aminta da hakan ba, domin akwai dabarun da muka shirya a sirrance don ganin mun sami nasarar da muke nema.
Idan kuwa muka katse yakin da wuri bukatarmu bazata biya ba.
Ke kuma fa Hirama fadi taki hikimar muji, domin na gamsu da cewa ke mai hikima ce tunda har kika iya kubutar damu a lokacin da mahaifinki ya jefamu a cikin kejinsa da nufin ya cinyemu.
Saadda Hirama taji haka sai tayi murmushi tace, ai ba hikimata bace ta kubutar daku ba, kawai dai saace da kuma taimakon ubangijin musulunci.
Ni a ganina yakin da za'ayi gobe mai hadarin gaske ne, saboda kun ga yakin da akayi yau mune da nasara kuma abokan gaba sunyi matukar bakin ciki dole ne suyi babban tanadi na ramuwa.
Abinda za'ayi shine, ya kamata kai ko Lafirat daya daga cikinku yayi bad da kama gobe ya shiga cikin dakaru dari biyar din da za'a fafata dasu domin ya ragargaji kafirai saboda babu mamaki suma sunyi irin wannan tunani.
Kodajin wannan batu sai uzaifat da lafirat suka jinjina kai da suka gamsu da wannan shawara uzaifat yayi ajiyar zuciya yace, wallahi nima nayi irin wannan tunanin naki don haka tabbas nine zan bad da kamannina na shiga cikin dakarun dari biyar din amma abinda nake so da ku shine kuyi shiru da bakinku kada ku fadawa kowa wannan shawara da muka yanke domin idan sarki yaji ba Zak yarda na shiga ba saboda bai yarda da hainci ba koda a cikin yaki. Shi mutum ne laifi daya mai magana daya.
Cikin hadin baki Hirama, Lafirat da uwar mayu su kace tabbas ba zamu bari kowa yaji wannan zancen ba.
Lafirat ta dubi uzaifat tace, abu na karshe da nake so da kai shine, ka zuba ido da kyau kuma ka lura da dukkan abubuwan da kowanne abokin gaba keyi a lokacin da kuke yakin a gobe saboda a cikin wannan yamutsin na mutum dubu za'a iya shirya makirci wanda ba lallai bane wani ya gani ba.
Uzaifat yayi ajiyar numfashi yace, tabbas wannan batu naki gaskiya ne don haka da izinin Allah zan kuma sosai.
Mu hadu a DAKARUN MUSULUNCI na Uku part G don Jin cigaban wannan Kasaitacce Kuma kayatacciyar Hikayar ✍️✍️✍️✍️🤝**DAKARUN MUSULUNCI**
Littafi Na Uku 3
Part G
Marubuci :- Abdul Aziz Sani Madakin Gini
Typing:- Umar Farouq Zango
Posting:- Najibullahi Muhammad 🥷🥷🥷
Marubucin Ya ci gaba da cewa
Kashe gari, wato rana ra uku dakurn musulunci da dakarun kafirci suka sake fitowa filin daga kamar yadda aka saba.
Nan take dakarun kafirai suka fito su dari biyar sanye da bakaken kaya kuma dukkanin su sun rufe fuskokin su da bakaken rawani idanunsu kadai ake gani.
Wani abin mamakin kuma kowannensu ya sanya katuwar bakar alkyabba a jikinsa sannan suna haye akan bakaken dawakai. Al'amarin da ya bawa dakarun musulunci mamakin kenan domin basu taba ganin an fita yaku da irin wannan shiga ba.
Lokacin da sarki uwaisul karni yaga dakarun kafirai su dari biyar sun fito filin daga, amma dakarun musulunci sun yi jinkiri basu fito ba sai ya fusata ya dakawa sarkin yakinsa na wannan runduna tsawa yace, ya Kai habinullahi ina dakarun da nace ka waresu ne tun jiya, me suka tsaya yi haryanzu basu fito ba.
Cikin rawar baki habinullahi ya budi baki da nufin ya ba da amsa kawai sai ya ga dakarun musulunci su dari biyar dukkanin su sanye da fararen tufafi da kjam fararen alkyabbu, kuma bisa fararen dawakai.
Dukkanin su sun rufe fuskokinsu da fararen rawuna.
Al'amarin da ya mutukar bawa habinullahi mamaki kenan domin shi akansa bai san da wannan tufafi ba da fararen dawakai.
Abinda yazamo kamar hadin baki, sai dai shigar da dakarun musulunci sukayi tafi ta dakarun kafirci ban shaawa da birgewa.
Koda sarki uwaisul karni ya ga dakarunsa a cikin wannan shiga sai ya cika da tsananin farin ciki ya rinka yiwa habinullahi kirari harma ya yi masa alkawarin bashi kyauta ta musamman saboda wannan hikima da basira da ya baje a filin yakin a wannan rana.
Nan dai dakarun musulunci suka iso tsakiyar filin daga suka ja linzamin dawakan su suka yi turjiya suna fusknatar abokan gaba.
Yarima ukasha ne akan gaba a cikin dakarun kafirci.
Haka ma yarima uzaifat ne akan gaba a cikin dakarun musulunci.
Duk da cewa kowannensu ya rufe fuskarsa da rawani suna yin arba da idanunsu suka shaida juna.
Nan take ukashat yaji zuciyar sa ta buga da karfi domin ya san cewa uzaifa zai iya hanashi aiwatar da babban shirin da yazo aiwatarwa yanzu.
Amma da ya tuna cewa ai cikin gwamutsi suke na mutum dubu, kuma da zarar an fara yakin kowa zai rasa nutsuwa. Sai hankalinsa ya kwanta ya gamsu cewa lallai sai ya sami nasarar abinda yazo aiwatarwa.
Bayan an yi kallon kallo tsakanin bangaren biyu sai aka busa kahon fara yaki. Nan take aka ruguntsume da masifaffen yaki, kura ta turnuke sararin samaniya.
Ihun mazaje da haniniyar dawakai da Karar karafa ta cika dodon kunne.
Nan fa aka fara turmutsi da yamutsi. Jim kadan kuma aka fara sarki ya hana dawa tsaiwa.
Wani lakacin sai dai kaga an safe kan mutum ya yi sama jini ya yi tsartuwa da feshi gangar jikin ta rikito kasa ana tattakata.
Abin da Ya firgita kowa shine, an kasa gano bangaren da ke samun nasara domin musulmai na zubewa suna shahada, kafirai na zubewa suna mutuwar banza.
Ana cikin wannan gumurzu ne uzaifa ya fara kokarin zuwa ya hadu da ukasha, amma da zarar ukasha ya ga uzaifa Ya tunkaroshi sai ya sulale ya bar wajen.
Haka ya yi masa zulliya ya ki yarda su yi gaba da gaba.
Kuma a hakan ci gaba suke da yaki kowannensu yana mummunar barna.
Yayin da aka sami kudan rabin Saa ana wannan bakin gumurzu sai rabin dakarun dake filin suka zamo gawa.
Koda ukasha ya fahimci hakan sai hankalinsa ya dugunzuma domin ya san cewa idan baiyi da gaske ba abin da yake son yi ba zai sami damar yi ba.
Kawai yana cikin yin yakin sai yayi wuf! Ya duro kasa akan wata gawa ta musulmi, ya lullube gawar da bakar alkyabbarsa.
Cikin tsananin zafin nama ya cure gawar tamkar an dunkule kayan wanki ya cafota da hannu daya ya dafa kasa da daya hannun nasa ya yi tsalle sama ya dira akan dokinsa ya na lullube da gawar Ya ci gaba da yakin a haka har ya tarwatsa dakarun musulunci dake gabansa da karfin tsiya, ya ratsa ta tsakiyar su ya sukwani dokinsa izuwa inda sansaninsu ya ke.
Ashe uzaifa ya ga saadda ukasha ya duro daga kan dokinsa amma bai ga abinda ya dauka ba a kasan amma tabbas zuciyar sa ta raya masa cewa lallai wani abu ya dauka. Cikin hanzari uzaifa ya tambayi kansa menene a filin yaki wanda ukasha zai dauka ?
Ai babu komai face gawa ko makamai.
Ya bawa kansa amsa.
Nan take ya aiyana a aransa kawai nima na sci gawar daya daga cikin gawarsu na tafi da ita tunda dai ban ga amfanin da makamin wani zaiyi ba.
Daga baya idan nayi nazarin gawar wakin da suka rage a filin yakin da dakarun da suka tsira da rayuwarsu zan iya ganowa idan ma gawar dayanmu ya sace.
Gama aiyana hakan ke da wuya sai shima uzaifa ya duro kasa daga kan dokinsa ya lullube gawar kafiri guda daya ya cureta kamar yadda ukasha yayi, ya daka tsalle sama ya dira akan dokinsa ya tarwatsa abokan gaba shima ya durfafi inda nasu sansanin yake.
Koda ganin haja sai sauran mayakan da ke faman yakin suka daina yakin kowa ya ruga da baya izuwa sansanin su. Al'amarin da ya mutukar baiwa sarki uwaisul karni mamakin kenan kuma ya fusatshi ya dubi habinullahi a fusakce yace, wannan wane irin shirine na banza da wofi?
Cikin biyayya habinullahi ya dukar da kansa kasa yace, ka gafarceni ya shugabana, hakika nayi kuskure.
Gama fadin hakan ke da wuya suka ji an busa kahon tsaida yaki.
Cikin fushi sarki uwaisul karni ya kada dokinsa ya nufi can sansanin su inda tantinsa yake.
A sannane kowanne bangare ya ruga ya debo gawarwakin jamaarasa.
Kafin a binne gawarwakin musulman da aka kashe sai da uzaifat yazo ya kirgasu sannan yaje ya kirga wadanda basu mutu ba, take ya gane cewa ba aga gawa daya ba.
Kawai sai yayi murmushi domin ya tabbatar da abinda yake zargi.
Bayan magriba tayi anci abinci. A can bangaren dakarun kafirci sai sarki shaaran ya rungume ukashat cikin tsananin Farin ciki sannan ya janye jikinsa daga cikin nasa yace, da kyau sadaukin sadaukai, aikinka yayi kyau, ka samo nasarar matakin farko.
Yanzu idan dare ya raba sai ka cire tufafin dake jikin wannan gawa da ka sato kasa a jikina ka sadada kaje har can sansanin mayakan su ba tare da an ganka ba ka binciko tantin da lafirat ke ciki ka satita ta kowanne hali ka kawota nan.
Koda jin wannan batu sai ukashat yayi murmushi yace, ya shugabana ai shan ruwa yafi wannan aiki sauki a wajena. Lallai zaka sameni nai cika umarninka.
Wannan shine abinda ya faru tsakanin yarima ukashat da sarki shaaran bayan an gama yaki.
* * * * * *
Alamarin yarima uzaifat kuwa, bayan ya Kai wannan gawar ta abokin gaba cikin tantinsa ya lullubeta da alkyabbarsa sai ya zauna ya kurawa gawar idanu ya shiga tunanin mai zurfi bisa abinda ya kamata yayi da gawar, amma babu wata dabara data fado masa.
Yana cikim wannan hali ne Lafirat ta shigo cikin tantin ta sareshi.
Koda taga yayi tagumi kuna ya kurawa kunshin kaya idanu yana tunani sai ta cika da mamaki.
Kawai sai ta wuce kai tsaye izuwa inda kunshin kayan suke ta yaye alkyabbar, nan take tayi arba da gawar badakaren mahaifita
Cikin kasuwa da mamaki ta dubi uzaifat tace, me zakayi da gawar abokan gaba?
Uzaifat yayi ajiyar zuciya yace, abinda dan uwana ukashat zaiyi da gawar bamu badakaren shi nake son yi da gawar tasu badakaren.
Lafirat ta sake dukansa cikin mamaki a karo na biyu tace, ni fa ban gane abinda kake nufi ba.
Uzaifat ya dubeta a nutse itace, lokacin da muke wannan yakin na fahimci cewa ukashat ya saci daya daga cikin gawarwakin mutanen mu ya tafi da ita izuwa sansanin su.
Saboda haka nima sai na sati gawar nasu badakaren na taho da ita.
Wannan tunanin da kika ga na shiga ba ta komai bace face ta kasa gano abinda ukashat zaiyi da gawar da ya sata, wanda shine nima abinda ya kamata nayi.
Saadda uzaifat yazo nan a zancensa sai lafirat ta bushe da dariya, sannan tace hakika kai bakon fita yaki ne.
Inda ace ka saba fita yaki da dole ne ka gano abinda zaiyi da gawar.
Abinda zai yi da ita shine, tufafin gawar zai cire yasa a nasa jikin domin ya sami damar shigowa nan sansanin a cikin dare, ko domin leken asiri ko kuma domin ya saci wani abin.
Don haka sai mu san matakin da zamu dauka akansa.
Koda jin wannan batu sai uzaifat yayi murmushi wannna ya dubi Lafirat yace, kada kk damu yake Lafirat, ki tafi izuwa tantinki ki kwanta kiyi bacci har da munshari babu abinda zai faru.
Na san dan uwana ukashat kuma na san duk irin motsinsa zan kuka da shi.
Dajin haka sai Lafirat tayi murmushi tace, na yarda da kai gwarzona dari bisa dari.
Na san zaka iya yin abinda yafi haka. Sai da safe, Allah ya tashemu lafiya.
Koda gama fadin haka sai Lafirat ta juya tafi ce daga cikin tantin ta tafi nata tantin ta kwanta.
Fitarta ke da wuya sai uzaifat ya mike tsaye ya cire tufafin dake jikin wannan gawa ya adanansu a cikin akwatinsa na karfe. Wanda ya zubo wasu makamansa na yaki, sannan ya kwalawa wasu dakaru biyu kira dake tsaye a kofar tantinsa suka shigo da sauri.
Uzaifat ya dubi dakarun yace, maza ku dauki wannan gawar ku fita da ita waje ku binneta.
Cikin biyayya dakarun suka dauki gawar suka fice da ita, a zuciyar su suna mamakin yadda akayi gawar ta shigo cikin tantin yarima uzaifat.
Uzaifat bai kwanta bacci ba sai da dare ya fara rabawa bayan ya gabatar da nafilfilinsa da adduoi sannan ya kashe fitilar tantin nasa ya kwanta yayi lamo kamar yana bacci.
* * * * * *
A can sansanin su ukashat kuwa lokacin da dare ya raba sai ukashat ya mike tsaye ya dauki tufafin gawar da yasato ya sanya a jikinsa sannan ya daukko wata sharbebiyar wuka ya baiyeta a cikin rigarsa ya fita daga cikin tantinsa.
Da fitarsa ya banga can inda sansanin muslmai yake yaga gaba daya nahiyar wajen a haskake yake sakamakon fitilun itatuwa da aka kukkuna masu yawa.
Sai ya tabbatar da cewa babu yadda za'ayi yaje wannan wuri batare da an ganshi ba.
Haka kuma ya tuna cewa sarki shaaran ya gaya masa cewa sihirin tsafi ba zai yi tasiri ba ballatana ya bace bat ya baiyana a can kawai.
Nan fa hankalinsa ya dugunzuma yayi shiru yana tunani.
Alhamdulillahi nan zan dakata sai kuma Allah ya kuma hada mu
Ni Umar Farouq Zango nake cewa sai mun sake saduwa.**DAKARUN MUSULUNCI**
Littafi na Uku 3
Part H ( Last )
Marubuci :- Abdul Aziz Sani Madakin Gini
Typing- Umar Farouq Zango
Posting Najibullah Muhammad legends 🥷🥷
Marubucin ya ci gaba da cewa...
Daga can sai ya dubi kasa ya ga ai kariyar ciyawace a wajen tun daga bakin sansanin su hat izuwa can sansanin musulmi.
Kuma ciyawar tana da dan tsawo har ta haifar da yar karamar duhuwa.
Nan take dabara ta fado masa yaje ya tsinko koriyar ciyawar da yawa ya manne ta a jikinsa gaba daya da ita sannan ya kwanta a kas yai ruf da jiki ya dinga tafiya da ina ciki a kas a hankali har ya durfafi sansanin musulmi.
Haka yaci gaba da jan ciki, da zarar ya ga wani motsi a gabansa ko giftawar wani sai yayi luf a cikin ciyawa, sai kaga ya saje da ciyawar ko alamarsa ba a gani.
Sannu a hankali har ya isa har cikin sansanin musulmi ba tare da wani ya ganshiba. Babu abinda zai baiwa mutum mamaki face yadda ukashat ke ratsawa ta tsakiyar kafafun dakarun musulunci yana wucesu amma basu ganshi ba kuma basu ki motsinsa ba.
Akwai lokacin da ma wani badakare ya taka masa yatsun hannunsa na hagu yaji mugun zafi da zogi saboda takalimin karfe ne mai nauyi a kafar badakaren.
Har ukashat yaji kamar ya tsandara ihu amma sai yayi ta maza ya daure ya dauke numfashinsa har sai da badakaren ya dauke kafarsa daga kan hannun nasa ya kara gaba, sannan shima yaci GBA da jan ciki ya durfafi tantin farko dake gabansa.
Da zuwansa bayan tantin yana daga kwancen a cikin ciyawar sai ya zaro wannan sharbebiyar wuka tasa ya tsaga tantin ya leka ciki.
Ai kuwa sai yaga ashe sarki uwaisul karni ne.
A lokacin sarki uwaisul karni na zaune bisa buzu ya idar da nafila yana lazimi.
Kawai sai ukashat ya bar wajen ya matsa gaba izuwa tanti na biyu, shima yasa wukarsa ya tsagashi ya leka.
Duk da cewar fitilar cikin tantin a kashe take ukashat ya gane cewa uzaifat ne a ciki a kwance domin ya karewa siffar jikinsa kallo ya shaidashi.
Ukashat ya kara wucewa gaba izuwa tanti na uku wanda Lafirat ke ciki.
Ukashat na barin wannan tantin na biyu sai uzaifat ya mike zumbur ashe yana ganin saadda ukashat ya tsaga tantin nasa da wuka ya leko ya kare masa kallo.
Shi ukashat bai san cewa kallon kallo akayi ba.
Cikin sanda uzait ya dauki wannan tufafi na gawar daya dauko yasa a jikinsa sannan shima ya cisgi ciyayi ya lullube jikinsa gaba daya da su kamar yadda ukashat yayi ya kwanta a kas yai ruf da ciki ya bi ukashat a baya ba tare da ya sani ba.
Lokacin da ukashat ya isa tanti na uku yasa wukarsa ya tsaya tantin sai yai arba da Lafirat kwance tana ta sharar barci abinta har da munshari.
Cikin sanda ukashat ya mike tsaye ya shiga cikin tantin ta cikin wannan kafar tsaga da yayi yaje kan Lafirat ya tsaya. Kawai sai yasa hannunsa a cikin aljihu ya dauko banji ya shaka mata a hanci.
Nan take barcinta ya kara nauyi. Duk da wannan abu dake faruwa uzaifat na labe a kasa bayan tantin yana lekensa.
Ukashat ya juyo da baya ya nufi inda ya shigo cikin tantin. Sai uzaifat yai sauri ya matsa gaba ya kwanta a cikin ciyawa yai lamfo.
Kawai sai ya ga ukashat ya fito ya cisgi ciyayi da yawa sannan ya koma cikin tantin ya lullube Lafirat da ciyawar sannan ya janyo ta a kas shima ya kwanta a kas ya ci gaba sa jan ciki kuma yana jan hannun Lafirat da hannu daya.
Koda ganin haka sai uzaifat ya bishi a baya a hankali ba tare da ukashat ya ankara ba.
Sannu a hankali suka isa har can sansanin.
Da zuwa sai ukashat ya mike tsaye ya saba Lafirat a kafadarsa ya shiga da ita cikin tantinsa ya kwantar da ita bisa shimfida.
Nan take ya cika da tsananin Farin ciki bisa wannan gagarumar nasara da ya yi ta sato gimbiya Lafirat.
Kawai sai ya juya da sauri da nufin ya tafi izuwa tantin sarki shaaran domin ya sanar dashi cewa ya cika umarninsa cikin nasara.
Juyowar da zaiyi haka sai yaji biri ya debeshi ya kama tangadi, bai Sam saadda ya sulale kasa ba ya kama barcin dole.
Ba komai ne ya haddasa hakanba face banji da uzaifat ya watsa masa a fuska ya shaka.
Koda uzaifat ya ga ukashat ya baje a kasa yana barci sai yai sauri ya janyeshi izuwa wajen tantin yayi ruf da ciki ya ci gaba da jansa a kas har ya isa can tantin musulmai janye da shi.
Ita kuwa Lafirat sai ya barta a can tantin ukashat dake sansanin kafirai.
Lokacin da gari ya waye sai mayaka suka fito sansanin yaki na kowanne bangare suka yi sahu sahu ana kallon juna. Wannan karon dai mutum dubu ne zasu kara da mutum dubu.
* * * * * *
A can bangaren sarki uwaisul karni babu uzaifat kuma babu Lafisai Habibullah, Hirama da uwar mayu da sauran dakaru, kuma ko kadan sarki uwaisul karni bai damu ba domin tun a daren jiya uzaifat ya dankara masa ukashat a hannunsa.
Nan take sarki uwaisul karni yasa aka daure ukashat da murtukekiyar ankwa kafa da hannu a jikin katon turke na karfe.
A daren uzaifat ya yai bankwana da sarki uwaisul karni ya sanar da shi cewa shi kam Yanzu zai durfafi can birnin shumbul domin yaje ya kubutarda rayuwar lahira da sauran mutanen su da aka tsare a kurkuku.
Nan take sarki uwaisul karni yacika da tsananin Farin ciki yayi ta sawa uzaifat albarka. Kuma ya bukaci sa ya bashi dakaru wadanda zasi masa rakiya.
Amma sai uzaifat yace dashi baya bukatar rakiyar kowa face ta Lafirat, don haka shi da ita zasu tafi.
Nan dai suka yi sallama uzaifat ya tafi ba tare da ya sanar da sarki uwaisul karni gaskiya lamarin ba cewar yabaro Lafirat a can sansanin kafirai.
Abinda yasa yaki gaya masa gaskiyar kuwa shine baya son hankalinsa ya tashi kuma akwai hikimar sa tasa ya barta a can din.
* * * * * *
A can sansanin kafirai kuwa,lokacin da dare ya tsala da yawa sarki shaaran yaji shiru wato har a sannan baiji dawowar yarima ukashat ba sai hankalinsa ya dugunzuma ya muje zumbur daga zaune ya ruga izuwa tantin ukashat.
Da zuwa sai ya iske Lafirat a kwance akan shimfidar sa ta na shara barci, amma babu ukashat a wajen.
Nan take sarki shaaran ya cika da mutukar Farin ciki bisa ganin ya sami nasarar sato Lafirat.
Amma kuma sai yayi mamakin rashin ganin ukashat a lokaci.
Kawai sai ya ga wata yar karamar takarda akan akwatin ukashat. Cikin sauri ya dauki takarda ya warwareta ya ga ashe sako ne aka rubuta waiska.
Nan take ya fara karanta bayanin dake cikin takarda kamar haka :- Takarda daga hannun ukashat zuwa ga shugabana kuma sarki na sarki shaaran na birnin shumbul.
Dalilin rubuta naka wannan wasika shine, domin na sanar da kai cewa na samu nasarar sato Lafirat wacce ita kadai ce zata iya yiwa makiyanmu jagora izuwa cikin birninka.
Ni yanzu tini na tafi izuwa birnin Darul Husuf domin naje na tono wadannan layu guda hudu don haka zan jiraku a can sai ku taho da sauri domin mu aiwatar da abinda ke gaban mu.
Koda sarki shaaran ya gana karanta wannan wasila sai ya takarkare ya bushe da mahaukaciyar dariya.
Karfin dariyar ne yasa Lafirat ta farka da ga barcin da take mai nauyi sakamakon banjun da ta shaka.
Koda tayi arba da sarki shaaran a gabanta kyalkyala dariya sai ta firgita ainun ta bude baki da nufin ta kira sunan Allah, amma sai sarki shaaran ya gabza mata naushi a wuya ta sulale kasa sumammiya.
Nan take yayi nuni da hannunsa izuwa kanta ta sake cigaba da
All Chapters
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 16 Chapter of 21