Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
iyaye da abokansa Na gida tabbas sai ya yi farin ckin ganinki. Abu guda daya zan rokeki Anisa shi ne kitsare mutuncinki, kada kiyarda soyayyarsa tasa kibiye mishi ya lalata miki rayuwa. Ta gyara zama tace "mom ban taba kallon khalifa da wata manufa ba mara kyau burina shi ne muzama miji da mata, ba zan iya bata rawana da tsalle ba akan khalifa. Mom tayi murmushi tace "anisa duniya fadi gareta abinda kika sani shi kika sani wanda baki sani ba baki sani ba, na san mutumcin soyayya kuma ina darajata, ni ce mace ta uku da mahaifin ki ya aura kinsan da wannan ko? To ina mai tabbatar miki da cewa ni ce mace tafarko daya fara so a rayuwarsa". ries : A DAREN FARKO 11 anisa tafiddo ido tace "to momi me ya hana yafara auranki har sai da ya auri su hajiya da mama? Momi tayi murmushi tare da girgiza kai tace "Anisa tun ina 'yar shekara goma sha daya mahaifinki yake so na, so ba na wasa ba tun muna ganin d wasa yake har kowa ya amince so yake min na gas*iya,yadinga hidima dani, duk abinda yasami niyake ba mawa, hr na kammala secondary dina lokacin aurena ya zo knan ba na kula kowa. Lokacin daya tuntubi babana da mganar aurenmu lokacin na yi candy sai yace ydaka ta masa sai ya yi shawara da 'yan uwansa, hnklin abbanku yatshi yanuna min damuwarsa akan haka nace yayi hakuri na san babana bazai ba mu matsala ba. Ahe kuwa matsala na tare damu domin babana biris yayi har takai ga ya kira abbanki yace yadaina zuwa guna dan kuwa ya yi min miji,munga tashin hankali abban ki Ibrahim a wannan rana domin kuka da hawaye yadi? ga yi yana rokin abbana yayi hakuri yarufa mai asiri kada yacuce shi da chan ba a hana shi ba sai yanzun, ba afi sati ba babana yadaura min aure dawani d'an d'an uwansa wanda yace shi yzaba min a matsayin miji. Wannan abu yajefa abban*u cikin matsanancin tashin hnkli domin kuwa ba karamin so yake min ba kowa ya san da wannan. Hakan yasa yan unguwa akayi ta zagin babana ana cewa bai kyauta ba anci amanar ibrahim, wannan ne dalilin dayasa mahaifiyar ibrahim tayi fushi tazo har gida tana gayawa babana bakaken maganganu yace da ita ai ba maryam ce kadai diya mace a duniya ba, bai ba wa ibrahim diyarsa ba ai ba wani yahaifa masa ita ba, idan anyi hushi ta aurawa ibrahim mata biyu koma hudu a rana daya shi ne zai tabbatar ita mai zuciya ce. Ai kuwa abinda yafaru knan, hajiyar ibrahim ta nemo mai 'ya'yan aminanta biyu itace hajiya hauwa uwar gidan abbanku ta yanzu da hajiya hafsa dakike ce ma mama. Ibrahim yayi namijin kokarin ba wa mahaifiyarsa hadin kai dan kada yakunya ta ta a idon duniya ganin walakancin da akayi mai a kaina,ya amince da auran hauwa da hafsa wadanda aka daura auransu rana daya aka fara kai hauwagdan da hajiyar ta sa tagina mai daga bisani bayan sati daya aka kai hafsa ,yayin da ni kuma bayan wata daya da daurin aurena da Aminu aka kaini gdan iyaynsa dake bayan layinmu. Na yi kuka na yi bakin ciki mara misaltuwa sbda ko ido ba na sn in buda in ga Aminu. Sai daga baya zance yabayyana cewa mahaifin Aminu ne yake bin babana wasu kudade masu yawan gaske yabukaci yabashi abinsa ba shi dashi, mahaifin aminu yace "tunda lokacin damuka yi za kabiya ya yi kuma babu to sai dai kabaiwa Aliyu auran maryam in ba haka ba kuwa zaiyi kararshi ne kuma nan take dole yabiya sa kudinsa, yace wadannan kudi in dai yabada maryama to sune a matsayin kudin aure da kayan lefe, sadaki kawai zai biya a daura aure, hnklin babana yatashi sosai sbda ya san dai da kunya yahana ibrahim auran maryam lokaci daya yabawa Aminu bayan lokaci mai tsawo ibrahim yadeba yana hidima da maryam tabbas ya san sai duniya ta zageshi, yayi duk tunanin dazaiyi dan yasamu mafita bai samu ba, kudi kuma bai da hanyarsu, hakan yasa yarufe idonsa yana takaici yaba Aminu aurena, lokacin daya ga damuwar goggona ya yawaita ne yasa yagaya mata yadda akayi shi ne nikuma tagaya min. Hakan danaji yasa zuciyata tadan sosu tadamu na tausayawa babana domin ko yaushe tunanina shi ne yadda babana ke son ibrahim meyasa yahana shi aurena rana tsaka ,bayan babana mutumun kirki ne ba mutum ne mai kwadayin abun duniya ba. : Shekarata biyu a gdan Aminu kowatan bata ban taba yi ba, shi da mahaifiyarsa suka shiga min walakanci suna cewa ba na son Aminu shiyasa naki yarda in haihu, ni kam ina iya kokari na duk da ba son Aminu nake ba ina mai biyayyaya shikuma yana wahalar dani kasancewar ba wani mutumin kirki ne sosai ba halayyarsa ba masu kyau bane. Watarana ina kwance a dakina yace dani "in fita inje gdanmu ya sakeni ba zai iya cigaba da zama dani ba, ba ni da wani amfani sai inci inyi kashi, natafi gda na fadawa babana daya tuntubi mahaifin Aminu kan maganar sai yakama fada yana cewa kar a gaya mai zancen banza mana maryama ce tahura wa Aminu wuta sai ya saketa gar da yi masa gori cewa ita ba shi takeso ba kuma tunda an yi masa haka kudinsa dinnan dai sai an biyashi tunda baiga amfanin auran maryama ga aminu ba, babana yace bai isa ba tunda dai yakafa sharadi kuma anyi auran a bisa sharadin daya kafa zancen kudi kuwa babu shi sai dai in kara zaiyi. Momi tadan yi shiru tana kallon fuskar anisa wadda tazuba mata ido tana mamakin labarin da take ba ta tace,"to momi yaya akayi har kika auri babana? Momi tace "Anisa hakika abbanku ya san darajar soyayya kuma ya mutunta kaunar dake tsakanina dashi; ahaifin Aminu yayi karar babana yace sai ya biyashi kudinsa tunda dai diyarsa maryam ta ki zama da Aminu, kiri kiri alkalin nan yagoyi bayan mahaifin Aminu bayan ni da baba na mun bayyana a kotu yadda abubuwa suka kasance wai sai alkalin nan yace sai na kawo shaidar mutum daya kwakkwara wanda zai min shaidar cewa Aminu ne yasake ni da kansa ba ni nace yasakeni ba, nace banda shaida sai Allah dan shi ne masanin dukkan abubuwan dasuka faru,, alkali yace dole sai babana ya nemo kudin Aminu ya biyashi lamarin daya tayar da hnklin kowa a gdanmu har kuka sai da babana yayi, kwasam Allah mai iko bayan kwana biyu dayin hakan sai ga abbanku ibrahim ya zo gun babana yakawo mai kudin da sukafi wanda baban Aminu yake binsa, mamaki yakamashi da kunya yarasa abinda zai ce, Ibrahim yace karka damu baba ni fa kaunar dana kewa maryam Allah kadai yasan iyakarta, duk abinda yashafe ni ya shafeku, Allah ne bai kaddara itace matata tafarko ba shiyasa abubuwan dasuka faru suka faru. Babana yabiya baban Aminu kudinsa kuma yace bai yafe masa ba, ina kammala idda aka daura aurena da Ibrahim, ban cika shekara daya ba na haifeki a cikin shekarata ta uku a gidan nan na haifi kaninki mahmud, kuma a wannan shekarar ne Allah yadaukaka arzikin mahaifinku wanda izuwa yanzu shi da kansa bai san abinda ya mallaka ba. Har yanzu iyayena ba su da abin Kauna kamar ibrahim kamar yadda nima ban iya hada shi da kowa, abinda nakeso inkaiki gareshi guda daya ne Anisa mahaifinki dani kaina mun san martabar soyayya muna mutunta ta. Mahaifinki ya nuna min kaunar da ban taba jin wani da namiji dayai wa mace halacci irin wadda ya min ba ko da kuwa a labari, shi yasa ban wasa da duk abinda yasha fe shi. Duk da kasancewarsa adali a tsakanin matansa amma kowa ya san soyayyar dayake nunamin ba karama bace shiyasa hajiya da mama suka tsaneni to amma ba su da ikon komi akaina sbda sanin halayyarsa. Wlh Anisa ni kadai ce matar da zan tunkareshi da kowace irin bukata yayi min ko baida ra'ayi don hka zan umarce shi da ya shirya miki tfya xuwa kasar germany don ki karasa karatun ki a chan. Anisa ina rokon ki kiji tsoron Allah a wannan tafiya da zakiyi kada kija min bacin rai,duk rintsi duk wuya kada ki lalata rayuwarki idan ban gani ba Allah ya gani ki min alkawarin tsare mutuncin kanki. Anisa tace "mom na maki wannan alkawari insha Allahu. Kowa yayi mamakin batun tafiyar anisa har kasar germany da sunan karatu tun da babanta dai ba shi da wannan ra'ayin ko babban dansa da hajiya hauwa tafara haifa anan kasar yake karatunsa na jami'a hakan yasa aka dauki hassada aka daura akan anisa amma dan ita abin bai dameta ba cikar burinta ne kawai damuwarta har a ranar da za tabar gida nigeria zuwa jamus batun mominta guda daya ne. "Anisa kiji tsoron Allah kada ki zubar da mutuncin ki baki da takamar data wuce budurcinki a gun mijin da za ki aura duk abinda zai rudeki kiji tsoron Allah kada ki biye masa bbu inda zai kaiki face ga nadama wadda zai sa kiyi ta kunkan da ba ki da ranar dazaki daina, duk abinda d'a namiji zai aikata a rayuwarsa ado ne mace ce a cikin hadari da bakin ciki idan batayi taka tsan tsan da rayuwarta ba. A cikin jirgin anisa ta hada kanta da guiwa ne tana tunanin wadannan maganganun na mahaifiyarta wadanda suka tsaya mata a rai, hawaye suka dinga zuba a idonta wani na bin wani, taji tausayin kanta da iyayan ta jikinta yayi sanyi sosai batasan yadda rayuwarta za takasance a wannan kasa ba. *********** Jiddah zaria Babban magana wai namiji dasuna Hajara, anya kuwa Anisa za ta iya cika wannan alkawari na mahaifiyarta???? ni ma dai jiki na ya yi sanyi amma dai ga mai fili ga mai doki........ karku gaji dai kukasance kuna biye dani a baya ganin yadda za takaya.... Ni ce dai 'yar mutan zazzau. Hawwa umar. a.k.a jiddah zaria. A DAREN FARKO 12 Kamshin da khalifa yaji ya halarci hancinsa yasa yamike xaune yana kallon Anisa, tace "ga abincin nan tashi kaci kayi wanka kayi sallah. Ya fubi abincin cike da gamsuwa yace "amma fa nagode Anisa kin fara ragemin damuwata zauna kigaya min dalilin zuwanki garin nan. Tayi murmushi tace "karatu nazo yi nima, rakiya nayo wa wata kawata za tayi tafiya kamar daga sama na ganka. Yajinjina kai yace "na godewa Allah daya kawoki daidai lokacin da zama ya kamani a nan. Farin ciki ya mamaye zuciyarta ta fara jiyo kamshin nasara a cikin muradinta duk da cewa ta san akwai aiki ja a gabanta. ******** Ruwan sama akayi kamar da bakin kwarya tun safe har gab da za ayi sallar azahar sannan yadauke, garin kano yadauki sanyi mai dadi kasancewarba sanyin takurawa jikin bil'adama ba. fatima tagama shiryawa cikin atamfarta maroon mai adon ja da fari, ta yi mata kyau sosai tadauki littafanta za tafara karantawa inna tadubeta ta ce "Ajiye littafin nan za ki yi ki kaiwa hajiya maijidda wamcan man shanun na soyashi tun daren jiya naso akai mata. Ta dan bata rai tace "nikam inna ba na son shiga wannan godan. Inna tarike baki tace "me mutanan gdan suka yi miki mutane masu kirki da mutunci wai ke meyasa ba kya son mutane ne fatima? Tace "ba haka bane inna kin sani duk abinda mutum yakeyi ana kallonsa idan ina yawan zuwa gdan karshe ace kwadayi ne yake kaini. To a fada din mana "inna tafada a fusace sannan tadora da fadin "idan har za kibiyewa surutun mutane ba abinda za ki aikata a rayuwarki dan duk abinda ka aikata din mutane ba fasa magana za suyi ba. Fatima ta dakko hijjabinta tasa ta dauki bokitin man shanun tanufo gdan abba. Hannu bibbiyu mama ta amshe ta suna zaune ita da ummi a falo suna hira, ta tsuguna ta gayar dasu tamika mata bokiti tace "Gashi inji inna. Tace "Oh Allah sarki inna da hidima take na gode Allah saka da alheri zauna sai anjima kya tafi ke in kin shigo gidan nan sai kace ana korarki na rasa sanda za kisaba da mutane fatima. A haka ta dan zauna a darare sai kace akan kaya tazauna, ummi tadubi ta da fara'a tace "fatima kin iya kitso ko rannan naga na kan kanwarki Aysha tace ke kikayi mata yaushe zanzo ki min irinsa? Tace 'idan kin shirya yanzu ma sai in miki. Tace "yawwa kamar kin san kan yadameni da yawa ina kuiyar saloon, tadkko kibiya da mai da komi tace "xo mu shiga daki kimin ma yi hira ma. Mama tayi murmushi tace "Ayi hira ko gulma idan ba gulma ba me zai hana a yi kitson a nan falon sai an shiga daki. Ummi tace "mama wannan hiran ai ta sirri ce. Tace 'gulma dai knan. Fatima na mamakin jin dadin da ake a wannan gida ita kanta ummi ace an shirya mata kasaitaccen daki irin wannan, tfara mata kitso suna hira tana ba ta labarin makarantar ta wadda saura shekara daya ta kammala, ummi tace "fatima amma idan kin gama za kici gaba da karatunki ko? Tace "a'a aure za ayi min in barda ma inna ta so inyi candy ai da yanzu anyi bikina da malam musbahu. Ummi tace "ba dai malamin ajinmu na islammiyr yamma ba. Tace "shifa ai dan gidan mu ne. Ummi tasake kallon fatima tana rayawa a zuciyarta yaya za ayi yarinya tanada kyau na garari irin wannan takare gun wani malamin islamiyya.,kwata kwata fati ba ajin malam musbahu bace, domin kyaunta yasa wasu har ce mata suke beauty, dukda cewa ba ta da sakin jiki da mutane ba ta ayyanar da tsabar kyaunta ta fi zama da nikab a fuskarta amma dukda haka kallonta ake ana zuzuta kyaunta, sbda zahiri Allah yayi mata kyakyawar sura tadaukar hankali da ace fati irin wayayyun 'yan matan nan ne masu budaddan ido ba karamin kudin maza zataci ba sbda in dai batun kyau ake fati ta fi gaban kwatance abin sai wanda yagani, ita kanta ummi aduk sanda tadubi fatima ji take kamar takwace kyaunta, tabbas ace tanada kyaun fati khalifa bai isa yace ba ya sonta ba, hankalinta bai kara tashi da fati ba sai watarana dataje gdansu fatima ta isketa ba dan kwali ta fito daga wanka tana taje gashin kanta, ummi taga yadda bakin gashin nan ya kwanta lanban a bayan fatima yana daukar ido kamar irin yammatan indiyawan nan, ga kirar jikinta abin sha'awa irin wadda ake cewa coca cola shape, ita kanta ummi datake mace saida taji tanason fatima sbda kyaunta kyaunta yayi mata ga tadai yar talakawa ba wani kayan ado dazai fiddo da itatake samu ba hakanan ta ki tawayar da kanta ,duk da haka fati ta isa abar kallo, kyaunta gdan wani hamshakin maikudi inda za ta jiku da jin dadi lallai za ayi kallon mace anan. Bayan ta gama mata kitson ummi taja hannunta zuwa kan dressing mirror tarike kugu tana kallonta tace "fatima kinga acikin kayan kwalliyarmu mata babu nau'in kalar da babu anan na baki dama ki zabi duk abinda kikeso wanda za ki dinga kayatar da kanki dashi gun ado, don Allah fati ki sani jikinki domin inason kizamo wayayyar mace mai ado za ki zama abar kallo fati, Allah ya yi miki baiwar kyaun sura wadda duk wata diya mace za taso ta mallaki sura irin wannan, dan banga abinda kika rasa ba fatima. Fatima tace "Nagode ummi da kaunar da kike nuna min, sai dai ina son kiyi hakuri ba zan dauki komi ba anan dan idan nadauka narabaki da abinki ba zan yi amfani dasu ba. Ummi tagyada kai tace "fati na fahimci kyamar dukiyar nan gdan kike yi. Fatima tace "haba ummi kada kiyi min muguwar fahimta mana. Ta tareta dasauri tace "me zai hana in fadi haka ba muguwar fahimta bane gskiya nafada miki. Ta girgiza kai tace "kiyi hakuri ba haka bane. Tace "to in dai ba haka bane zan hada miki kayan kwallia dakaina dan Allah kidaure kidinga amfani dasu. Tayi dariya tace " to na ji ummi amma dai zan tunasar dake abu daya wanda kwalliya ana yinsu ne dan afita kinga dai ni babu inda nake zuwa in banda makaranta,kuma ba wasu maza ke zuwa guna ba kinga dai ba su da amfani a gareni. Ummi tace "to in banda abinki fatima shi malam musbahun ba ya da bukatar yaga kwalliyarki, gskiya kanki a duhu yake dayawa kibani hadin kai in wayar miki dashi kada kiyi aure a cikin wannan yanayin dukda kasancewar malam musbahu malami ne amma xa ku iya samun matsala acikin zaman auranku idan kika cigaba da tafiya a wannan tsarin na ki, namiji dakika ganshi ko wani iri ne yana bukatar matarsa tayi masa ado yana bukatar matarsa takasance wayayya mai iya lura da abubuwa na jan hankali, idan akace mazan suke waje kadai za ayiwa ado banda na mazajen aure hakika kwalliya bata biya kudin sabulu ba knan, mace in har ta amsa sunan mace to tattalin rayuwar mijin auranta take domin shi ne na ta, wata kila kina ganin misbahu malami ne kuma dan gdanku ne ba ya bukatar sai kin masa wata kwalliya ta jan ra'ayi, wannan kuskure ne idan ma ra'ayinki ne haka to kisauya domin misbahu namiji ne kamar kowa rayuwar da zakuyi ta aure tanada banbanci mai yawa da wadda kukayi a gida, dole sai kin ajiye wannan kunyar da kke fama da ita domin tuni na fahimci kunya itace tahana ki sakin ranki ki zama wayayyiya mace, idan nace wayewa ba ina nufin kizamo mara kunya ba a'a kizamo mai wayewa ta fuskar rayuwa, matukar baki bin wannan hanyar dana ke son doraki a kanta ba, za kisamu matsala ba za kiji dadin zaman auran ba. Fatima tayi shiru tana tunanin abinda ummi tafada mata, ummi taci gaba da fadin "kiyi nazari sosai za kiganoinda nasa gaba, kinada kyau fatima kyaunki kadai ya isa yamallaka miki da namiji to amma fa masu iya magana kan ce in kanada kyau ka kaara da wanka,, dan Allah kisaki ranki da misbahu kidinga tsala ado sosai kina tsayawa kuna hirar soyayya za kiga yana dada rudewa akanki, a tunanina babu wani abun Burgewa ga mace wanda yawuce mijinta na aure yayi ta sonta ya kasance kullum hankalinsa na kanta, matukar kuwa bata bi hanyoyin dazata rike shin ba ba zata samu yadda takeso ba daganan sai kiga anata samun matsalar rayuwar aure a dalilin a dalilin hakan za kiga aure ba ya danko kiyi taganin kananan zawarawa a gari, wadannan abubuwan da matan mu na hausa ba sa kulawa dasu suna taka muhimmiyar rawa gun lalacewar zamantakewar aure. ****** A DAREN FARKO 13 Har fatima tadawo gida tana tunanin maganganun ummi wadanda suka jefata a wasi wasi amma tana karfafa kanta dacewa gaskiya ne mamakinta shi ne yadda ummi tasan wadannan abubuwan ba tare da ta yi rayuwar auren ba ballantana tasan matsalolinsa da abubuwan da ke haifar da matsalolin, koda yake kallo daya inkayiwa ummi za kasan kanta a waye yake sosai ta fuskar rayuwa haka karance karancen datake na littafin hausa suna taimaka mata sosai nagano abubuwa da dama da suke ckin rayuwar auren. Fatima na zaune a dakin da suke kwana ne a wannanlokaci da bai wuce karfe takwas na dare ba sallar isha'i ta idar tadauko kayan da ummi tahada mata na kwalliya tana dada kallonsu har da kayan sawa materail ne kala biyu da mayafinsu da fashions da agogi ga turarruka har kala uku, kuma taroke ta idan gari yawaye tadawo daga makaranta tazo zata rakata saloon u gyara mata gashin ta, a dazun da wayo da wayo sai da ummi taja hankalin fatima takai la'asar a gdansu tana cusa mata maganganu na jan ra'ayi don dai ta samu ta aminta da maganganunta har sai da taci nasarar da fatin tasaki jikinta take ba ta labarin yadda shi kansa malam musbahu yake nacin son tadinga sakin jikinta suna hirar soyayya tadaina gudunsa, tace wani lokacin har tausayi yake bata idan yafaye mata magiyar tayi mai hirar soyayya ko kaka ne dan yaji sanyi a zuciyarsa, amma ina tsabar kunya yasa ba ta iyawa, ko hada ido ba ta yi dashi, ummi tace "kinji ko ? " Tace "wannan idan baki bar wannan halin ba idan anyi auran yagaji zai dinga kula wasu yammatan ko yadaina baki kulawar dakike bukata kema. Lokacin data dawo gida innarta rike baki tayi tace "Tabdijam kece kika yini yau a gdan hajiyar ? Tace "uhm ummi ce tatsareni da magana kinga kayan ma data ba ni. Inna taduba tayi godiya. Fatima ta san cewa ummi na kaunarta kawai don Allah, don haka tasaki jikinta da ita sosai tana kokarin kwatanta abinda take gaya mata, tadaina dari dari da ummin zama take suyi hira sosai tazamo tazamo kamar irin aminan nan dasuka jima da shakuwa da juna, ita kanta fatin ko dayaushe idan takalli irin alherin da ummi take mata da yadda tadamu da ita tana nuna mata tsantsar kauna sai ta dinga mamakin kaunar da take mata, yakasance ko yaushe ummi na gdansu fatima ko ita tana gdansu suna hira, malam musbahu yana matukar jin dadin kawancen fatima da ummi sbda ta samu cigaba mai yawan gaske a cikin rayuwar fatima, hakan yasa yake mutunta ummi tazamo abokiyar shawararsa kan abin da shafi fatima, duk abinda yataso ita yake fadawa. ,kuma ckin ikon Allah sai ta nusar da fatima hanyar data dace nan da nan abubuwa suka dawo daidai kunyar nan ta fati duktazama tarihi har tana iya caba ado tatsaya suyi hira sosai da malam musbahu. ******** Yadda Anisa tashiryawa khalifa abincin safe hka ta tsara mai na dare wanda yafi na safen dadi yana can yana baccinsa ya iske an shirya tebur sai kamshi mai dadi ke tashi tana zaune kan kujera tana kallon wani fim da ake haskawa ya dubeta yana mur. mushi yace "godiya nake ranki yadade. Tace "na fika farin ciki da yabawarka Abbakar dan haka ni yafi dacewa in yi godiya gareka bisa karbar bakunci na dakayi a gdan ka, idan ka kammala zan koma masauki na abokaina na karatu suna jirana yanzu muka gama waya dasu. Ya rausayar da kai har yanzu da murmushi a fuskarsa yace "bakiyi laifi ba idan kin tafi dole in barki ki tafi domin bansan zan sameki ba na hadu dake amma dai va zan ji dadin tafiyarki yau ba me zai hana ki daure ki tayani kwana. Ta lumshe ido tare da ajiyar zuciya takwantar da kanta tana kare mai kallo lokacin daya zauna yabude abincin yana fadin "A bisa ra'ayinki za ki kwana a hidan nan idan gari yawaye sai muje nima inga na ki masaukin, amma idan kinga da takura sai muje yanzu ba na son inyi abinda xan matsawa mutum. Bai jira abinda za tace ba yafara cin abincinsa, idanunta a lumshe taje tunanin abi ? da kwananta a gidan zai haifar, har yau idan sunyi waya da mominta rokon da take mata shi ne tarike mutuncin kanta kada tayarda wani ya yaudareta ya lalata mata kuka yaja mata abinda za tayi kukan da ba ranar karewa., ance idan mace da namiji suka kebenta a wuri daya su biyu na ukun su shaidan ne, soyayyat da takewa khalifa ita kanta har tsoro yake ba tazuciyar ta ta tsananta da ciwon so mai zafi da tsanani shin akwai abinda zai nema a gareta ta hanashi. Bayan ya kammala cin abincin ya wuce dakinsa ya zuba wasu kananan kaya da suka kama jikinsa kam kam sun mai kyau abin har ba a magana, kamshin turarensa ne yafara baibaye Anisa kafin yabayyana gareta, hawaye suka taru a ido? ta Allah ya taimaketa suka koma ba tare da sun zubo ba amma duk da haka idanuwan ta sunyi jawur zuciyarta ta kuntata tunda take rayuwa da ciwon sonsa dake hana zuciyarta sakat bata taba jin abinda taji yau yana mata yawo a zuciyarta ba, hakan ne yasa tamike dasauri tace "bari in dakko jakata muje in wa sisters di na bayani sai mudawo. Yanayin muryarta yakarantar dashi wasu abubuwan game da ita, ko da yake yana sane dacewa tana son shi duk wasu alamu ta nuna masa ya dai ki nuna mata ya fahimci inda tadosa ne sbda tausayin ta yakeji. Ganin bata fito ba yasa yazauna kan kujera kafarsa daya kan daya yana tuna watarana a b. u. k aboki? sa bukhari ke ce masa "khalifa kafito kanunawa yarinyar nan anisa ce ba ka ra'ayin ta don tadaina wahalar dakanta son da take maka ba kadan bane. Ya ja tsaki yace "wai ku mesa ba kwa rabuwa da gutsiri tsoma, ita anisan ce tace ma tana so na? Buhari yace "kai da Allah kar ka raina min wayo ka fi kowa sanin son da take maka idan kuma za ka iya ba ta soyayyarka to kabata fuskar da za ta bayyanar ma da abinda ke ranta. Yayi murmushi yace "Buhari tausayin anisa nakeji sosai a zuciyata, ban shirya batun aure ba ba ni da ra'ayinsa idan nayi soyayya da ita naravu da ita wahala za tasha gara tayi hakuri dani a yanxu akan ta shaku da soyayya ta a gaba ta rasa ni, shiyasa nake nuna mata kamar bansan abin da takeyi ba. Anisa ce takatse mai tunani lokacin data murda kofar dakin tafito rataye da yar madaidaiciyar jakarta tace "inaga ba sai mun fita ba na yi masu waya sun taho nan din yanzu. Yace "ba laifi. Suka zauna shir7 kowa tunanin dayake kara kaina a zuciyarsa, lokaci zuwa lokaci takan kalleshi tashare kwallan dake taruwa a idonta, ta kagu sisters dinta su zo tahuta anya za ta iya kwana a gda daya da khalifa? Namijin data kwallafa rai akansa take masa son da batayi tsammanin anawa wani d'a namiji ba, suka kirata a waya sukace ga su a kofar gdan tamike dasauri taje tashigo dasu. Fadilat da Ramat su ne abokan anisa wanda take ji dasu komi na su tare suke aiwatarwa gida daya suke zaune wanda yake kusa da makarantarsu, amincewar da iyayanta suke nuna mata yake tsoratata yasa take matukar kiyaye rayuwarta, Fadilat da ramat suna rayuwar dasuke so da samari? su yayin da ita ba ta da sakewa da mazan. Ita kanta anisan bata ji dadin irin tarbar da khalifan ya yi wa su Ramat ba, ta dai daure tagabatar dasu a gareshi sannam taya musu cewa za ta taya shi kwana ne, basu jima sosai ba sukace xa sukoma tabiyo su don yi musu rakiya, suna fitowa fadila datake ta fi ramat zafin kai ta hau ta da fada tace "dama haka Abbakar din yake kika gayyato mu gdansa? kina sane da cewa a rayuwata babu ab8nda natsana kamar walakanci, meye dalilin na nuna mana isgilanci haka? Tace "kuyi hakuri nima banji dadin abinda yyi mukun ba haka halinsa yake bai da son magana. Ramat tace "halinsa yake bai da som magana kuma to haka kike tsammanin za ki iya mallakarsa, gskia anisa jikina ya yi sanyi da yanayin khalifa dole ki sassautawa zuciyarki burin da kika ci akansa. Jikin anisa yayi sanyi tace "ina bukatar ku tayani da addu"a xuciyata ba wanda za taso bayan shi, fadila tayi tsaki tace "aikin banza wai dole sai kin rayu da khalifa? Suka tafi suka barta tsaye, ta jima a gun daga bisani takoma ckin gdan, a nan falom data bars&i ta tadda shi yana magana da iyayensa a waya har sai da barci ya dauketa, bayan ya gama da iyayansa yai

Chapter 6 of 19